Muntari.
"Kai Sadiya. Ba fa Muntari sunan shi ba. Ba ki iya cewa Ya Muktar, muktar ne fa sunan kuke ɓata masa da sunan tsoffi wai Muntari."
In ta ce haka sai na balla mata harara sannan na ce"Ke kika san Muktar. To da bakin sa ma ya ce sunan shi Muntari ko Gwaggo?
A lokacin Rahila ta riƙa tura baki kenan ta na ƙunƙuni. Ta yi ƙokarin sauya sunan Muntari zuwa Muktar amman bai sauyu daga bakina ba, da gayya ma ma ke faɗa Ma'u dai da ya ke makira ce har wani ƙalƙala take yi wajen faɗin sunan.
"Ya MUKTARR."
Makircin Ma'u fa haifaffan ne, ta tsotsa a nono ne shi ya sa in ta buga acting ke yi mata kyau.
Haka Khaleesat ta zo ta same ni ina ta dariya. Domin mun yi dogon charting da Ya Muntari yana tamnbaya ta laifin me suka yi tun ranar suna Rahila ta ce ban dawo ba, na fa san Rahila ta faɗa masa dalili zai yi min wayau su na maza ne ni ko na ce ya tambayi matarsa ta san dalili.
"Ke da waye kike ta dariya haka? Ko Yallaɓan ne?
Ina mirmishi na ce"Wani Yallaɓan? Wai wannan Hubby na Rahila ne."
Ina faɗa ina dariya Khaleesat ta kwashe da dariya kafin ta ce"Au kema kin gani? Nima yanzu na gani ina ta dariya a raina na ce Rahila manya ta Muntarin ta."
Miƙewa na yi daga kishigiɗen da na ke ina faɗin" Ta fa kashe wannan sunan. Muktar ko Hubby."
Na faɗa ina kwaikwayon bakinta ni da Khaleesat har muna tafawa saboda dariya, Ita kuma faɗi ta ke yi" Ni ya na burgeni ba shi da damuwa. Ga barkwanci kuma ya na son Rahilatun nan ta bakin shi ba."
Jinjina kai na yi kafin na ce"Ai Muntari na ƙaunar Rahilatu."
"Sadiya ba ki da dama, na shigar ma Rahila. A bar yankan mana Hubby ahto.'"
Ni dai ina ta dariya. Sai kuma mu ka cigaba da hiran Rahila da Ya Muntari muna cin dariya. Kukan Amna daga bedroom ɗinsu ya sa Khaleesat ta bar ɗakin da sauri ta fita ba daɗewa mijinta ya dawo sai ban ƙara ganinta ba sai dare wajen dinner.
"Sadiya Ya ya? Fatan dai ba matsala ko?
Yaya Hamza ke tambayata. Bayan mun haɗu a Dinining muna cin abinci.
"Ba wata matsala. Yanzu dai ta yi min transfer zuwa Aminu kano ta haɗa ni da wata consultan."
Da kai ya amsa kafin ya ce" Tunani mai kyau.'" Daga nan
bai sake mgana ba. Shi ya fara tashi kafin ya goge bakin shi da Tissue sannan ya kalleni ya na faɗin" Yaushe za ki wuce? Ina kallonsa na ce" Gobe in sha Allahu"
"Ba ki bari weekend mu shiga kanon tare"
Kai na girgiza kafin na ce"Ya Hamza. Yara su kaɗai a gida Yallabai kuma ba ya zama in ya fita tun safe sai dare."
Ya na wucewa falo ya ce"Wasu yara? Yallaɓan dai amman Jidda yarinya ce? Shekaranta nawa?
"13 in to 14 fa Ya Hamza. "
"Ehem.."
Ya ce kawai alamun maganarsa ta farko dai itace Yallaɓai dai ina dariya khaeesat na faɗin" E, mana Yallaɓai dai take yi ma kewa kar ta ƙara kwana ta barshi shi kaɗai."
Mirmishi na yi kafin na rage murya ina faɗin"Da shi ɗin ma, mata ba ta yi kewar mijinta ba? Miji mai kama da dubu irin Yallaɓai na."
Harara ta zuba min kafin ta ce"Mu kuma na mu mazajen masu kama da bolar sharar ki ko?
Ina dariya na ɗaga hannu ina faɗin" Ba ruwana.".
Ba ta biye min ba, nan ta bar ni ina ƙarisa cin abinci ta bi mijinta falo suna hira nima ina gamawa ganin mata da miji na buƙatar privacy sai na ce musu zan shiga na kwanta. Ina shiga na yi shirin barci Yallaɓai na kira an ci sa'a yau ɗin ya koma gida da wuri.
"Yaushe za ki dawo? Yallaɓan Sadiya ya yi kewarta sosai."
Ina jin kewata a muryansa nima cikin muryan kewan na ce"Gobe gobe nan Yallaɓai. Kwana biyu ban ji ɗumin ka ba kamar ban da lafiya Am baby na."
Kalamai na ƙarshe suka bashi dariya har sai da ya dara, hira muka yi sama sama na ce ya haɗa ni da su Jidda ya ce suna falo suna kallo tare da Saude.
"Ki dawo gobe Sadiya ta. Da gaske Yusuf ya yi kewar HalimatuSaddiya."
Ina mirmishi kamar ya na ganina na ce"In sha Allahu Yallaɓai na."
Mun ɗan dade muna waya ina ta bashi labarin Ya Muntari fa ya koma Hubby ina dariyan shaƙiyanci ya ce"In kika dawo za ki haɗu da Rahila kun fi kusa."
Hiran sa ya ɗauke min hankali na tsawon lokaci sai da ya ce min zai yi wanka sannan muka yi sallama.
Nima daga nan na ijiye wayar na yi addu'an barci ba daɗewa sai barci.
Yallaɓai na baya son tafiyan dare ya sa da wuri na shirya. Kafin Yaya Hamza ya fita sai da ya sake ba ni 10k ya ce na yi na mota sai na yi kawaici na ce"Yallaɓai fa ya ba ni na mota ina ta saka ka ɗawainiya Ya Hamza"
Wani kallo ya yi min ban san lokacin da na karɓi kuɗin ina cewa" Allah ya ƙara ma nema albarka."
Kai tsaye ya ce"Amin. Yallaɓai mijin ki ne, ni kuma Yayanki ne kin ga ne? Sai na ɗaga masa kai ina danne dariyata. Mun rabu ya ce shima suna tafe karshen Sati na ce gida zai yi albarka Zaratan Alhajinmu za su yi hutun karshen mako a gida.
Ƙarfe goma mu ka yi sallama da Khaleesat daga nan na hau adaidaita zuwa tasha ina zuwa motar kano saura mutum huɗu na shiga ba daɗewa ta cika muka tashi. Ban samu Yallaɓai a waya ba sai na yi masa saƙo.
Mun shiga kano ɗaya da wani abu ne. Daga tasha na samu abin hawa sai gida. Ba key a hannuna sai na buga get ɗin Saude ta zo ta buɗe mini tana ganina ta washe baki ta na faɗin"Sannu da zuwa Anty Sadiya."
Ina shiga gidan na ce"Yauwa Saude ya gidan"
Ta biyo ni tana karɓan ƙaramin akwatina.
A falon farko na jaɓe ta kawo mini ruwa na sha na huta sannan na iya tashi na ƙarisa ciki na ɗauro alwala na gabatar da sallar Azahr da ta suɓumu ce mini a hanya.
*Janafty"
*TURKEN GIDA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Arewabooks:Jamilaumarjanafty*
*SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)*
https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC
No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba.
*🅿️08*
Ina idar da Salla Saude ta kawo mini abinci shinkafa da miya ce, daman na yi miyata tun kafin na tafi Zariya.
Ban iya fita ba a cikin ɗaki ta kawo mini komai na ci ta kuma zo ta ɗauke filet ɗin da kofin ruwa. Ni na ce ta jira su Jidda su dawo daga makaranta sai ta tafi saboda yau ɗin ba su da islamiya. Saude ba ta karatun boko amman tana allo tana kuma islamiya.
Khaleesat kawai na iya kira na faɗa mata na isa gida lafiya sai Yallaɓai da na kira bai ɗauka ba sai na tura masa saƙon na sauka lafiya.
Daga nan na haye gado na kwanta sai barci daman na gaji bayana har wani sagewa ya yi. Barci na sha sai la'asar na iya tashi da na ji kiran salla daga masallacin gefen mu. Daƙyar na iya tashi na shiga tiolet na ɗauro alwala na yi salla. Sai bayan na yi sallah sanna na samu daman rage kayan jikina saboda ɗazu gajiya ya sa ban iya sauya kaya ba kawai na kwanta.
Daga ni sai siket na ciki under. Sai bra na zauna a gefen gado ina duba wayata. Sai na ga Rahila ma ta kira ita da Datti.
Kiran Datti na fara bi bayan mun gaisa sai ya ce.
"Yaya Sadiya kin dawo ko kina can Zariyan ne?
Kai tsaye na ce"Na dawo ɗazu. Ya aka yi ne? Su Alhajinmu dai lafiya ko?
"Kowa lafiya. Zan koma makaranta gobe ne ina so na shigo yau da daddare."
Kai tsaye na ce" To sai ka zo."
Daga haka muka yi sallama. Sai na bi bayan kiran Rahila kamar ta na jira ta yi zaraf ta ɗauka.
"Sadiya Allah ba na son wulaƙanci."
Ina danne dariyata na ce"To Sadiya yar laifi. Me kuma na yi?
Cikin jin haushi ta ce"Ban sani ba. Sunan mijin nawa ne abin shakiyancin ki?
Ina dariya na ce"Allah ya huci ran gimbiya Rahila a gidan Hubby."
Ƙaramin tsaki ta ja kafin ta ce"Shegiya Allah zan rama ne."
"Ba a kira mu sunan sabon sunan Ya Muntari ba? Ko ba a riga an yi taron ba ne?
Na san ta buɗe baki ne ta kasa mgana saboda yadda na ji ta yi shuru. Fahimtar haka ya sa da sauri na ce"Allah ya huci zuciyar My Baby"
Tsaki ta yi mai ƙarfi ta ƙatse wayar ta barni ina ta dariya. Sake kiranta na yi ba ta ɗauka ba sai na kyaleta. Ijiye wayar na yi na tashi na saka wata rigata ta zaman gida yar doguwa mai sauƙin kwari sannan na fita falon farko na iske Saude zaune ita kaɗai ta na kallo.
Zama na yi nima ina ta ya ta. Kallonta na yi kafin na ce"Ko za ki bari in Yallaɓai ya dawo ne mu kai ki gida Saude?
Kanta na ƙasa ta ce"To Anty"
Saboda in samu in yi ma Balaraba godiya sannan mu ƙarisa gida in gaida su Alhajinmu.
Muna nan a falo biyar na yi na ce ta mayar mini Tauraruwa an fara Indiyan hausa sai ta sauya mana tasha ana wani film mai kyau, har su Jidda suka dawo daga makaranta suna ganina gabaɗayansu suka faɗa jikina suna murnan ganina nima da fara'ata na tare su Jidda da ta yi girma ban iya ɗaga ta ba, amman na ɗaga Baby sama ina mata dariya.
Faɗi take yi" Umma mun yi kewarki."
Ina shafa kumatunta na ce"Nima na yi kewarku ƴa'ƴan Umma."
Ni na cire ma Baby Uniform na kuma zauna tare da su suka ci abinci suna ta bani labarin makaranta ina sauraransu. Bayan sun gama cin abinci na ce Saude ta taya Jidda su wanke Uniform ɗin su da safuna. Suka bar mu ni da Baby a falo tana ta min labarai ina sauraranta zuciyata kamar farar takarda saboda farincikin na dawo gida na ga iyalaina cikin koshin lafiya.
Har aka kira mangariba lokacin su Saude sun dawo cikin gida sun gama wankin na ce su yi awala su yi salla. Ni ma na shiga ciki na ɗauro alwala na yi sallah ina kan darduma ina azkar na ɗauki wayata abin ya ba ni mamaki na ganin Yallaɓai bai kirani ba kuma na san ya ga kirana kuma ya ga saƙo na.
Ban yi fushi ba sai na sake kiran shi sai da ta kusa katsewa ya ɗaga kirana.
"Yallaɓai na."
Dagacan bangaren na ɗan ji hayaniya ban kawo komai ba sai na yi tunanin ƙila yana wani waje na mutane sosai.
" Ina Rano. Amman yanzu zan taso."
Haka kawai ya ce mini. Cikin mamaki na ce"Rano kuma? Aikin ne ya yi dare haka?
"A'a. Tun dazu muka tashi na biya gidan su Nene ne. Yanzu dai ina gidan Baba ne."
Kai na gyaɗa kafin na ce"Allah Sarki. Ka gaishe su."
Sai ya ce mini za su ji, naji ana mgana a kusa dashi ban gane da muryan ba amman ta mace ce.
Ina shirin mgana na ji ya na ce min" Ga Sameena ta dawo daga kano yau."
Bai bani damar mgana ba kawai na ji muryan Sameena.
"Matar Baba ɗazu da rana na dawo gida. Ashe sai yau kika dawo?
Sai na amsa mata. Mun gaisa sannan tace za ta sake dawowa in sha Allahu.
"Ko kafin ki dawo ni na zo ba."
Tana dariya ta ce"Allah ya sa'
Daganan muka yi sallama sai ta miƙa ma Yallaɓai wayarsa.
"Yallaɓai ka dawo da wuri. Ka siyo min kaza a hanya saboda yau za mu sabunta amarci ne."
Na faɗa cikin wani salo. yar dariya ya yi kafin ya ce"Amarya ko? To shikenan ango zai taho kazar amarci.'
Ya faɗa kamar cikin raɗa domin na ji ya rage murya.
Mirmishi na saki kamar yana ganina na buɗe baki da niyyar mgana kenan na ji muryanta. Muryan da ba zan manta da ita ba saboda daban take. Ko mgana za ta yi cikin isa da gadara da salo. Kuma kamar ta fi yin salo matuƙar da za ta yi mgana da Yallaɓai.
"DADDY. Ba ka ji ba."
Yaushe ta zo garin? Haka na ke tambayan kaina a cikin raina. Baki na saki lokacin da na ga kawai Yallaɓai ya katse wayar ba tare da ma mun yi sallama ba.
Gabana ya faɗi Ras!. Amman sai na lallashina kaina da cewa duk tsiyanta dai ita yanzu matar wani ce. Ba ta isa ta bibiyan min miji da auranta ba ko ita ta yi Yallabai na aminattace ne ba zai taɓa biye mata ba.
Kauda tunanin komai na yi a cikin raina na tashi na cire hijabin da na yi sallah. Gyaran ɗakin na fara duk bai da datti na san Yallaɓai na gyarawa. Sai da na share na gyara gado na goge komai na saka turaren wuta a ɗaƙin ya ɗau kamshi sannan na shiga wanka. Daga can na ɗauro alwala na fito bayan na shafa mai na yi kwalliyata kamar yadda na saba domin Tarban Yallaɓai na cikin zumuɗi da muradi mai girma. Da gaske ne na yi kewarsa sosai.
Ina sallar isha'i Jidda ta shigo ta na faɗa mini Uncle Datti ya zo. Shi ya sa ina idarwar na ɗauko wayata zuwa falo ina sanye da riga da wando na wani material na saka mayafi abaya baƙi a saman kaina ina tashin kamshi. Kaina ba kitso har lokacin amman ina tunanin zuwa gobe zan je a wanke mini na yi kitso.
Mun gaisa da Datti da tambayan su Gwaggo ya ce duk suna lafiya. Saude na ce ta zuba masa abinci. Bayan ta kawo masa na ce ta ja su Jidda ɗakin su ta zauna kafin Yallaɓai ya shigo.
Datti na cin abinci muna hira sama sama.
"Na ɗauka sai wani satin za ka koma. Ya Auwal na tafe wannan weekend ɗin fa."
Sai da ya sha ruwa sannan ya ce min" Na so haka amman ranar Friday an saka mana wani test ne, ina bukatar komawa na yi karatu"
Kai na jinjina kafin na ce"Haka ne. Allah ya bada sa'a. "
Da ya ke yana karatu ne A kaduna state University KASU"
Ko bai faɗamin ba na san abin da ya kawo shi. Alhajinmu yanzu ba kuɗi duk suna gona daman karatun na su shi Ya Auwal da su Ya Hamza ne ke taimakawa sai ni da Amina da ɗan abin da ba a rasa ba nan take na tura masa 20k cikin kuɗin da ke acct ɗina.
"Ga 20k nan ka lallaɓa zuwa karshen wata in sha Allahu."
Godiya ya yi mini kafin ya ce" Yaya Auwal ma turamin 20k zan ɗan yi siyayya kafin goben na wuce."
"Allah ya kai mu."
"Ma'u ta zo gida jiya muka haɗu na ce mata yau zan koma. Shi ne yau da safe ta kirani ta ce na je tana son ganina ta bani kayan tea da sabulun wanka da na wanki."
Ya na mgana ina masa wani kallo sai da ya gama maganar sannan ya fahimta da sauri ya ce"Wallahi ba ni na roƙeta ba Yaya Sadiya."
Ƙaramin tsaki na ja kafin na ce"Allah ya ba da lada." Da na so na yi wata mgana sai kuma na fasa tuna nima na sauya taku akan Ma'u.
Mun saki wannan hiran sai kuma muka kama na Yaya Abubakar a bakin Datti na ke jin shekaranjiya Zaituna ta kwaso rigima har da yan sanda aka kira mata. Ita wai uwar adashe ta cinye kuɗin jama'a. An ce dakyar suka ba da belinta sai dare da ta yi kwana cell.
Mamaki ya kamani na riƙe haba ina faɗin"Kai matar nan wai har yanzu ba ta daina saka Yaya Abubakar a uku ba! Shegiya ka rasa abin da take yi da kuɗin jama'a sai ta jawo rigima ta bar ɗan'uwanmu da biyan bashin ta"
Datti ya ce"Wallahi nima har mamaki na ke yi. Kuma shi Yaya Abubakar ɗin bai iya ɗaukan mataki a kanta ba."
Tsaki na ja kafin na ce"Yaushe wannan zai iya? Tun fa muna gida ni nasan Yaya Abubakar sai mace ta bautar dashi. Da dai irin su Ya Hamza ne kai kasan Zaituna ba ta isa ba. Shi fa yana jin sa kamar ba namiji ba"
Datti na yar dariya ya ce"Sanyi gare shi ne."
Cikin jin haushi na ce"Sanyin me? ya dai auro wacce ba ta san ciwon kanta ba. In bai tashi tsaye ba sai ta kashe sa lokacinsa bai yi ba"
Datti dai ta na dariya. Ban san adadin awannin da muka ɗauka muna hira dashi ba. Ni a bakinsa na ji wai Alhajinmu ma ba shi da lafiya jiya ya yini da ciwon kai nace ni ba wanda ya faɗa min ya ce su Yaya Bahijja duk sun sani sun je sun duba shi har da Ma'u."
Takaici ma ya hana ni mgana. Sai shi ne ganin raina ya ɓaci ya ce" Ƙila saboda sun ga bakya nan ne." Uhm kawai na ce ina duba agogon wayata tara da rabi na dare sai na zaro ido Yallaɓai bai dawo ba har yanzu.
Wayarsa na kira ta na ringing amman bai ɗaga ba har sau biyu tuni zuciyata ta harba ina hashashen ko har yanzu yana can Ranon ne tare da ita? Ga Saude ta na jiran mu mu kaita gida ganin har goma ta yi Datti ya ce min zai tafi sai kawai na ce ya tsaya ya tafin mu da Saude gida.
"Ba nan take kwana ba daman?
Ina miƙewa na ce"Ba a nan ba ne. ta zo ta kwana da yara. Yallaɓai bai dawo da wuri ba shi ya sa na ce ka wuce da ita."
Sai ya amsa mini, ɗaki na koma na ɗauko 2k cikin jakata na wanda Yaya Hamza ya bani na fito. Sai na iske su afalo Datti ya ba ma su Jidda Chaculate din da ya zo musu dashi ya ce har ma zai tafi ya manta bai ba su ba.
Na ba ma Saude 2k ɗin ina cewa"Yallaɓai bai dawo ba sai gobe zan shigo anguwan. Ki gaida mamanku sai na zo."
Ta karɓa tana min godiya Baby ta makale mata sai ta je dakyar na riƙe ta na ce ta bari ranar da ba makaranta sai su je can Ɗorayin su kwana.
Har haraba na rakasu. Suna fita na rufe get ɗin muka dawo cikin gida. Ganin dare ya yi sai na rakasu ɗakin su suka yi shirin barci sai da na tabbatar sun yi addu'an barci sun kwanta sannan na rage musu hasken ɗaki na rufe musu ƙofa na dawo falon farko na kame kan kujera. Ga TV a kunne amman ba na fahimta duba lokaci kawai na ke yi a wayata har goma da rabi har sha ɗaya na dare Yallabai bai dawo ba. Bai kirani ba sannan na ƙara kiran shi amman bai ɗauka ba again.
Na yi ta ƙokarin boye yanayina. Na zauna ina jiransa a falo ni kaɗai duk kwalliyan da na yi ta gama susucewa. Lallashin kaina kawai na ke yi ina zaune. Sha ɗaya da mintina sha ɗaya sannan na ji ana buɗe get da ƙaran shigowan mota.
Ajiyar na sauke ina zaune har ya shigo falon. Muka haɗa ido dashi ya na shigowa da leda a hannunsa mirmishi ya ke yi min irin na shi mai sanyaya mini zuciya.
Amman sai na ji na kasa maida masa martanin mirmishin na shi, ya ƙariso har gabana ya na sauke ledan hannun shi ya ɗago kawai ni kuma na miƙe na wuce ma mukunnin wuta na kashe hasken falon na fice a falon na bar shi tsaye sake da baki yana bina da kallo.
Na sake kashe hasken falon na biyu daga nan na shiga tiolet na kama ruwa ko da na fito na same shi a cikin ɗaki yana tsaye kawai ya harɗe hannu a kirjinsa yana kallona.
Yi na yi kamar ban gan shi ba. Na isa gaban wardrope na laluɓo rigar barcina. Ina shirin tuɓewa na ji ya rumgumeni ta baya ƙamƙam bayan ya sagalo hannunsa ya riƙe rigar barcin dake hannuna.
Na ja shima ya ja kawai sai na sakar masa. Numfashi ya fesar min ta saman wuyana. Duk ina jinsa sai na yi masa bakam mugun haushin sa na ke ji da wani abu mai zafi da ya tokare mini a ƙirji.
"Sadiya ta. Fushin kike yi da ni?
Haka ya faɗa ya na mai zuro da kansa wajen fuska.
Kauda kai na yi kafin na ƙwace jikina ya juyo muna fuskantar juna ni da shi cikin basarwa na ce"Fushin me? Ka yi wani abu ne?
Haka na faɗa kai tsaye kuma na miƙa hannu ina faɗin"Ba ni rigar barcina. Ina so na yi shirin kwanciya ne "
Sai ya maƙe kafaɗa alamun ba zai bayar ba. Ni kuma kawai sai na juya na sake buɗe wardrope ɗin na ɗauko wata itama yasake ƙwacewa na bar masa na sake ɗauko wata itama ya sake ƙwacewa a ƙufule na kalle shi kafin na kira sunan shi.
"Yusuf.."
Haka na faɗa ina tsare shi da ido. sai ya yi wani iri da fuska kafin ya ce" Yallaɓan naki ne kuma yau ya dawo Yusuf?
"Ai sunan ka ne ko ba sunan ka ba ne Yusuf?
Na faɗa cikin gatse ina hararan shi. Sai ya yi dariya ni kuma sai na juya ina ƙara laluban wata rigar barcin kai tsaye ya ce" Ko sau dubu za ki ɗauko sai na ƙara ƙwacewa gwara ma ki tsaya mu yi mgana."
Ni na san halin ɗan kayana. Shi ya sa na dakata na juyo ina kallonsa kafin na ce" Ni fa ba ka yi min komai ba. Kawai dai ina so na kwanta ne."
Takowa ya yi gabana ya saka hannunsa guda ɗaya ya riƙe min hannuna guda ɗaya ya zaunar da ni a gefen gado sai ya durƙusa a gabana lokaci ɗaya ya na riƙe duka hannuwana cikin tafin hannunsa.
"Am Sorry. Na yi dare. A gidan Baba Hajiya ta matsa mini sai na tsaya na ci abinci sannan kuma Tariq ya zo gida shi da iyalansa shi ya tsaida ni muna hira ban san dare ya yi ba. Na ga kiran ki ina hanya shi ya sa ban ɗauka ba."
Har ya gama mganarsa ina kallonsa. Zuciyata ta ɗan yi sanyin jin ba abin da na yi tunani ba ne amman ban nuna masa ba sai na ƙara hade rai har ina kauda kaina gefe.
"Ki yi haƙuri kin ji ko?
Ya faɗa ya na matse min yan yatsuna. Zare hannuwana na yi daga cikin na shi sannan na miƙe ina faɗin" Na ji."
Daga haka kawai na fara ƙokarin tuɓe kaya da sauri ya taso ya rike ni lokaci ɗaya ya na faɗin"Ban riga na natsu na ga kwalliyar ba. Ballantana har na yaba na biya tukwaici shi ne kuma za ki hana ni samun wannan ladan?
Ya faɗa ya na tsare da ido. A idanuwansa na fahimci ya gaji kuma ya na bukatar wanka ya huta. Sai kawai na ƙwace hannuna ina faɗin" Na yau dai ka makara. Amman ƙila gobe in ba ka makara ba ka rabauta"
Da sauri ya riko ni na faɗo jikinsa sai ya rumgumeni ya na faɗin" kin manta kin ce yau zamu sabunta amarci? Na taho mana da kazar amarcin mu part 2"
"Shima ka Makara. Amarci kuma ka gama shan romonsa shekaru goma sha a baya."
Na faɗa ina ƙokarin kwace kaina kai sai ya juyo da ni muna fuskantar juna na buɗe baki zan yi mgana ya haɗe bakin mu waje ɗaya yana kissing ɗina ni kuma na ƙi bashi haɗin kai sai kawai ya matse min cikina da ɗayan hannunsa ɗayan kuma ya riƙe wuyana dashi tamau yadda ya matse bakin mu waje ɗaya in na ce zan ƙwace
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 31