Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
fansa take yi saura ke, Allah kaɗai ya san me za ta yi miki" "Ita ta isa, sai dai dangin uban naku ƙauyawa, gidana  nawa ne babu mai sake zaun mini, ya takura mini rayuwa, kai kuma kar ka kuskura ka gaya masa ka ɗaga masa hankali su je can su ƙarata" Shi kansa Abdul ya shiga tsaka mai wuya, bai taɓa zaton ummi za ta aikata haka ba, amma dama mai haƙuri bai iya fushi ba, kusan kullum sai an kira shi daga gagarawa. Babu zato babu tsammani, raihan ya duba wayarsa ya ga ummi ta turo masa adress ɗin in da take a can Maiduguri, gashi a washegari zai tafi Abuja, ga tarin ayyuka a office, ba shiri ya soke ayyukan da zai yi ya shirya ya ɗauki mota ya tafi Maiduguri. Tiryan-tiryan ya bi adress ɗin, babban abun da ya ɓata masa rai, bai wuce adress ɗin hotel bane ba, sai dai yayi iya ƙoƙarin sa ya danne fushinsa, har ya ƙarasa full address ɗin. Ya je har ɗakin, yana tura ƙofar ƙamshin turaren ta, da sanyin AC suka dake shi, hakan ya rage kaso mafi yawa na ɓacin ran da yake ciki. Tana zaune a gefen gado, kanta babu ɗan kwali, duk da ta rame amma ta yi fresh da ita, gashin kanta ya sha gyara, sai ƙyamli yake yi. Jiki a sanyaye ta tashi tsaye, ya rufe ƙofar ya kalleta ya ce "Ummi me ki ke yi a hotel da aurena?" "Kana zargina ne? Ban taɓa zuwa ba, wannan shi ne last option ɗina, babu yadda na iya, ina fatan ka taho mini da takardar sakin" A ƙule ya ce "Ni na furta na sake ki ne? Ni ban rubuta miki saki ba, na dai karɓi takarda na yi rubutu, amma ai ban baki ba, kuma ban furta ba, amma ki ka yi tafiyar ki, kalli yadda ki ka din ga wahalar da ni, duk na shiga tashin hankali kowa na tambaya bai san in da ki ke ba saboda ina matuƙar sonki shiyasa ki ka zaɓi ki wahalar da ni? Kuma a ƙarshe ki rasa a ina zan ganki sai a hotel da aurena kuma a kan ki, kin yi mini adalci kenan?" Ya hasala matuƙa, sosai yake yi mata faɗa" ta ƙare masa kallo babu ƙarya ya rame sosai da sosai, sai dai ta san fushi ba nata bane ba a wannan yanayin, da ya shiga mood ɗin da ba ta so da yake ba ta tsoro, duk da ta ji kamar zuciyarta ta yi ƙeƙashewar da ba ta jin tsoron, sai dai girman miji mussaman nagartacce kamar raihan, kwarjininsa daban ne a idon iyalinsa. A hankali ta taka daf da shi, ba tare da ta ce masa komai ba ta kwanta a jikinsa, ta zagaye hannayenta a bayansa ta ce "Da gaske MD ba ka sake ni ba? Ranar kasa jurewa na yi in kalli rabuwata da abun da nake matuƙar ƙauna, in ga ka rubuta mini saki, zai shiga jerin abun da ba zai taɓa gogewa a rayuwata ba. Na je gidanmu, Antynmu ta ce ba zata riƙe bazawara har karo biyu ba, na je gagarawa kakata ta ce bani da wurin zama a gidan, tun da na bar gidan na riga na bar shi, ba gidan ubana bane ba. Dangin mahaifina sun saba yi mini haka, idan na je wurin mama tayaya zan fara yi musu bayanin mutuwar aurena, suna yi maka kallon mutumin kirki, ko baka da laifi sai sun tsaneka. Kwata-kwata yaushe na koma rayuwarsu, da zan fara yi musu sintiri da matsala? Ga mama ba cikakkiyar lafiya, duk da ta fara warkewa, ina tsoron ɓacin rai ya sanya ta sake rasa lafiyarta. Duk wannan lokacin ina gagarawa, gidan yaya magaji, babu wanda ya sani sai shi, yayi iya ƙoƙarin sa a kan in yadda ya kiraka a tattauna ya sasanta na ƙi, saboda bana son ka samu matsala da mami, idan ka mayar da ni zaku cigaba da samun saɓani, daga baya na dawo Maiduguri, ina gidan su mama, na yi niyyar gaya musu na kasa, ga zuciyata na ta azabtuwa da rashinka, wallahi yau ne na zo nan, saboda ba na son su mama su sani, bana son soyayyar da suke yi maka, da mutuncinka da suke gani, ya ragu a idonsu. Ban yi haka dan na ɓata maka rai ba, rashin gata ne ya sanya hakan faruwa. Dan Allah ka yi haƙuri MD na, ka yi haƙuri ka daina fushi da ni, na wahala da yawa Please" ta ƙarasa maganar tana fashe masa da wani marayan kuka. Gaba ɗaya sai jikinsa yayi sanyi, ya ƙanƙameta a jikinsa yana shafa gashinta zuwa bayanta. A hankali ya ce "Is ok sweetheart, kukan ya isa haka" ya ɗagota yana share mata hawayen fuskarta sannan ya ce "Duk da kin neme ni da haka ba ta faru ba, amma ki ka ƙaurace mini gaba ɗaya haba Salmana" "To ka ce baka sake ni ba, kuma na riga na ce ka sake ni" "Baki da shaida ai, dan haka ni ban sake ki ba, takardun gidan suna mota ta, amma kina ganin babu matsala abun da ki ka sa na yi? Ina za su koma su zauna?" Ummi ta ce "Cewa aka yi bani da masauki a gidan, ba gidan ubana bane ba, tun da bana ubana bane ba, yanzu na mijina ne, sonake a rushe gidan ma ya zama tarihi na daina ganinsa saboda na manta mummunar rayuwar da na yi a cikinsa". Ya ce "Mu bar wannan maganar for now, i so much miss you sweetheart, abinci babu daɗi, ko san tunkarar gida bana yi, saboda babu ke a cikinsa" Ta kwaɓe baki ta ce "Ba amarya zaka yi ba? Meye na damuwa da ni" "Salma kin fa san komai, kuma waye ya ce miki zan yi aure? Kema kin san ba so nake yi ba". Ta harare shi ta ce "Ni zaka yi wa daɗin baki, duk wadda take ganin za ta iya kishi da mummunar mace kamar ni, bisimillah" Raihan ya ce "Innalillahi, wai ummi anya ba canza mini ke aka yi ba? Dan Allah mu bar wannan zancen i so much miss you kairun nisa'i" yayi maganar yana ƙara ƙanƙameta. "Na kusa gama idda, kar ka ɓata mini iddata" "A'a takaba ki ke yi ba idda ba" Nan suka shiririce, suka manta da duk wata damuwa da suka shiga a ƴan kwanakin. Tare da nuna wa juna tsantsar soyayya da yadda suka yi missing ɗin juna. "My" "Na'am sweetheart" "Meye abun yi yanzu?" "A ina?" "Ban gayawa kawu abun da ya faru ba, ban sani ba ko ya sani, ina ga dai wurin mama zan koma na zauna dole" Raihan ya ce "Ke a tunaninki zan bari ki sake kufce mini ne? Gobe in Allah ya kaimu da sassafe zamu tafi Abuja" "Amma mami fa? Kuma ga aure zaka yi, kar ka kuma samun saɓani da ita" "Ke ina ruwanki da aurena ne? Kin san wani abu?" Ta ce "A'a" "Har cewa su Alhaji na yi, bani da lafiya ba zan iya ƙara aure ba, kema haƙuri ki ke yi da ni" A zabure ummi ta kalleshi ta ce "Amma da wasa ka ke yi ko?" "Wallahi da gaske nake" "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wai kai ba ka jin kunya ne?" "In dai a kan ki ne bana jin kunya, a wurinki ne kawai nake da lafiya" haka suka manta da damuwa da matsalolin da suke ciki. Washegari da sassafe, suka shirya suka tafi Abuja da shi da ummi. Ya danƙawa ummi takardun gidan gagarawa ba tare da ya cigaba da takura mata a kan me za ta yi da gidan ba. Sai dai ta ce masa ya ajiye mata. Raihan ɗin da sai da Alhaji yayi ta fama da shi a kan tafiya Abuja, amma daga baya ya ji raihan shiru, ya tafi babu ko sallama. Ummi har mamakin irin son da raihan yake yi mata take yi, kullum fatanta da Addu'arta Allah ya sa kar ya daina sonta. Ummi ji take za ta iya ɗaukar kowace kasada dan ta cigaba da rayuwa da mijinta, dan sai dai ta bar gidansa ta ƙara tabattar da ɗakinta shi ne rufin asirin ta, dan sai da ta yi wa maryam Allah ya isa. A gidan su wani abokin raihan suka sauka, gidan babu kowa a ciki, kuma kafin su je an gyara gidan komai akwai a cikin gidan. Cikin dare suna bacci, raihan ya farka ummi na jikinsa, sai dai jikinta ya ɗau zafi sosai. Ya haskata ya ga baccinta take yi hankali kwance, washegari da safe da ta tashi, idonta ya ɗan yi wani iri. Ta dube shi ta ce "Good morning" "Sweetheart, wai ba ki da lafiya ne? Jiya da daddare na ji jikinki ya yi zafi?" Tayi murmushi ta ce "Duk cikin murnar ganinka ne, amma lafiyata ƙalau" Ya rungumeta a jikinsa ya ce "Anya kuwa, idonki kamar wadda ba ta da lafiya" wayarsa ce ta fara ringing, ya kai hannu ya ɗaga yayi sallama. Muryar Safiyya ya ji ta ce "Yaya ina kwana?" "Lafiya lau" "Dama mami ce ta ce na kiraka, maganar kuɗin party, sannan kuma kayan da zan yi fitar biki". Raihan ya ce "Ai dama auren na mami ne, dan haka ita zaki tambaya bani ba" Ya katse kiran, ya kalli ummi da take ta sauke numfashi. "Salma ya dai?" Ƙoƙarin tashi take yi daga jikinsa, ya riƙe ta ya ce "Meyafaru ne?". "Dan Allah idan kana sonta, kar ka yi pretending dan ka kwantar mini hankali, dan Allah ka yi aurenka". "Haba ummi tun yanzu? Kin fara karaya ni ya zan yi to? Dan Allah kar ki ce zaki daina kulawa da ni, wallahi banda tursasawar mami, ni babu agender ƙara aure a gabana, wannan ɗin ma da yaya aka yi ana cewa na yi ƙanƙanta?" Ummi ta yi masa shiru, dan wani irin zafi ƙirjinta yake yi mata. Ya tashi zaune ya ce "Me zan yi mana order mu karya, zan fita da wuri ne" Ta juya masa baya ta yi shiru. Sai a lokacin ta ji ashe ƙarya take yi, da take cewa ba zata ɗaga masa hankali idan zai ƙara aure ba. Ya leƙa fuskarta ya ga yadda ta haɗe rai. Bai ce mata komai ba, ya tashi ya shiga banɗaki, har ya gama shirinsa ya fita ba ta sake kula shi ba. Sai dai fitarsa ke da wuya ta fashe da kuka, yayi wuri ace za ayi mata kishiya tana tsaka da karɓar kulawa da soyayya daga wurin mijinta, an hanata samun cikakkiyar nutsuwa tare da shi. Ya dawo da takeaway, nan ma ta ce ya ci nasa ba yanzu za ta karya ba. Haka ƴan kwanakin yayi ta fama da ummi, ita kanta ba ta san tana da azabar kishi har haka ba, sai yanzu dan ta fara zancen ita maiduguri za ta koma. Ta addabi kanta da zuciyarta ko abincin kirki ba ta iya ci, idan baya nan sai ta zauna ta sha kuka kamar ƙaramar yarinya, idan ya dawo babu ruwanta da shi, ko shimfiɗarsu ya je, sai ransa ya ɓaci. Ga kiran waya da mami take babu ƙaƙƙautawa a kan maganar auren sa. Yau da ya kai ƙarshen ƙulewa da halinta, ya hau zazzaga mata bala'i. Tayi masa shiru abun da ya fi komai ɓata masa rai. "Ai gara na yi auren, tun da kin gaji dani kin daina tausayi na, ina ta taki kina wahalar da ni". Kai tsaye ta ce "Da ka huta dama kana son abun ka a ranka" Sai da ya sake ɗaga kai dan ganin ko ba ummi ce ta yi maganar ba. Janyota yayi da ƙarfi yana fuskantar ta, zai sake balbale ta da faɗa, ya ji tana sheshsheƙar kuka, sai kuma jikinsa yayi sanyi. "Ummi wai meye haka? Gaba ɗaya kin canza". "Dan Allah ka bari na koma maiduguri na zauna, ka je ka yi aurenka" "Ummi ni ɗin ne ba kya so kuma yanzu?" Cikin kuka ta girgiza kai ta ce "Ba fa abu ne mai sauƙi ba, wallahi ba zan iya jurewa ba, kishi zai kashe ni, ba zan iya pretending ba ɗan aljannata, i so much love you sweetheart, ba zan iya pretending ba, kullum zuciyata da sauri take bugawa idan na tuna zaka zama namu ni da wata, ka yi haƙuri ba dan in ɓata maka rai nake yi ba, ban san haka kishin yake ba, na ɗauka ba shi da wahala" ta ƙarasa tana ƙanƙame hannunsa tana kuka mai ratsa zuciya. Tausasan kalamanta sai suka sanya tausayinta ƙara shigarsa. "Na san babu sauƙi, amma ki jure dan Allah na samu na yi wa mami biyayya ko na gama da duniya lafiya, idan ina ganinki a haka zan iya bujirewa, ki daure Salmana ki yi haƙuri na san da ciwo" ya din ga rarrashinta tana wata irin ajiyar zuciya, da sai da ta din ga bashi tsoro kar wani abu ya sameta. Cikin dare jikinta yaƙi daɗi, dama tana zazzaɓinta a tsatstsaye, idan ta ci abinci tayi ta amai, ba abun da yake zama a cikin ta, sai dai na yau ya tsananta, da har sai da raihan ya gane, tun tana iya zuwa banɗaki yin aman har ta kasa. Ranga-ranga ya tafi da ita asibiti, a karon farko gwaje-gwaje suka tabattar da ciki ne da ita. Raihan kamar yayi tsalle dan murna. Tun da tayi ɓarin nan ba ta ƙara yin period ba. Aka din ga saka mata ruwa, sai dai zazzaɓi ba ya sauka, kuma ko ta ci abinci ko ba ta ci ba sai tayi amai. Tausayinta ya cika raihan, ga zafin laulayi ga kishi, sai da likita ya zo dubata ne ma take gaya masa ta fi wata tana zazzaɓi a kaɗan-kaɗan. Raihan yana saka ran a sallame su, amma likita ya ce sai sun riƙe ta, saboda low bp, ga jininta ma yayi ƙasa, sai an ba ta kulawa ta musamman. Kwananta biyu a asibiti, da sassafe ya dafa tea zai kai mata, ya fito daga motar sa, sai ga kiran wayar Alhaji. Ya ɗaga yana gaida Alhaji sai dai yanayin muryarsa ya tabattar masa ba lafiya ba. "Kana ina?" "Ina Abuja Alhaji lafiya?" "Ban sani ba, ina ummi take?" Gaban raihan ya faɗi ya ce "Tana gida?" "Ni zaka yi wa ƙarya? Ashe baka da hankali ba ka da mutunci raihan? Jiya da daddare babanta ya kirani cikin damuwa ashe sakar masa ƴa ka yi, kuma an nemi in da take an rasa, ga wani case can a familynsu ma ana ta nemanta, ka gaya mini ka sakar masa ƴa? A baka yarinya cikin girma da mutunci amma ka wulaƙanta ta, yarinya mai tarbiyya da nutsuwa, bilki ce ta saka ka saketa ko?" Raihan ya girgiza kai ya ce "A'a ba ita ba ce ba". "Koma waye ya saka ka, ka cuci kanka, kana ina? Kuma ina ƴar mutane" Raihan ya ce "Muna tare a nan Abuja" "Uban me ka ɗauketa ka yi mata a abujan bayan ka saketa?" "Alhaji ba sakinta na yi ba, rashin fahimta ne" A fusace ya ce "Kai ka sani, baka ma da kunya, in anjima zan shigo garin Abujan, ka bani ƴar mutane da takardarta na danƙawa mahaifinta ita, kai kuma tun da mutumin banza ne ka je ka ƙarata, am so disappointed on you!. 08081012143 PAID ADVERT!. Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi. Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku Oll types of Turaran wuta Sandal Halut Irik Difur Gab Gab Kajiji Habil Nabak Humra Kulakcha Dilke da kalta Kayan Garan jiki Muna turara Kaya Kujerar garan jiki Kannada Madarorin turare masu kamshi  Man garan gashi  Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche Ku nememu a wan nan no 08065728702   08025453921 *TALLA!TALLA!TALLA!* *INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*. *BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU* *MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA* CUTARWA! AYSHERCOOL (BRIGHT PENS) MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g 45 PAID ADVERT *Hajiya ina zaki? Saurin me ki ke yi haka? Ɗan bani aron mintuna biyu kacal, na gaya miki albishir ɗin da na zo miki da shi. Shin ko kin san sirrin sheƙin fatar ummi, da ya sanya ta kama zuciyar MD raihan ta hana shi sukuni? Kai ba ma skin care ba, har da sirrin gyaran gashi, ina masu fama da amosani, karyewar gashi ko kuma sanƙo, jan gashi ne da ke? Ko taurin gashi kamar soson ƙarfe. Idan matsalar ki budurwar fata, tare da rashin glowing, Annur skin scrub da hair bliss sun shirya tsaf domin magance muku kukanku, me ku ke jira ku tuntuɓe su a kan lambar wayar su dan ƙarin bayani 07045971194 ko 08140450950* 45 Raihan ya rasa ta ina zai fara kare kansa ma, haka yayi shiru Alhaji ya gama faɗan ya kashe wayarsa. Kamar wanda aka gayawa saƙon mutuwa, haka ya ƙarasa cikin asibitin, ya taimakawa ummi ta wanke baki, ya haɗa mata tea da dankali yana bata. Cikin ɗari-ɗari take ci, dan ta san ƙarshen abun ta amayar da abun da ta ci, ga yunwa tana ji sosai. "MD ka ga wancan cikin ban san ma da shi ba, ban yi laulayi ba wannan kuwa sai wahala nake sha" Yayi murmushi da ƙyar ya ce "Wancan kin ci bonus" "Wai ya na ganka duk wani iri ne? Na san zaman asibiti da gajiya, ba daɗi shiyasa gara ka mayar da ni maiduguri" Raihan ya ce "No, ba gajiya na yi ba, da ke da babyna kuna buƙatar kulawata. Ai gazawa ce in ce ki koma gida dan baki da lafiya, ni zan yi abun da ya dace na kula da ku" Tayi murmushi ta ce "To aikin fa?" "Shima duk zan iya" "Ɗan Aljannana, Allah ya saka maka da mafificin alkhairi, ya barmu tare har aljanna" Ya amsa mata da Amin, ƙasan zuciyarsa yana fargabar hukuncin Alhaji, dan daga ji ya ɗau zafi sosai. Yadda ta gama cin dankalin nan, sai da ta amayar da shi gaba ɗaya, abun har tsoro yake bawa raihan, duk ta rame saboda laulayi. Yana nan zaune tare da ita, har ta samu bacci, bayan wasu awanni ta din ga jin hayaniya kamar a mafarki. Ta buɗe idonta, ta ga Alhaji a ɗakin tare da Salim, ga raihan a gefe ransa a haɗe sai kuma likita a tsaye da file. A hankali ta tashi zaune, tana mamakin zuwansu ta ce "Alhaji sannu da zuwa" Ya dubi Ummi ya ce "Sannu ya jikin? Dan Allah kalli yadda duk ta bi ta ƙare ta rame, meke damunta ne? Ko kuma duk tsiyataku da rashin mutuncinka ne ya sanya ta rame" Yayi maganar yana kallon raihan. Likita ya ce "Ahh ba wani abun damuwa bane, laulayi ne na mata, ba ta iya cin komai shiyasa muka ajiyeta mu ke ta saka mata ruwa" Alhaji ya ce "Ka rubuta mata sallama, gida kano zamu tafi, za a cigaba da kula da ita a can" Ya mayar da idonsa kan ummi ya ce "Banda abunki ummi, gani menene amfanina? Ko dr. Ba ya nan wani abu ya haɗaku sai ki zo ki gaya mini, ni ƴa ta ce ke ba sirika ba, kawai sai ki biye masa ki tafi wani wurin ace ba a san ma in da ki ke ba? Kuma dan baka da kunya ka lallaɓa ka mayar da ita ka taho da ita nan ba wanda ya sani, hankalin mahaifinta na can a tashe bai san ina take ba, ka bani kunya" daga ummi har raihan aka rasa mai magana, ummi ba ta taɓa zaton Alhaji ya iya faɗa haka ba, saboda kullum fuskarsa cikin murmushi yake. Haka aka sallami ummi, suka nufo kano, raihan ya sha faɗa a wurin Alhaji,kuma yayi shiru bai ce komai ba ummi gaba ɗaya ta ji babu daɗi. Asibiti suka zarce da ummi, aka cigaba da ba ta kulawa ta musamman, saboda suna tafe a hanya ma tana amai. Alhaji ya kira dr. A waya ya sanar masa ya gano ummi, tana tare da raihan a maiduguri. Dr. Ya ce ya haɗa shi da ummin a waya, Alhaji ya ce masa ba ta da lafiya, ba za ta iya amsa waya ba. Dr. Ya ce a cikin satin zai shigo Nigeria, dan hakan yayi dai-dai da lokacin zuwansa hutu. Ya karɓi kwatancen asibitin, ya kira Abdul a waya, ya ce su je asibiti da shi da noor, su duba masa jikin ummi. Ko da suka je, sai da Abdul ya yi wa raihan ƙorafin, meyasa bai gaya masa ba ya ga ummi. Babban abun da ya bawa ummi mamaki, bai wuce yadda Salim da noor suke yi wa juna murmushi ba, kamar sun saba. Kuma a iya sanin ummi ba shi da fara'a ko kaɗan. Noor ta ƙarasa gaban gadon ummi ta na yi mata sannu. "Yaya ummi shi ne ki ka tafi aka neme ki aka rasa ko? To ƴan gagarawa ne suka samo wani abokin Abba, suka saka ya kira musu shi, aka gaya masa abun da ki ka yi, ya bi ba'asi ban san dai me suka ce masa ba, ya kira waya yana faɗa ya cewa yaya Abdul ya je gidanki ya duba masa ke dama ba ya samunki a waya, aikuwa dai ya gaya masa gaskiya, amma fa mun sha faɗa saura ke idan ya dawo dan ransa ya ɓaci" Salim ya ce "Ba ki ga bata da lafiya bane?" Ta ce "Au, haka ne fa, zumuɗi nake na ganta, ba ka san yadda na shiga tashin hankali ba da aka ce ta ɓata". Yayi murmushi ya ce "I see" Alhaji ya ce "Ai daga ita har shi, sun yi laifi, kuma ba zan matsa da bincike ba, sai dr. Ya dawo, amma fushi dole ayi fushi da su" shi dai raihan ya rasa menene yake yi masa daɗi, ga rashin lafiyar ummi, ga faɗan Alhaji da yaƙi saurarensa. Salim ya ɗauki Alhaji suka tafi gida, tun da yaje gida yake cigaba da faɗa a kan abun da ya faru, hankalin mami yayi mugun tashi, dan yadda ransa ya yi mummunan ɓacin nan, zai iya aikata komai dan kamar ƴar cikinsa aka yi wa haka ɗauki lamarin da zafin gaske. Ta din ga kiran raihan tana jaddada masa, kar ya kuskura ya gaya wa Alhaji ita ce ta saka ya saki ummi. "Mami na ji, ni ba zan faɗa ba, amma ummi fa?" "Au kai sai ka bari ta faɗa ɗin?" "Mami ya zan yi, tayaya? Zan yi mata dole ne, tana kwance muna fama ba ta da lafiya, ba zama ta fahimci me nake nufi ba" mursisi raihan ya nuna wa mami ba zai tursasa ummi ba. Bayan ya kashe wayar ya kalli wayar ya ce "Mami ina fatan zaki fahimci cewa, ɗan adam duk ƙin da ki ke yi masa wataran zai iya yi miki rana, ko ki nemi alfarma a wurinsa. Kwana biyu ummi ta ɗan warware, ranar dr. Ya dawo, Alhaji dai tare da Salim suke zuwa asibiti, haka Hajiya ma take sintiri. Tun da raihan yayi aure, Alhaji da Salim suke ɗasawa saboda Alhaji ya jinjinawa Salim yadda yayi playing role ɗin sa na babban yaya ga raihan ba tare da wata adawa ba. Kuma a hankali ya lura da ya rage fitina sosai da sosai, dan ko fita baya son yi suna tare da Alhaji. Alhaji ya kasa shiru, sai da ya tambaye shi, dalilin canzawarsa lokaci ɗaya yayi murmushi ya ce "Alhaji kenan, ai ko dabba idan kana mutunta uwata zata so ka, balle ɗan Adam ni dama wasu lokutan babarsa ke sanyawa nake ja baya da shi, duk abun da yake faruwa ina sane da yadda mutunta da girmama mahaifiyarmu. Da na raka shi maiduguri ma, yadda dangin matarsa suka din ga yaba kamalarmu na ji daɗin hakan sosai, na ƙara yadda da zama mutumin banza ba shi da wata fa'ida. kuma ƙanina zai yi aure very soon zai fara tara zuriya, kuma yaransa namu ne, abun kunya ne a garemu yaranmu su taso su ganmu a irin wannan yanayin. Ina ta addu'a kuma ina jan hankalin Sagir ma. Abu na gaba rayuwar raihan da matarsa ta burgeni, da har na ji nima ina son yin aure, amma na san za a iya hanani aure saboda halina,

Chapter 47 of 54