Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
nan. Jamila ta qarasa tana shafa qofar ta juyo ta kalli Binta da taje tunga tace "Kinga basa nan, ko ina suka tafi se Allah amma babu komai gobe ma ranace se mu dawo" tana rufe baki sega Qanin Bara'atu ya shawo kwana ta washe baki tace "To qila ma gasu nan kinga qaninta". Ya qara gurin ya gaishesu a mutunce Jamila tace "Ina mutanen gidan mun tarar qofa a rufe? Ka ganta can ka ganeta ko Matar Alhaji Audu ce tazo muku Allah sanya Alheri". "Ai kuwa kunyi sabani dan basu koyi Minti Ashirin da fita ba sun tafi Rano" ya bata amsa. Ta dafe qirji tace "Rano? Kai sun luluqa da nisa, to kuma yaushe zasu dawo?" "Gaskiya ban sani ba" ya bata amsa cikin qaguwa da maganarta ya fara tafiya ta tareshi tana cewa "Aida ka bude mana to taga gidan tunda kaga ita ba mazauniyar nan bace balle ace ta sake dawowa idan sun dawo, qaraso Hajiya ya bude mana mu Shiga" ta fada tana kallon sashen da Binta ke tsaye sedai wayan bataga kowa a gurin ba. Ta hau waige waige qanin Bara'atu me suna Isah yace "Indai wannan Hajiar ce ai ta dade da tafiya tun sanda nace miki basa nan" daga haka shima ya wuce ya barta tsaye tana cizon yatsa. Bawai da zuciya daya ta sanarwa da Binta wannan maganar ba so tayi ta hada bala'i ta kuma so ace sun tarar da su Bara'atun dan ta tabbatar da Binta bazatayi haquri ba se tayi musu tijara da rashin mutunchi iyakar qarfinta. Cike take da qyashi da hassadar ya za'ayi ace dukda Bara'atu bata tare da Audu kuma taci gaba da kere masu ta kowanne fanni na rayuwa? Shekaru Aru Aru suna zaune gidan qasa lokaci daya Audu yazo ya tadawa Bara'atu da Iyayenta ginin Jan bulo ya danqara musu gida kamar na wani sarki Alhalin su suna fama da jar laka? Shiyasa ta kwazawa Binta maganar tunda ta lura bata sani ba yanzun ko tasan inta koma Birni wacce za'ayi se Allah ita dai fatanta Audun ya kwace gidan kawai tunda dai yana tsoron Binta. Farar safiya Binta ta kammale kayanta tsaf tasa a nemo mata shatar mota zata tafi gida. Goggo Fadi ta ringa tambayarta abinda ya faru data tashi tafiya gagaga haka Alhalin sati guda tace zatayi bata da abin fada mata a matsayin dalilin tafiyarta dan haka kawai ta laqawa Danta ciwo tace shine bashida lafiya gara su tafi ta kaishi Asibiti. A wata mota da Jaki ya fita dadin hawa da saurin tafiya ta kamo hanyar Kano, ita ma din da dakyar aka samo mata ita dan masu motocin daukar kaya tuni kowa ya fita ai kuwa taji jiki kafin taje gida, baya da qafafunta sun fada dan jinjirinta kansa ya gane kurensa a wannan tafiya seda sukayi jinyar gaske ita dashi ga qarin baqin ciki ta tarar Audu baya gari seda taje gidan Turai a kwana na uku bayan taji dama dama sannan ta gaya mata ai sun tafi Legas tareda Ali zasu dakko kayansu. "Karki tareshi da hayaniya kibishi ta siyasa idan kika gano bakin zaren sannan musan abinyi" Turai ta fada mata bayan data shaida mata zancen gidan da Audu ya ginawa su Bara'atu. Haka kuwa akayi, tayi matuqar qoqarin boye tashin hankalinta da damuwa akan Al'amarin harya dawo daga tafiya seda ya kwana biyu ya ware gajiya kafin ta tada masa da zancen ai taga gida akace shiya ginawa su Bara'atu. "Badan Bara'atu na gina musu gida ba nayine saboda Yarana, ya za'ayi ace da raina ban mutu ba a watsarwa da Yayana da uwarsu kayansu a waje bayan ina da halin da zan iya siye garin gaba daya ma ba iyakar gidan da suke ciki ba (kuji fariya). Shiyasa na yanke shawarar yi musu gini na Alfarma irin wanda babu shi a kaf garin da makwafta" ya bata amsa. Binta tayi murmushi a qoqarinta na boye tashin hankalinta tace "Gaskiya hakane amma dai basu kyauta ba suma se kace ba yan uwa ba? Kuma naji ma kamar nace fin qarfi kawai suka gwada musu amma tun Baban nasu yana da rai ya fitar da kowa ya bashi kason kudinsa?" "Oho musu wannan su ta shafa tunda na rigada nayi abinda nayi, gidan ma kuma zan siyeshi na mayarwa dasu Bara'atun se naga ta tsiyarsu ko?" Ya bata amsa, ta zabura se kuma tayi saurin daidaita zama tace "Aiko dai, ka barwa su Bara'atu ko ka barwa su Babangida?" "Ita dasu ai duk dayane kuma duk abinda zanyi mata Alfarmarsu take ci ko iya ruqonsu da takeyi ai tayi qoqari Alhalin ubansu nada rai kuma ina da yanda zanyi" "Uhm hakane, ni da zakayi haquri ma ka yafe abinda ya wuce daka maido su munci gaba da zamanmu kawai hankali kwance. Duk se naji rashin dadi saboda mutane zasuyi ta kallona a matsayin wadda tayi silar raba Yaya da Mahaifinsu" Bintan ta zartar da hukuncin da take ganin shi kadai ne ze datse alaqar Audu da Bara'atu, tunda dai yace saboda yara yake mata komai to gara a kwaso mata yaran suzo suyi ta dabdala a tsakar gida da dai uwarsu tacigaba da morar Audun. Wani kallo ya watsa mata me ma'anoni da yawa fuskarsa ta nuna mamaki qarara yace "Dagaske kike ko wasa? Kina nufin kin yafe mata abinda tayi miki su dawo muci gaba da zama tare?" Seta rausayar da kai ita ala dole gata Allah tace "Abinda ya faru ai ya rigada ya faru na dauki qaddara tunda Allah ya qadarta Yaron bame doguwar rayuwa ko bata silarta ba ze mutu, kuma yara ai basu suka mun laifi ba itan ma kuma na yafe mata Albarkacinsu" "Amma naji dadin wannan magana matuqa in sha Allahu nan bada dadewa ba kuma zan shirya dawowarsu, harkin wankemun baqin cikin abinda ya faru kuma kin qara daraja a zuciyata saboda ba kowa za'ayiwa babban laifi irin wannan ba ya yafe harya cigaba da zama da mutum" Audu ya fada cikin madaukakin farincikin da shi kansa besan dalilinsa ba. Ta maka masa harara a fakaice kafin tace "A kullum burina kenan na faranta maka rai, inda na san wannan ze saka naga farin cikinka haka da tuntuni an aiwatar dashi amma yanzun ma lokaci be qure ba". Daga haka suka tashi daga maganar da kowannensu da kalar manufarsa akan abinda yake fadi. Binta tana maganane akan Babangida da Babannan, su take nufin Audu ya dakko su dawo gidan saboda kar Bara'atu taci gaba da cin arziqinsa ta dalilinsu yayinda shi kuma tasa kwakwalwar ta fassara masa Maganar ta a matsayin ya maido da Bara'atu taci gaba da zama da Yayanta a gidan wannan ne ya sanyashi farin cikin da beyi tsammani ba. Allah ya sani bazeyi qarya ba ba kuma ze iya boye tarin qaunar da yakeyiwa Bara'atun ba saboda ita ya fara so har kawo yau kuma be dena sonta ba Halayen dara tsiro dasu daga baya ne sukayi tasiro gurin ruguza zamansu wanda yake fatan a yanzu ta hankalta ta gane kuskurenta. Abu na biyu daya qara masa jin dadi shine ya san maida Auransa da Bara'atu ze gyara alaqarsu da Yan uwansa data gurgunce musamman Yakubu da Bilki, wannan farin cikin kadai ya hanashi bacci ranar, washe gari kuwa yayiwa Bechi tsinke sedai ya tarar da su Bara'atun har sannan basu komo ba. Izza da girkan kan dai yana nan, ya saka a ransa Mace tayi kadan daya je bikonta, Hayatu Abokinsa ya barwa sallahu akan idan Sun Dawo yaje ya tuntubeta yaji ra'ayinta akan komawa gidansa. "Kai yanzu Audu kana nufin kafi qarfin ka tare ta baki da baki kuyi maganar nan?" Hayatun ya tambayeshi cikin mamaki. "Ga Amsar nan ka bawa kanka ai, ko yanzun saboda Yayana zan mayar da ita bawai dan ta cancanci na maida itan ba" ya bashi amsar da har ransa yasan qarya ya fada. "Ai shi kenan, girman kai dai rawanin tsiya, kuma shi ya halakar da mafiya yawan Magabata" Hayatu ya bashi amsa. Page 25 Wasa ya wasa, qaramar Magana ta zama gaske, kamar yanda Audu ya barwa Hayatu sallahu ya isar da saqo dan Bara'atu na dawowa gida ya doma sallama kofar gidansu, ta fita suka gaisa, batayi mamakin ganinsa ba saboda Abokanan Audunna Bechi sukan leqa sa'i da lokaci suga Yaranta. Sukance Audu ya musu rana dan haka bazasu yada yaranshi da suke kusa dasu ba dan idan ka ture halin Audu na Rashin son gaskiya da shegen girman kai yana da kirki, kuma abun hannunsa be rufe masa ido ba daidai gwargwado yana kyautatawa Yan uwa da Abokanansa. Bayan sun gaisa da Hayatun ta tambayeshi jikin matarsa datayi samu da jijjiga lokacin haihu da yake abun a gida ya faru se daga baya aka kaita asibiti abin se yaso ya taba mata kwakwalwa dakyar dai da taimakon Allah aka samu kanta dukda har yanzun dai bata koma yanda take a canbaya ba. Seda suka gama gaishe gaishe kafin ya amayar mata da ainihin abinda ya kawoshi, tayi shiru tana sauraronsa harya gama kafin tace "Shi Audun da kansa ya gaya maka ko kuma aike yayi maka?" "Dakansa yazo lokacin baku gari shineya barmun sallahu akan nazo na tayashi biko da banbaki kafin ya dawo". "Ya yardada gaskiyar ban kashe masa Da ba kenan yanzu?" Ta tambayeshi cikinkar yayyar murya, tausayinta ya kama Hayatun, Bara'atu mace ce me nutsuwa da matuqar haquri, sun taya Abokinsu baqin cikin rasata kuma a cikinsu da akwai wadanda sukayi niyyar neman Auranta se dai sanin waye Audu da tabbacin da suke dashi na cewar be dena sonta ba yasa suka gaza aiwatarda nufinsu saboda Tijarar Audu abar gudu ce tun zamanin yarintama balle a yanzu da karansa ua kai tsaiko. "Bamuyi wannan maganar dashi ba, amma na tabbata a zuwansa baya raba nasaba da warwarewar komai, ta yiwu ya samu gamsuwar cewar baki aikata abinda aka zargeki dashi ba shiyasa ya dawo ku daidaita. Nidai abinda zan iya ce miki kiyi haquri ki mayar da komai ba komai ba ki koma dakinki kodan saboda rayuwar Yaranki. Kowa ya sani Audu be kyauta ba kuma shikeda laifi cikin duk al'amuran da suka faru amma kin sanshi, qi fadinsa baze barshi ya nuna gazawarsa ba sedai na tabbata ko be furta da baki ba zakiga Nadamarsa a aikace dan haka karkiyi wasa sa damar da ubangiji ya baki, kiyi tunani ki yankewa kanki hukunci". Ta koma gida tana ta juya maganganun Hayatu, Inna Hajara bata ce mata komai ba dukda chanjin yanayin da ta ganta ciki se tayi tunanin kodai Hayatun yazo mata da Maganar Aure ne saboda irin zaryar da yakeyi tuntuni tasa tayi tunanin hakan. Har aka kwana biyu da zuwan Hayatu Bara'atu bata sake ba, walwalarta ragu ainun, wani irin cakudadden yanayi take ji na farin ciki, damuwa da kuma zullumi. Farin cikinta Bikonta da Audu yayi domin ba zatayi qarya ba Allah ya sani tana qunar Audu ba kuma ta tsammanin zata iya zama da wani Namiji a duniya ta soshi bayan Audun wannan dalili yana daga abinda yasa zamanta a gida babu marshinshini be wani dameta can ainun ba, Damuwarta kuma tunanin idan ta yarda ta koma wace kalar rayuwa zatayi a gidansa Alhalin Binta tana nan? Zullumin da take ciki kuma shine na tunanin shin Audu ya gane cewar Binta sharri tayi mata ne da har ya nemi ta koma ko yaya? Zata so ta san amsar tambayar nan domin itace zata qara mata qwarin guiwar Amincewa buqatarsa ko akasin haka. Zata so su hadu dashi suyi maganar nan kafin ta kaiga yanke hukunci, "Nikam lafiyarki Bara'atu? Yaro na tsaye kanki yana magana tun dazu kamar me bacci kin masa shiru alhalin idanuwanki a bude suke?" Inna Hajara data leqo daki dalilin maganar Babannan da take jiyowa yana ta maimaita abu daya, Gidan kitso Bara'atun tace yaje ya tambayo mata tunda ya shiga dakin yake fada mata matar tace taje yanzu bataji ba balle ta bashi amsa tayi zurfi cikin tunani har seda Inna Hajar tayi magana da qarfi kafin ta ankare. "Banji shi bane Inna, me kake cewa kai kuma?" Ta fada tana gyara zamanta. Inna Hajara ta shiga cikin dakin da kyau tace "Ai daman ba zakiji shi ba, kai yi tafiyarka wasa, ki fadamun me yake damunki tun randa Hayatu yazo gidan nan na ke lura dake yanayinki ya canza". Barin maganar a ranta baze magance mata komai ba kuma a wannan gabar tabbas tana buqatar Abokin shawara wannan abun yasa ta fuskanci Inna Hajarar ta shiga fada mata yanda sukayi da Hayatun ranar da yazo. Baki ta saki galala tana kallon Inna Hajara wadda ta taqarqare ta rangada guda kafin ta daga hannu sama tana cewa "Allah na gode maka daka sa zanga wannan ranar da raina ban mutu ba, Allah na gode maka daka karbamun Addu'ata. Dama bangaya miki ba? Ba a banza Audu ya jibanci lamuranmu fiye da da ba, tun baroqarki gidansa ban taba yin salla na tashi ba tareda na roqi ubangiji daya bankada sirrin duk wani Azzalimi daya qulla miki wannan mugun shairin ba gashi kuma Allah maji roqon bawansa ya amsa roqon mu. To meye abin damuwar daya kika kasa walwala? Wannan ba abin kiyi rawa kiyi shewa ki godewa Allah ne amma shine kika tsangwami kanki kwana kusan uku bana tsammatar kinyi dariya? Ko kuwa bayan Batun komen akwai wata maganar ne?". "Babu wani abu bayan wannan amma ni abinda ya dameni Inna banida tabbacin cewar Audu ya zabi ya maidani saboda gane gaskiyar abinda ya faru a baya ni nafi kyautata zaton zeyi hakan ne saboda Yayansa. Sannan Inna karki manta har yanzu fa Binta tana cikin gidansa, kina dai ji har ta kori Amaryar da yayi kin kuma ji rade radin da akeyi a gari kan itan ma wata qullalliyar ta qulla mata kenan bata canza zani ba tana nan da halinta babu abinda ya sauya" Bara'atun ta fada a sanyaye cikin karayar zuciya. Inna Hajara ta galla mata harara tace "Ai bari kiji, wlh wannan karon kika kuskura kika tsaya tsoron kishiya yayi tasiri a ranki se kinci ubanki. Ai maciji baya saran mumini a guri daya sau biyu, kin zauna da ita kinsan duk wani salon tuggu da munafuncinta dan haka kema seki shirya irin naki da zaki goga da bata hanyar cuta ko Ha'inci ba. Sannan da kike cewa saboda yayansa ne koma saboda menene dai abu daya ake fata kuma ya tabbata idan baki koma gidansa ba zaki cigaba da zama hakane babu Aure tunda dai kina kallo cikin Garin nan da kewaye labarinki babu inda be ratsa ba wanene ze Aureki? Gidan san dai da kika gogo baqin fentin acan zaki koma ki wankeshi karma ki kuskura naji kin tado da wannan maganar balle har dalilin haka yasa ya janye muradinsa idan ma besan gaskiyar ba. Ko iya komawar da zakiyi ta isa ta karya Alqadarinta saboda ta dauki haqqinki ne saboda tayi silar ki fita daga gidan yanzu kuma Allah ya nufa zaki koma dan haka ma shiri zamu fara, yace da zarar kin amince yana zuwa za'a maida Auranko? To ki aika a kira Hayatun yau ki sanar masa kin Amince, in sha Allahu bazaki rufa qarshen watan nan cikin gidan nan ba zaki koma dakin Mijinki yan hassada da baqin ciki da masuyi mana dariya sedai su mutu Allah yayi abinda basu isa su hana ba". Duk yanda taso fahimtar da Inna Hajara buqatar taja lokaci Audu yazo da kansa su tattauna kafin qulluwar kowacce magana qi tayi, daga qarshe ma takans taje ta samu Qanin Babansu ta sanar masa da cewar Mijin Bara'atu yazo biko bata ko tunanin maganar ta rushe tunda dama ba wani ginuwa tayi ba. Malam Sadi wanda yake cike da wulaqancin da Audu ya musu ya ginawa su Bara'atun sabon gida sannan ya siye gidan da sukaso tozartasu akanshi sedai kuma tsoron Tijarar Audun daya tuna furucinsa na cewar duk seya siye gidajen da suke ciki in suka bata masa rai sanda suka goranta masa cewar meye hadinsa da Bara'atun da har ze siya musu gida? banda Rashin zuciya matar data kashe masa Da ze dawo yana bibiya take ya kora musu gargadi sun kuma san ze aikata domin cefane Bechi yake tayi yana siyan gidaje da filaye tamkar wasu yan tsaki tuna wannan tasa yace babu komai duk sanda suka shirya suzo. Dataga Bara'atu ba zata nemo Hayatu ba dakanta ta tura aka kira mata shi suka qulla magana ba'aja lokaci ba yayi takakkiya yaje ya sanar da Audu abinda ake ciki. "Ashe har yanzu Bara'atu tana sona tana kuma muradin zama dani?" Audun ya fada kamar wani soko sanda Hayatu ya gaya masa yanda ake ciki. Hayatu ya karkace yace "Bana tsammanin haka, domin munyi magana da ita kuma ban fahimci wata alama taso ko muradi a tattare da ita ba se Damuwar data nuna mun ta son sanin ka yarda da ita ko kuwa har yanzu kana mata kallon Mara Imani Azzaluma?" "Bana son maido da wannan maganar tunda har wadda ta zalunta ta yafe mata magana ta qare a gurina" ya bawa Hayatu amsa yana wani dauke kai kamar bashi ya gama shauqi yanzun nan ba, Hayatun ya sake cewa "Kenan har yanzu kana kan bakanka? Dagaske Zuciyarka ta aminta da cewar Bara'atu ta aikata abinda Binta ta zargeka dashi?" Hayatu ya tambayeshi yana tsareshi da ido, seya miqe tsaye yace "Ya za'ayi kazo ka tsitsiyeni kamar wani yaronka kana tambayata? Wannan fa abu ne daya shafeni nida Iyalaina kuma ni nake zaune dasu duk wani wanda ze bayar da shaidar Halin Bara'atu bafa ze kai kamar ni da nayi zaman shekaru sama da biyar da ita ba, ku sanin zahiri kukayi mata ni kuwa na santa har badini dan haka ba ku zaku ringa gayamun abinda zatayi da wanda zatayi ba. Saqo na baka ka isarmun na gode kwarai kuma zan sallameka yanzu In Allah ya yarda cikin zatin da ze kama nima zan shigo garin" ya qarasa yana laluba Aljihunsa ya zaro Rafar Yan goma na Takadda sababbi qal ya irgi dari biyar ya miqawa Hayatun. Girgiza kai yayi cikin tsananin takaicin Audu ya miqe shima yace "Banzo gurinka dan ka bani kudi ba kuma banyi maka abinda nayi shima saboda ka biyani ba nayi ne saboda Allah saboda kuma na daidaita rayuwarka tunda na fuskanci kai baka da alqibla ba kuma kasan ina kakw dosa ba. Abu daya da zance maka shine in har Allah yasa auranka da Bara'atu ya maidu kayi qoqari ka riqeta da kyau dan wlh muddin ka sake yarda Tuggu da makirci yacika ka rabu da ita se kayi nadamar hakan" yana gama fada masa ya fice daga Ofishinsa ya barshi nantsaye da kudi a hannu dan daman a sabon Kamfanin daya bude ya sameshi. *MAMAN MARYAM ONLINE BUSSINESS* *Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments* *Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*❓ *Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT* *Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya* *Muna da magunguna iri iri* *NA GYARAN JIKI* *NA GOGE NANKARWA* *NA RAGE QIBA* *NA CIRE TUMBI* *NA QARIN HIPS* *NA GIRMAN BREAST* *NA QARA TSAHON GASHI* *NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA* *Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa* *Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*, *Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba* *Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku* *INA MASU HAWAN JINI?* *INA MASU CIWON ZUCIYA?* *INA MASU CIWON QODA?* *INA MASU CIWON HANTA?* *INA MASU SICKLER?* *INA MASU HIV?* *INA MASU CANCER?* *INA MASU NEMAN HAIHUWA?* *Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku* *Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce* *Munanan a KANO KUNTAU* *Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa* *Kutuntube mu ta wannan number 📞08129249549* *📲07011401314* Karo na farko da jikinsa yayi sanyi akan bacin ran daya gani qarara kan fuskar Abokinsa koma yace Amininsa. Ya mayar da kudin Aljihu yabi bayan Hayatun da har ya fita farfajiyar gurin ya kwala maaa kira. Dalilin ma'aikata dake kai kawo a gurin ya tsaya, da yawansu duk Yan uwane da qannen Abokanan nasa ya kwaso daga Bechi ya basu aiki se kuma manyan ma'aikata wanda masu kwalayen makaranta ne ya dauka aikin su suke riqe da manyan muqamai a gurin. "Mu koma ciki muyi magana" ya fada sanda ya cimmasa. "Tsayuwar da kaga nayi anan ma Albarkacin wadan nan yaran kaci bazanso su gane cewar kowa kana da Baraka dashi ba" Hayatu ya bashi amsa. Audu ya bata fuska yace "Wai wane irin abu ne wannan? Ni wai a wane kalar mutum kuka daukeni da duk abinda nayi kuskurene kowa ganin baikena yakeyi?" "Ni kuma tsanina da kai ai magana ta qare Alhaji Audu, kayi haquri ma da katsalandan din da na maka bakina da bashida linzami ne ya kasa yin shiru, bari naje kaga Rana da daga zan iya rasa motar komawa gida" Hayatu ya fada daga nan yasa kai ya tafi ya bar Audu a tsaye a gurin. Jiki babu kwari ya koma Ofis ya zauna ya shiga Auna zamansa da Bara'atu da halayenta tareda na Bintan kamar yanda Hayatun ya shawarceshi. Magana ta gaskiya ba tun yanzu ba yayi tunanin abubuwa da yawa da suka faru lokacin zaman Bintan da Bara'atu wanda ya fahimce su dalilin Auran Zubaida. Ya gasgata cewar A bayan idonsa Binta tana cusgunawa Bara'atu tayi amfani da yarintarta da wautarsa tayi wasa da hankalinsa abinda yasa ya fahimci hakan kuwa yanda ta kasa danne Kishinta akan Zubaida kuma har a gabansa bayyanawa takeyi shi kansa dalilin Auran Zubaidan ya fahimci halayenta da yawa da bata bayyana masa su ba a baya se yanzun kuma yaji rashin jin dadin yiwa Bara'atu uzuri a wancan lokacin har ya tsaya ya fahimci gaskiyar abinda yake faruwa ko ya bincika amma maganar mutuwar Zakariyya itace abinda ya gagara tsayar da matsaya akanta. Magana ta Allah shida kansa ya zargi kansa daga baya da yanke danyan hukunci. Ya tuhumi kansa akan kasa bawa Bara'atun kariya koya shaideta saboda ai rainonsa ce, shine mutum na farko daya kamata ya gasgata duk abinda akace tayi ya san kuma tabbas bata da muguwar zuciyar da zata aikata kisan kai amma yanda Al'amura suka kasance a lokacin da yanayin zamansu hade da tasirin maganganun Binta ne suka juyar masa da hankali be kuma tashin gano hakan ba se bayan faruwar al'amarin daya wakana tsakaninsa da Zubaida inda qiri qiri Bintan tayi amfani da Duhun kansa ta ingizashi ruwa wannan ce tasa harya fara tunanin anya kuwa Lamarin Bara'atu ma babu lauje cikin Nadi kuwa? To amma kuma seya tuna Idan sharri Binta tayi mata Ya Za'ayi yan uwanta harda Yaya Sakina su goya mata baya? Gaskiya baya tsammatar ace gaba dayansu sun hada baki akan al'amari irin wannan tilas da akwai qamshin gaskiya a cikin maganar koda ba duka ba. Wannan abin ne har yasa yayarda ze maido da Bara'atun a ganinsa hakan ze wanke laifinsa a gurinta sannan ya daidaita tsakaninsa da yan uwansa qarfin guiwar sa kuma daya samu hadin kan Binta. Kai shi kansa ma ya sake qullewa kuma, Binta ta nuna tana son Bara'atu batayi kishi da ita ba ya auro Zubaida ta kusa haukace masa balahira babu kalar wadda be gani ba sannan yanzu kuma da kanta ta sake cewa ya maido da Bara'atu wai menene hakan ma tukunna? Shine a birkice ko kuwa Binta ce bata da alqibla???? To duk yanda ake ciki madai ya himmatu ze maido Bara'atu, kuma kamar yanda aka saba inya nausa baya jin kira dan haka baya tsammatar akwai abinda zesa ya canza wannan qudurin. Cikin satin ya shirya yaje Bechin, ya tara yan uwansa ya sanar dasu qudirinsa Yakubu

Chapter 24 of 32