Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
cikin sanyin jiki. Babanta na cikin daki yana jiyosu yayi gyaran murya yana cewa "Wannan wace irin maganace Zubaida, kana jina ko Yaro kaje in Allah ya yarda bata da wani Miji idan ba kai ba. Banda rashin wayo ki samu miji kamarsa har ki tsaya kinibibi ai yafiki sanin abinda ya dace dashi din kuma yace ke yake so" "Shikenan Baba nagode, in sha Allahu kuma zan turo da magabata na e a tsaida magana". Watanni uku bayan dawowar Zubaida gida, a hankali tun tana sharewa harta yarda ta sakarwa Audu fuska soyayya me sanyi ta qullu tsakaninsu, dukda tana matuqar jin kunyarsa kasancewar yasan komai na rayuwarta ta baya, ta kanga kamar wata rana ze goranta mata bama shi ba babban damuwarta yan uwansa take zaton ya zasu dauketa idan har sukaji ita din wacece a baya gashi yace mata yana da mata ire iren wadannan tunanin yake sare mata guiwa taji kamar ma Auranta da Audun baze yuwu ba. Watanninsu hudu tare Malam Hassan yace ya turo magabatansa saboda yana so ya hada da Auran Surayya ayi gaba daya, su uku suka rage cikin yaya shiga da mahaifiyarsu ta haifa ukun sun rasu suma bayan rasuwar Mahaifiyar tasu se Surayya da Ibrahim Wanda yake bin Zubaida ne suka rage masa be kuma sake Aure ba tun rasuwar Habiba shekara bakwai kenan. Babu damuwar komai Kai tsaye Audu ya tafi Bechi ya samu Yaya Baba ya gaya masa cewar zasuje nema masa Aure nan da sati daya, mamaki ya kama Yaya Baba saboda Yakubu yaje Bechi ba'afi sati daya da tafiyarsa ba kuma beyi musu zancen Auran Audu ba dukda yaga alamar kamar Audun ma be san yaje din ba, tun rabuwar Auransa da Bara'atu abubuwa sukayi zafi tsakaninsa da Yakubu. Yakubun Yayi fushi me tsanani shi kuma Izza da ganin yanzu ya isa ya hanashi ya neme shi su sulhunta. Yaya Baba bashida ta cewa dan haka ya amsa masa da Toh, ya kuma sanarwa da sauran yan uwansu abinda ake ciki take Hashimu yace ba zashi ba. Aminu ya samu Audu ya tambayeshi Yakubu yasan da magabar kuwa yace masa Aa. "Wannan abinda kukeyi sam be kamata ba, kaine qarami dan haka ka nemeshi ku sasanta. Me yasa kakeyin tufka kana warwara? Kayi nasarar hade kanmu sannan kuma ka koma ka bata da Yayanka da kuke ciki daya akan Mace wannan wane irin abu ne?" "To ni Aminu menene laifina a ciki, Shi ya fiya damuwa ne kawai idan ba haka ba menene nayin fushi akan na rabu da Bara'atu nifa nake zaune da ita ni nasan matsalarta amma shi ne da fushi dan na saketa?" "Saboda yafika hango abinda yake daidai ne shi yasa kai kanka kuma da zakayi duba na tsanaki zaka gane abinda ake qoqarin fahimtar da kai. Da ace zaka ji shawara da ka haqura da sabon Auran nan ka maida Bara'atu dakinta" Aminu ya sake fada. Audu yayi shiru kafin ya kalle shi yace "To kai ka aureta mana ko kuma shi din ya aureta tunda kun fini sanin darajarta". Page 17 Badan Audu yaso ba sedan Yaya Baba dayace muddin ba sanarwa da Yakubu ba bazasuje masa neman Aure ba tilas ya kirashi ta wayar Landilayin wadda ya hada a gidansa shima kuma Yakubun suna da ita a Ofishin da yake aiki dan haka ya kirashi. "Allah ya sanya Alkhairi yasa ayi a sa'a" abinda Yakubun ya fada masa kenan bayan daya shaida masa zancen Auran se kuma yaji babu dadi dan haka yace masa "Amma zaka zo ko? Saboda ina tunanin a daura Auran kawai idan an kai kudin" "Ina da Ayyuka da yawa a gabana bana jin zan samu halarta sedai daga baya nazo naga Amarya amma a ina ka samo matar?" Yakubu ya tambayeshi, Audu yayi shiru kamar mara gaskiya kafin yace "Amm yar nan cikin gari ce unguwar Alkantara, yarinyar nada hankali da nutsuwa sosai se ka ganta ma" "Amma da zan baka shawara ka dauka da nace kayi haquri ka maido da Bara'atu kodan darajar yayanta ka dubi rayuwar da zasuyi a Bechi babu wadataccen Ilimin Islamiyy ada Boko" "To ya kake so nayi da wannan din bayan na sanarwa da Iyayenta zan turo so kake na zama qaramin mutum?" Audu ya fada a dake dan ya gaji da maganar ya maido Bara'atu da suka dameshi da ita, Yakubu yayi murmushi yace "Bance ka fasa ba kana iya hadasu su ukun ai Alhamdulillahi Allah ya hore maka abinda zaka iya riqe su nidai yaranka nake dubawa saboda zuwan nan da nayi na gansu banji dadin yanda suka koma ba gashi sun fara tasawa" "Naga muma a Bechin nan aka haifemu muka girma, yanzu kai bada shekarunka ba harda Aure ka kammala sakandire ka tafi Jami'a? Suma idan sun girma sun kai munzalin da zasu iya wahaltawa kansu se su dawo nan gidan su zauna yanzu dai ba wannan maganar mukeyi ba ka daure dan Allah kazo kasan dai nan duniya bani da kamarka" Audu ya fada. Yakubu yayi dariyar takaici yace "Zanyi maka Addu'a daga nan kuma da ace abinda ka fada da gaske be baka da kamata da baka qi karbar shawarata ba muddin ba cutar da kai nayi niyya ba, yanzu ina aiki ne zamu sake magana idan na samu lokaci" daga haka ya ajiye waya ya bar Audu sororo da waya a hannu seda ya kashe ma sannan ya tuna dayar maganar da yake so ya masa ta jin dalilin daya saka ya dauki Baballiya ya tafi da shi Lagos zeyi hutu ba tareda su. Sanar masa ba seda sukayi magana da Alhaji Zakariyya yake gaya masa dan a gidan Baballiyan yake zama idan sun samu hutu yanzu haka yana ma yana shekararsa ta qarshe shirye shiryen fita sukeyi. Duk yanda Audu yayi da Yakubu akan yazo Auransa qi yayi dole ya haqura badan yaso ba kuma har ransa yaji rashin jin dadin hakan saboda bashi da tamkar Yakubu sannan ya rasa abinda yasa Yakubu ya dauki wannan fushin dashi. Yanzu kenan yana so ya nuna Bara'atu ta fishi a gurinsa kenan? Haka nan ya tura su Yaya Baba da wasu Abokanansa sukaje masa neman Auran wanda ba'a tashi daga gurin ba seda aka daura shi. Yana gida ranar be fita ba yana tsammatar dawowarsu Binta natayi masa gwalgwaso ta aje wannan ta kawar da wancan surutu kuwa har kunnensa ya gaji ga babu halin yace tayi shiru ko ta fita ta barshi ya huta. Lantana ce ta kwankwasa musu qofar saman, rawar kan matar ya zarce misali seda Binta ta taka mata burki sannan ta dena zirgillin shigar mata turakar Miji. Bintan ce ta bude qofar ta leqa fuska a hade tana cewa "Meye? Wai sau nawa zanja kunnenki akan tako benen nan ballantana kiyi tunanin shiga dakin nan? Ke wace irin daqiqiyar mace ce ne Lantana?" "Kiyi haquri Hajia, baqi kukayi shine nace bari nazo na sanar miki" Lantana ta fada cikin qasqantar da kai amma a ranta zagin Binta takeyi. Binta ta yatsina fuska tace "Baqi kuma daga ina? Ni yau babu wanda babu wanda nayi da ita zatazo" "Ai Hajiya Maza ne ba mata ba kuma kamar yan Uwan Alhaji ne dan naga wasu suna yanayi dashi" Tsaki me qarfi Binta taja, ta tsani wannan zaryar maukar da yan uwan Audu suke musu. Ba'a rufa sati se wani yazo daga Bechi badan ta taka burki bama har kwana suke so su ringayi amma duk zatayi maganinsu dan ba zata dauki wannan abun ba suzo su dabaibayeshi su cinye musu dukiya to bada ita ba. Ciki ta juya ba tareda tacewa Lantana komai ba, Audu na kwance kan kujera tace "Kayi baqi" Da gaggawa ya miqe kamar wani mara gaskiya, be ko tambayeta su waye ba ya shige daki ya zuro rigar wandon jikinsa ya sauka qasan seta bishi da sauri dan se anyi komai a gabanta. Haka take duk sanda yan uwansa suka zo seta kasa ta tsare komai zasu fada ko ya basu seta gani idan akayi dace kuwa saqo ya biyo ta hannunta daman se abinda mutum ya gani. Qannensa Mata dai da suke ciki daya tun fitar Bara'atu babu wadda ta sake taka qafarta gidan se yan dakin Goggo Maryo ne suke zaryar zuwa ko gajiya basayi da wulaqancin Binta dan Mazan sun fisu kamewa da wadatar zuci muddin sukaje to dole ce ta saka ko kuma maganar Gonarsa wadda Aminu da Yaya Baba ne suke kula masa dasu yanzu. Bayan Audu ya sauka qasa a tsakar gida ya tarar da Baqin nasa a tsaitsaye. "Bismilla muje can falon" ya fada yana musu jagora zuwa falon da Bara'atu ta fita can ya gyara ya saka kujeru yake sauke baqinsa amma haka Binta zata bisu har can din. Suna zama tana shiga ko gyale bata yafo ba ta dirirce ganin harda Yaya Baba ko babu komai shidin babbane a cikinsu yanayin rayuwa yasa take ganin kamar ma ze girmin Dadynta dan wahala tasa tsufa ya masa sammako banda yanzu da Al'amura suka fara daidaitar musu ya dawo hayyacinsa dalilin Alkhairan da yake samu daga kula da Gonar da yakewa Audu amma da kam anji jiki ga tarin iyali ga Abinda suka Dogara dashi na Noma Hashimu ya ringa Ha'intarsu yana Azurta kansa su da wahala amma shine cikin walwala da jin dadi wannan ya saka suka yada makaman yaqinsu suka rungumi su Audun hannu bibbiyu gashi kuwa suna sharbar romon damakaradiyya har ya sauke farali a dalilin hakan. "Au kune sannunku da zuwa ina wuninku?" ta fada tana jada baya tareda sunne kai, suka amsa mata a tare, ta tsaya daga qofa bata fita ba bata shoga ciki sosai ba Audu ya kalleta yace "Kawo musu ruwa mana" "Ayyo toh, bari a kawo" ta fada ta juya tana dannan masa Ashar a ranta. Mairo ta kwalawa kira ta gaya mata ta kawo ruwa tayi sauri ta koma bakin qofar ta labe. "Munje kuma Babanta ya sanar mana da daman kun gama magana shiyasa bamuyi gardama ba dayace a Daura auran, to Alhamdulillahi anyi komai kamar yanda shari'a ta koyar yanzu ya rage kuma ka saka ranar da matarka zata tare, Allah ya sanya Alkhairi ya sa Abokiyar arziqi ce" Yaya Baba ya fada. Ihun da Binta ta fasa ya hanshi yin magana se ya miqe da sauri ya fita suka rufo masa baya kowa da tunanin abind aya sameta, tana tsaye ta dora hannuwa biyu a kai, ganinsu yasa ta qara fashewa da ihu me firgitarwa da tayar da hankali har tana dira qafafu kamar qaramar yarinya. "Lafiyarki? Meya sameki? Ko kunama ce ta harbrki?" Audu ya jera mata tambayoyin cikin rikicewa yana qoqarin riqeta amma taqi tsayawa, ihu take tsalawa duk qarfinta kuma taqi magana haka nan bata dena dire diren ba. "Kodai shafar jinnu ne tana dasu?" Yaya Baba ya tambaya yana ja baya, takaici ya qume Audu na abinda takeyi ya juya yana ce musu "Muje dan Allah lafiyarta qalau wulaqancine da rashin son a zauna lafiya ya sakata haka" seta ruqo rigarsa ta baya cikin gunjin kuka tace "Wlh baka isa, idanna yarda shegiya uwata ta haifeni aure? Aure fa naji suna zancen an daura maka ni zaka munafunta kayi mun kishiya da kudin ubana har yaushe ka nemi auran ban sani ba? Na rantse da Allah kayi kadan" ta fada tana cukuikuye masa riga, bayaninta ya fahimtar dasu dalilin kukan, Yaya Babba ya baza riga yace "To mu bari mu wuce dan me motar daya kawomu yana waje dama yana jiranmu, Allah ya zaunar lafiya ya kade fitina idan an tsaida ranar Biki ka sanar mana mu shirya a can ai za'a kai Amaryar kamar wannan itama ko?" Ya qarasa yana nuna Binta. "Ku koma ciki Yaya bamu gama magana ba ke kuma sakeni" ya fada yana qoqarim banbare hannunta daga rigarsa amma ta qara riqewa tam tana qara tabbata masa idan ta sake shi shegiya take. "Kaga ka kashe wannan wutar tukunna bari muje Allah ya rufa Asiri" daga haka suka fice suna waiwayen Binta dake ihu tana qara maimaitawa Audu be isa ya mata kishiya da kudin ubanta ba. Mari me kyau ya kwasa mata bayan fitarsu daya saka ta sakeshi babu shiri. Ya nuna ta da yatsa yana cewa "Kinyi na farko kinyo na qarshe ni ba sakarai bane da zaki cimun kwala a gaban mutane, Aure kuma nayi, ba'a qaro mata ke na Auroki ko ba wata kika tarar a gidan ba? To ki kiyayeni wlh" yana gama fadar haka fuuuu ya wuce cikin gida ya barta a tsaye taba sharbar kuka. A haukace ta zari mayafi tabar gidan bata ko dauki Zakariyya ba ta tafi gidan Turai can ta tarar da ita a wani birkitaccen yanayi dan itama gyale ne a hannunta da alama fita zatayi qiris ya rage suci karo kowacce taja baya. Binta ta fashe da sabon kuka tana shigewa cikin falon Turai tabi bayanta tana cewa "Gidanki zani" "Ai gani nazo, Turai ni Audu ze wulaqanta a duniyar nan ni ya tozarta yayi mun kishiya ban sani ba da kudin ubana?" "Danqari, Binta amma Audu ya shammace mu kuma wlh ko a bakin Ali banji zancen auran nan ba se yau, to ya akayi haka? Kin ma san wadda ya aura wai?" Turai ta fada cikin Tashin hankali. Binta na sharar hawaye da Majina tace "Ina na sani, badan nabi bayansa bama da yan uwansa sukazo da qila sedai naji ana gafara za'a shigo da Amarya ki taimaka mun Turai ya zanyi? Wlh bazan dauki wannan wulaqancin ba Audu be isa ya tozartani a duniya ba yayi kadan har marina fa yayi yanzun me kike tsammanin zeyi mun idan matar ta shigo". "Uhm Binta kenan, nifa Auran Audu bashi ya daga mun hankali ba kamar wadda ya auro din, Kilaki fa ya kwaso miki a matsayin kishiya, idan har Auran nan ya tabbata ai kin gama yawo Binta wlh kashinki ya bushe kishi da Karuwa" Sakare Binta tayi kukan ya tsaya mata kamar anyi ruwa an dauke kafin ta lailayo wata Ashariya me maiqo ta maka tana cewa "Kilaki? Ni aka aurowa karuwa a matsayin kishiya? Ashe barinkin Audu har tayi qaurin da ze auro Karuwa ya kawo cikin gidana? Lallai kuwa be siyo zaman lafiya ba ze kuma san ya tsokana tsuliyar Dodo, na rantse da Allah daga ita harshi se sun gane kurensu, zasu san ni Binta ba kanwar lasa bace" yeeyeyey ta cigaba da kuka. Turai ta sauke tagumi tareda yin Ajiyar zuciya me qarfi tace "Qawata wannan Al'amarin fa ya zarce yanda kike tsammani, duk fa iya kissa da manaqisarmu bamu isa mu kama qafar matan bariki ba. Ke iya qoqarinda tayi har ya Aureta ai kinsan ba qaramar kai bace wannan tararta se anyi babban shiri" ta matsa kusada Bi ta dake kuka ta dafata taci gaba da cewa "Kina ji qawata, yanzu dai tunda me afkuwa ta rigada ta afku mataki biyu ne zamu iya dauka a kai,ta siyasa zamu bullowa abun kuma ba mu zamuyi yaqin da kanmu ba, na tabbata yan uwansa basu san waya aura ba dan haka farke mata laya zamuyi duk wanda ya isa ya fada aji a danginsa ki sameshi ki gaya masa wacce Audun ya auro sannan ki sanar da iyayenki abinda ake ciki da kuma abinda ya miki ki qara maggi da gishiri ke kice dukan mutuwa ya miki ma sannan na biyu dole mu binciko ko wacece mu bi ta qarqashin qasa mu watsa auran tun a waje babu yanda za'ayi ta tare a gidanki" Turai ta fada. Haka suka ci gaba da kitsa yanda za'ayi har dare Binta na gidan kafin ta koma wujiga wujiga fuska ta kode saboda kuka ido yayi luhu luhu. Ranar bata ko kalli qafar benen Audu ba, cikin daren ta hada kaya daman Turai ta shirya mata direban da ze kaita Kaduna ai kuwa washe gari Asubar Fari tana jin Audu ya dawo daga masallaci ta dauki Jakar kayanta ta saba Zakariyya a baya ta fice. Can inda sukayi da Direban ze tsaya taje ai kuwa ta tarar dashi babu bata lokaci suka yanki hanya se Kaduna. Yanda ta wuni ta kwana da yunwa ga tashin hankalin da take ciki ya saka duk ta fita hayyacinta, inda Audu ya mareta yayi shati abinka da fuskar Ajebo, saboda iya sharri har kanta ta buga a bango yayi quli ta karci wasu gurare a jikinta da farce saboda ita kadai tasan meta shirya zata fada idan taje gida. A Makeken compound dinsu ta kwanta tana malelekuwa wai ba zata iya takawa ba bayan isarsu, Direban kansa bude baki yayi tsabar mamakin kaidin wannan matar. Qalau suka taho da qafafunta sau biyu suna tsayawa a hanya harta fita tayi uzurinta amma shine da zuwansu zatace bata iya tafiya lallai mata ababen tsorone. Mamansu na Kitchen tana bada umarnin abinda za'a girka na rana ta jiyo ihu da kururuwa a waje babu shiri ta fita tayi tozali da Binta kwance a qasa tana wannan ihu qurjinta ya buga, abinda ya fara zuwar mata shine mutuwa akayi dan haka jiki na rawa ta qarasa ta kamata. "Na shiga uku na lalace Mama wayyo Allah na" abinda take ta fada kenan sanda Maman suka shigar da ita ciki da taimakon Munira qanwarta. A falo suka barta ta sake kwanciya qasa har wani numfashi take ja tamkar wadda ake zarar ranta. "Dan Allah kiyi shiru kimun bayanin meya faru Binta, karkisa ka zuciyata ta buga ki gaya mun meya samu Mijin nako" Maman ta fada cikin tashin hankali. "Meyake faruwa haka? Ke Mamana menene? Accident kukayi ko wanine ya mutu acan?" Alhaji Zakariyya daya taso daga bacci dalilin kuwwar Binta data isa ko ina a gidan ya fada yana isa gareta, ganinsa yasa ta qara rikicewa ta shiga qoqarin miqewa tana miqa masa hannu ya riqota jikinsa har rawa yake saboda tashin hankali "Kiyi magana Binta, zakici ubanki wlh idan baki mana shiru kin fada mana abinda ya faru ba" Mama ta fada cikin tashin hankali ta jimqe hannayenta da suke fitar da zufar fargaba. *MAMAN MARYAM ONLINE BUSSINESS* *Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments* *Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*❓ *Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT* *Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya* *Muna da magunguna iri iri* *NA GYARAN JIKI* *NA GOGE NANKARWA* *NA RAGE QIBA* *NA CIRE TUMBI* *NA QARIN HIPS* *NA GIRMAN BREAST* *NA QARA TSAHON GASHI* *NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA* *Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa* *Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*, *Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba* *Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku* *INA MASU HAWAN JINI?* *INA MASU CIWON ZUCIYA?* *INA MASU CIWON QODA?* *INA MASU CIWON HANTA?* *INA MASU SICKLER?* *INA MASU HIV?* *INA MASU CANCER?* *INA MASU NEMAN HAIHUWA?* *Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku* *Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce* *Munanan a KANO KUNTAU* *Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa* *Kutuntube mu ta wannan number 📞08129249549* *📲07011401314* Dakyar ta iya nutsuwa dukda ba sosai ba ta shiga kora musu qaryar data tsara ta haddace dangane da Auran da Audu yayi ba tareda saninta ba kuma akan ta masa magana yayi mata dukan kawo wuqa dakyar ta kwaci kanta shine ta gudo. Yanda ta tsara labarin babu wanda ya isa ya qaryata ta musamman ga shaida nan jikinta ya nuna. Mamaki madaukaki ya kama iyayenta musamman Alhaji daya ringa dubanta kamar me son ya tabbatar da dagaske take ko qarya takeyi. "Wlh bazan koma ba, sedai ya zaba koni ko ita haka kawai bazanje su shafamun cuta ba kuma idan ya zabi zama da ita Dady ka gaya masa ya maido maka da duk wata dukiya daya samu ta dalilinka ai daman saboda ni ne kuma idan ya sakeni dole ya bayar tunda bata ubansa bace" Binta ta fada cikin gunjin kuka. Alhaji Zakariyya ya wuce bangarensa ba tareda yace mata qala ba ya kasa yarda da abinda ta fada, meya hada Audu da matan banza har ya gano matar Aure a cikinsu sannan da gaske Audu ne yayiwa yarsa gudan jininsa wannan dukan babu kara balle ya taci arziqinsa to kodai shaye ya fara toh? A can falo kuwa da Mama ta gaji da ihu da kururuwar Binta ta daka mata tsawa tace "Ki rufe mana baki, Audun ai ba mahaukaci bane da ze kamaki da duka haka kawai waye be san halin tsiwarki ba a gidan nan kuma Aure daman kin sani a rubuce take zeyi, ba wata kika tarar a gidan ba dan haka ba zaki fitar da ran kema za'a kawo miki wata ba. Abinda na jiye miki tun farko a Auran Tifical Bahaushe kenan wanda be yi Ilimin Boko ba balle ya waye da yanda rayuwa take, irinsu Audu a kullum tunaninsu be wuci su samu kudi su tara mata da Yaya ba basu damu da jin dadinsu ba balle walwala ko yanda zayuwarsu zata kasance, ke kikace kinji kingani dan haka yanzu babu wani dalili da ze saka kice zaki dawo mana nan, Munira ma Addu'ar Allah ya kawo wanda zero dauke mun ita nakeyi ballantana ki kaso Auranki ki dawo mun". "Kai Mama ya zakice haka bakiga abinda ya mata ba se kace ba yarki ba, kuma ko auran zeyi ya rasa wa ze auro is Karuwa haba mana wannan ai ba abune me yuwuwa bama" Munira ta fada aiko ta juya kanta tana cewa "Idan na sake jin bakinki a nan sena gwabjeki shashasha ai kema ba sanin ciwo kanki kikayi ba "Ya isa haka Firdausi, ke kuma Mamana ki shiga ciki kiyi wanka Munira ki rakata clinic a dubata, ku dauke yaron nan daga qasa sannan wanda ya kawoki tafiya yayi ko yana nan?" Alhaji Zakariyya saya sake fitowa shirin shirin fita ya fada. Se sannan suka lura da Zakariyya dake kwance qasa abinsa yana bacci Direban ne ya shigo mata dashi ya watsar dashi a qasa tareda jakar kayanta. Ta miqe tana dingisawa Munira ta dauki Yaron suka wuce ciki. KANO Rai fes Audu yayi bacci babu damuwar komai tattare dashi illah mafarkin Amaryarsa daya kwana yanayi tareda shirya yanda tariyarta zata kasance nan da sati biyu masu zuwa shima saboda ya bata damar yin shirye shirye ne daga bangarenta dan shi a shirye yake fenti kawai ze saka a sakewa dakin can tazo ta zauna. Rashin zuwan Binta dakin be dameshi ba saboda yasan koda taje qarshe rigima zasuyi, da ya dawo daga sallar Asuba har ze shiga ya dubata kuma ya fasa dan yana so ya koma bacci yasan kuma muddin ya shigan bacin rai ze kwaso dan haka ya bari akan sa hade idan gari ya waye sosai. Bugun qofar gidan da ake kamar za'a ballata ne ya tayar dashi. Ya ringa sakin tsaki yana tunanin wanene haka? Jallabiya ya saka ya sakko yana mamakin Ina Binta ta shiga ake irin wannan dukan qofar bataji ba ko itace ta fita qofar ta kulle ta waje. Takaici ya qumeshi ganin Lantana me aiki, ya tsani matar saboda kana ganinta kalar munafukai ne da ita. Ta durqushe a qasa kamar zata kwanta tana gaishe shi ya amsa a dake yana cewa "Wane irin abu ne haka zakizo kina dukan qofar mutane" "Kayi haquri yallabai kasan dokar Hajiya qarfe bakwai nake zuwa gidan nan to Nazo tun bakwan na buga ba'a bude ba na tafi shine na dawo na sake bayi bugun da qarfi ne ko bacci take kar nayi laifi tace banzo da wuri ba" Tsaki yayi ya juya ciki, harya fara hawa sama ya dawo jin tanata qwanqwasa qofar Bintan shiru ba'a bude ba, ta matsa ya isa jikin qofar

Chapter 16 of 32