tafi da ke ummi, sai dai hakan ba zai yiwu ba, ki je aji idan an tashi ki jirani mu tafi tare, zamu je gidan mansura, an kawo mata takalma daga Kano, idan da wanda zai yi miki, sai na saya miki na biki"
Ummi ta ce"Ba zaki tafi da ni ba?"
"Ki yi haƙuri ummi, ba zai yiwu ba"
"Kema tafiya zaki yi ki bar ni? Mama ma ta tafi taƙi dawowa"
Na'ima ta yi ajiyar zuciya ta ce "Maza je ki ajinku, ga malam can ya tafi" ta miƙar da ummi tsaye, ummi ta tafi ajinsu.
Naja da take ƙawar na'ima, ta ce "Ke dai ki na son yarinyar nan naima, gashi kin saka mata ran tafiya da ita"
Na'ima da hawaye ya taru a idonta ta ce "Wallahi naja ina tausayin ummi sosai, wallahi da za a bani ita zan ɗauke ta, kakarta matsiyaciyar tsohuwa ce, ai babarta uwar ɗakina ce, mun yi mutunci sosai, baban ummi ya rasu, ta koma garinsu, Kakarta ta ƙwacw ta take azabtar da ita, ko a lahira na ganni gani g matar nan na san ban yi kyakkyawan ƙarshe ba" Duk da a ƙufule Na'ima tayi maganar, bai hana naja dariya ba, saboda maganar ta ta ƙarshe ta bata dariya.
Bayan tashi daga makaranta, tare suka tafi da ummi, hannunta cikin nata suna tafe tana yi wa ummi hira, tana bugun cikinta, dan jin zaman da take yi, sai dai abun babu daɗi mussman da ta gaya mata abun da su auwwalu suka yi mata, da aka yi mata aski.
Na'ima ta ce "Bakomai Allah ya isanki wallahi, duk wanda yayi nagari kansa,. Ki yi ta haƙuri kin ji ummi, duk tsanani duk yunwar da ki ke ji, kar ki bari wani a mazan gidan ku, manya ko yara, su kai ki wani wuri, su saka hannu a jikinki, kin ji ko?" Maimakon ummi ta amsa sai ta ɗaga kai tana kallon na'ima.
Cikin sauri na'ima ta tsaya ta ce "Suna yi miki wasan banza ko?"
Ummi ta girgiza kai ta ce "A'a"
"Ki gaya mini gaskiya, suna taɓa ki ko?"
Ummi ta girgiza kai ta ce "A'a"
"Duk wanda ya saka hannu a cikin jikinki, kar ki yadda kar ki tsaya, ki yi masa ihu ki gudu kin ji ko" ta jinjina mata kai alamar eh.
"Ko bayan na tafi, idan kina jin yunwa, ki je gidanmu wurin babarmu ta baki abinci"
Da haka suka ƙarasa gidan mai takalmi, aka yi sa'a aka samu dai-dai ƙafar ummi.
Na'ima ta ce "Zan ajiye a wurina, ranar bikina in yi miki kwalliya ko?"
Ummi ta ɗaga kai tana murmushi, daga nan suka ƙarasa gida.
Ummi ta shiga gida hannunta riƙe da wani kara tana wasa da shi "Ke!" Idris ya kwaɗa mata kira a wulaƙance.
Ta juyo tana kallon sa.
"Zo ki sayo mini sukari a kanti" yayi maganar yana watso mata kuɗi.
Ta durƙusa ta ɗauka, ta je ta sayo masa, sai dai ta din ga tuna gargaɗin Na'ima na hanata zuwa ɗakin su idris.
Ta nemi wuri ta zauna a ƙofar shiga wurin, ya gaji da jiranta ya fito.
"Dan ubanki ina aiken da na yi miki?"
Da sauri ta miƙe tana nuna masa sukarin.
"Ba zaki shigo ki kawo mini ba saboda baki da mutunci, sai ki nemi wuri ki zauna?"
Tayi shiru tana kallon sa, "Ba zaki kawo mini ba" ya sake yi mata maganar cikin tsawa.
Ta ƙarasa in da yake cikin jin tsoro, sai dai ya ya haɗa da hannunta, ya ja ta cikin ɗakin.
Kuka ta fara yi masa iya ƙarfin ta, yau ya samu damar da rabonsa da ita an daɗe, amma ta nuna masa tayi wayo yanzu, dan haka ta din ga yi masa kuka da ƙarfi, kamar yadda Na'ima ta gama gaya mata ɗazu.
Wawan marin da ya kifa mata ne, ya tafi da ji da ganinta na wani ɗan lokaci, ta dafe kuncinta jikinta na wata irin tsuma, tana karkarwa.
Wata sharɓeɓiyar wuƙa ya nuna mata ya ce "Ki ka cigaba da yi mini kuka, sai na yanka wuyanki" kallonsa take yi, kallo mai cike da tsoro da tsana, ya ajiye wuƙar tare da sanya hannayensa cikin rigarta, rigar da bakomai a ciki sai teɓa dan wannan dai ba nono bane.
Ba ta karaya ba, ta fara kokowar cire hannayensa daga jikinta, tana kuka mai cin rai, iya ƙarfin ta.
Bankaɗo ƙofar ɗakin aka yi, hakan ya razana shi, dan bai yi zaton zuwan wani a dai-dai wannan lokacin ba.
"Idris meye haka?" Hashim yayi maganar yana kallon sa.
"Kamar yaya meye haka, abun da ka gani" a fusace ya ƙarasa ya hankaɗe idiris, ya janye ummi, ya kalli idiris ya ce "Wani irin banza ne kai, ba zaka girma ba a rayuwarka, da me yarinyar nan za ta ji ne?"
Wani uban tsaki idiris yayi, ya ce "Ka daina shiga sabgata ba ruwanka da ni".
"an shiga sabgar taka, wallahi idan baka rabu da yarinyar nan ba, sai na ɗauki mummunan mataki a kan ka"
"To ka ɗauka mana kar ka fasa" ya sake jan tsaki ya fice.
Cikin ƙunar ran yadda ƙaninsa ya raina shi, duk saboda iya na goya masa baya, ya kalli ummi ya share mata hawaye, ya fito da ita daga ɗakin, shaidar yastun idiris kwance a kan baƙar fuskarta, da har idonta yayi taruwar jini.
Ya zubawa ummi ido, da haryanzu jikinta yake tsuma, ga wata irin nannauyar ajiyar zuciya da take yi, har a lokacin a tsaorace take, kuma hawayenta ya ƙi tsayawa.
"Ummi" ya kira sunanta, sai dai bata amsa ba, ta sake fashewa da kuka.
Wani irin tausayinta ya ratsa zuciyarsa, ya din ga share mata hawayen, ya riƙe hannunta suka nufi sashin iya, tana ta dakan fura tana waƙe-waƙe.
Tana ganinsu tare ta hau bala'in tun ɗazu take neman ummi, zata aiketa amma daga zuwa makaranta ta zauna.
Magaji ya ce "Iya"
"Ya aka yi"
"Dan Allah idan ba za a iya riƙon yarinyar nan ba, a mayar wa da uwarta ita, idiris fa na kama yana neman haike mata a ɗakinmu, wace irin rayuwa ce wannan, kalli yadda ya mare ta, haba dan Allah"
Iya ta dafe ƙirji ta ce "Shi idiris ɗin? Ita uban me ya kaita in da yake, me ya kaita ɗakin ku, ai ita ta kai kanta, amma shima zai zo ya same ni, da ni yake zancen. Kai kuma sai ka ce ba ɗan uwanka ba, ka ke ɗaga murya tona masa asiri zaka yi?"
"Iya to zuba masa ido za ayi, idan abun da ba a so ya faru fa?"
"Ba abun da zai faru sai alkhairi, jeka zai zo ya same ni, ke kuma canza kayan ki zo ki kai dusar nan gidan lami, ta bawa dabbobina"
Hashim ya ce "Ni bani dusar na kai, kalli yadda take a razane"
"Ba wani a razane, da a razane take ai da ba ta kai kanta ba, yarinya ƙanƙanuwarta da ita, ta san ta je wurin namiji"
"Haba iya, me ummin ta sani da zaki faɗi wannan mummunar maganar a kanta?"
Iya ta ce "Zaka zo ka kai mini dusar ko ta ɗauka ta kai mini?"
Ya ƙarasa ya ɗauki dusar ya fita, zuciyarsa kamar ta tarwatse, tausayin yarinyar na damunsa sosai da sosai.
Kwanaki biyu tsakanin abun da ya faru, sannan idiris ya shigo sashin Iya.
Iya ta dube shi ta ce "Idris, kashedi zan yi maka a kan yarinyar nan, kar ka kuskura ka sake saka yarinyar nan a loko kana lalubeta, wallahi idan ka sake wani abu ya afku ba zan rufa maka asiri ba, kuma ba zaka janyo mini masifa ba, kai gashi ba sana'a ba balle ace ayi maka aure, in huta. Ina yi maka kashedi, wallahi wani abu ya faru ba zan saurara maka ba, na gaya maka"
Cikin fushi ya ce "Me kuma na yi, magaji ne ya zo ya ce na yi mata wani abu?"
"A'a ni banga magaji ba, bai gaya mini komai ba, fuskanta kawai na yi"
Ficewa yayi ba tare da ya sake magana ba.
Rashin samun biyan buƙatar sa a jikin ummi, ya sanya ya ji ya ƙara tsanar yarinyar, ko son ganinta ba ya yi, ita kanta ummi, har fargaba take yi a aike ta, saboda bayan iya ta yi masa wannan faɗan, sai da ya zane ta, saboda a zaton sa ita ta gaya wa Iya.
Duk wannan cin kashin da ake yi wa yarinyar, daga ƴan uwan ubanta da suke ciki ɗaya, da wanda uba suka haɗa da matayen su, babu wanda ya taɓa shawartar iya a kan sassautawa ummi azabtarwar da ake yi mata, tamkar ƴar tsintuwar da ta faɗo daga sama.
Azumi saura wata biyu, aka yi bikin na'ima, ta yi kuka sosai, ciki har da na rabuwa da ummi, dan har cikin zuciyarta take jin rabuwa da ummi.
Mariya kuwa tun ƴan uwanta na ta tata, suna rarrashin ta, suna bata haƙuri, har suka zubawa sarautar Allah ido suka ƙyaleta, ta riga dai ta kamu da larurar hawan jini, a hankali kuma ciwon damuwa ya fara addabar ta, kullum tana ɗaki, daga bacci, kuka sai shiru.
Yaya ɗan lami ya fara tunanin ko ta koma makaranta, amma yanayin da take ciki, ya tabbatar masa da ko an mayar da ita makarantar ba za ta iya mayar da hankali ba.
Dama labarin haihuwar ta ta ko su iya ba a gayawa ba, dan gaba ɗaya sun fuskanci sabgar Iya babu Allah a cikinta.
Yaya ɗan lami kuwa da suka ga mariya taƙi sakin ranta, ya ƙare mata cin mutunci, tare da tabbatar mata da muddin ta je wurin su Iya babu su babu ita, ƴa ce idan ta girma da kanta za ta neme ta.
Watan azumin ramadana ya kama, wanda hakan ya sake jefa ummi tsaka mai wuya. Ba iya azumi take yi ba, dan haka babu mai kulawa ya bata abinci, haka za ta yi ta gararanba ta wuni a kwance, idan makaranta ta je, tana kallo yara na ciye-ciye, ita ba raɓar su take yi ba ma, balle ta yi musu kwaɗayi, ko kuɗin makaranta ba bata ake yi ba, dan haka bata saba da kashe-kashen kuɗi ba.
Sai an sha ruwa take samu ta ci abinci, sai da hashim ya fuskanci ba ta samun abun da za ta ci da rana, shi ne yake rage mata abincin sa, da safe ya bata, da rana ya sai wani abun ya bata. A haka har aka ƙare azumi.
Da salla kowane ɗa cikin kyakywar shiga mai kyau, ummi kuwa kayan bikin na'ima ta saka, da suka fara koɗewa, da takalmin makarantar da kawunsu ya saya mata, shi ta koma tana sakawa tayi yawo da shi a gari, saboda ko silifas ba ta da shi, wanda naima ta saya mata tuni ya lalace.
Yara na ta shiga su na fita, ummi kuwa na ƙofar ɗakin mamanta, ta zauna tana wasa da duwatsun wurin.
Hashim yayi sallama, ummi ta amsa cikin ƴar siriyar muryarta.
Ya ƙarasa in da take zaune, ya ce "Kin je sallar idi ne?" Ta girgiza kai alamar a'a.
"Me ki ke yi a nan wurin?"
Ta ce "Bakomai"
"Kin ci tuwon salla kuwa?"
Ta ce "A'a iya dai ta ce zata bani"
Ya miƙa mata hannu ya ce "Taso mu je"
Ta saka hannunta a nasa, ya ja ta zuwa sashin mahaifiyar sa.
Babansa ma, da ake cewa baba sagir, yana zaune yana cin abinci.
Ummi ta durƙusa ta gaishe shi, ya amsa mata babu yabo ba fallasa.
Ya ce "Yaya a zubawa ummi abincin salla dan Allah"
Ta ce "Ga maimuna nan, ya zuba mata" ta kalli ummi ta ce "Ke ummi baki da kayan salla ne, ki ka saka wannan koɗaɗɗiyar atamfar?"
Ummi tayi shiru tana kallon ta.
Aka kawo wa ummi abinci, ya saka ta wanke hannunta, ta zauna ta saka tuwon sallar nan a gaba tana ci, tana yi tana kallon yadda yara suka yi kyau sosai a sababbin kaya.
Ta gama ci ta hau tattara musu kwanukan wanke wanke, ta share musu tsakar gida.
Hashim ya dawo sashin, ya tarar da ummi ta haɗa kwanukan wanke-wanke.
"Me kuma zaki yi?"
"Wanke-wanke zan yi".
"Ke yara na can waje suna tsalle-tsalle, suna wasanni, amma ke kina nan ki na haɗa wanke-wanke, ki je ki yi wasanki sa yi wanke-wanken da kan su"
"A'a bani da kayan salla, idan na fita tsokanata za ayi, su ce mini baƙa" tayi maganar tana ƙoƙarin jan kujera ƴar tsuguno tayi wanke-wanken.
Shiru yayi yana kallonta, cikin tausayawa.
Yana zaune yana kallonta, gata yarinya ƙarama amma ta riga ta saba da wahala, yadda yake wanke manyan kwanukan da aka ɓata da miyar abincin salla.
Wata ragowar miya da ta rage, ta zuba mata ruwa zata zubar, idirisa ya kawo kai ta watsa masa a jikinsa.
Ayshercool
08081012143
*CUTARWA!*
Watpad ayshercool7724
Arewabooks ayshercool7724
YouTube https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
What's app 08081012143
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
BRIGHT PENS
(FREE BATCH)
P8
Tuni ummi ta zabura, ta jefar da kwanon hannunta, jikinta ya hau rawa, a fusace ya ƙaraso kan ummi, yayi ball da ita ta hantsila cikin kwanukan da take wankewa.
A cikin azama hashim ya ƙarasa, ya hankaɗe idiris, yana faɗin "Idirs meye haka?"
"Ban gane meye haka ba, ba kaga abun da ta yi mini ba? Dabbar ina ce? Ko makauniya ce?"
"Kai za a cewa dabba, ya za ayi ka shigo babu sallama, ya za ayi ta san da zuwan ka? Idiris zaluncin da ka ke yi wa yarinyar nan yayi yawa fa"
Ummi kuwa karo tayi da ƙafar tukunyar ƙarfe, fiƙarta ɗaya ta karye, nan da nan bakinta ya rine da jini, kuka take yi sosai, saboda ciwon buguwar da tayi, har cikin kanta take jin azabar ciwo.
Babarsu da ta jiyo hayaniya ta fito tana faɗin "Wai lafiya ku ke yi mini hayaniya da tsakar ranar nan?"
Idonta ya sauka a kan ummi, da yawun bakinta ya gauraye da jini".
"Ita kuma wannan meya sameta?"
"Ga wanda ya yi ball da ita cikin kwanuka nan" Hashim yayi maganar cikin takaici, yana nuna idiris.
Nuna wa mahaifiyarsu kayansa yayi, da ummi ta ɓata da miya.
Hashim bai tsaya jin abun da mahaifiyarsu za ta ce ba, ya ja hannun ummi, ya tafi da ita.
Sun sha yawo sosai, kan su samu chemist, kasancewar salla ce, aka bawa ummi magani.
Haka aka gama bikin salla, ummi ba kayan salla sai jinyar baki, da ya sanya ta ciwon kai sosai da sosai.
***
Mariya na zaune a ɗaki tana ninkin kaya, fuskar nan kamar wadda aka yi wa mutuwa, tana jiyo hirar da mama, da jimmai maƙwanciyar su suke yi, wadda ƴar ta aka kai gagarawa, suka haɗu da balarabe suka yi aure.
Tana bawa mama labarin ƴar ta mijinta ya samu sauyin wurin aiki zuwa ikko, sun bar gagarawa.
Mariya ta yi shiru, tana tunanin ya aka yi ba tayi tunanin ta din ga bayar da abu, idan an samu mai zuwa gidan ƴar jummai a kai a bawa ummi ba.
Sai dai ta tuna ba shiru suke yi ba, dan ƴar gidan jimmai, tana ganin tana auren mai kuɗi mijinta ɗan sanda ne, idan suka haɗu da mariya a hanya, kamar ba su san juna ba, saboda yadda take jin kanta.
Tunaninta ne ya katse lokacin da ta jiyo jimmai na cewa "Ai nan asalamiyya ke bani labari, ƴar da mariya ta baro, wahala kawai take sha, ranar ta ganta ko takalmin kirki babu a ƙafarta, na ce ta ɗan din ga taimaka mata, to kin ga ma yanzu sun bar garin, na ce da kun je kun ɗaukko yarinyar nan"
Mama ta ce "Da zai yiwu da anyi hakan ai, ba yadda ba ayi ba su bayar da Yarinyar sun ƙi, shiyasa muka ƙyalesu, ba su da mutunci ko kaɗan, da aka je musu da maganar cikin mariya, cewa suka yi ba nasu bane ba, shiyasa malam ya ce babu mu babu su, a ƙyale su idan yarinyar ta girma ta nememu"
Jimmai ta ce "Ashsha! To Allah ya kyauta".
Mama ta amsa da "Amin"
Mariya ta ajiye ninkin, ta haɗa kai da gwiwa ta din ga kuka.
Bayan tafiyar jimmai, mama ta shiga ɗakin, dan ta san mariya na jin su, ta ce "Mariya na san kin ji abun da jimmai take faɗa, amma haƙuri zaki yi ki kawar da kanki, ki sakawa zuciyarki salama a kan yarinyar nan, idan ba haka ba kuwa ciwo zai cigaba da cin jikinki, kin san dai ki na da hawan jini" shiru mariya ta yi, ta cigaba da rera kuka, mai ƙona zuciya, tana ji a ranta ba zata taɓa yafe wa Iya ba.
An doshi shekaru huɗu, da rasuwar Bashir, ummi ta cigaba da rayuwa ba tare da ta sake sanya idonta ana mahaifiyarta ba, tamkar baiwa a cikin gidan nan haka take rayuwa, babu gata babu kulawa, wahala ta yau daban ta gobe daban, ga Iya ta tsiri yi mata kunu ranar asabar da lahadi ta kai kasuwar garin, ta sayar mata, har ma wasu su yi abun sayarwar su a gidan su haɗa mata.
Babu yadda Hashim bai yi da iya ba, a kan ta daina ɗorawa ummi tallar nan, azabar da take sha tayi yawa, amma iya ta zage shi tsab, ta ce idan ya cigaba da yi mata katsalandan, za ta ci mutuncinsa ta tsine masa.
Babu kunya ba tsoron Allah, Iya ta saka aka ɓalle ƙofar ɗakin mariya, aka kwashe kayanta aka sayar, ta karɓe kuɗin, wai da su zata tarawa ummi kayan ɗaki, ɗakin ya zama wurin tara itace, hatsi da sauran shirgi.
Ummi ta dawo daga makarantar boko, takalminta ya kusa rabewa biyu saboda tsufa ƙasansa kuwa ya huje, malaman su, sun gaji sun ƙyaleta, ƙafarta futu-futu. Ta tarar da Iya a tsaye tana jiran isowarta.
Jiki a sanyaye ta ƙarasa in da Iya take, ta ce "Iya laifi na yi ne?"
"Au tambayata ma ki ke yi, saboda tsabar kin shahara, nan gaba makami zaki fara nuna mini, ki yi mini ƙwace, kuɗina zaki bani da saminu ya zo jiya da daddare, ban gan su ba, kuma daga ni sai ke a ɗakin"
Gaban Ummi ya faɗi, ta girgiza kai ta ce "Wallahi iya ban ɗauka ba, ki sake dubawa".
"Ni ki ke gaya wa na sake dubawa? Ƙarya zan yi miki kenan? Ki zo ki bani kuɗina kan jikinki ya gaya miki"
Ummi kawai tayi shiru tana kallon iya, dan ta rasa me za ta ce mata ma, ta san kawu saminu ya bata kuɗi jiya, amma ba ta san ma a ina ta ajiye su ba.
"Au saboda kin mayar da ni ƴar iska ki ka tsaya kina kallona, ba zaki bani kuɗina ba?"
Ummi ta sunkuyar da kai, dan gaba ɗaya kanta ya kulle.
Iya ta saɓa mayafi ta fice, jiki a sanyaye ummi ta ƙarasa cikin ɗakin iya, ta hau duddubawa, ko za ta ga in da Iya ta ajiye kuɗin.
Maganar Iya ta jiyo da idris ta ce "Ka tambayeta ina ta kai mini kuɗi, ka yi ta dukanta, har sai ta faɗa" kan ummi ta ankara sai ganin idiris ta yi a kan ta, hannunsa riƙe da manyan reshen bishiyar darbejiya.
Kafin ta yi magana, ya shiga shimfiɗa mata tsumagiyar nan a jikinta, gashi ya tare duk wata hanya da zata bi ta fita. Kasancewar dama haushinta yake ji, ya sanya ya zage duk wani ƙarfin sa, ya dinga jibgarta, har da taka ta da ƙafa.
"Fito mini da ita daga ɗaki, ɓarauniyar banza da ta wofi, kuma daga yau kin bar kwanar mini a ɗaki" a ƙasa haka ya din ga jan ummi, ya fito da ita tsakar gida.
"Ga ɗakin uwarta can da ake tara itace yanzu, rufe mini ita a ciki, ko abinci kin daina ci, sai kin bani kuɗina"
Haka kuwa aka yi, idris ya rufe ummi a ɗakin mariya, da yanzu ake tara itace da hatsi a ciki, ya rufe ɗakin bisa umarnin iya.
Ummi ta kwanta a ƙasa, jikinta sai zafi yake yi, hannunta da Idris ya din ga hauri da ƙafarsa, tamkar ba a jikinta yake ba, hannun yayi sanyi ga ciwo yana yi nata.
Sai da ummi ta kwana ta wuni a cikin ɗakin nan, shima magaji ne ya ga baya ganinta, ya matsa da tambaya, su Alhassan suka ce masa ai Iya ta sacewa kuɗi dubu goma sha biyu, ta saka idiris ya zane ta, aka kulle ta a ɗaki.
Hashim ya ji kamar ya ɗora hannu a ka yayi ihu, ya buge kwaɗon, ya tarar da ummi a zaune a takure wuri ɗaya, saman idonta ya kumbura, ko ina jikinta rauni ne. Dogon gashin nan duk ya kwashi datti da karare.
"Ummi" ya kira sunanta, ta ɗago ta kalleshi ta sunkuyar da kai.
"Da gaske kin ɗaukar wa iya kuɗi"
Ta girgiza masa kai, ya ce "Na san ba zaki ɗauka ba ummi, yi haƙuri taso ki fito"
Ta girgiza masa kai ta ce "Dan Allah yaya magaji ka ce Allah ya sa na mutu, bana son zama da iya, dan Allah ka kai ni wurin mama, wallahi zan mutu" tayi maganar tana sheshsheƙar kuka.
Ya kalleta yarinya shakaf, amma tana iƙirarin ta mutu, "Ba zaki mutu ba, wuya bata kisa ummi, tashi kar wani abun ya cije ki" Da ƙyar ya fito da ita daga ɗakin.
Iya kuwa duk ta gama barbaɗawa mutanen gidan ummi ta sace mata kuɗi.
Ko kallonsu Iyan ba ta yi ba, ya nemo abinci ya bata, ya ce tayi wanka.
Tana banɗaki, Hashim ya samu Iya ya ce "Iya dan Allah meyasa ba kya ƙaunar ummi ne?"
"Kamar yaya, in haifi ubanta ka ce bana son ta? Tarbiyya nake bata, uwarta na tsana ne, bana ƙaunar uwarta ne, kuma alamu sun nuna halin uwarta ta yi"
"Ba wannan ba, Iya kin duba ɗakin nan da kyau baki ga kuɗin ba? Ummi bata taɓa yi miki sata ba fa?"
"In ji uban wa? Faɗa ne kawai ba na yi, amma sata kam ba yau ta fara ba, kamar ta sha nonon ɓeranya"
Zai yi magana ummi ta fito daga wankan, tana ɗingisa ƙafarta.
Bai cewa iya komai ba, ya tashi ya bata kujera ta zauna, ya kamo hannunta da ya kumbura, ya fara matsawa a hankali. Nan ta din ga yarfe hannu tana kuka.
Fatar ummi duk wannan wahalar da take sha, jikinta tamkar auduga saboda taushi.
Iya ta watso mata ƙullin kayanta, ta ce sai dai ta koma ɗakin itace ta cigaba da zama.
Babu magiyar da magaji bai yi mata ba, amma ta ce bata san zancen ba.
Da kansa ya share wa ummi ɗakin, ya samo buhu ya shimfiɗa mata, ya kawo tabarma ya shimfiɗa mata, ya din ga rarrashin ta, yana bata haƙuri, ji yake kamar ya zauna ya yi wa ummi kuka.
Iya ta aika a kirawo mata Alhassan zata aike shi, ta ce ya duba ƙasan katifarta ya ɗaukko ɗari biyu, Alhassan ya fito da wata leda a hannunsa ya ce "Iya ba wannan kuɗin ki ke nema ba?"
A razane ta karɓa tana ƙifta masa ido, gaba ɗaya ta manta ina ta ajiye su.
Hashim yayi kamar bai ji me ta ce ba, haka ummi, sarai ummi ta ji Alhassan yana gaya mata kuɗinta, duk wasu kalaman rarrashi, sai da Hashim yayi amfani da su, wurin ba wa ummi haƙuri, saboda ƙarfin hali, har da Murmushin ta, tare da ƙoƙarin nuna bakomai.
Da daddare ya sayo gyaɗa da rake, ya kai wa ummi, duk cikin son ya ƙara rarrashin ta, ya daɗe yana sake kallon ɗakin da zata kwana a ciki, babu ko fitila a ɗakin, kuma ba za a rasa ƙwari masu cizo a ciki ba.
Ya kalli ummi ya ce "In sha Allah zan sayo miki fitila, sai ki din ga haskawa, sannan tun yamma ki din ga karkaɗe ko ina, ki tabattar babu wani abu a ɗakin kan ki kwanta".
"To yaya na gode" ya jinjina mata kai ya fice.
Iya tana kallonsa daga tagar ɗakin ta, yanayin yadda yake shishshigewa ummi, abun ya fara ƙular da ita, dan haka tayi ƙwafa, tare da aniyar ɗaukar mataki a kansa.
Sai dai can ƙasan ranta, ta ji babu daɗi ganin kuɗin da aka yi, gashi ta riga ta saka an zane ummin, an rufeta a ɗaki kwana da wuni, ba tare da hakkinta ba. Haka nan abun ya din ga damunta, da safe ummi ta je har ɗaki ta gaisheta, da uniform za ta tafi makaranta.
"Kin karya ne zaki tafi makaranta?"
Ummi ta ce "A'a"
"Ki je wurin sa'adatu ta zuba miki kunu idan ta dama" ummi ta ɗan yi shiru ta tuna yadda sa'adatun ke haɗe rai idan ta je karɓar kunun.
Ummi ta ce "Na san idan na je ya ƙare"
Iya ta bankaɗa ɗan tofinta, ta ciro naira ɗari, ta ajiye wa ummi ta ce "Gashi nan ki sai waina a hanya ki ci"
Ummi ta kalli kuɗin, tana wani irin murmushi da ita kaɗai ta san ma'anarsa, ta miƙe tsaye idonta fal hawaye ta ce "Ki bar shi iya, idan na dawo
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 54