Wa na ke tsoro?
Gwaggo ba ta nan ta na ciki wajen Alhajinmu.
Ya Muntari ne a wajen ya kirana sunana ya na faɗin" Asibiti ne fa nan ba gidan biki ba. Ku bari ku koma gida mana."
Yaya Murja kuma sai ta taɓe baki ta ce"To daman ai mun san baki tsoron kowa mara kunya. Hassada ce da kishi saboda ta ga Ma'u ta riga ta zuwa. An ce ki yi hakuri kuma sai ki na neman gaya mana mgana"
Anty Aina ta tsawatar ta ce a bar mganar ni ko ba na barin ta kwana na ce"Allah ya tsari Sadiya me Ma'u ta mallaka a duniya nan da ni ban da shi sai na yi mata Hassada! Ai ba ta kai ba tukunna dai."
"Zan fa ci ubanki Sadiya ni ba tsaran ki ba ne wallahi."
Zan sake mgana Anty Aina ta daka min tsawa ta na faɗa min" Wai ba na ce ki yi shuru ba ne Sadiya?
Kaina na kawar gefe ina kaɗa kafata cikin bacin rai. Yaya Balki ta ce"Ita Yaya Murja saurun fusata ita kuma Sadiya rashin kunya. Alhajinmu na kwance ba lafiya ma ba za su fasa ba."
"Ba za su fasa ? Me ya faru?
Yaya Abubakar ya faɗa yana ƙariso wajen tare da Ma'u sun jero
Ba wanda ya yi mgana sai Zaituna.
"Sadiya ce da Anty Murja suke cacan baki."
Yaya Abubakar ya kalleni ya kalleta kafin ya ce" Me ya faru?
Anty Balki ce ta maida masa yadda aka yi kawai sai ya juyo yana kallona kafin ya ce" Ni ne nan na kira Murja na faɗa mata na kuma ce ta kira Ma'u da sauran ta faɗa musu. Tun da sun ce ki yi hakuri sun yi kuskure ba shike nan ba? Ko ke shikenan ba a baki hakuri ki hakura?
Ko kallonshi ban yi ba sai da na ji ya ce"To kar ma ki fasa. Ke daman ba ki son zaman lafiya ko da yaushe cikin ƙananun mganganu kike."
Ɗagowa na yi ina kallonsa cikin ɓacin ran dake cikin idanuwana shi kuma sai ya juya yana ma Ya Muntari mgana.
"Ka na ji suna hayaniya ba ka tsawarta musu ba?
Kai tsaye ya ce" Na yi mgana sun ki ji shi ya sa na kyale su. "
Kawai sai ya juya ya na kallona kafin ya ce" Duk wacce ta san hayaniya ya kawota ta tashi ta ƙara gaba. Mu lafiyan mahaifimmu muke nema ba tashin hankali ba."
"Ka yi hakuri ya Abubakar. Sadiya kema don Allah ki yi hakuri. Har ni na kira wayarki ba ta shiga."
Ma'u ta katse surutun na shi.
"To kin ji ma."
Ya faɗa ya na kallona dakyar na iya danne ɓacin raina na kalli Ma'u ina faɗin" Ya wuce."
Sai ta yi mini mirmishi na mayar mata da yake. Kusa damu ta zauna amman gefen Rahila. Shuru kawai na yi ina danne yanayina ni fa daman da Yaya Murja da Yaya Abubakar haushin su na ke ji tun kan abin da ya faru. Kuma har gobe na san suna bayan Ma'u ne. In da suka ijiyeni nima nan na ijiye su.
Kiran wayar Yallaɓai ya sa na tashi na bar wajen.
Yana tambayanta ya jikin Alhajinmu na faɗa masa da sauki da yadda ake ciki.
"Allah ya ƙara sauki muna idar da sallar jumma'a zan taso kin ji ko? Ban da damuwa ok?
Sai na gyaɗa masa kai kafin ya cigaba da faɗin" Yara fa! Ina kika kai su?
"Suna gida tare da Saude."
Sai ya sauke numfashi kafin ya ce"Sai na dawo."
Da haka muka yi sallama. Ganin har azahar ta yi sai na fita haraban asibitin na tambayi wata nurse masallaci sai ta nuna mini. ga mata nan suna alwala mazan dai ina ga waje za su fita su samu sallar jumma'a nima sai na bi bayansu na yi alwala muka shiga masallaci na yi sallah na zauna ina addu'o'i bayan na shafa sai na kira wayar Amina sai ta ce minI ita Yaya Aina ta kira ta faɗa mata mijinta baya nan amman in ya dawo in sha Allahu suna tafe gobe na ce Allah ya kaimu.
Muna waya Khaleesat na kirana bayan na katse sai na kirata jikin Alhaji ta tambaya na ce da sauƙi ya na barci ita ke faɗa min suna hanya na yi musu fatan isowa lafiya. Na daɗe a masallaci sai da Rahila ta kirani ta ce ko na tafi ne? Na ce a" a ina masallaci.
"Oh mu ai nan muka yi tamu sallar. Ki zo ga su Baba Aminu nan sun iso."
Sai na ce mata gani nan zuwa. Ji fa har mutanen jihar katsina sun ji labari sun iso amman ni ana raina min wayau. Kuna ina da tabbacin cikin su ne wata ta kira su ta faɗa musu.
Na fito daga masallacin zan wuce bangaren dakin da Alhajimmu ya ke na ci karo da Baaba Asiya ta na ta neman ɗakin kamar ma ta na kiran waya ne ƙila Ma'u take kira sai na ƙarisa wajenta ina faɗin" Baaba."
Sai ta juyo ta na kallona fuskarta kadaha kadahan kamar yadda muka saba karɓan juna tun bayan faruwan rushewar auran Ma'u da Yaya Hamza da na zama ni ce sila."
"Yauwa. Ma'u bari ma ga Sadiya na gani."
Daga haka ta katse wayarta. Da yar jaka a hannunta da kayanta a ciki.
"Sannu da zuwa Baaba"
"Yauwa dai."
Sai na mika hannu zan karɓi jakar sai ta hanani ta wuce gaba tana faɗin" Ina ne ɗakin da aka kwantar da Yaya Sulen?
Ban damu ba na wuce ina faɗin" Ciki ne."
Ba tun yau ba ni na san ta tsane ni ita da yarta. To nima dai ɗin ba wani son su nake yi ba shi ya sa ban taɓa damuwa ba matar da na san ba ta ƙaunar uwata ina zan taɓa ganin farinta.
Ta bakin Hajiya Dubu da ke yawan faɗin" Asiya ki daina wannan dabi'un naki karki tsufa kuma tsufar ta zo ta yi miki gardama."
Allah ya jiƙan Hajiya Dubu da gafara. Mutuwarta da mutuwar Mama sai nima na mutu zan iya mantawa da su.
Muna tafe ina gaba ta na baya har zuwa ɗakin da Alhajinmu ya ke. Baba Aminu ne ashe da Baba Sani suka zo. Ma'u na ganin uwarta ta yi wajenta tana mata barka da zuwa.
Ban ƙara ta kan su ba na isa wajen su Baba Aminu ina gaishe su.
"Lafiya lau! Dubu ce?
Sai na ansa musu domin kaf gidan su Alhajinmu ba mai kiran sunansa sai dai Dubu saboda na ci sunan Hajiya Dubu ce kuma ita ɗin mai Daraja ce ta matsayin uwa a wajen su.
Da ɗaya da ɗaya likita ya ba su izinin shiga su ga Alhaji. Da suka fitio ne na ji Baaba na faɗin Yaya Sule ya ya ɗan farka yana ta mganganu har yana kiran sunan Ruƙayya
Gabana ya faɗi Mama kenan fa. Kar shima dai Alhaji tafiya zai yi ya bar mu? Likita ne ya ce daga yanzu ba wanda zai sake ganinsa sai dare a barshi ya huta.
Kowa ya ji labari amman ban da Datti na ce aƙyale shi saboda suna da test kar mu ɗaga masa hankali. Ma'u ta kira gida yar aikinta ta yo abinci direba ya kawo tare da Zainab. Dukkanmu ba wacce ta koma gida sai Zaituna da mijinta ya ce ta koma gida Gwaggo ma sai bayan la'asar da su Baba Aminu suka matsa sannan ta yarda Yaya Abubakar ya ɗauketa a mashin ɗinsa ta koma gida ta yi wanka sannan ta ɗauko ma Alhaji wasu kaya ruwan zafi da kayan Tea Ma'u ta saka an kawo. Abincin da ta kawo shi kowa ya ci amman ban da ni. Har su Baba Aminu shi suka ci Rahila ta ce ba zan ci ba na ce ta san ban iya cin wani abu a asibiti.
Wajajen biyar Yaya Hamza suka iso tare da Khaleesat da yayansu Amna da Tasleem. Ba daɗewa tsakani sai ga Yaya Auwal da Anty Laila suma sun iso asibtin diret ko gida ba su je ba sai da suka leƙa Alhajinmu suka ganshi sannan hankalinsu ya kwanta. Yaya Auwal yana zuwa ya ba da kuɗi aka siyo kata katan ɗin ruwa da lemuka. Ya yi kuma oder abinci na dare tunda muna nan ba wacce ta iya koma gida sai Gwaggo. Ita kuma a can gida Yaya Abubakar ya siya anta ya kai mata za ta dafa ma Alhaji tunda sun ce yana bukatar cin wani abu mai ruwa ruwa haka.
Yallaɓai na ji sa shuru har bayan mangariba sai da na kira sa ya ce bai dawo da wuri ba ne. Zai je gida ya yi wanka sai na ce ya taho da su Jidda tare da Saude asibitin ya amsa min da toh.
Gabaɗayanmu muna asibitin har sai da likita ya yi mana tsiyar Alhaji ba zai mutu ba zai ta shi mu je gida hakanan saboda sun ga zugan ne da yawa.
Tare da Alhaji Mustapha Yallabai suka shigo wajen da muka zazzaune. Kowanne da leda su Jidda na baya Yallaɓai dai kayan lambu ya siyo shi kuma mijin Ma'u ban sanin masa ba. Su dai an bar su sun shiga duba Alhaji ya farfaɗo da sauki wannan karon har sun gaisa ya ce ina yan matansa Yallaɓai ya ce suna waje suma sun zo duba megidansu.
Ganin ya farfaɗo da sauki sai likita ya ce mu shiga gabaɗaya mu duba shi amman da sharaɗin ban da hayaniya kuma muna dubashi mu fito mu tafi gida. Haka ko aka yi ɗaya bayan ɗaya muna ƙarisa gaban gadon shi muna gaishe shi yana amsawa ga jikokinshi kusa dashi Jidda har ta na bare masa ayaba ta nufi bakin shi tana cewa" Alhaji ga ayaba."
Aka saka dariya Baba Aminu na cewa" Ka ji min ja'ira tun ɗazu ta ganni amnan ba ta bare min ayaba sai Yaya Sule dake kwance rai ga hannun Allah."
Su dariya mu ma muna ta dariya Alhajinmu ya buɗe baki ta saka mai sai da ya haɗiye sannan ya ce"To ai ta ga duk yinii yau ina kwance ban ci abinci ba. duk ta fi min sauran matan nawa ita maimuna ban ma ganta ba "
Yana mgana sai ga Gwaggo ta shigo ta na faɗin" Gani nan na zo. Wace ce ta zo za ta yi min fashi miji."
"Gani nan. Tunda kin yi tafiyarki kin bar shi."
Jidda ta faɗa ta na mirmishi gabaɗaya aka kwashe da dariya ban da Baaba da ke wani taɓe baki kamar ta ga kashi.
Yaya Hamza ya ce" Ai sai ba ɗiyar Sadiya ba."
Anty Aina ta karɓe da faɗin" Ai Baby ce Sadiya sak. Jidda kuma Yallaɓai ce ba ta da hayaniya"
Likita ne ya zo ya ce dubiyar ta isa haka kowa ya fita shi ya sa muka yi ma Alhaji sallama muka fito. Khaleesat na haɗa da Saude tunda can gida za su kwana na ce su wuce mini da ita. Ina jin Ma'u na neman yan kwana a gidanta ba ta samu ba Anty laila yar kano ce amman nan gida ta ce min zata kwana Baaba dai ban sanin mata ba na dai ganta da yarta suna ƙuskus. Baba Aminu daman gida ne Baba Sani ne aka bari zai kwana da Alhajinmu Yaya Abubakar ya so ya je gida ya Huta ya ce miye amfanin shi? Shi zai zauna ya kwana har a sallami Alhaji.
Wajajen tara muka bar asibitin Gwaggo a motar Ya Auwal. Shi Yaya Abubakar ya ɗauki matarsa a mashin dinsa ita kuma Rahila ya Muntari shima yana da mashin Baaba kuma a motar mijin yarta ni kuma a motar Yallabai ni da Ya'yana.
Mun yi sallama gabaɗaya Yaya Murja ta riga tafiya daman da megidanta ya dawo suka tafi tare Anty Aina ma mijinta na da wata tsohuwar benz shi ya zo ya ɗauketa.
Sai goma saura muka shiga gida yunwa na ke ji ya sa Yallaɓai ya siya mini tsire a hanya da lemu sai ya siya biredin da zamu ƙarya da shi da safe in Allah ya kaimu.
*Janafty*
*TURKEN GIDA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Arewabooks:Jamilaumarjanafty*
*SSADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)*
*🅿️10*
Tun da na tashi da safe na fara tunanin wani abinci zan dafa na kai ma Alhajinmu. Gashi kayan abincin mu duk sun ƙare kuma Yallaɓai har yanzu bai ce mini komai ba. Da safe ma Tea muka sha shima kayan tea ɗin saboda ya na yawan siyan shi ne ba sai ya ƙare ba shi ya sa shi ya kan zama na ƙarshen ƙarewa.
Na daɗe ina tunanin abin da zan yi. Kafin na tsaida shawara yin tuwon shinkafa miyar agushi tunda shinkafar tuwon kaɗai gare ni. Sannan ina da kayan miya nikaƙƙe a frizer sauran kayan cefanen ba zai gagara ba. Tun safe na kira wayar Ya Auwal mun yi mgana ya ce sun je ma asibitin sun duba Alhaji da safe jikin sa da sauƙi ya na ta barci sun ɗan dawo gida su karya ne sannan su koma ni ma na ce in na gama abin da na ke yi zamu zo asibiti tare da Yallaɓai in sha Allahu.
Yana falon farko ya na aiki na je na same shi na faɗa masa ina so zan yi ma Alhajinmu girki in za mu je mu tafin mai dashi.
"Me za ki dafa masa?
Ya faɗa ya na ture takardan gabansa lokaci ɗaya yana kallona.
Kai na rausaya kafin na ce" Tuwo zan yi masa miyar agushi. ".
Kai ya jinjina mini kafin ya ce" Kina buƙatar wani abu ne?
Kai na gyaɗa kafin na ce"E. Ina son Nama da ganda. Sai ganyen Ogun ina da sauran stock fish da agushi ɗin."
Sai ya gyaɗa min kai kafin ya ce" Shike nan. Zan yi ma Musbahu waya sai ya siyo ya taho dashi."
Duƙawa na yi na sumbaci bakinsa kafin na miƙe ina faɗin" A huta lafiya Yallaɓai na."
Kai ya jinjina min yana ɗan mirmishi fita na yi daga falon bayan na rufe masa ƙofar saboda zane ya ke yi ba ya son hayaniya ɗakin su jidda na shiga ba hasken sai da na kunna dukkansu suna kwance suna barci ga darduman da suka yi salla nan da azkar din su ko kwashewa Jidda ba su yi ba ban tashe su ganin yau asabar kuma suna hutun Tahfeez ya kamata su huta tattara kayan na yi na maida shi a muhallin shi sannan na gyara ma Baby kwanciya ita kuma Jidda na zare mata Hijabin jikinta ganin da shi ta kwanta. Sake kashe musu hasken ɗakin na yi bayan na rage musu iskar fankar a hankali na rufe ƙofar kar ƙara ya tashe su.
Tuwon na kunna gas na fara ɗorawa. Saboda ina so mu fita da wuri duk da za mu fara biyawa ta Gwammaja mu kai su Jidda sannan mu wuce asibitin. Ɗaki na koma ina gyarawa saboda Yallaɓai ya ce na haɗa kayanmu waje ɗaya mai wanki zai zo ya ɗauka sai na firfito da kayan ina haɗawa. Ni kaya ba su da yawa atamfofi ne da lesuna ƙananun kayana ni na ke wanke su da kaina in na samu lokaci tare da unders ɗin Yallaɓai na na yara kuma ba su taru ba ko sati biyu ba a yi da kawo musu wanki ba.
Bayan na gama haɗa kayan na saka su cikin ghana must go ɗin da daman saboda kai wanki ne in kuma za a dawo dasu a ciki ne a goge. Gyara ɗakin na fara saboda ya ɗan yi ƙura, sai na fara tunanin unders ɗin Yallaɓai duk sun yi datti ya kamata na wanke masa. Amman sai na duba ya na da sauran wankakku zan bari in Alhajinmu ya koma gida ya samu natsuwa sai na yi mana wankin. Allah ya sa ma ya na da su da yawa tun da in na samu kuɗi ina siyan masa da turaruruka in yi masa kyauta a matsayinsa na mijina.
Ban ma gama gyaran ɗakin ba na koma kitchen na wanke shinkafar na saka kafin ma ya tafasa saboda in ya jiƙu ya fi danƙo. Ƙara komawa ɗakin na yi na gama gyaran na ɗauko abin shara na share sannan na ɗauko towel ɗin goge na gege madubi da jikin wardrope ɗina tunda ya na da glass. Sai kawai na ji yau gwara na yi aikin gidan tunda ba ma nan kar na ba ma Saude wahala tuna haka ya sa na ɗau waya na kira Sauden tun da ni na siya mata wayar saboda matsala irin haka bayan mun gaisa na ce yau ta yi zamanta ba sai ta zo ba sai ta ce mini toh.
Ina tuwona ina aikina. Ban share falon farko ba saboda Yallaɓai na aiki amman gabaɗaya na share gidan na yi mopping sannan na turare gidan da turaren wuta na kajiji a burner.
Kitchen kuma ma bari sai na gama girki gabaɗaya. Sai da na tuƙa tuwon sannan Jidda ta taso ta na murza ido ta ganni ina fito da sabbin kolilina in da zan saka abincin.
"Ina kwana Umma."
Na waiwayo ina faɗin" Lafiya lau jidda. Ina Baby ba ta tashi ba ne?
Ta na murza ido ta ce" Ta na wajen Abba"
Sai na gyaɗa kai ina faɗin" Akwai ruwan zafi a flasks a saman dining ni da Abbanku mun ƙarya. "
Ta na kallona ta ce" Umma ba ki tashe mu ba to?
Ina kai kololin wajen sink ina faɗin" Na ga yau weekend sai na barku ku huta. In kun gama karyawan ki yi ma Baby wanka tare za mu fita. Gwammaja za mu kai ku ku zauna har dare."
"Umma ya jikin Alhaji?
Na ce mata da sauƙi ina ƙokarin fara wanke kololin sai ta ce in kawo kallonta na yi ina faɗin" Ki je ku karya. In gama aikin sai ki wanke sauran ki gyara mini kitchen ɗin" sai ta amsa da toh sannan ta wuce. Ni kuma bayan na wanke su na saka Towel na goge su tas sannan na kwashe tuwon a leda na ƙulla. Wajen guda goma na saka a kula sauran kuma guda huɗu na bar mana a gida in mun dawo mu ci ban ɗora miyan ba tunda har lokacin musabahu bai zo ba.
Ban ko kai ga barin kitchen ɗin ba sai ga Jidda da leda ta kawo min ina karɓa na kalle ta ina faɗin" Uncle Musbahu ya zo ne?
Sai ta gyaɗa min kai. Ijiye ledan na yi na koma ɗaki na sako hijabin na fito falo in da suke da Yallaɓai muka gaisa.
"Anty Sadiya ya jikin Alhaji? Yallabai ke faɗa min bai ji daɗi ba?
Sai na amsa masa shi kuma sai ya yi masa fatan samun sauƙi na amsa da Amin Amin nan falon na bar su na koma ciki Ina ce ma Jidda in sun gama karyawan ta gyara ɗakin su kafin ta yi ma Baby wanka.
Da ya ke miyar ba ta da yawa sosai ba ta ɗau lokaci ba tunda agushin ma soya shi kawai na yi. Naman kuma na rago ne akwai ƙashi ƙashi a jiki sai da na tafasa sannan na yi amfani dashi kafin ka ce me gida ya ɗau kamshi miya. Na gama ɗiban ma Alhajinmu miya na saka a kula har na haɗa shi cikin kwandon da za mu tafi dashi sai ga Yallaɓai ya shigo kitchen ɗin.
"Ni fa an gama cika mini ciki da ƙamshi. Me muka samu ne?
Ya faɗa ya na tsaye a ƙofar kitchen ɗin. Kallonsa na yi kafin na juya ina goge jikin gas ɗin da miya ya ɗan ɓata. Mirmishi na yi kafin na ce"Sai anjuma za ka ci na ka fa Yallaɓai."
Koƙarin shigowa ya ke yi na wurgar da abin hannuna na nufe shi ina turashi waje lokaci ɗaya ina faɗin" Mu je ka yi wanka lokaci na tafiya."
Ba shi da mafita haka na riƙa tura shi har cikin bedroom ɗin mu. Takardun hannunsa na karɓe ina faɗin" Mai wankin bai zo ba?
Ya na saɓule dogon wandom jikinsa ya ce"Sakarai ne. Na fa kira shi ya riƙa ce mini yana hanya amman sama da awa ɗaya bai zo ba"
Ina dariya na ce"Kai da Sabitu ba" saboda suna shan dirama shi Sabitu karya da saɓa alƙwari shi kuma Yallaɓai ba ya son mutum mai ƙarya da saɓa alƙwari. Su yi ta samun matsala kuma ko ya ce ba zai ƙara bashi wanki ba sai Sabitu ya yi ta magiya domin ya na samun alheri a wajen Yallaɓai.
Cikin side drower na ijiye masa takardunsa ina juyowa muka ci karo da Yallaɓai fuska na kwabe kafin in yi mgana ya rumgumeni ni kuma ina ture sa na ce"Ban yi wanka ba Yallaɓai."
"Nima ai ban yi ba. Kawai yau mu bar ta ranar tsami na duniya ne."
Ina dariya na rumgume shi ta baya ina ɗan dukan bayan shi mun daɗe a haka kafin mu saki juna hammatar shi na ɗaga tunda bashi da riga ina rufe baki kafin na ce"Yallaɓai na na bukatar shaving gaskiya."
Hannuwansa ya ijiye saman kafaɗata yana faɗin" Sadiya ta sangarta Yallaɓanta. Ki zo kawai ki yi aikin ki Madame.'"
Dafa kafaɗansa na yi shima ya dafani muka fara tafiya ina faɗin" Muje Tiolet na gyara mijina."
Kallona ya yi ƙasa ƙasa kafin ya ce"To wai da na ce ko ni na fara gyara ki anan ne a ciki kuma ke sai ki gyara ni?
Ina jin haka na sake shi na yi gaba ina faɗin" bar shi kawai. Na gode Cafinter"
Sai ya biyo ni yana dariya har ya na cewa" Wai kada mu yi ta asaran ruwa. Gwara mu haɗa aikin."
Ko juyawa ban yi ba na buɗe kofar tiolet na shiga bayan na yi addu'a shima sai ya biyo bayana zai shigo na ce" Yallaɓai addu'ar fa"
Sai ya koma da sauri ya yi sannan ya shigo ya maida ƙofa ya rufe zai yi mgana na masa alama da bakina na ja zif alamun ya yi shuru sai shima ya yi haka alamun ya kama bakin shi mirmishi na yi masa kawai Towel na zaro daga hanger dake sama na mika masa sai ya karɓa ya juya yazare gajeren wandon da ke jikinsa ya ɗaura towel ni kuma sai na ciro veet din a saman wajen ɗan dirowan ajiye su kayan wanka a cikin sink na ce ya shiga ya zauna kamar dai yadda muka saba.
Ni na shafa masa a ƙasan sa da hammatarsa sannan bayan minti biyar ya yi na kwashe na goge wajen sannan na wanke masa. Tare muka yi wanka ranar bayan na chuɗasa nima sai ya chuɗani muna yi muna ɗan wasannin mu da muka saba cike da so da ƙauna muka fito dukkanmu ɗaure towel shi a kugunsa ni kuma asaman ƙirjina.
Yallaɓai na fara tayawa ya shirya cikin shadda mai ruwan ƙasa domin ya ce min suna da ɗaure aure na wani abokinsu da suka yi secondary tare zai ƙara aure.
Ina saka masa link ina faɗin" Har da Uncle Abba zai zo daurin auran?
"E. Har da ma Tariq. Muhammad Bello ai ajin su ɗaya ma da Tariq lokacin muna makaranta."
Sai na jinjina kai kafin na ce"Abokan ku sun fara biyu kuma kuna hanya kenan"
Ya na yar dariya ya ce"Wasu ma ko ɗayan ba su ijiye ba. Irin su kawu ba. Da wani Salihu bala wallahi sun zame mana tazuran kawai. Yau ina ga yau sai sun sha caccaka tun da kaf mate ɗin mu za su zo wajen ɗaurin auran nan "
Ina dariya na ce"Kar a taɓa min kawunaa. Ina nan ina nema masa mata."
Yallaɓai na kallona ya ce"Allah ya sa kar kawun naki ya baki kunya. Tun da kika har Nene ta ƙyale Abba da mganar aure kin san lamarin ya fi karfin kowa"
"Bai fi ƙarfin Allah ba. Muna addu'a in sha Allahu in lokaci ya yi zai yi."
Sai ya amsa min da cewa" Allah ya sa muna da rabon gani." Agogo na ɗauko masa wani ɓaki na fatar damisa na saka masa.
Turare na fesa masa sannan ya ce na zaba masa takalmin da zai saka. Wani baƙin takalmi na zaɓar masa ni na siya masa kwanki lokacin ina da ɗan kuɗina na ga wata mate ɗina a BUK na tallarsu suka yi mini kyau na ce ina so 18k na siye shi Yallaɓai na son takalmin nan fiye da sauran takalmansa duk da ya na ma cikin masu saukin kuɗi amman saboda ni ce na yi masa kyautarsa ya sa ya ke ji da shi.
Sai da na gama shirya shi tsaɓ sannan nima na ce ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 31