ɗin sa duk a wayar, har da saƙo yana tambayarta meyafaru ba ta ɗaga wayarsa?.
Ta kashe wayar gaba ɗaya ta ajiye, tana son fara koyawa kanta janye wa raihan.
Ta yinƙura ta fito daga ɗakinta, amma ta jiyo hayaniyar kawu da farida, kuma duk a kanta, jiki a sanyaye ta koma ɗakinta, da tana da wurin zuwa da zata bar wa farida gidanta, ko kawu ya samu sassauci daga wulaƙancin da farida ke yi masa.
***
Anty Rakiya ta cigaba da matsa lamba, da ƙarfafa mami, a kan lallai a haɗa auren nan na zumunci, ita kuma mami ta cigaba da matsawa raihan, tare da ziga Alhaji a kan lallai a takura raihan yayi aure.
Abun ya fara damun raihan, dan haka ya samu hajiya da maganar, Hajiya ta ce "Babban mutum, menene a ciki dan ka yi aure, gaskiyar maminka ne shi ne cikar kamalarka ai".
"To hajiya sai in yi aure su yaya ba su yi ba, kuma nema ake fa a sakani na auri wadda ba na so, ni bana son yarinyar nan"
"Raihan, dan ka riga su Salim aure babu laifi a ciki, bujirewa umarnin mahaifiyarka ba shi da fa'ida, ko ba ka auri wadda take so ba, ka yi ƙoƙari kai ka kawo musu wadda ka ke so"
Yayi shiru yana nazari, sannan ya kalli hajiya ya ce "Shikenan hajiya na gode sosai da sosai"
Ya tashi ya fita, yana nazarin maganar Hajiya.
Gefe guda kuma yana mamakin kasa samun ummi a waya, har ta what's app, ya fara tunanin ko dai wani abun ya sameta ne.
Yaje wurin aikinsu Ummi, ya tambayi mai yi musu shara, ya ce masa ba ta je ba.
Ita ma ummi a lokacin da take ƙoƙarin ƙauracewa kiran raihan, headmastern su ya kunno kai, sai ya din ga kiranta a waya, wai su gaisa, wannan satin har da bata dubu biyu wai ta hau mota, saboda ɗawainiya da take yi da ɗalibansu.
Hankalinta ba a kan wannan yake ba, kamar ta fi raihan azabtuwa da ƙauracewar da ta yi masa, gashi pressure cikin gidansu, ta ƙara yawa, dan kuwa farida kullum cikin masifa da tashin hankali take a cikin gidan nan.
Babu tsammani dr. Ya samu ummi ya ce mata "Mamana, wani mutum ya zo wurina, ya ce mini yana sonki, kuma babu daɗewa yake son ayi auren, na bashi damar ya zo ku gana, sai dai ba ina nufin lallai sai kin aure shi bane ba, bana son yi masa karambani, ganin babban mutum ne, amma duk yadda ku ka yi sai ki gaya mini"
Ummi ta amsa masa da to ne, amma ta shiga cikin fargaba da zullumi, tare da tunanin, waye wannan? Kai tsaye ya tafi wurin dr.?
Abun yayi ta bata mamaki, sai dai sam ba ta ɗokin abun, domin kuwa bayan saka wayarta a flight mode, sai ta koma tana duba messages ɗin raihan.
Gaba ɗaya ummi ta manta da dr. Ya ce za ta yi baƙo, saƙon raihan na ƙarshe ya tsaye mata a rai.
"Ummi na bincika kina lafiya, amma you are avoiding me, ban sani ba ko nayi miki laifi ne, idan na yi miki laifi ne dan Allah ki yi haƙuri ki yafe mini, ina cikin damuwa sosai wallaahi, ban zaci shaƙuwarmu ta kai in shiga damuwa haka ba, dan Allah ki yi mini reply ummi, zan tafi italy gobe in Allah ya kaimu da asuba, dan Allah ki yi mini magana"
Ajiye wayar ummi tayi, idonta na cika da hawaye, "Ban kyauta maka ba raihan, amma yanzu ko na yi maka bayani ba zaka gane ba, buyagi zaka yi mini" tayi maganar a hankali, tana sake kallon wayarta.
"Yaya ummi, wai baƙonki ya zo" noor tayi maganar ba tare da ko sallama ta yi ba.
Ummi ta jinjina mata kai, tare da jin matsananciyar faɗuwar gaba, dan wannan ne karon farko da zata tsaya tayi zance da wani, da sunan yana sonta, gashi alamu sun nuna da gaske yake, tunda ya biyo ta wurin dr., Duk da abun da take ta addu'a a kai kenan, idan tana da rabon aure, Allah ya kawo mata miji nagari, sai dai gaba ɗaya ba ta murna da lamarin a yanzu, kuma ta rasa dalili.
Sai dai ta tsinke da al'amarin, ganin headmastern su a gareji, wai shi ya zo wurinta, kenan shi ne baƙon?
Suka gaisa suka zauna a kan fararen kujeru, tana bin sa da ido, dan ba ta gama yadda da shine baƙon ba.
Yayi gyaran murya ya ce "Wato ummi na san zaki yi mamakin ganina, da dalilin zuwana, duk da nasan mahaifinki yayi miki bayani.
To ni dai ummi ba wani abu ne ya kawo ni wurinki ba face alkhairi, na daɗe ina sonki, tun ranar da na ga kin cire hijjabi kina alwala, watannin baya baki ganni ba ke amma, to a lokacin gidana mata huɗu ne, amma yanzu Alhamdilillah mun rabu da ta ukun, dan haka akwai gurbin mutum ɗaya, ya sanya na ce tun da naga alamar babu tsayayye bari ni na tsaya, mu dai-daita mu rufawa juna asiri, dan yanzu kin san maza tsada muke yi" yayi maganar yana murmushi yana kallonta.
Ummi dai sama-sama take jin sa, ƙasan zuciyarta lissafi take yi, ta yi wa raihan reply ko ta ƙyale shi, ta san duk daɗewa idan ya dawo sai ya nemeta.
Dan haka sama-sama take jin maganganun headmastern.
"Ba zan takuraki yanzu ba, amma dai ki yi tunani, dan kuwa da wuri nake son ayi auren nan, bana son ɓata lokaci, kuma za ayi abu ne dai-dai talaka da tsarin addini, ba wani ɓarnar bidi'a, in kawo abun da Allah ya yassare ayi"
Ummi ta yi ajiyar zuciya ta ce "To malam, idan na yi tunanin sai mu yi magana"
Ya ce "Yauwwa ummi, Allah ya wuce mana gaba " ta amsa da Amin, ya tashi ya tafi, ita kuma ta dasa sabon zama tana nazari da tunani.
Sai da ta ji sauron wurin na neman halakata, sannan ta tashi ta koma cikin gida.
Kitchen ta nufa ta zubo abinci, zata fito farida ta tare ta ta ce "Ubanki ne ya kawo abincin?" Ummi ta girgiza kai.
"To ajiye ki fita, mayya mara zuciya, ai si ki je wurin waɗanda ki ke bi ku watse su saya miki kaya, su saya miki abincin, wallahi takura da masifa yanzu ki ka fara ganinta, sai ranar da ki ka bar mini gida, ko ki yi aure, ko ki koma in da ki ka fito ko ki bi duniya "
Salin alin ummi ta ajiye abinci, ta bar kitchen ɗin.
'Tabbas! Tura ta kai bango, yakamata na yi wani abu na matsa daga gidan nan, na fuskanci ƙalubalen da ke gaba, zaman gidan nan yana neman fin ƙarfina" tayi maganar a zuciyarta.
Abokin kukan nata ga ƙoƙarin da take yi a kansa, ta nesanta kanta da shi.
Abubuwa suka cigaba da ɗaukar zafi, dan da kawu zai koma aiki, sai da ya gindawa farida sharaɗi, a kan muddin ya dawo ya tarar ummi ba ta nan, sai ya saketa.
Farida har mamaki take yi, yanzu asirin ya daina kama dr. Al'amari in dai ya shafi ummi, ba ya saurarawa.
Ummi ta din ga sallar dare tana kai wa Allah kukanta, amma a ƙasan zuciyarta ta ji ta amince da auren headmaster, no matter what wahala ba yanzu ta fara shigar ta ba, tarwatsewar gidan dr., Da kuma alƙarsu da raihan su ne manyan barazanar ta a yanzu, idan ta yi aure ta san ta rage kaso mafi yawa daga matsalolinta.
Raihan ya sha mamakin burus da ummi ta yi da shi, ba dan ba ta ganin saƙonninsa ba.
Gajeren saƙo ta tura masa "Baka yi mini komai ba raihan, tarayyarmu na barazana ga kwanciyar hankalina, da jefa zargi a zuciyar mariƙana, ka yi haƙuri da hukuncin da na yanke"
Message ɗin ya nuna blue tick, alamar ya ga saƙon amma yaƙi reply, tun ummi na jiran yayi reply, har ta sare, sai kuma abun ya dame ta ta rasa sukuni, ga headmaster ya matsa mata kamar maye, ita har mamaki take yi, duk lokacin da suka shafe, bai ji yana son ta ba, sai watannin baya da ya ganta tana alwala, mata huɗu sun rabu da ɗaya zai aureta, kodayeke wannan duk bai dameta ba, wutar gabanta take ƙoƙarin kashewa, dan haka ta ce masa ta amince.
Tamkar ya goya ummi, saboda murna da nishaɗi, ta amince da aurensa, ya ce mata zai zo wurin kawu su yi maganar kawo kuɗin aure, ta ce masa baya nan sai ya dawo.
Ya fara yi wa ummi huɗubar shi talaka ne, dan haka kuɗin sadaki, da na lefe da na aure, zai bayar dubu ɗari, dan Allah ta ce ta yarda a haka, ko da babanta zai ce ba yadda ba.
Ummi ta amsa masa da to, dan ba ta da burin da ya wuce ta ɗaga daga gidan nan, ita ma tana burin ta ganta a ɗakinta, ko ta samu sauƙin gorin da take sha.
Kullum cikin duba wayarta take, taga raihan yayi mata reply na message ɗin da tayi masa, amma yaƙi yin reply, wasu lokutan tana kallon sa online, amma bai yi responding ba.
Tunani ta din ga yi hanyar da ta bi tana neman maraba da raihan tayi musu tsauri daga ita har shi, amma ta san idan tayi masa bayani, ba zai taɓa tsayawa ya fuskanceta ba, dan akwai shi da kafiya wasu lokutan.
Noor tana ta gyara wa ummi kan mudubin ta, tana jera mata mayukanta tana faɗin "Ai yaya ummi ba sai kin cigaba da ɓoyewa ba, kawai ki jera abun ki, dama na san dr. Ba zai yi miki faɗa ba" ta lura hankalin ummi baya kanta, dan haka ta ce "Wai yaya ummi me ki ke jira a wayar ne, ko salary ki ke jira ne?"
"Noor raihan ya daina kulani"
Noor ta ɗan waro ido ta ce "Faɗa ku ka yi? Innalillahi yaya raihan ɗin namu?"
Ummi ta ce "Ni na fara daina kula shi, noor bana son zargi ya shiga ran kawu a kaina ne, kuma aure nake son yi, bana son na yi aure mu kasa rabuwa".
"To yaushe zaki auren?"
"Malam ya ce idan kawu ya dawo zai zo su yi magana ya kawo kuɗin aure, sonake ya kawo kan raihan ya dawo"
Noor ta kwaɓe bakk ta ce "Wai wani malam, ni fa bana son malam ɗin nan, Astagfirullah bari dai na yi shiru, amma dan Allah kar ki auri wani malam, ki auri raihan mana" ummi ta zare ido ta ce "Ke ƙanina ne fa, kamar ɗan uwa yake a wurina, malam ya ce zai bayar da dubu ɗari kuɗin komai da komai, kar a wuce wata uku, amma ban san yadda za su yi da kawu ba".
Kamar shashasha noor ta kalli ummi ta ce "Wai ke yaya ummi, ni na rasa me zance, shikenan ke ba za a kawo miki lefe ba? Matansa fa uku, gashi tsoho, to kina son sa ne?"
"Mama ƙyaleni, surutun nan naki ma ya fara damuna".
"Hmm, Yaya raihan yayi fushi da ke fa, har makarantarmu ya je, bayan mun dawo daga gagarawa, ya tambayeni idan tare muka dawo kuma lafiyarki ƙalau, na ce masa eh. Ya jinjina kai ya tafi"
Cikin tsananin mamaki ta ce "Ya aka yi ya san makarantar ku har ya je? Sau biyu fa kawai kuka taɓa haɗuwa, Kin ga dalilin da yasa nake son mu rabu, raihan ya iya rigima fa"
Noor ta ce "Eh amma yana da kirki sosai ai, tun da ya taɓa bani kuɗi, wannan malam ɗin gaskiya talaka ne, ko kuma wayo, dubu ɗari fa ba ta da yawa sosai, shikenan ke ba za a kawo miki akwatuna masu yawa ba, kamar na inteesar"
Ummi kawai ta kwana ta yi wa noor shiru.
Ta cigaba da kallon wayar, a ranta ta ce 'Haba babban mutum, manyan ba sa haka fa' ta cigaba da duba chats ɗin su na baya.
Headmaster ya kira dr. A waya, yana tambayarsa yaushe zai dawo, so yake da ya dawo, ya kawo kuɗin, dr. Ya ce masa baya son gaggawa ya jira shi tukuna.
Wasa-wasa kusan sati uku kenan, raihan da ummi ba su yi magana ba, ba kuma dan hakan yana yi wa kowanensu daɗi ba.
Ummi ta kira direban da yake aikowa ya karɓar masa abinci, ta tambaye shi ko raihan ya dawo, ya ce mata a'a.
Yanayin sintiri da nacin da headmaster yake yi mata, abun har mamaki yake bata, kamar ya ɗauketa ya kaita gidansa ya ajiye.
In da Allah ya rufawa ummi asiri, aikin nan nata, tana ɗan samun salary, idan tayi girki ta gama farida sai ta hanata abinci, tayi ta janyo mata masifa da bala'i da miyagun alkaba'i, tare da fatan ta sha wahala a rayuwa kamar yadda ta wahalar da ita a gidan aurenta.
Ummi a ranta ta ce 'Wahala waccece ban sha ta ba, kuma ban cutar da ke ba a zamanmu ke ki ka cutar da ni!"
Tun da dr. Ya zo gida, headmaster yake sintiri, a kan zai kawo kuɗin, dr. Ya ce ya ɗan ba shi lokaci tukuna.
Hatta wurin aiki manager ya lura yanayin ummi ya sauya, kamar wani abu na damunta, amma dai yayi shiru bai ce mata komai ba.
Dr. Ya kira ummi ya tambayeta ko tana son malam Isa, ummi ta ce eh.
"Ummi, kar takura ko damuwa ta sanya ki kai kanki ga halaka, rauwar aure ba rayuwar gida ba ce da babu nauyin kowa a kanki, kar ki kai kanki in da zaki yi dana sani, mutumin nan babban mutum ne, kar ki zo daga baya azo a samu matsala, ki dai je ki sake tunani" ummi ta amsa masa da to, ba dan ta so ba, ita fatanta kawai dr. Ya amince.
Kasancewar yau babu coustomers, ummi ta bar reception ta koma in da take zuwa ta yi salla ta ci abinci ta kwanta, tana cigaba da duba chat's ɗin su da raihan.
Ƙamshin turaren raihan ne ya fara yi mata sallama, ta zaci hallucinating kawai take yi, sai dai ba ta gama tunanin ba, ta ganshi a tsaye a kanta.
A zabure ta tashi zaune, tana bin sa da kallo.
Wani irin kwarjini ta gani a tare da shi, wanda ba ta taɓa gani a tare da shi ba, fuskarsa a matuƙar haɗe, kamar ba ya dariya.
"Raihan" ta kira sunansa a hankali.
Ya nemi wuri ya zauna, ya ƙura mata ido sannan ya ce "Salma wannan shi ne tukuicina daga gareki ko? Ko rabuwa ki ke son mu yi, yanke alaƙa da ni kai tsaye ba tare da wani dalili ba kina ganin shi ne mafita? Bafa a rana ɗaya muka gina alaƙar nan ba, ummi dama zaki iya wulaƙanta ɗan Adam har haka kamar yadda ki ka yi mini?"
Cikin rauni ta ce "A'a raihan, ba haka bane ba, dan Allah ka fahimce ni" nan ta gaya masa bayan dawowarta gida abun da ya faru, yadda farida tayi mata bincike ta nuna wa dr.
"Raihan wulaƙanci ba halina bane ba, ina ma naga ƙarfin gwiwar da zan iya wulaƙanta wani? Raihan ba kowa zan yi wa bayanin alaƙarmu ya kalli abun da idon basira alaƙar ta yi masa ma'ana ba, bana son zargi ya shiga ran dr. Duk da ya goya mini baya, amma ban san ta yaya zan wanke kaina ba, kafi ƙarfin wulaƙanci a wurina raihan, ban yi haka dan wulaƙanta ka ba"
Ya girgiza kai ya ce "Ban yadda ba ummi, duk a ƙoƙarinki na guje mini, ki ke shirin kai kan ki ga halaka, zaki auri shugaban makarantar ku ko? Malam isa"
A zabure ta kalli raihan, ya aka yi ya san wannan maganar?
"Mamaki ki ke yi ma? Ni zaki juya baya rana tsaka ummi, har ki yi shirin aure ban sani ba? Ina bibiyar rahuwarki fiye da yadda ki ke tunani, gani nake ko yaya na kawar da kai a kanki wani abu zai faru da ke, rabuwa da ni ba mafita bane"
"Raihan haka ne kawai mafita a wurina, matar gidanmu ta matsa mini da yawa, ƙalubale ko ta ko ina, ba zaka gane a mawuyacin halin da nake ba...
Ya katseta da cewa "Kuma sai ki kai kan ki ga halaka, mutumin da ya saki mata sun kai biyar, ya saki wata ke ma zai aureki ya biya buƙatar sa ya sake ki, ba irin wannan mijin nake roƙa miki ba"
Ta ce "Raihan alkhairi nake fata"
"Yi mini shiru" yayi maganar a hasale, galala take bin sa da kallo.
"Yakamata mu daina yaudarar junanmu, daga ni har ke, idan saboda ki rabu da ni ne, ki ke ƙoƙarin yin wannan auren, kin riga kin makara, ba za ayi shi ba. Ban damu da koma me wani zai yi zargi ba, ba zaki iya rabuwa da ni ba, kin riga kin makara. Ke banda rashin lissafi ma me zaki yi da wannan dattijon, shekarunsa nawa ke naki nawa? Me zai tsinana miki, ko ke ba kya wannan lissafin, ko an ce miki ci da sha ne kawai aure? Kodayeke ai kin san me nake nufi" kai ka ce gunki haka ummi ta koma, yau raihan ya zama wani abu na daban.
"Salma, ki yi haƙuri ba zan iya barin wani ya aureki ba, saboda ni nake sonki"
Tamkar ya jona mata shocking ta zabura ta ja da baya tana kallon fuskar raihan, yadda farar fatarsa ta koma ja, da irin kallon da yake yi mata, ya sanya ta tabattar da ba ƙarya yake yi ba.
"Ummi ki yi tunani, wace irin alaƙa ce a tsakani na da ke?"
Kamar zata fashe da kuka ta ce "Raihan, ni fa ƙanina na ɗauke ka, ƙanin ƙawata ce kai, mutum ne kai mai muhimmanci ne a gareni, amma ba irin wannan alaƙar ba".
Tashi yayi ya taka, ya je gabanta ya durƙusa, ya ɗan tsura mata ido ya ce "Bamu haɗa alaƙa da ke ba, ta uwa ko ta uba ba, kuma tarayyar mu da muka yi da ke ta wuce yadda ki ke tunani, ta kuma wuce gurbin da ki ka ajiyeta. Salma son juna muke yi. Lokacin nan da muka ɗauka ba ma tare, ki ka yanke alaƙarmu, kin sani a mummunan yanayin da yakamata ki ce na yafe miki, na shiga matsananciyar damuwa"
Da sauri ta girgiza kai ta ce "A'a Raihan, ina ganin mutuncinka, babu wannan maganar a tsakanin mu dan Allah a barta, kar ka sake yin ta bana so"
Ya shafi gefen fuskarsa, yana jin zafi a zuciyarsa, ya kalli ummi ya ce "Na gode Salma" ya tashi ya fice daga wurin.
Ummi ta takure tana ajiyar zuciya.
"Salma, ki yi haƙuri ba zan iya barin wani ya aureki ba, saboda ni nake sonki" shi ne abun da ya din ga yi mata kai kawo a zuciyarta.
Manager ne ya biyota yana tambayarta me ta yi wa ƙaninsa ya ga ya fita rai a ɓace, ummi ta ce masa babu komai.
Kwanaki biyu a tsakani, headmaster ya daina kiranta a waya gaba ɗaya, messages ɗin ma da yake tura mata ya daina.
Sai dai ko a jikinta, tunanin ya raihan yake yafi tsaya mata a rai.
Gashi ya ce halin da ta saka shi a ciki, yakamata ta nemi yafiyarsa.
Ganin ba ta da mafita, ya sanya ta neme shi a waya, amma shiru ba ya ɗagawa.
Tana cikin jimamin lamarin, dr. Yayi sallama a ƙofar ɗakinta, ta amsa sannan ya shiga.
Ya nemi wuri ya tsaya, sannan ya dube ta ya ce "Ummi, baya fa ta haihu, mutumin nan malam Isa ya kirani a waya, ya ce mini ya janye maganar aurenku, kuma hakan yayi mini dai-dai, dan kuwa ko bai janye ba, ba zan bashi aurenki ba, binciken da na yi a kansa bai yi mini daɗi ba, dan haka ki cigaba da addu'a, Allah ya kawo mafi alkhairi" har kawu yahaya ya fita, ummi na tunanin me raihan ya yi wa headmaster ya fasa aurenta, kenan da gaske yake yi sonta yake, ba zai bari kowa ya aureta ba!?
Gabanta ya faɗi tare da tabattarwa da kanta ba ta ga ta zama ba, idan ba raihan da rigima ba, ai ya san zaren ba kalar yadin bane ba, ina shi ina ita? Kyakkyawan matashi kamarsa me zai yi da ita, ga uwa uba ta girme shi, dole ta lallaɓa shi su rabu lafiya.
Sanin baya ɗaga wayarta, ya sanya washegari da ta shirya, ta tafi office ɗin su raihan.
Sai dai ba a bari ta shiga ba, sakataren shi yayi mata sannu da zuwa, tare da tambayarta raihan ya san da zuwanta?.
Ta ce "A'a, amma ace masa ummi ce"
Sakataren ya tashi ya shiga cikin office ɗin raihan, ya dawo ya ce mata ta jira, zai neme ta.
A ƙalla ta shafe awanni biyu tana jira, bai fito ba, ba kuma dan yana abun da ya fi ganinta muhimmanci ba, sai dan ya sanya ta yarda da alaƙarsu soyayya ce.
Yana office ɗin sa, ya kira waya ya saka aka kai mata ruwa da lemo da snacks.
Ya koma ta window ya tsaya yana kallonta in da take zaune, fuskarta duk ta faɗa, tana ta wasa da yatsun hannunta.
Ji yayi ya kasa jurewa, ya nufi ƙofa ya fita, tana hango shi ta tashi ta tsaye, sakataren ya fara yi masa bayanin ita ce baƙuwar da take son ganinsa, ta daɗe a wurin. Buɗar bakin raihan sai cewa ya yi ta rubuta a rubuce tana son ganinsa, idan yayi approving ya bata date da time ya fice ya bar ummi.
Ayshercool.
08081012143
[4/20, 7:21 PM] Authoresses: *CUTARWA*
*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
FOLLOW AND SHARE
AYSHERCOOL
08081012143
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
31
Har raihan ya bar harabar gidan bayansa ummi take kallo, ko sau ɗaya bai waiwayo ba, ita kuma ba ta daina zubar da hawaye ba, gani take kamar kallon ƙarshe take yi masa, ba zai sake dawowa rayuwarta da sunan yana son ta ba.
Ta tashi jiki babu ƙwari, ta tafi ɗakinta, ta rufe ɗakin ta saka sakata, saboda kar noor ta zo ta isheta da surutu.
Ta zauna ta din ga kuka, ta ma rasa kukan me take yi.
Ta yi shiru tana tuno irin rayuwar auren da ta yi a gidan idiris, ta kasa manta irin wulaƙantar da ta yi a gidan idiris, irin tozarcin da ya yi mata, tamkar ya auri mushen dabba ba ɗan Adam ba, kuma ɗan Adam ɗin ma ƴar uwarsa.
Ta tuna yadda abokansa suke zunɗensa da angon ɗoɗɗoya, ba zata manta tonon asiri da wulaƙantarwar da Idiris yayi mata ba.
'To idan kuma haryanzu ban warke ba fa'?" Ta tambayi kanta.
Ta dafe ƙirjinta tana zancen zuci, ita dai tun da Allah ya sa kawu yahaya ɗaukkota, yayi ta ƙoƙarin saya mata magunguna, cikin ikon Allah ba ta sake jin wannan matsalar ba, ko maƙiyinta ba ta fatan Allah ya haɗa shi da bala'in da yake cikin larurar sanyi.
Tun da farida ta dawo daga gidan inteesar, tamkar ita za ayi wa kishiya, kamar za ta yi hauka, domin kuwa da ita da wasu daga ƙannenta suka dawo gidan, suna ta bata haƙuri, a kan sai ta daure ita ma, idan ba haka ba inteesar ba zata kwantar hankalinta ba.
Sun cika falo suna mayar da yadda aka yi, noor kuma na ta kokowa da remote tana ƙara volume ɗin tv.
"Wai ke noor baki da hankali ne? Ba ni san meya samu yayarki Inteesar ba ne?"
Noor ta juyo ta kalli mai maganar ta ce "Mutuwa ta yi ne?"
"Wane irin mutuwa, ke ko gidan nata ma baki je ba, balle a haɗu a rarrasheta da ke, kina kallon mahaifiyarku hankalinta a tashe, ita ma can muka baro ta tana kuka, amma ke kina nan kina ƙure wa mutane kunne da ƙarar tv"
Noor ta taɓe baki ta ce "To tun da dai ba mutuwa tayi ba ai barkanta, wanda ba shi da kunya ai dole ayi masa kishiya, haka wata malama ta ce rannan a tv, na ce ashe saura maama"
"Ke uwar taki ki ke cewa ayi wa
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 29 Chapter of 54