Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

lokacin girmansu".


Maida kallonta ta yi kan mijinta sannan ta ce. "Kada ka ce haka mai gida, nayi wa Mrs Laila alƙawarin cewa zan yi iya bakin ƙoƙarina wajan ganin na taimaka wa yarinyar ta sannan na riƙe ta a matsayin ƴar da na haifa. Ita ɗin da yarinya ce kaɗai, bai kamata a ce laifim uwa ya shafi ƴa ba, yanzi idan ka ce na fitar da ita ina ka ke son na kaita?, rayuwarta zai kasance tana shan wahala ne, a yayin da kuma ba bu wanda zai share mata kuka ko ya sata farin ciki domin bata da uwa a kusa da ita. Ba ita kaɗai bace ba su uku ne matan kuma kaga tun basu san kan su ba haka raba su domin tseratar da rayukansu dana mahaifiyar su, sannan kuma domin su san mahimmanci da rayuwa take dashi. Dan Allah kada ka ce A'a kaji na roƙe ka". Ta ƙaradhe maganar tare da fashe wa da kuka.



**"Yanzu mene ne abin yi kenan?, mun bi diddigin mijin nata sannan munje gidan ance ya daɗe da barin ƙasar baki ɗaya, yanzu kenen dole dai a kai yarinyar nan gidan marayu". Cewar DPO wanda ke zaune kan bencin dake cikin magarƙamar a yayin da sauran ƴan prison ɗin suka zagaye jami'an suna kallon jaririya mai brown eyes ɗin da ke kwance kan cinyar ƴar sanda mace, a sa inda ba bu abinda jaririyar keyi sai kuka.



"Haka ne sir, nima abin da nayi tunani kenen, ina ga kawai best solution shi ne a kaita gidan marayu, dan ba lallai a samu wanda zai iya riƙe ta ba a nan dole dai chan za'a kaita domin sai ya fi mata alkhairy". Cewar ɗaya daga cikin warders ɗin.


"Shi kenen tom ku shiyar jami'ai, domin zamu kaita gidan marayun".

Daga sama suka ji an ce. "Ni ce nan nafi cancanta dana riƙe ta". Waigawa gaba ɗaya suka yi rareda zuba wa Hajiya Binta idanuwa.

Cikin rashin fahimta DPO ya ce. "Kamar ya ke ki ka fi cancanta da ki karɓi yarinyar nan?, kenen a tunanin ki mu baki ita ki lalata yarinyar mutane, so ki ke a barta cikin magarƙama ta zama irin ku?, ta ina ma ki ke da halaƙa da ita da har zaki buɗi wannan ƙazamin bakin naki kice ke zaki riƙe ta?".


Ta kowa Hajiya Binta ta fara yi, bata tsagaita da tafiyar ba har sai da ta tabbatar da isa gaban shi sannan ta jefa idanun ta cikin nasa ta ce. "A matsayina ta mai riƙo, kuma sannan nayi wa mahaifiyar ta alƙawarin cewa zan kula mata da ita sannan na bata ingantacciyar rayuwa. Kada kuyi tunanin ko saboda ni mai laifi ce ku gna bi yarinyar, samm abin da ku ke tunani ba haka bane ba. Na riga dana ɗaukar mata alƙawarin cewar ba zan taɓa barin hannun yarinyar ba har izuwa numfashina na ƙarshe sannan ba zan bari ta san mene ne hake nufi da kalmar hawaye ba, domin ba zan taɓa bari ruwa ya fita daga idanuwanta ba saidai idan bana raye, ba zan bari tasha wahala kamar yadda tasha a rayuwarta na yanzu ba. Kunji dan Allah ku bani ita ". Ta faɗa kanta a ɗuƙe.


Kallon juna jami'ai Da DPO suka shiga yi. Gyaran murya DPO ya yi sannan ya ce. "Zamu baki ita ne mundin kotu ta aminta da hakan, amma in har kotu taƙi amincewa to sai dai kiyi haƙuri dan ba bu abin da zamu iya yi a kai".

Miƙe wa tsaye ya yi sannan ya mika wa hajiya Binta jaririyar. Hannu Hajiya Binta ta sa tare da karɓar yarinyar.

Kallonta DPO ya yi sannan ya ce. "Ni zan ɗauki nauyin kula da yarinyar nan, kama daga abinci, tufafi, da dai sauran abubuwan da ba za'a rasa ba. Yanzu dai zan saka wasu daga cikin jami'ai suje su suyo baby food domin ga dukkanin alamu jaririyar nan yunwa take ji, kuma ya kamata a ce shayar da ita a kayi bawai a bata abinci ba, don haka yanzu ki riƙe ta, zanje na samu alƙali da sauran jami'ai indai har yarinyar ta dace ta zauna a nan to za'a barta, idan kuma suka ƙi amincewa ko wani nata yazo to zamu damƙa masa ita ne. Kin amince da hakan?".


Girgiza kai Hajiya Binta ta yi ta ce. "Na amince". Ta faɗa tare da rungume jaririyar kan kirjinta.



*"Mrs Laila ki dakata, jami'ai za su iya ganinki sannan su maida ki magarkama, kuma hukunci da za'a yi miki zai ninka na da ne domin guduwa ki ka yi". Tsayawa Mrs Laila ta yi tana mai fuskantar sa ta ce.


"Dama bayan rataya akwai hukuncin da ya ninka shi?, rataye ni da za'a yi, to faɗa min wane hukunci ne ya ninka rataya?, ni na gwammace su kamani su yi min abin da yafi rataya dana bi ka. Da a ce kasan irin ƙuncin da mutane suka dasa mun a cikin rayuwata da ba zaka faɗi hakan ba. Dan haka ni ko kuma ƴata bamua da buƙatar taimakon ku". Ta faɗa tare da ci-gaba da tafiya.


Ƙaran motocin ƴan sanda be ya karaɗe ilahirin wajan. Jin hakan ya sa ɗan sandan ya fara ƙwalla kiran Mrs Laila tare da cewa. "Ga sunan sun zo kama ki, ki tawo mu gudu kada suyi nasarar ɗauke ki, don idan suka kama ki za su raba ki da ƴarki kuma rabuwa ta har abada".


Jin hakan ya sa Mrs Laila waigawa tana mai fuskantar ɗan sandan. Kafin ta yi wani yinƙuri. Ƴan sandan suka zagaye su da motocin su.


"Sir gata nan mun ganta tare da wani, yanzu haka ƙoƙarin kama su muke".
Cewar ɗaya daga cikin jami'an wanda waya ke riƙe a hannun shi.

Murmushi ya saki ta cikin waya sannan ya ce. "Very good, aikin ku na kyau kuyi maza-maza kumata domin muna da bukatar fingerprint ɗin ta yanzu".
Mutumin dake kan waya ya faɗa.


Ganin suna ƙoƙarin kama su ya sanya ɗan sandan ya yi hanzarin jan hannun Mrs Laila tare da bangaje wasu daga cikin jami'an suka fara gudu. Ganin hakan ya sa jami'ai suka gyara zaman bindigogin su sannan suka fara shooting ɗin bullet.

Da gudu suka tafiya ba bu gaggautawa yayin da jaririyar dake hannun Mrs Laila keta faman kuka. Cikin rashin sa'a ɗaya daga cikin bullet ɗin da jami'an suke harba wa ya samu wajan ƙafar ɗan sandan dake tare da mrs Laila. Nan take ya faɗi ƙasa yayin da jini ya fara fita daga ƙafar. Ƙara mai sauti ya saki!, da sauri Mrs Laila ta koma kan shi tare da ƙoƙarin ɗaga shi. maida kallonsa kan mrs Laila ya yi sannan ya ce mata.


"Maza ki tafi ki tseratar da rayuwarki da kuma ta ƴarki, kada ki tsaya, maza kije".

Cikin kuka Mrs Laila ta ce. "Ba zan iya tafiya na barka a cikin wannan mawuyacin halin ba, idan nayi hakan ban kyauta ba, karka damu kafin su iso zaka tashi". Ta faɗa tana mai fashe wa da kuka.


"Ki tafi ki barni, ni ba zan iya tafiya ba daga nan. Dan haka ki tafi!". Ya faɗa cikin ɗaga tsawa.

Miƙe wa tsaye Mrs Laila ta yi yayin da taga jami'an sun kusan ƙaradowa inda suke. Da sauri ta bar wajan sannan ta ci gaba da gudu.

Ƙarasowa wajan jami'an suka yi yayin da wasu suka tsaya tare da kama ɗan sandan sannan wasu suka bi Mrs Laila a baya.

Tun da ta fara gudu bata san inda take nufa ba, yayin da ƙafafuwanta suka ji rauni saboda bata sanye da takalma.


Haka ta ci gaba da gudu ba tare da ta dakata ba. Yayin da zufa suka bi suka lulluɓe jikinta baki ɗaya. Cikin rashin sa'a kafarta ya bugu wani dutse. Nan take ta faɗi tare da fara gangarawa cikin daji mai cike da bishiyu da namun daji.

Haka ta ci gaba da gangarawa a ƙasa harta faɗa a cikin wani kogi mai wanda ya cika da ruwa. Nutse wa ta yi cikin ruwan yayin da kukan jaririyar ya karaɗe gaba ki ɗaya ilahirin dajin.


Wani itaciya ta hango daga chan nesa da sauri ta fara swimming harta isa ga wannan itaciyar sannan ta saka hannu tare da riƙe itaciyar ƙamm a hannunta sannan ta fara yinƙurin fitowa. A hankali ta fara jan itaciyar yayin da ta fara sama daga cikin ruwan. Cikin rashin sa'a itaciyar ta tsinƙe yayin da mrs Laila ta faɗa a ciki ruwan.

Nan take ruwa ya shige mata baki da hanci, yayin da hakan ya jawo ta kasa numfashi sosai. Nan da nan namomin daji suka fara fitowa. Birririka ne gaba ɗaya suka zagaye kogin.

Da sauri Mrs Laila taja da baya tana mai ambatar sunan Allah. Fuskanta suka yi da cewar tana da buƙatar taimako, hakan ya sa suka fara tsalle kan bishiyu suna ciccire itacuwan dake jikin bishiyoyin sannan suka fara haɗa igiya dashi tamkar mutane. Nan da nan suka ɗaure igiyar jikin wata ƙatotuwar bishiya sannan suka jefa wa Mrs Laila dake jikin ruwa igiyar a yayin da su kuma suka ja da baya.


Riƙe igiyar Mrs Laila ta yi ƙamm a hannunta sannan ta fara jan igiyar tana yin sama. Saida taje sama daga ciki kogin sannan ta ajiye yarinyar tare da yi wa Allah godiya da ceton su da su birrirukan suka yi. Cikin farin ciki ta kalli yarinyar sannan ta ce. "Bayan wuya sai dad'i, Allah ya yi wa rayuwarki albarka. Daga yau sunanki zai kasance Amrah". Ta faɗa tare da rubuta sunan da jinin dake fita daga hannunta a jikin ƙaramin dutsen dake kusa da ita a kogin.


Bayan ta gama rubutawa ta fara ƙoƙarin fitowa daga cikin kogin da igiyar dake hannunta. Nan take taji saukar bindiga a saitin zuciyarta, yayin da jininta ya fesu jikin jaririyar da dutsen. Nan take ta saki igiyar yayin da ruwa ya yi hawon gaba da gangan jikinta.


Nan take birrirukan suka hau jami'ai tare da fara yayyaƙushi su da cizo. Ihuuuuu! Jami'an suka yi yayin da suka fara guduwa tare da barin ilahirin dajin baki ɗaya.

Komawa kan jaririyar suka yi jin yadda take ta faman kuka ya sanya sauran namun jejin fitiwa baki ɗaya.



*"Wallahi Nadiya ba zan bari ki ajiye jaririyar nan a cikin wannan gidan ba, shin kin yi hauka ne da har zaki kawo min wata baren yarinya cikin gidana?, Nadiya ki fita daga idona na rufe, kada ki bari na chanza daga yadda ki ka sanni a da. Idan har kina son zaman lafiya to ki san yadda zaki yi ki fitar da yarinyar nan daga cikin gidan nan".

Hawaye nurse Nadiya taji suna ƙoƙarin sauko mata, saurin share su ta yi sannan ta ce. Shi kenen zan yi kamar yadda ka ce amma ka bari na bata abinci ko cerelak ne saboda na san tana jin yunwa sosai gashi ko shayar da ita ma ba'a yi ba".

"Shi kenen". Mijin ya faɗa tare da shige wa ɗaki. Maida kallonta nurse Nadiya ta yi kan jaririyar ganin yadda take ta faman kuka ya sa ta miƙe tsaye tare da nufar cikin kitchen domin haɗa mata cerelak. Cikin ƙanƙanuwar lokaci ta gama haɗa wa yayin da ta fito da cerelak ɗin cikin ɗan ƙaramin fida da alamu ita ma tana da ƴa ko ɗa. Ajiye fidar ta yi kan table sannan ta ɗauki jaririyar daga kan kujera ita kuma ta zauna, yayin da ta ɗora jaririyar ksn cinyarta sannan ta fara bata cerelak ɗin tana sha.

Saida ta gama tsaff sannan ta kuma yi wa yarinyar wanka a karo na biyu. Yayin da ta shigar da ita ɗaki tare da saka mata kayan jariran da mijinta ya siyo domin yaranta.

Sakawa yarinyar su ta yi yayin da kayan suka yi wa yarinyar kyau tare da karɓar jikinta. Nan da nan bacci suka kwashi yarinyar. Ganin hakan ya sa ta ɗaukar towel tare da goya yarinyar a bayanta sannan ta shiga toilet tare da ɗauro alwala. Bayan ta gama ne ta fito daga toilet ɗin yayin da ta ɗauki dadduma tare da hijabi sannan daga bisani ta tada sallah.

Bayan ta idar da sallan ya sa ta fara azkhar tare da lazumi yayin da ta fara kaiwa Allah kukan ta.

Bayan ta gama ta miƙe tsaye tare da nufar hanyar palour. Zuwanta keda wuya ta tarar da mijinta riƙe da akwati yayin da yake s tsugunne yana ƙoƙarin buɗe akwatin.

Da mamaki ta bishi da kallo sannan ta ce. "Mai gida me kuma zaka yi da akwati a wannan tsakar daren?".

Murmushi ya sakar mata sannan ya ce. "Wannan akwatin ina zuge shi ne domin mu saka yarinyar a ciki sannan mu jefar da ita kan titi kinga duk wanda ya tsince ta ya yi sa'a sai ya riƙe ta".

Saurin ja da baya nurse Nadiya ta yi sannan ta ce. "Wannan ai rashin adalci ne, ta ya ya muna ji muna gani zamu saka marainiyar Allah cikin wannan akwatin, zafi ma kaɗai ya ishe ta. Kuma mu rasa inda zamu ajiye ta sai bakin titi. Mundin ina nan to ba zan taɓa barin hakan ta faru ba".

Miƙe wa mijin nata ya yi sannan ya fara tunkaran inda take. Bai yi wata-wata ba, ya zuba mata lafiyayyun maruka har guda biyu. Dafe ƙuncin ta nurse Nadiya ta yi yayin da jaririyar dake kwance s bayanta ta yi matuƙar razana da jin sautin. Nan take ta fara kuka.

Ɗago idanuwanta Nurse Nadiya ta yi wanda suka ciko da hawaye. Nuna ta mijinta ya yi da ɗan yatsarta sannan ta ce. Mundin baki bi umarni na kinyi abin da nace ba, wallahi sai kin gane cewar Allah ɗaya ne. Domin ni ba zan lamunci naje magarƙama saboda wannan yarinyar da dangi uwa ba ba dangin uba ba. Don haka kiyi min shiru ki miƙo min yarinyar naje na jefa ta a chan bakin titi".

Girgiza kai nurse Nadiya ta yi tare da fara ja da baya ta ce. "Ba zan taɓa miƙa maka wannan yarinyar ba sai dai ka kashe ni idan zaka iya amma ba zan bari ka jefar da yarinyar nan ba, domin ba alƙawarin dana ɗaukar wa mahaifiyar ta ba kenen".

A fusa ce ya yi kanta tare da fuzge zanin da ta goya yarinyar dashi. Nan take jaririyar ta faɗi ƙasa yayin da kanta ya bugu da jikin table dake tsakiyar falon. Nan take yarinyar ta fashe da matsanancin kuka mai sauti.

Ture nurse Nadiya mijin ya yi yayin da ta faɗi ƙasa. Maida kallonsa ya yi kan jaririyar tare da miƙa hannu ya ɗauke ta sannan ya nufi inda akwatin yake da jaririyar.


Saurin riƙe ƙafar sa nurse Nadiya ta yi hawaye na zarya kan ƙuncinta ta ce. "Na roƙe da girman fiyayyen halitta, kada ka jefar da yarinyar nan, kayi tunanin idan da ƴar kace a kayi mata haka zaka ji dad'i, dan Allah ba dan ni ba kodan duban halin maraicin da take ciki na rasa kowa nata ka kyale ta. Dan Allah na roƙe ka, idan kace zaka yi haka, zaka shiga hakkin marainiya, ka taimaka ka ƙyale ta". Ta faɗa tare da fashe wa da kuka.

S hassale ya wafce ƙafarshi daga hannunta ya yi ya sa ƙafarsa ta dama tare da naushin cikin ta. Take nurse Nadiya ta saki wata iriyar razananniyar ƙara, nan take idanuwanta suka fara lumshe wa. Kallon jaririyar dake hannunsa ta yi sannan ta ce. "Allah ga baiwar ka nan, ka kare ta a duk inda take sannan ka shiga cikin alamuranta, ka sanya maƙiyanta suyi danasanin abubuwan da suka aikata mata tare da sauran ƴan uwan ta mata. Ya Allah ka saka yarinyar nan tare da sauran ƴan uwanta sune za su zamo jagororin wannan garin, yayin da maƙiyansu waɗan da suka yi sanadiyar faɗawarsu cikin wannan mummunan yanayin su zo suna duƙa musu". Tana kaiwa nan ta yi shiru alamun ta suma.


Saka yarinyar mijin nurse Nadiya ya yi cikin akwatin yayin da ya nufi hanyar waje da ita. Saka akwatin ya yi a bayan mota yayin da kukan jaririyar kawai ka ke ji domin ta kasa shaƙar iska daga cikin akwatin yayin da idanuwanta waɗan da suke blue suka ƙara rinewa sosai saboda kuka. Buɗe gate ya yi yayin da ya koma jiki motan tare da shiga ciki.

Tada motar ya yi daga bisani ya fita daga cikin gidan.

Saida ya yi tafiya mai nisan gaske yayin da gaba ɗaya mutane sun rurrufe shagunan su saboda dare ya ratsa sosai. Chan ya samu guri a tsakiyar titin da ba bu kowa ko mai wuce wa balle a samu mai ganinsa ya yi parking ɗin motar. Sannan ya fito daga cikin motan tare da buɗe bayan boot. Fito da akwatin ya yi daga cikin motan. Saida ya tabbatar da ba bu mai ganinsa sannan ya ajiye akwatin a tsakiyar hanya inda mutane ke wucewa sannan daga bisani ya bar wajan da sauri tare da shige wa cikin mota ya bar harabar wajan baki daya.





🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
*Ohh waɗan nan ƴan ukun suna ganin rayuwa tun kafin sun san mene ne ciwon kansu, ko yaya zata kasance da jaririya mai blue eyes?, yanzu ɗaya na daji tare da namun jeji, ga kuma ɗaya a magarƙama, yanzu kuma ɗaya na bakin hanya sannan yaya girman su ukun zai kasance?, ko ta ya ya za su hadu da juna nan gaba sannan su san su ɗin su uku ne. Muje dai zuwa domin jin yadda zata kasance*.


COMMENTS & SHARE FISABILULLAHI 🙏🙏🙏
ALKALAMIN ✍️
A'ISHA M.B💞💞💞
(Zinariyar🧝♀️Jajirtattu)

https://whatsapp.com/channel/0029VaeK0CGLo4hfFWLtYL2g

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KhkWs8eY42GETnGLk2JC9G

https://whatsapp.com/channel/0029VaeK0CGLo4hfFWLtYL2g
Ku shiga channel ɗina domin samun sauran littatafai na👆👆👆👆👆

*🔥KUNDIN CINIKAYYA*🌎 *(Three siblings from different part in the world)*🪐🌎🪐.
Daji 🌲
Magarƙama🏢 da kuma
Birni🏙️

WRITTEN & DIRECTED BY ✍️ A'ISHA M.B 💞💞💞
(Zinariyar🧝♀️Jajirtattu)


https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=159698751105534&mibexti=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️

*DIAMOND 💎 STAR⭐*
*LADIES 🧝♀️🧝🏼♀️🧝♀️*
*(We stand together)*
🤝🤝🤝

بسم الله الرحمن الرحيم
*BISSMILLAHI RAHAMANI RAHIM*
Da sunan Allah mai rahama mai jinƙai!

*🔥KUNDIN CINIKAYYA* *🌎 PAGE 9️⃣▶️🔟
*_________________________________________________*
Ba bu abin da jaririyar ke ta faman yi sai kuka, yayin da namun jejin suka bita da kallo. Nan take wasu daga birrirukan suka fara arewa kan bishiya yayin da suka nufi gidan zuma tare da ɗaukar kashin zuma suka nufi inda jaririyar take.


Suna isa suka saka mata a baki, nan take ta fara tsotsan zuman tana yi tana kuka. Ɗaukar ta gwagon biri ya yi tare da ɗora ta kan cinyarsa, a yayin da ya yi mata lulluɓi da ganye sannan ya fara bata zuman da kansa.


Nan da nan gaba ɗaya namun daji suka tsaya tare da zagaye su. Nan take jaririyar ta kalle su tare da sakin murmushi.


**Saka shi suka yi a cikin cell yayin da suka fara jibgarsa ta ko ina, saida suka tabbatar ya jigata sannan suka ƙyalesa. Zama DPO ya yi yana kallonsa ya ce.


"Shin wane ne ya tura ka don ka taimaki Mrs Laila?, ba za ka faɗa ba ko sai an ƙara maka duka?".

Ɗago da rinannu isanuwansa ɗan sandan ya yi sannan ya ce. "Ni ɗin jami'i ne, kuma doka bata yarda jami'i ya daki jami'i ba tare da wani ƙwaƙwaran hujja hakan abin da ya aikata ba, sannan kotu bata baka damar yin hakan ba, mundin kotu ta gano to tabbas sai an cika tarar maƙudan kuɗaɗe sannan kuma a dakatar da kai daga aiki".

Baki sake DPO ke kallon ɗan sandan sannan ya ce. "Ni tun da nake ban taɓa ganinka a cikin rukunin ƴan sanda ba, ƙarya ka ke kai ɗin ba ɗan sanda bane, so dai ka ke ka faɗi abin da za ka kare kanka da shi, to ni kuma ba zan bar hakan ta faru ba, mundin ina nan saina tabbatar da cewa kotu ta hukunta ka bisa ƙwaƙwaran hujjoji da nake dasu a kanka. Don haka ka faɗa min gaskiya domin a sassauta maka hukunci da za'a yanke maka".

Murmushi ɗan sandan ya yi sannan ya ce. "Ko za ka kai gobe kana duka na tare da tambaya na ba zan taɓa faɗa maka ba, sai dai kayi duk abin da ka e ganin za ka yi".


Tashi tsaye DPO ya yi sannan ya ce. "Ohh haka kace?, nayi duk abin da nake ganin zan yi ko?, shi kenen za ka ga aiki da cikawa".

Yana kaiwa nan ya ƙwallah jami'ai kira. Nan da nan jami'ai suka hallara a ciki cell ɗin, yayin da ya ce da ɗaya daga cikin jami'ai da ya ɗauko masa iron. Nan da nan jami'in ya ɗauko masa dutsen guga kamar yadda ya buƙata.


Saka iron ɗin ya yi a jikin socket wanda ke kunne, yayin da ya saka suka tuɓe masa kaya. Ɗaukar iron ɗin ya yi wanda ke fitar da tiriri saboda zafi sannan ya kalli jami'in ya ce.


"Zan ƙara tambayar ka a karo na ƙarshe, idan har baka bani amsar da nake buƙata ba, zan ɗora maka wannan iron ɗin a jikin ka".


Cikin rashin tsoro ko fargaba ɗan sandan ya kalle shi sanann ya ce. "Me ka ke jira?, maza ka aiwatar da abin da ka ke niyar yi, kada kayi tunanin za ka tsorota ni da wannan dutsen guga, idan wahala ne jiki na ya saba da wahala, dana faɗa maka gaskiya na gwammace na fuskanci kowace tsanani ko duka da zata fito daga gare ku. Don haka maza ka fara".


Kallon jami'an DPO ya yi, yayin da ya sa suka kwantar da ɗan sandan. DPO bai yi wata-wata ba ya ɗora iron mai zafi a jikin ɗan sandan.



**"Haba Zainab, kina magana kamar wacce bata san ƙaddara ba, haihuwa fa na Allah ne, na san mundin lokacin mu ya yi za'a ƙwanƙwaso mana ƙofar alkhairy ne. Don haka dan Allah ki daina kuka, likita ya ce idan kina shan maganin ki a kan lokaci za'a samu sauƙi". Dattijon ya faɗa yana mai ci-gaba da tuƙi.


Matar dake kusa da shi ce ta ɗago da jajayen idanuwanta tare da ɗora wa a kansa sannan ta ce. "Mai gida me ka ke so nayi to?, yanzu kimanin shekaru goma kenen muna ta fafutuka wajan neman haihuwa, ta ya ya ka ke tunanin ba zan yi kuka ba?, ƴan uwanka da mahaifiyar ka gaba ɗaya sun sa min ido. Kuma nima ban taɓa ganin laifin su ba, saboda ba bu wata uwa da zata so ta bar duniya ba tare da ta ga jikanta ba?, ni kawai ka barni na ci-gaba da kuka na ko zan ɗan samu sassauci a cikin zuciyata"


Girgiza kai mutumin ya yi sannan ya ce. "Karki damu Zainab, Allah yana sane damu, in sha Allahu next week zamu je America domin a duba ki kinji. Kuma da yardar Allah komai zai yi dai......
Da wani irin sauri yaja wani mugun birki.

Saurin ɗago da kai Zainab ta yi ta ce. "Me ya faru mai gida?".

Fita daga cikin motan mutumin ya yi, yayin da ita ma matar ta fito waje.


Kallon akwatin mutumin ya yi sannan ya ce. "Kinga wani akwati ina tunanin mutum ne ya manta shi s wajan".


Kasa kunne matar ta yi jikin akwatin. Zaro ido waje ta yi sannan ta ce. "Kamar fa naji motsin wani abu a ciki, dan Allah ka zo mu tafi kada wani abu ya cutar damu, yanzu fa dare ya yi sosai ya kamata mu bar nan wajan".


"Ki tsaya Zainab, zanje na ɗauki akwatin kedai ki zuba ido ki gani". Ya faɗa tare da nufar inda akwatin take. Addu'a ya yi yayin da ya yi bissmillahi sannan ya ɗauki akwatin.

Jin da nauyi ya sa ya kuma tabbatar da cewa akwai wani abu s ciki. Zuwa ya yi har gaban motar sa sannan ya ajiye akwatin.

Dafa kafaɗar shi matar ta yi cikin tsoro, sannan ta ce. "Dan Allah kada ka buɗe inajin tsoro".

"Dan Allah Zainab kiyi haƙuri ki barni na buɗe akwatin nan in ba haka ba hankalina ba zai kwanta ba". Ya faɗa yana mai zuge akwatin.

Saidai ya zuge akwatin gaba ki ɗaya sannan ya yi bissmillahi tare da buɗe murfin akwatin. Zaro idanuwa waje gaba ki dayansu suka yi. A yayin da zuciyoyinsu ya fara dukan uku-uku.

Baki na rawa matar ta ce. "Me nake gani haka?, jaririya ce da suka saka ta a akwati, wane mara imanin ne ya aikata miki haka?".

Fiddo jaririyar mutumin ya yi sannan ya

Please Login or Register in order to submit comment