"Ke, ina kuɗina?"
"Anty ban ɗauka ba" ta faɗa kamar numfashin ta zai ƙwace, saboda fargaba da tashin hankali.
Ashar ɗin da farida ta yi mata cikin tsawa ya sake gigita ta, ta ma rasa me za ta ce.
Shaƙeta rahama ta yi tana zazzaro mata ido ta ce "Zaki faɗa ko sai na kashe ki" girgiza kai kawai ummi take yi.
Farida ta ce "Rahama ƙyaleta, kar ta ja miki bala'i, ta riƙe miki kurwa kamar yadda ta yi mini, wallahi sai ya biyani kuɗina, kuma a wannan karon ko ubanta zai fito daga kabari ta din ga yawo da shi, sai ta bar mini gida ta koma in da ta fito, ba zan zauna da ɓarauniya ba, ga sata ga maita ba zai yiwu ba".
"Antyn dan Muhammadurasulillah ki yi haƙuri, dan Allah kar ki mayar da ni ƙauye, wallahi ban taɓa sata ba, ban san menene maita ba"
"Zaki santa yau, ɗaukko ƙullin kayanki ki wuce, ba zai yiwu ba"
Suka hankaɗo ummi waje, duk attention ɗin mutanen gidan ya dawo kansu, noor da ta fara dariya, tana hango ummi ta hau dariya tana ɗaga mata hannu.
"Lallai farida an haɗaki da masifa, satar kuɗi kuma, wannan wataran sai ta ganki a makara hankalinta zai kwanta" a tsakiyar falon suka zazzage mata kayanta, sai ga dubu ɗaya sabuwa fil wadda kawunta ne ya bata.
Rahama ta ce "Anty ta fito da sauran, suna wurinta wallahi, kalli dubu ɗaya fa a ina ta samu".
Inteesar ta ce "Tashi a caje ki, olay" kausar ta ƙyalƙyale da dariya tana maimaita olay.
Dr. Yayi sallama tare da Abdul ya tarar da ummi a durƙushe, tana ta gursheƙen kuka, noor sai zillo take ummi ta ɗauke ta.
"Lafiya kuwa?"
"Dr. Ni fa na gaji, da abun da yarinyar nan take yi mini, daga bawa rahama ajiyar kuɗi ta kwashe, ta bani kuɗi tun da girma da arziki amma taƙi".
"Shi ne zaki ajiyeta a gaban mutane kina tozarta ta haka? Idan yaranki ne haka zaki yi handling ɗin su? Nawa ne kuɗin?"
Cikin mamaki ta ce "Au haka ma zaka ce?"
"Na ce nawa ne kuɗin?"
"Dubu hamsin" ta bashi amsa tana riƙe ƙugu.
"Sana'ar me ki ke yi da har ki ka tara dubu hamsin? Idan ma akwaita na san a jikina aka sameta, zan biya na kashe maganar nan daga yau, kuma daga yanzu. Ummi ba ɓarauniya ba ce ba halin ta bane". Ta yinƙura za ta sake magana ya tari numfashin ta ta hanyar cewa "Na ce na kashe maganar nan"
Ya dubi ummi ya ce "Ummana, tashi kiyi tafiyarki"
Ba tare da ummi ta yi zuciya ba, ta dubi yarinyar da take ta zillo tana kuka, ta ƙarasa ta ɗauketa, ta nufi ɗaki da ita.
Abdul ya durƙusa yana kwashewa ummi kayanta.
"Farida anya maganin nan yayi kuwa? Kin ga fa abun da yayi miki".
Farida ta kasa magana saboda takaici, yau ta ƙuduri aniyar ummi ta bar mata gida, tun da yau sun yi sababbin ayyuka a gidan.
Ummi kuwa zuruuu tayi da ido, tana kallon noor da ke ta ɓangale baki tana yi mata dariya.
Cikin kuka take yi wa noor surutai, ta ce "Mamana, kin gani ko, tun tafiyarki ban taɓa kwanan farinciki ba, dan Allah mama ki dawo, ko ina ne ki tafi da ni, mama kamar in sha guba in mutu" tayi maganar tana kifa kanta a kan ƴan ƙafafuwan noor, tana wani irin kuka mai sauti"
FOLLOW ME ON WATPAD VIA THIS LINK.
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
Masu neman free books ɗina, da free pages duk akwai a kan watpad account ɗina. Irinsu
Abduljalal
Wata kissar sai mata
Wuta a masaƙa
Cutarwa
Ƙanwar maza
Gaba da gabanta
Aƙidata
Ruɗin ƙuruciya
Zaku iya samun paid pages ɗin a Arewabooks @ayshercool7724. Ko ku tuntuɓe ni kai tsaye ta lambar wayata.
08081012143.
And also don't forget to subscribe my YouTube channel via this link.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ayshercool.
Ayshercool
08081012143
*CUTARWA!"
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
P17
FOLLOW ME ON WATPAD VIA THIS LINK.
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
Masu neman free books ɗina, da free pages duk akwai a kan watpad account ɗina. Irinsu
Abduljalal
Wata kissar sai mata
Wuta a masaƙa
Cutarwa
Ƙanwar maza
Gaba da gabanta
Aƙidata
Ruɗin ƙuruciya
Zaku iya samun paid pages ɗin a Arewabooks @ayshercool7724. Ko ku tuntuɓe ni kai tsaye ta lambar wayata.
08081012143.
And also don't forget to subscribe my YouTube channel via this link.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ayshercool.
PAID ADVERT!.
Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi.
Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku
Oll types of Turaran wuta
Sandal
Halut
Irik
Difur
Gab Gab
Kajiji
Habil
Nabak
Humra
Kulakcha
Dilke da kalta
Kayan
Garan jiki
Muna turara
Kaya
Kujerar garan jiki
Kannada
Madarorin turare masu kamshi
Man garan gashi
Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche
Ku nememu a wan nan no 08065728702 08025453921
*TALLA!TALLA!TALLA!*
*INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*.
*BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU*
*MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA*
BRIGHT PENS A SHIRYE MUKE, WURIN KARƁAR TALLACE TALLACENKU CIKIN FARASHI MAI SAUƘI
P17
Shiru noor tayi, tamkar tana jin abun da ummi take faɗa.
Sosai ummi ke kuka, tamkar za ta shiɗe, duk da ba wannan ne karon farko da aka yi mata ƙazafin sata ba, amma na yau yayi mata zafi da ciwo ba kaɗan ba.
Ji tayi an dafa ta, ta ɗago da sauri dan ba ta ji shigowar mutum ba.
Abdul ta gani a bayanta da kayanta a hannunsa, cikin damuwa ya ce "Dan Allah yaya ummi kiyi haƙuri, na san ba zaki yi sata ba, amma ki yi haƙuri dan Allah ki daina kuka, kar kanki yayi ciwo".
"Yaya Abdul, ya aka yi kai ka yadda ba zan sata ba, amma anty farida da rahama suka ɗora mini sata? Suka ci mutuncina a gaban mutane?" ya durƙusa ya ce "Na san babu daɗi, kiyi haƙuri dai dan Allah"
Ta jinjina masa kai, dan kuwa tana ganin mutuncin Abdul sosai da sosai.
Ya ɗora da cewa "Kar ki ga ɗakinki a haka, mun yi magana da abba ne, ya ce a bari mu tare ya ga ɗakin da maama zata baki, sai ayi miki furnitures, kar a saka miki ta hanaki ɗakin".
Ummi ta girgiza kai ta ce "Dan Allah kar ka bari yayi mini, ya kashe kuɗi da yawa, ni katifata ta isheni, duk kyan furnitures ɗin da za a saka mini, ƙarshe a tsakiyar ƙasa za a binne ni, hakan ma ya isa"
Shiru yayi yana kallon ummi, ta kwanta a kusa da noor, ta sanya hannunta ta riƙe ɗan ƙaramin hannun jaririyar.
Abdul ya tashi ya fita yana waiwayenta, duk abun da aka yi mata, bai sanya tayi zuciya taƙi kula noor ba.
Kasancewar a gajiye take, wani irin nannauyan bacci yayi awon gaba da ita, baccin da rabon da tayi makamancinsa har ta manta.
Kwanki uku da tarewarsu, aka kawo wa ummi ƙatuwar katifa, da wardrobe mai biyu, sai ɗan mudubi da stool.
Ba ƙaramar murna ummi tayi ba, tare da wani farinciki, wai duk wannan nata ne abun mamaki.
Kawu yahaya ya fara deciding zuwa ƙauye, ya gaida Iya, dan haka ya tambayi ummi ko za ta bi shi, ta je a gaggaisa.
Amma tayi shiru ba ta ce komai ba.
"Ummana baki ce komai ba"
"Kawu ka ce ina gaishe su, ba sai na je ba" tayi maganar tana addu'a a zuciyarta, kar ya matsa ya ce sai ya tafi da ita, saboda tana tsoron ya tafi da ita, Iya ta sake cewa ba zata biyo shi ba.
"Ƙauyen ne ba kya son zuwa ko ummana?"
Ummi ta gyaɗa masa kai alamar eh.
Yayi murmushi ya ce "Kwantar da hankalinki kyakywar uwa, abun da ki ke so shi za a yi, zan sanar da su saƙon gaisuwarki, ko ni ba zan so ki je ba, sai kin zama cikakkiyar mutum, da babu wanda zai tursasaki yin abun da ba kya so a rayuwarki".
Kawu yahaya da kansa ya je ƙauye dan ya ɗaukko iya, ta zo ta ga sabon gidansa da jaririya, amma ta ce ba zata ba, saboda matarsa ba ta da mutunci.
Hashim kuwa yana ganin kawu yahaya ummi ya fara tambayarsa.
Ya ce "Ummi na nan lafiya ƙalau Alhamdilillah, tana nan tana karatunta duk ta ce a gaishe ku"
"Allah sarki ummi, muna amsawa".
Iya ta ce "To wai yaushe zaka dawo mini da ita ne?"
Kawu yahaya yayi murmushi ya ce "Ai Ummi sai Allah ya kaimu lokacin aurenta zamu gayyace ku, ba zata sake zuwa gagarawa ba".
A ɗan hasale ta ce "Saboda me?"
"Saboda babu abun da za ta zo tayi muku"
"Kai yahaya bana son sakarci, zumuncin fa? So kake ka raba mini kan iyali?"
Ya girgiza kai ya ce "Ba haka bane ba, na nemi iznin zuwa da ita, ta ce in gaishe ku, saboda makarantar ta"
"Innalillahi wa Innalillahi raziƙuna, ita ummun ce ta faɗi haka? Ta fifita boko a kaina?"
Magaji ya ce "Iya wa Innalillahi raji'un ake cewa ba raziƙuna ba"
"Zan ci uwarka idan na sake magana ka tsoma mini baki, tun kan a haifi uwarka haka ake faɗa, ba damar mutum ya motsa sai ka ce zaka ci gyaransa?"
Ganin Iya na son dasa faifan cin zarafin ummi da iyayenta, ya sanya shi bawa Iya abun da zai bata ya tashi ya ce zai tafi.
Har mota hashim ya raka dr., Ya ce a cewa ummi yana gaisheta, tayi karatu da kyau.
Kawu yahaya yayi alƙawarin isar da saƙonsa ga ummi.
Kasancewar fitar sassafe yayi, yana gama abun da zai yi ya dawo kano, a falo ya yada zango, ummi tuni ta gama girki tayi shirin tafiya islamiyya, ya tsareta a falon yana bata labarin saƙon ƴan gidan na gaisuwa a gareta.
Ganin yadda ummi ta ɗan sake da kawu yahaya, har tana tambayarsa wasu daga mutanen gidan, ya sanya farida yi mata tsawa, ta ce ta tashi ta tafi makaranta.
Abdul ya shigo da noor a hannunsa, ummi tayi saurin karɓarta, ta ɗan ɗagata sama ta ce "Mamana tafi ta kowa" noor kuwa ta buɗe baki tana dariya.
Wata irin zabura farida tayi, tun da ummi take kiran noor da maman wasu lokutan, ba ta taɓa kawo sunan mahaifiyar ummi bane ba sai yanzu, tayi wata irin zabura ta ce "Dr. Sunan matar ƙaninka ka saka wa noor? Babar ummi?".
Kai tsaye ya ce "Yes"
"Saboda me? Meye alaƙata da ita? Ita tayi mini cikin? Ko ita ta haufa mini, wai tsaya meye alaƙarka da ita?".
"Alaƙar da ki ka faɗa mana, na kawo miki amanar yarinya kina ta wulaƙanta ta, gashi tana ta yi miki bauta kamar baiwar da ki ka sayo da kuɗinki, dan haka na saka mata sunan mahaifiyarta, atleast ta samu ƴar uwa, kuma wadda zata din ga kallo tana jin daɗi".
"Yahaya gaba ɗaya na kasa gane kanka, na rasa in da ka dosa a kan yarinyar nan yanzu saboda tsabar wulaƙanci da rashin mutunci, matar da ban sani ba kawai ka saka wa ƴa ta sunanta? Ni wai wace irin alaƙa ce tsakanin ka da ummin nan, ko zagata ka ke yi ne ban sani ba, da a duniya kullum abun da zai faranta mata kawai ka saka a gaba?".
A fusace ya ce "Wace irin maganar banza ce haka farida"
"Ba wani maganar banza, maganar gaskiya dai, to ga noor ɗin nan na bar mata, ta je ta raine ta na bar mata, tun da sunan uwarta ne ba na uwata ba".
Duk da ummi a tsaorace take rungume da noor, jin kawu yahaya suna faɗa, sai dai jin abun da farida ta faɗa, ya sanya cikin wauta da ƙuruciya, ta risuna ta ce "Anty na gode Allah ya saka da alkhairi, Allah ya jiƙan magabata na gode in sha Allah zan kula da ita, a bani kayanta da abincinta na gode" a zaton ta da gaske ta bar mata noor.
Kawu yahaya duk da a fusace yake, sai da yayi dariya, aikuwa cikin ɓacin rai farida tayi kan ummi, ta fizge noor ta ce "Ai ba uwarki ce tayi mini naƙudar ba"
Kawu yahaya ya ce "Ummana, jeki makarantar ki kin ji" ta ɗauki jakarta, ta fita cikin damuwa.
Ummi ba ta cika makara ba, dan haka da wuri ta je makarantar islamiyya.
Zama tayi ita kaɗai, tayi shiru tana tunani, tana son sake yi wa kawu yahaya maganar ya gano in da mamanta take? Sai dai ta kasa tana jin nauyinsa, shi ya ce mata ta bashi lokaci, dan haka ba ta son cigaba da takura masa.
"Ummi" maryam ta kira sunanta.
"Na'am" ta amsa a taƙaice.
"Taso ga mami can ta zo, ita ta kawo mu, ta ce yau dai tana son ta ganki"
Jin mahaifiyar maryam ce ke son ganinta, ya sanya ta tashi da sauri, dan duk in da aka ce wannan babba ne mussaman sha'anin uwa, ummi na bashi girma sosai da sosai.
A ƙofar makaranta suka tarar da mamin a wata zuƙeƙiyar mota, suka ƙarasa gaban motar, ta buɗe ƙofar motar tana murmushi.
Ummi ta durƙusa ƙasa ta ce "Mami ina wuni"
Matar ta ƙarewa ummi kallo, sannan ta yi murmushi dariya na neman suɓuce mata ta ce "Lafiya lau ummi, ya gida ya makaranta?"
"Lafiya ƙalau, Alhamdilillah"
"Yau Allah yayi na ga ummi, kusan kullum sai tayi zancenki a gida"
Ummi tayi murmushi tare da sunkuyar da kanta ƙasa.
"To Ubangiji Allah yayi muku albarka baki ɗaya, ina fatan wataran kuma zaki kawo mini ziyara gida"
Ummi ta ce "To, zan tambaya idan aka bar ni zan zo in sake gaishe ki"
Tayi murmushi ta ce "Masha Allah, ku koma aji to, Allah ya yi albarka"
Ummi ta amsa da "Amin ya Allah na gode, Allah ya tsare hanya"
Maryam ta ce "Bye bye mami, drive well"
Ta amsa mata da "Thank you dear"
A haƙiƙanin gaskiya maryam bata da aiki sai bayar da labarin baƙin ummi, da gidadancinta da rashin wayo, da yadda take kullum cikin kuka, abu kaɗan sai ta hau kuka, da irin yadda malamai kan yi mata ba'a, ko yadda su kan su ɗaliban ke attacking ɗin ta, amma ba ta iya cewa komai.
Babban abun da ya burge mamin da ummi, shi ne nutsuwarta, da kuma gudun duniya da ta gani yau da wanda take jin labari a wurin Maryam.
****
Yau babban burin Idris ya cika, dan kuwa ya hilato hindu shagon wani abokinsa, ya aiwatar da abun da yake muradi a kanta.
Hindu tayi kuka kamar ranta zai fita, sai dai ya zuba mata ido, a tunainsa yanzu hankalinsa zai kwanta, sai dai ina, kasancewa da ummi kawai yake burin yi.
Duk da babu abun da ya shiga tsakaninsa da ummi, yana jin kamar akwai wani abu na musamman da ummi ke da shi, da baya tunanin ya samu a tattare da hindu.
Iya taushin fatar ummi ya isa saka mutum annashuwa, ya daɗe yana jin haushin kansa, da har suka rabu da ummi, bai amfana da ita ba.
Kukan hindu ne ya dawo da shi hayyacin sa, ya din ga lallaɓata yana bata haƙuri, tare da yi mata alƙawarurruka kashi-kashi irin na yaudara.
Tun da farida ta san sunan babar ummi, aka saka mata, ya sanya ta ƙara tsananta ƙiyayyarta ga ummi, azabtarwa iri-iri.
Rayuwa ta cigaba da garawa, sai dai al'amura sun tsananta ga ummi, lokacin da dr. Ya samu canjin wurin aiki, daga Kano zuwa kaduna, wasu lokutan sai yayi wata guda bai zo gida ba, wasu lokutan kuma ya kan zo weekends.
Idan ummi ta karaya ta ji kamar ta mutu ta bar duniya ta huta, sai kuma taga wahalarta ta tashi a banza kenan, ba ta yi acheiving komai a rayuwa ba.
Ko ina babu daɗi, gida azaba da wahala, makarantar boko, ba'a, cin zarafi daga ɗalibai har ma da malamai wasu lokutan, sukan aibata ta ko su muzantata da halittarta.
Sai da ta kai ta kawo, kuɗin makaranta idan dr. Ba ya gari, idan ya turowa farida, ba zata bawa ummi nata ba, har korota ake yi daga makaranta.
A ci mata mutunci, Saboda rashin biyan school fees, sai da ta kai Maryam ta saka babansu biya wa ummi kuɗin makaranta.
Shugaban makarantar ya hana malamai korar ummi, a duk lokacin da ba ta biya kuɗin makaranta ba, sai ya yi wa kawu yahaya waya, sai a lokacin dr. ya san abun da yake faruwa game da kuɗin makarantar ummi da yake bawa farida ba ta bata, daga nan har makarantar boko, direct transfer yake yi musu.
Duk wani aiki ko aike da yakamata namiji yayi ga Abdul, ummi ce za ta yi shi, sayen fetur, cefane, refilling ɗin gas, duk ummi ce ke yin sa, intee da kausar babu abun da suke tsinanawa a gidan nan, ko ɗauke cokali kuwa a kan hanya, saboda azaba har tayar da inji sai da ummi ta iya.
ƙawayensu intee idan suka zo, su yi ta nuna musu ummi a matsayin ƴar aikin gidan su.
Allah ya taimaki ummi, aka sakawa rahama ranar aure, ta din ga murna ta san ko ba komai ta ɗan samu rangwame.
Gefe guda soyayya da shaƙuwa mai ƙarfin gaske ta shiga tsakanin ta da noor, noor komai ummi, kai ka ce ummin ce ta haifeta ba farida ba, dan ita ce ta yaye noor ma.
Ummi na ta aiki a kicin da safe, ta je ɗakinta ta dawo, ta zo ta tarar da ƙwai guda biyu a kan drower kitchen, ita dai ba ta ajiye ƙwai ba, dan haka ta kai hannu ta ɗau ƙwan tana duddubawa, rubutu ne a jiki, an zana wani hatimi da sunan wanda rahama za ta aura, har da zanen kan ƙwarangwal.
"Ke!" Tsawar da farida ta daka mata, ya sanya ta zabura ta saki ƙwan ya faɗi ya fashe, maimakon ruwan ƙwai ya fito, sai jini da wani baƙin abu ya tsiyaye.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wai wace irin karfa ce ke ne?"
Cikin magiya ummi ta din ga bata haƙuri, amma tsabar mugunta matar nan ta ɗauki muciya ta din ga bugawa ummi.
Abdul yana falo yana video game, ya shigo kitchen ɗin da sauri ya tarar da ita tana ta bugawa ummi muciya, tana ƙoƙarin karewa.
"Maama lafiya, meyasa ki ke dukanta da muciya"
"Dalla rabu da ni, na gaji da abubuwan da yarinyar nan take yi mini"
"Amma maama bai kamata ki dake ta da muciya ba, idan kuma ki ka ji mata ciwo fa?"
Cikin ko in kula ta ce "Na daki banza"
Tayi maganar tana sake kwaɗawa ummi muciyar iya ƙarfin ta.
"Maama dan Allah ki daina cin zalin anty ummi, wannan CUTARWA! ce, maybe tsautsayi ne ya sanya ta yi miki laifin"
A fusace ta ce "Ni ka ke gayawa ina cin zalinta?" Tayi maganar tana nufo shi.
Babu tsoro ko fargaba ya ce "Idan ba CUTARWA! ba ce dai-dai ne Allah ya sa a yi wa intee ko kausar abun da ki ke yi mata" sak tayi tana kallon Abdul, ba ta taɓa zaton wannan maganar daga bakinsa ba.
Ta ji jikin ta ya yi sanyi, ta jefar da muciyar ta fice.
Ya girgiza kai shi ma ya fita, dan kunyar ummi ma yake ji, bai san me zai ce mata ba, saboda abun da mahaifiyar su take mata.
BAYAN SHEKARU BIYU
***
Ummi na tsaye a gaban mudubin ɗakinta, tana ta aikin taje gashin ta, ta nemi wuri ta zauna tana kallon kanta a mudubi, gashin duk ya rufeta, ta sunkuya tana cire gashin da yake jikin comb ɗin, ta tare shi a gefe sannan ta nannaɗe gashin kanta ta tufke shi.
Ta sanya doguwar rigar shadda brown, ta kawo dogon hijjabi milk ta saka, ta ɗauki niƙabinta ta sanya.
Ta shashshafa turare, tafin hannunta har ɗaukar ido yake yi, saboda tafin hannunta fari ne ƙal, kamar mata jini a jiki, kuma aka ɗora mata jan lalle a kai.
Ta ɗauki ƴar ƙaramar jakarta ta fito, Abdul ya ce "Inyee ka ga amaren sauka"
Kawu yahaya ya dube ta cikin fara'a ya ce "Congratulations dear, Ubangiji Allah ya sanyawa karatunki albarka, ya ƙara hasken makaranta" ta risuna ta ce "Amin kawu, na gode sosai da sosai"
Ya kalli farida da ƴan matanta da suke ta sabgoginsu, kamar ba su san da zaman su a falon ba ya ce "To mu mun tafi wurin saukar"
"Allah ya tsare" ta faɗa a yatsune.
Kawu yahaya yaji babu daɗi, da yaransa ko mutum ɗaya babu wanda yayi saukar nan, idan baya nan sai sun ga dama suke zuwa makaranta, dan kuwa farida wurin koyon kwalliya ma ta sama musu, maimakon zuwa makarantar.
Ummi gaba ɗaya bakinta yaƙi rufuwa, kaf a ƴan saukar ita ce ƙarama, danma tana da jiki ne, dan ko Maryam shekara biyu ta bata, itakaɗai ce mai shekaru sha shida a cikinsu, maryam na da sha takwas.
Aka gabatar da abubuwan da suka kamata, sannan aka fara raba musu alluna.
Ana bata nata ta nufi rumfar iyaye maza, har da gudu, wurin kawu ta ƙarasa ta durƙusa a gabansa tana cewa "Kawu ka ga"
Ya karɓi allon yana murmushi ya shafa kanta ya ce
"Allah ya sanya albarka ummana"
"Amin kawu na gode" tayi maganar cikin tsantsar farinciki.
Abdul ya ce "Rufe bakin mana"
Ta kalleshi ta ce "Ta ina ka san bakina a buɗe yake a cikin niƙab".
"Yadda ki ke magana ne ya sa na gane"
Ta ce "Bari Yaya Abdul, Alqur'ani da daɗi wallahi".
"Wannan gaskiya ne ummana, kalli baƙin ki na waccan rumfar" ummi ta waiwaya ta ɗaga kai.
Wa zata gani? Yaya Magaji da auwwal, har da su Alhassan.
Maimakon ta yi murna sai gabanta ya faɗi, ta kasa magana, dan fatanta Allah ya sa babu Idris suka zo, dan bata ƙaunar ganinsa.
Sunanta aka din ga kira a speaker, ta zo ta karɓi kyautarta ta ɗaliba mai hazaƙa.
A hankali ta tashi ta nufi in da ake kiranta, tafiya take cikin nutsuwa, shugaban makarantar ya ce "Ƙaramar su babbar su, Salma Muhammad Bashir, kun ganta nan duk ita ce ƙarama a ƴan sauka, amma babu ɗalibar da ta kai ta cin maki lokacin screening"
Ummi ta karɓi kyaututtuka daban-daban, na hazaƙa, ladabi da biyayya da sauransu.
Mamin su maryam ummi ta hango, ta tafi wurin da take, dan jan lallen da aka yi mata ma, gidan su maryam ta je, mamin ce ta biya.
Mamin ta rungume ta tana faɗin "Allah yayi albarka ummi, Allah ya sanya wa karatunku albarka"
Ta risuna ta ce "Amin ya Allah"
Sau ɗaya ya ɗaga kai ya kalleta, ya lura da yadda ko iya haɗa ido da mamin ba ta yi, saboda tsananin tarbiyya da girmama manya, ya so ta ɗaga niƙabin ya ga ainihin fuskarta.
Ya dubi Maryam ya ce "Ke ba uban da aka baki? ba na ƙoƙarin, babu na ɗa'ar" yayi maganar yana sake gyara zaman face mask ɗin sa.
Cike da tsiwa Maryam ta ce "Ina ruwanka da ni? Ba a bani ɗin ba sai ka ƙwace allon saukar ma gaba ɗaya, mami ki rabani da shi wallahi, ai da yake ma ba gayyatarka na yi ba, waye ya ce ka zo?"
"Rufen baki kan na ɓarar da ke a wurin nan"
Ummi dai murmushi kawai take yi, duk ta san yayyen Maryam, wannan ne dai bata sani ba, kuma da alama maryam ɗin ta raina shi.
Aka tashi daga filin sauka, su yaya magaji suka nufo su, "Ummi masha Allah, kin ga yadda ki ka girma?" Magaji Yayi maganar yana kallon ta.
Alhassan ya ce "Ummi har kin yi sauka anya ba zuƙu ba ce ba?".
Ummi ta yi murmushi ta ce "Ai makarantar nan ba a saukar zuƙu"
Suka rankaya zuwa gida, suna komawa gida ta tarar da Iya, sai da ta ɗan ci burki, domin kuwa ba ta zaci Iyan za ta zo ba.
Ta ɓoye mamakinta ta ce "Iya sannu da zuwa, dama zaki zo?"
Ta harari ummi ta ce "Eh, da ki ka ce ke ba zaki zo in da nake ba, kar na yanka ki na cinye ko?"
Ummi ta girgiza kai ta ce "A'a makaranta ce take hanani zuwa, ya gida ya kowa da kowa?".
A ciki Iya ta amsa mata da lafiya lau.
Dai-dai gwargwado kawu ya yi wa ummi ƙoƙari, dan naman kasuwa ya sayo fal, ya bata tayi girkin da zata rarrabawa mutane da ƙawayenta.
Ita ummi ma kasancewar ba ta da ƙawaye, sai maƙwabta ta babbawa, sai su Iya da suka zo.
Sam farida ba ta bi ta kan Iya ba, ummi ce take ta ɗawainiya da su, suna ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 54