Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

"Shi ke nen ta so mu ta fi tun da kin samu lafiya".

Murguɗa baki Zahra ta yi sannan ta ce. "Ku fita to zan yi wani abu".

Duk abin da za ki yi kiyi babu in da zamu je, wato so ki ke ki gudu ko?".

Haɗe rai Zahra ta yi ta ce. "Idan na gudu ina zanje?, wa na sani a wannan garin?, zan yi turoso ne shi ya sa".

"Shashasha kawai". DPO ya faɗa tare da fita daga cikin ɗakin. Fice wa sauran ƴan sandan suma suka yi daga cikin ɗakin.

Tsaki Zahra ta ja ta ce. "tsohon banza kawai, idan an girma a san an girma. Ya tsaya yana biye wa sa'anin ƴaƴan sa. Guduwa ce kuma ya zama dole, domin tabbas saina gudu, haka kurun za'a kaini wani gidan gyaran hali sai ka ce wacce take rashin ɗa'a".


Ta faɗa tana mai waige-waige. Nan take wani dabara ya faɗo mata. Tashi ta yi tsaye tare da nufar ƙofar window sannan ta buɗe tare da fita ta wajan.

"Yess". Ta faɗa cike da farin ciki". Sauri-sauri take domin ta fice daga cikin asibitin. Babu zato ta ji an rungumeta ta baya.

Zaro ido waje ta yi tare da juyawa. Nan take gabanta ya yi mummunar faɗuwa?, yayin da zuciyarta ya fara dukan uku-uku. Take ta tsinci kanta cikin baƙon yanayi.

Sakinta matar wacce ta yi burzuzu da gashin kanta tamkar mahaukaciya ta yi. Kallonta matar ta yi ta ce. "Ki fitar da ni daga nan ni ba mahaukaciya ba ce kinji, ina so na koma ga ahali na, ina son na ga yarana".

Nan take jikin Zahra ya yi sanyi dubar matar ta yi ta ce. "Kiyi haƙuri ki koma, magani suke miki fa". Ta faɗa tana mai ƙoƙarin barin wajan.

Da sauri likitoci suka ƙaraso wajan suna mai rirriƙe matar. Kallon Zahra suka yi sannan suka ce kiyi tafiyar ki yarinya, ita ɗin mara lafiya ce, kada ki damu da duk abin da za ta faɗa miki".

Girgiza kai Zahra ta yi tare da fice wa daga cikin asibitin. Ta rasa me ya sa tun da ta ga wannan matar hankalinta ya kasa kwanciya.

Zama ta yi a bakin titi tana mai hasko matar a cikin idanuwanta. "To wannan matar wace ce?". Ta tambayi kanta. Basar wa ta yi sannan ta ce. "To koma wace ce ina ruwanki zahra, kiyi abin da zai finshe ki kawai".

Dafe cikinta ta yi jin yadda yake murɗawa saboda yunwa. Daga nesa ta hangi shopping mall. Da sauri ta miƙe tsaye sannan ta ce. "Dole na je na ci wani abun don ba zan zauna da yunwa ba".


Ta faɗa tare da nufar wajan. Nan take ta ga fadawa da securities na fito wa daga cikin wajan. Yayin da ta ga mutanen wajan gaba ɗaya sun ɗuƙa ƙasa.

Shiga cikin wajan ta yi yayin da ta ga kowa gwiwar sa a ƙasa. Sakin baki ta yi tana kallonsu. "To me ya mi waɗan nan mutanen kuma na ga kowa a durƙushe. Koda yake wannan ba damuwar ki ba ce ba". Ta faɗa tana mai ƙara shige wa cikin wajan.

Chan ta hangi ma'aikacin wajan a durƙushe a ƙasa. Ƙarasawa ta yi wajan sannan ta ce. "Ina son a bani snacks ko lemo duk abin da ku ke da shi wanda zai ƙosar da ni".

Alamu mutumin ya yi mata da ta yi shiru. Hangame baki Zahra ta yi ta ce. "Bangane ba, na ce ka zo ka saida min da abu ka ce nay shiru, saboda me?, ko kyauta ku ke bayar da kayan naku ne?". Ta faɗa cikin ɗaga murya.

Daga sama ta ji an ce. "Wane ne yake mana wannan tsawan?". Nan take mutanen wajan suka sha jinin jikin su.

Juyawa ta yi da zimmar zuwa ta ɗauki abin da ranta yake so. Nan take idanuwanta ya sauka kan wani handsome mature guy mai jini a jiƙa.

Kallonta ya yi da idanuwansa masu matuƙar rikitarwa sannan ya ce. "Me ya sa ke baki tsungunna ba bayan kowa dake cikin nan ya durƙusa min, kin san wane ne ni?".

Sakin baki Zahra ta yi tana mai bin shi da kallon rainin wayo. Kallon sama da ƙasa ta yi mishi sannan ta ce. "First of all matsa min daga hanya". Ta faɗa ranta a matuƙar ɓace.

Ƙara tunkaro in da take ya yi sannan ya ce. "Idan na ƙi fa?, kin san waye ni? , ni ɗin yarima ne understood?".

Dariya Zahra ta kwashe da shi sannan ta ce"au haba da gaske?, amma sam baka yi zubin ƴan sarauta ba, ka san da irin su wa ka ke kama a jigawa?, kana kama ne da ƴan daƙo, domin kuwa wannan kayan da ke sanye a jikin ka su ƴan daƙon jigawa suke sawa".
Ta faɗa tana mai kuma fashe wa da dariya a karo na biyu.

A fusa ce. "Yariman ya ce. "Za ki san ni ki ka gaya wa wannan maganar".

Nan take yanayin Zahra suka sauya izuwa ɓacin rai sannan ta dube su baki ɗaya ta ce. "Idan kun isa ku tunkaro in da nake".

**************************
Umar na isa asibiti, likitoci suka saka Amrah kan gado yayin da suka shiga yi mata aiki domin cire bullet ɗin da ke ƙafarta.

Fita ya yi tare da koma wa cikin mota sannan ya nufi hanyar gida. Da mugun gudu yake tuƙa motan yayin da yake ji kamar ya tashi sama domin zuwa in da mahaifinsa yake. Mintuna ƙalilan ya yi masa a gida. Ko gama parking bai yi ba ya fito daga cikin motan tare da nufar hanyar gida. Ƙafar sa na dama ya sa tare da ɓalla ƙofar parlourn.

Nan take mahaifinsa tare da jami'an dake cikin wajan suka miƙe tsaye.

Kallonsu gaba ɗaya Umar ya yi sannan ya ce. "Me ya sa ku ka je ku ka kashe kowane halitta a cikin wannan dajin?, ba na ce bana buƙatar wajan nan ba?, to me ya sa za ku kuma koma wa wajan?, why Abba?".

Ajiyan zuciya Gov. Musa Muhammad ya sauke sannan ya ce. "Nayi hakan ne saboda farin cikin ka son".

Girgiza kai Umar ya yi ya ce. "Farin ciki na?, kayi hakan ne saboda farin cikin ɗanka, baka ji kunyar abin da ya fito daga bakin ka ba, ka tsayar da fari cikin wasu domin samar min da gurɓatacciyar fari ciki mara ɗore wa, kuma a hakan ka ke kiran kanka ɗan siyasa?, shin dama haka shugabanni suke wa waɗan da basu ji ba basu gani ba?".

"To gaba ɗaya ku saurare ni kuji, muddin wannan yarinyar ta mutu ba zan ƙyale kowane mutum daga cikin ku ba hatta kai Abba, kuma sannan wannan farin cikin da ka ke faɗa to za ka rasa shi na har abada ne, domin kuwa ba za ka sake sanya idanuwanka a kaina ba".

"A'a Umar, kada ka yi haka, in sha Allahu babu abin da zai same ta kaji, kada ka nesanta kanka da ni Please".

Murmushi wanda ya fi kuka ciwo Umar ya yi sannan ya ce. "Saboda gudun abin da zai bata min rai hakan ya sa na koma london da zama, kuma duk saboda kai, me ya sa ka ke ƙoƙarin cusa min tsanar ka a cikin zuciyata Abba?. To zan faɗa zan ƙara maimaita wa muddin yarinyar chan ta mutu saikun gane kuranku baki ɗaya. Kuma sannan shi companin ma bana da buƙata, domin bana son koda naira goma daga cikin dukiyar ka, bana so".

Yana kaiwa nan ya fice daga cikin ɗakin.

Kallon jami'an Gov. Musa Muhammad ya yi sannan ya ce. "Shashashan banza ku sani cewa muddin ɗana ya yi nesa da ni saina ga bayan ku, maza ku ɓace min daga gani".

Fita jami'an gaba ɗaya suka yi. Wayarsa ya ji tana ringing.

Ɗaukar wayar ya yi yayin da ya ga private number bayyane kan screen ɗin. Ɗaga kiran ya yi tare da karawa a kunnensa.

Daga ɗayan ɓangare haka ce. "Barkan ka dai govnor Musa Muhammad. Na san za ka yi mamaki to ni ne, ban mutu ba ina raye. Na kira ka ne domin sanar maka da bad news a gare ka, mrs Laila wacce kayi sanadin rugujewar rayuwarta har izuwa yanzu tana raye".

Zumbur gov. Musa Muhammad ya miƙe tsaye. Yayin da zufa ya fara ƙeto masa ta kowane sashi na jikinsa. Duda iskan AC da ke kaɗawa a cikin parlourn hakan bai hana shi yin zufa ba.

Cikin rawar jiki Gov. Musa Muhammad ya ce. "Waye kai?".

Amsa mutumin ya ba shi da cewa. "Ni ne ɗan sanda wanda ku ka saka haka rufe tsawon shekaru, ni ne MK wato Mubarak. Ka ɗauka ban san duk wani shirin ka ba?, na san da cewa ka aiki ɗaya daga cikin masu ta ya ka aikata miyagun laifuka domin ya yi magana da ni a cikin magarƙama domin neman in da yarinyar Mrs Laila take. Amma sai dai kafin ya zo waje na wata ta dakatar da shi. Ka san wace ce?, to ƴar Mrs Laila ce".

Jiki na rawa Gov. Musa Muhammad ya ce. "Tana ina?, ina da buƙatar thumbprint ɗin ta domin buɗe wannan ma'ajiyarta, ka gaya min in da ƴar tata take".

Murmushi MK ya yi sannan ya ce. "Idan na gaya maka, saka wa za ka yi a kamata?, daga nan kuma fa?, ka saka yaranka su kashe ta?, ko da yake safara mata ita ce aikin ka ko?. To ka sani cewa ƙarshen ka ya kusan zuwa, domin kuwa ba yarinya ɗaya Laila Abdullahi ta haifa ba, su uku ne, blue, green and brown, ƴan uku daga gurare da ban- da ban . Su ne za su yi nasarar kawo ƙarshen ka sannan su wanke mahaifiyarsu daga zargin da kotu da jama'ar gari keyi mata. Sannan kuma su ja ka a kan titi, kamar yadda ka sanya ta gudu a kan titi, haka suma yaranta za su saka ka kayi gudu a titi yayin da jama'a za su yi ta jifar ka da duwatsuna, kana ihuuu kana neman taimako, amma babu wanda zai zo domin ya agaza maka. Ka jira ka gani, domin kuwa ranar tana nan zuwa. Saina tabbatar da ka gurbi abin da ka shuka. Ƴar daji, ƴar magarƙama, da kuma ƴar birni. Gaba ɗaya suna nan zuwa domin ɗaukar fansar abin da ka aikata wa mahaifiyarsu, ka jira ka ga sakamakon abin da ka aikata".

💃💃💃💃💃💃💃💃
*HANA WATA GA WAYA*. *WAI SHIN DAMA MRS LAILA BA TA MUTU BA TANA RAYE?, KENEN ƊAN SANDAN DA YA CECI MRS LAILA NA RAYE?, MENE NE HAƊIN MAHAIFIN UMAR DA MRS LAILA?, MUJE DAI ZUWA DOMIN JIN YACCE ZATA KAYA*

*KADA KU MANTA DA LIKING, COMMENTS, DA KUMA SHARING*💃💃🥰🥰🥰😍.

ALƘALAMIN ✍️
A'ISHA M.B 💞💞💞
(ZINARIYA JAJIRTATTU)


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KhkWs8eY42GETnGLk2JC9G



Follow the 💖 A'ISHA M.B✍️ HAUSA NOVELS 📚 WORLD 🌎 📚💗💖 channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaeK0CGLo4hfFWLtYL2g



*🔥KUNDIN CINIKAYYA*🌎 *(Three siblings from different part in the world)*🪐🌎🪐.
Daji 🌲
Magarƙama🏢 da kuma
Birni🏙️

WRITTEN & DIRECTED BY ✍️ A'ISHA M.B 💞💞💞
(Zinariyar🧝♀️Jajirtattu)

https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=159698751105534&mibexti=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️

*DIAMOND 💎 STAR⭐*
*LADIES 🧝♀️🧝🏼♀️🧝♀️*
*(We stand together)*
🤝🤝🤝

بسم الله الرحمن الرحيم
*BISSMILLAHI RAHAMANI RAHIM*
Da sunan Allah mai rahama mai jinƙai!

*🔥KUNDIN CINIKAYYA* *🌎 PAGE 2️⃣1️⃣▶️2️⃣2️⃣
*_________________________________________________*
Nan take cikin Gov. Musa Muhammad ya ɗuri ruwa. Katse wayar ya yi yana mai faɗin.


"Tabbas in dai da gaske tana a raye ba za ta barni na cika ƙudiri na ba, ga shi zaɓe ya kusan gaba to wa, ya zama dole nayi wani abu".


Nan take wani dabara ya faɗo masa. Ɗaukar wayar sa ya yi tare da shiga cikin contact list, nan ya lalubo wata number wanda aka rubuta Aliyu a jiki.


Kiran wayar ya fara yi amma tana ba shi switch off. Wurgar da wayar Gov. Musa Muhammad ya yi ya ce. "Pick up Aliyu! Pick up. I need your help urgently please". Aka yake ta faman magana shi ɗaya.


********
Ɓangaren su Aliyu kuwa, har an shirya musu visa sun shiga jirgi sannan suka kashe wayoyin su. Kowa na cikin jirgin su suke kallo ganin Safeera a goye bayan Mom kamar ƙaramar yarinya.


Ganin cewa kowanen mutum a jirgin su yake kallo ya sa Aliyu faɗin. "We should all concentrate on something necessary please". Ya faɗa tare da ɗaura seat belt. Jin hakan ya sa kowa ya kawar da kansa. Nan take aka sannan cewa kowa ya kasance a shirye sannan kowa ya saka seat belt tare da kashe wayoyi domin jirgi zai tashi.


Saida kowa ya kammala sannan jirgin su ya tashi.



*************
"Wai ke ƴar gidan wace ce?, daga gani ma daga magarƙama ki ka fito domin kuwa wannan kayan ƴan magarƙama ne sanye a jikin ki".


Murmushi Zahra ta yi ta ce. "Wannan ba abin da ya shafe ka ba ne, idan ma hakan ne mene ne naka a ciki, kada ka ce za ka faɗa min magana wanda raina baya so".


Kallonta yariman ya yi ya ce. "Kada ki manta fa Kano ki ka shigo, kano ko da me ka zo an fika. Don aka ki ajiye wannan jiji da kan naki domin kuwa ba za ta yi miki amfani a nan Kano ba".


Kallonsa Zahra ta yi tare da sakin wani miskilin murmushi sannan ta ce. "Au aba da gaske?, kenen dai ko da hauka na zo an fini ko?. Ka sani cewa ni Zahra ce, kuma ba'a haifi wanda zanji tsoron sa ba, bayan ma'halicci na sai fiyayyen halitta. Don aka ka matsa domin bani da lokacin ɓata wa".


Zuwa ya yi daff da ita sannan ya ce. "Idan na ƙi fa?, me za ki yi?".



Kallon cikin idanuwansa Zahra ta yi sannan ta mayar masa da martani da cewa. "zan yi maka sambaɗe-baɗe, zan yi maka dukan da gaba ɗaya masarautar ku sai an gagara gane ka". Ta faɗa tana mai ƙoƙarin wuce wa ta gefen shi.


Babu zato ta ji ya janyo hannunta tare da janyo ta jikinsa.


Zaro idanuwa Zahra ta yi waje, nan take ta kurma ihuuu! tana mai faɗin. "Kai ɗan iska ne?, wato dama kai dan iska ne ko?, ni ƙanwar ka ce da za ka jawo ni jikin ka?, maza ka sake ni kafin nayi maka abin da ba za ka ji dad'i sa ba".


Matse hannunta yarima ya sake yi a karo na biyu sanann ya ce. "Ba zan saki ba".


Duk abin da ke faruwa a gaban idanuwan jama'an da ke wajan.


Nan take fadawa suka shigo tare da ƙwace Zahra daga hannun yarima sannan ɗaya daga cikin su ya ce. "Ranka shi daɗe, mai maryaba ya umarci da mu dawo da kai gida yanzu, ya kamata ka tawo mu bar nan wajan".



Ɗaga musu hannu ya yi ya ce. "Naji shi ke nen". Maida kallonsa ya yi kan Zahra ya ce. "Ke kuma, muddin ki ka bari muka sake haɗuwa saina hukunta ki bisa raina ni da ki ka yi".


Gwalo Zahra ta yi masa ta ce. "Kaje ka ji da abin da ke damun ka malam yarima mai ɗagaggen wando". Ta faɗa tana mai kwashe wa da dariya.


Kare shi fadawan suka dinga yi har suka isa bakin mota. Shiga ciki gaba ɗaya suka yi tare da barin harabar wajan.


Murmushi Zahra ta yi ganin cewar ta yi nasaran zaran wasu kuɗaɗe a aljihun yarima tare da wani ɗan ƙaramin maƙulli. Saka maƙullin ta yi a cikin aljihun ta. Maida kallonta zahra ta yi kan ma'aikata tare da jama'ar wajan sannan ta ce. "To ku ta shi mana, kun wani durƙusa ƙasa kamar masu bara. Shi da mutum ne kamar kowa amma shi ne ku ke ba shi wani girmama wa har kuna durƙusawa ƙasa saboda mutum ɗan adam irin ku, tirr gaskiya kun bani kunya".


Miƙe wa gaba ɗaya suka yi yayin da ɗaya daga cikin ma'aikatan wajan ya kalle ta ya ce. "Yarima Junaid kenen, mutum ne mara tausayi, mara imani. Baya tausayin talakawa sannan baya da mutunta wa, duk in da ya samu ƙusa kai yake ba tare da yana jin tsoron kowa ba, an sha kai ƙarar sa gidan mai martaba sarki. Kuma sarki yana ɗaukar mataki hakan abin da yake yi sai dai kuma muddin ya fito sai ya je har gidan wanda ya kawo ƙararsa sannan ya tozarta shi ya sa shi ya bar gari gaba ɗaya. Sai dai yana da yahya wanda yake matuƙar tsoro, tun da yahyansa ya bar ƙasar nan ya je ƙasar waje aiki shi ke nen ya ƙara iskancin sa a kan na da. Amma da a ce yana nan ba za ka taɓa ganin koda inuwar sa ba".


Girgiza kai Zahra ta yi sannan ta ce. "Ni dai karya sake ya gwada min wanann shashanci don ba zan rabu da shi ba.". Ta faɗa tana mai ɗaukar lemo da biscuit sannan ta miƙa wa ma'aikacin kuɗin da ta zara a aljihun Yarima Junaid. Karɓa ma'aikacin ya yi tare da yi mata godiya.


Fice wa ta yi daga cikin wajan yayin da ta samu bakin hanya ta fara kurɓan lemo. Nan take mutane suka fara binta da kallo.


Ɓangaren asibiti kuwa su DPO na shiga ɗaki suka tarar Zahra ba ta ciki. Nan take suka bazama neman Zahra yayin da suka fara patrol a cikin wajan fita suka yi daga cikin asibitin sannan suka fara bibiyar Zahra.



**********************
*JIGAWA*
Yallaɓai tun ɗazu muke ce mata ta sauko amma ta ƙi sauko wa.


Ajiyan zuciya Umar ya sauke!, sannan ya ce. "Yanzu tana ina?".

Amsa Nurse ɗin ta ba shi da cewa tana cikin room 6. Jin hakan ya sa shi nufar in da ɗakin take. Baiyi wata-wata ba ya shiga cikin ɗakin.


Duba ko ina ya yi ya ga babu Amrah a cikin ɗakin. Hankalin sa ba ƙaramin tashi ya yi ba. Duban nurse ɗin da ke tare da shi ya yi ya ce. "Ina mara lafiyar da na kawo?".


Amsa nurse ɗin ta bashi da cewa. "Ka duba saman silin yallaɓai. Jin hakan ya sa Umar ya maida kallonsa sama.


Abin da ya gani ba ƙaramin firgita shi ya yi ba. Saurin ja da baya ya yi ganin Amrah zaune kan fankan ɗakin ta rirriƙe shi gamm tamkar bishiya.


Maida kallonsa ya yi kan nurse ya ce. "Garin ya ya ku ka bari ta au kan fanka?, ita ɗin fa mara lafiya ce, ya kamata a ce kuna kusa da ita domin ku dinga kula da lafiyar ta".


Kallonsa Nurse ɗin ta yi ta ce. "Munyi hakan yallaɓai, amma kwatsam sai mu ka ga ta firgita ta miƙe tsaye, bamu yi aune ba kawai muka ga ta buga tsalle tare da aye wa saman fanka tamkar buri, Allah ma ya sa babu wuta a jikin fankan da shi ke nen mun rasa ta".


Ajiyan zuciya Umar ya sauke jin abin da nurse ɗin ta ce. Sannan ya dube ta ya ce. "Wace ce special nurse ɗin da aka aje a nan domin ta dinga kula da ita?".


Amsa nurse ɗin ta bashi da cewa. "Nurse Nadiya ce, ita ce take kula da ita kafin ka zo".


"To ki je ki ce mata ta zo ina da buƙatar ganinta". Cewar Umar.


"Shi ke nen". Nurse ɗin ta faɗa tare da fice wa daga cikin ɗakin.




*******
Ɓangaren su Aliyu kuwa, hawanni ƙalilan ya yi musu suka iso Nigeria. Yayin da suka sauka a airport. Fito wa suka yi tare da neman taxi suka hau kai tsaye suka nufi hanyar asibiti.


******
Mitin ƙalilan nurse Nadiya ta isa ɗakin da su Umar suke. Da sallama ta shiga ɗakin Umar ya amsa. Dubansa ta yi ta ce. "Naji an ce kana kira na lafiya dai ko?".


Amsa Umar ya bata da cewa. "Lafiya ƙalau, ina neman taimakon ki ne, yanzu zanje gida ne na ɗauki abun da zai sa ta sauko ƙasa. Ina so ne ki jire min ita dan Allah kinji?, bana son ta fita ko ina please".


Murmushi Nurse Nadiya ta yi ta ce. "Aiki na ne yin hakan, don aka kada ka samu damuwa za ka iya tafiya ni zan zauna na kular maka da ita".


Godiya Umar ya yi mata sannan ya fice daga cikin ɗakin.


Zama nurse Nadiya ta yi tana mai maida kallonta sama sannan ta girgiza kai ta ce. "Allah mai iko, ko ta ya ya na aka yi ta ɗane kan fanka oho. Kina jina ƴar lele, maza sauko ƙasa kinji kyakyawa, zan siya miki alewa".


Ganin Amrah ba ta kula ta ba saima ƙara zama da ta yi kan fankan. Furzar da iska nurse Nadiya ta yi sanann ta ce. "Shi ke nen tun da ba za ki sauko ba". Ta faɗa tare da ɗaukar lemon ɓawo da ke cikin plate ta fara ƙoƙarin kai bakin ta.



Hango lemon ɓawo da Amrah ta yi ya sa ta dira ƙasa tare da wafce lemon, sannan ta fara haɗa wa da bawon jikin sa tana sha.


Zaro idanuwa Nurse Nadiya ta yi ganin irin launin idanuwanta. Cikin ranta ta ce. "Wannan green eyes ne da ita, sakk kalar idanun ɗaya daga cikin yaran Mrs Laila. Allah sarki". Ta faɗa yayin da hawaye suka fara bin kan ƙuncin ta.





*************
Bayan isar Yarima Junaid fada ya shiga cikin part ɗin sa ba tare da ya kula kowa ba. Shiga wani ɓangare ya yi a gidan sannan ta duba aljihun shi domin ya ɗauki maƙulli. Zaro idanuwa ya yi waje gani cewar babu muƙullin ɗakin sa a aljihun shi.


"Ta ya ya hakan za ta faru?, ina maƙullin ya shiga kuma?, na shiga uku!, muddin banga maƙullin nan ba sai Yahya ya hukunta ni, yanzu me zan yi kenen?".


Nan take ya tuna da cewar ɗazu ya riƙe Zahra. "Kodai ita ce ta ɗauka?". Ya tambayi kanshi.


Da sauri ya fita daga cikin part ɗin sa. Tare da fita hanyar waje. nan take ya ci karo da mai martaba.


Sunkuyar da kansa Junaid ya yi sannan ya ce. "Allah ya ƙara maka nisan kwana ranka shi daɗe".

Dubansa mai martaba sarki ya yi sannan ya ce. "Junaid me ya sa ka fita daga cikin masarautar nan bayan na hana ka fita?".


Nan take cikin Junaid ya ɗuri ruwa.



***************
Ɓangaren su Safeera kuwa, shigar da Safeera aka yi cikin room 8, yayin da likitoci suka rufa a kanta. Babu abin da Mom ke yi in banda addu'a yayin da take ta kai kawo a cikin reception ɗin.


Saida suka ɗau lokaci sosai a kanta kafin daga bisani suka samu numfashin ta ya dawo. Nan take suka yi mata allurar bacci.

Fito wa likitocin suka yi suna sharfe zufa. Ganin sun fito ya sa su Mom suka nufi in da suke tare da tambayar ya lafiyar Safeera.


Ɗaya daga cikin doctor's ɗin ne ya dube su ya ce. "Alhamdulillah, mun samu numfashin ta ya dawo yanzu kuma ta samu bacci. Zamu saka ɗaya daga cikin nurse ɗin mu ta je ta duba ta.


"Shi ke nen". Daddy ya furta.


Shiga cikin room ɗin da nurse Nadiya take likitan ya yi sannan ya dube ta ya ce. "Nurse ina son ki je ki dinga kula da wata mara lafiya tana room 8".


Kallonsa Nurse Nadiya ta yi ta ce. "Am sorry to say sir, but ba zan iya rabu wa da wannan mara lafiyar sannan na koma kan wata ba, wannan an bani amanar ta ne. Kuma nayi alƙawarin zan kula da ita, kuma yana da kyau idan mutum ya ɗau alƙawari ya yi ƙoƙarin cika wa. Ka saka wata nurse ɗin ta je ta kula da ita Please sir ". Ta faɗa cikin ƙasa da murya.


Kallonta doctor ɗin ya yi sannan ya ce. "Ina mara lafiyar da ki ke kula da ita take?".


Amsa nurse Nadiya ta bashi da cewa. "gata chan a sama".


Maida kallonsa Doctor ɗin ya yi sama. Zaro idanuwa waje ya yi domin abin da ya gani ya yi matuƙar bashi mamaki. "I can't believe this, how can this be possible". Ya faɗa. Maida kallonsa ya yi kan nurse Nadiya sannan ya ce. "Ina so yanzu kiyi maza-maza kije ki duba patient ɗin ke cikin room 8 yanzu". Ya faɗa hankalin shi a matuƙar tashe.


Kallonsa nurse Nadiya ta yi ta ce. "Lafiya dai Doctor, naga kamar hankalin ka a tashe".


Doctor ɗin ya dube ta ya ce. "Dole hankali na ya kasance a tashe domin naga abin da ya firgita ni, kije ki duba ɗakin ko mara lafiyar mu tana wajan, ni zan wuce office".


"As you wish

Please Login or Register in order to submit comment