gagara"
Suka kammala tattaunawa, suna ta yi wa kawu godiya, ya kama hanya ya koma kano.
Ummi taga gata da ƙauna, babu kyara, babu hantara babu cin zarafi, duk ba a rasa wanda sukan yi maganar cewa ummi ba ta kama da mariya, mariya ta fita kyau da haske, maryam ce ma a tsaye take faɗan kar wanda ya sake yi musu wannan zancen.
Ummi murmushi kawai tayi, dan da ta san abun da tayi going through, da wannan bai ɗaga mata hankali ba.
***
A ka yi bikon raihan da ƙyar ya koma kano, Alhaji sai tsokanarsa yake "ni zaka yi wa yaji ko? Zamu gauraya da kai ne".
Hajiya ta ce "Raihan ba a fushi da iyaye, nan gaba kar sake aikata abu makamancin haka"
Raihan ya ce "Hajiya ba fushi na yi ba, na tafi ne dan na je na samu nutsuwar zuciya, amma in sha Allah hakan ba zai sake faruwa ba"
Cikin tsananin fargaba ya tashi ya nufi sashin mami, ba addu'ar da bai karanta ba, saboda ya san dole ne zuwansa ya tarar da sabon ɓacin rai.
A bedroom ɗin ta ya tarar da ita a zaune, cikin ladabi ya durƙusa ya ce "Mami barka da gida"
Maimakon ta amsa sai ta ƙure shi da ido, da har sai da ya fara tsarguwa.
"Ai gara in ƙare maka kallo, in tabattar da ni na haifeka kuwa? Ba matar ubanka ce kuwa ta haifeka ba ko har ubanka? In haifi ɗa a cikina ya janyo mini zagi da cin mutunci, raihan kana son gamawa da duniya lafiya kuwa? Ka sani sarai matar nan ba ƙaunata take yi ba, ka je ka sameta ka kai ƙara ta ta kira ni ta ci mini mutunci"
"Wallahi mami ba ƙararki na kai ba"
"Yi mini shiru tun kan na fasa maka baki, ka kyauta ba dai wannan mummunar yarinyar ba ce ba, ka je gaka nan gata, amma ka sani babu yawuna babu saka hannuna a aurenka raihan, kuma bayan ka aireta sai ka auri safiyya. Kuma ban lamunci ka yi mata kayan lefe ba, tun da bazawara ce, dubu ɗari biyar ɗin ta isa komai da komai"
Cikin damuwa raihan ke ƙoƙarin yin magana, amma ta dakatar da shi, tare da bashi umarnin ya bar mata ɗaki.
Kansa har wani sarawa yake yi, wai ita safiyyan nan dole sai ya aureta kamar wahayi? Baya son ta ba ya ƙaunarta amma an dage sai ya aureta, ga kuma wata magana, wai ba zai yi wa ummi kayan lefe ba, to iyayenta ne zasu saya mata sutura da kayan kwalliyar da za ta yi masa a gidansa? Kuma a wannan marrar nawa dubu ɗari biyar take, da har za ta isa ayi wa ummi kayan lefe, nauyin ai sai ya yi wa iyayenta yawa, shi abun kunya ne ma a gare shi ace bai yi wa ummi kayan lefe ba. Haka yayi ta wasi-wasi yana nazarin abun a ransa.
Farida ba ta damu da in da ummi take ba, sai dai tana tambayar dr. Tana fatan ummi ta tafi kenan, amma yayi mata banza ya ƙyale ta.
Noor kuwa sai bin sa take tana tambayar sa, wai yaushe ummi za ta dawo, ita fa gidan babu daɗi idan ummi ba ta nan, ya ce mata zata dawo nan ba da daɗewa ba.
Ummi a gabanta aka fara haɗa kayan turarukan wutanta, wai akwai turarukan da sun fi shekara a binne a ƙasa ana tsuma su.
Yaya maryam ta kasa zama, kullum tana yawon kasuwa ita da mama, matar malam wurin yi wa ummi sayayyar kayan aure.
Ita babban abun da yafi faranta mata, bai wuce kasancewar ta da babarta ba.
Mami ta ƙara matsanta wa raihan, ga gefe guda kuma, Safiyya sai ta wani kira shi wai za ta gaishe shi, duk rashin son wulaƙanta ɗan Adam irin na raihan, ƙarshe sai da yayi blocking ɗin ta, dan ta daina damunsa da kira.
Ya cewa ummi zai zo Maiduguri ya ganta, ya kuma gaida mama, amma gudun matsala ya sanya ta ce masa ya bari ta kusa dawowa.
***
Sai da ummi tayi sati uku cif, sannan dr. Ya koma ɗaukar ta, kamar ta ce masa dan Allah ya barta a nan, amma sai ta ji nauyin hakan ta kasa, kayanta ƙwaya biyu da ta je da su, sai da aka ɗinka mata kusan kala goma a can, kuma tuni suka haɗa kayan gyaran jiki masu haɗe da turarrruka, ummi ta fara amfani da shi.
Yaya maryam sai jaddada mata take yi, kar ta yi wasa da kayan gyaran da aka ba ta ta yi, da sabulan da aka haɗa mata.
Mariya ta kalli dr. Ta ce "Ka yi mini alƙawarin ba wurin Iya zaka mayar da ita ba?"
Yayi murmushi ya ce "Ai aronta na ce ki bani, ba zan kai miki ita wurin Iya ba"
"To ai zaka dawo da ita ko?"
"In sha Allah"
"To dan Allah ka kula mini da ita sosai da sosai, kar ka bari ta yi kuka"
"In sha Allah zan kula da ita sosai da sosai"
Ta kalli ummi ta ce "Kar ki yi musu kuka kin ji ummi, ban da ƙyuya da kuka, ba ruwanki da yara, kar ki je su din ga dukanki kin ji ko?"
Ummi ta riƙe hannunta ta ce "To mamana, me ki ke so na taho miki da shi idan zan dawo?"
Ta ɗan yi jimm sannan ta ce "Bakomai, ni dai kawai ki dawo, ba dan ina jin kunyar kawu yahaya ba, ba zan bashi ke ba"
Ummi ta cigaba da kallon mariya tana jin daɗi.
Da ƙyar suka rabu suka nufo hanyar Kano.
Duk rashin surutun ummi, haka ta sake ta din ga yi wa kawu hira tana bawa kawun labarin mamanta.
Bayan azahar suka sauka a kano, noor kamar ta mayar da ummi cikin ta, dan murnar ta dawo.
Ummi ta shiga har falo, ta ce wa farida sun dawo, ta amsa mata a yatsune, sai dai fuskar inteesar kawai ta kalla ta san matsala ce ta kawota gida.
Ummi ta koma ɗakinta, suka din ga hira ita da noor tana bawa noor labarin mamanta.
Noor ta ce "Kuma ki ka yadda ki ka dawo, wallaahi idan ni ce ba zan dawo ba, amma na san saboda yaya raihan ki ka dawo ko?"
Ummi ta ce "Ban sani ba"
Suka din ga dariya, noor ta ce "In gaya miki, Inteesar mijinta ya ɗauki amaryarsa sun tafi umara, shi ne take kuka wai ba a tafi da ita ba"
"To waye ya tambaye ki?"
Noor tayi shiru tana ƙifta idanu.
Haka nan take murna, ta san yau za ta ga raihan, ta rasa dalilin da ya sanya take murna.
Haka nan ta samu kanta da yin shirin haɗuwa da shi.
Ta ɗauki kayan tsaraba da ta zo da su, har da su kayan turaren wuta ta kai wa farida, ta karɓe ba tare da godiya ba.
Bayan sallar magariba ummi ta saka rigar atamfa bubu, tana ta fama ta ɗaura ɗankwali, abu ya gagara saboda ba ta saba ba, ƙarshe noor ce ta ɗaura mata da ƙyar, shima gashin ya ƙi rufuwa, sai da ta saka hula sannan aka ɗaura ɗan kwalin.
Ta yafa mayafi, tana ta rufe-rufe tana tunanin anya za ta iya fita a haka? Kiran wayarsa ta gani, ta tashi ta kalli noor ta ce "Anya in fita a haka kuwa?"
"Wallahi kin yi kyau, kin rufe ko ina kuma"
Da ƙyar ummi ta iya fita, tana ta kare jikinta, ta ƙarasa in da yake.
"Oyoyo sweetheart, long time"
Tayi murmushi ta zauna, tana kawar da kanta gefe.
"Congratulations once again, ya ki ka baro mini maman?"
Ummi ta yi murmushi ta ce "Tana lafiya ƙalau"
"Kin bata labarina kuwa?"
Ummi ta ce "Idan na yi mata babu lallai ta gane ma"
Ya ce "Ba ki yi niyya ba dai, zan je da kaina mu gaisa ai"
"Ka gama yajin?"
Yayi murmushi ya ce "Ke ma haka zaki ce?"
Ummi ta ce "To ba yajin ka yi ba, ko kunya ba ka ji ba?" Yayi dariya ya ce "Na samu mafita ai, kin yi kyau sosai da sosai wallahi, Allah ya nuna mana ranar nan lafiya babyna" ummi ta yi shiru tana sunkuyar da kanta.
Kausar ce ta nufo in da suke zaune, dan haka yayi shiru yana kallon ta.
Cikin mamaki take kallon raihan, yanzu wannan ne zai auri ummi? Wannan yaron, amma kuwa tayi asara, ko kuma shi yayi asarar kyakykyawan matashi kamar wannan ya auri ummi. Ta yi maganar a zuciyarta
Cikin gadara ta ce "Ke ki zo maama tana kiranki, wa ki ka barwa yin abincin daren da haryanzu baki ɗora ba," tayi maganar cike da son wulaƙanta ummi a gaban raihan.
Raihan ya ce "Tana magana da mijinta ne, idan kun matsu ku ci, ku dafa, tana buƙatar hutu, tun da yau ta dawo daga tafiya, kuma ina buƙatar yin magana da ita"
Zare ido ummi tayi ta ce "Na shiga uku, raihan"
"Shhh" ya ɗora yatsansa a kan lips ɗin sa yana zare mata ido.
Ya sake kallon kausar ya ce "Ki koma ki ce ba za ta yi ba"
Ayshercool
08081012143.
*CUTARWA*
*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
34
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
FOLLOW AND SHARE
AYSHERCOOL
08081012143
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
Wani irin gumi ne ya dinga gangaro wa mami, duk da yadda sanyin AC ke ratsa ko ina a falon.
Raihan ƙararta ya je ya kai wa wannan masifaffiyar yar uban nasa kenan? tuno maganar Alhaji Tahir, da tuni ya bar falon da yayi ya sanya ta jin wata muguwar gudawa, saboda yadda cikinta ya murɗa mata.
Afujajan ta fita ta nufi sashinsa, har da tuntuɓe.
"Wallahi Baka isa ka gaya mini maganar da zata hana ni sukuni ka fice ka bar ni ba, kai yanzu saboda abun kunya goɗai-goɗai da kai sai ka auri yarinyar da ɗan ka ya ce yana so?"
Alhaji Tahir ya ce "In dai haka shi ne mafita a gareni me zai hana? Ku mata ku kuka san wani abun kunya, mu maza abu in dai mu yayi mana ba ruwanmu da abun kunya, kuma ina sake tunatar da ke, bana magana biyu, wallahi da gaske nake, sai dai idan na aureta wanda ba zai iya zama da ni ba ya ƙara gaba, shawara ta rage ga mai shiga shiga rijiya" ya ƙarasa maganar tare da ɗaukar wayarsa ya fita.
Kamar wadda ta zare, haka ta sake kwasa har da gudu, ta tafi ta kira Anty rakiya a waya.
Rakiya na ɗagawa mami ta fashe da kuka, "Anty rakiya na shiga uku na lalace"
"Wane irin kin shiga uku, meyafaru ba yanzu muka gama waya lafiya ba?"
"Ashe raihan bauchi ya tafi, ya je ya haɗo ni da wannan masifaffiyar matar yayar babansa, kin ga yadda ta ci mini mutunci kuwa? shi kuma Alhaji wai idan ban bari an yi auren ba, wai shi zai aureta ya kawota gidan nan a matsayin matarsa"
Anty Rakiya ta ce "Kai haba, dalla rabu da shi, barazana ce kar ki fasa wallahi, kar ki yadda a kawo miki bazawara a matsayin sirika"
"Anty Rakiya waye ya gaya miki Alhaji Tahir yana barazana ne? Magana ɗaya yake yi ko ta yi maka daɗi, ko kuma akasin haka, har rantsuwa yayi mini, na shiga uku, kuma wai raihan ya ajiye aikin nan ina na kama?"
Anty Rakiya ta ce "Taɓ, lallai raihan ba shi da hankali, to wallahi idan ki ka zuba masa ido, haka zai aurota ya fi ƙarfinki, tun da har ya san yayi miki yaji, ki kira shi ki ce lallai ya dawo dan ubansa"
Mami cikin takaici ta ce "Lamarin fa ya wuce yadda ki ke tunani, kin san taurin kan raihan kuwa? To cewa tayi wai ba zai dawo ba, ya bar aikin kenan, ya kuma ce idan aka karɓo kuɗin auren nan, shi da aure har abada, ga babansa ya ce idan aka fasa zai aureta, na shiga uku ina na kama? Kin ga suna nema su haukata ni, raihan kafiya da taurin kai kamar ubansa, idan ya ƙi aure ya lalace yaya zan yi?"
Anty Rakiya ta ce "Ai kawai ki dage ki samu ya dawo tukuna, ki kira shi a waya"
"Wayoyin da duk ya kashe su, ina zan yi?"
"To ki koma ki samu babansa ki lallaɓa shi, ya dawo da shi kar a rasa wannan damar kuma ta kasuwancin nan "
Mami tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, zan kira ki mayi magana anjima" ta katse wayar ta ajiye tana wani irin haki, ita ba mai asma ba.
***
Dr. suna tafe a mota da shi da ummi, ya ce "Mamana zaki ga zamu yi doguwar tafiya, ba sayar da ke zan yi ba abun alkhairi ne"
Ummi ta yi murmushi ta ce "Idan sayar da ni ɗin ma ka yi ai na saidu kawu"
Yayi murmushi ya ce "Idan na sayar da uwata ina na kama? Yakamata ace kin yi azumin farinciki kan mu yi tafiyar nan"
"To Ubangiji ya tabattar mana da dukkanin alkhairin da yake cikinta"
Ya amsa mata da "amin"
Ummi ta gaji da zaman motar nan sosai da sosai, sai dai tun da taga symbols da sunan borno, jikinta ya fara sanyi, har ta rasa tunanin me ma za ta yi ne?.
Kawu kuma ya mayar da kai sosai a kan tuƙinsa, sai lokacin salla ya tsaya suka yi salla, ya saya mata abinci.
Ta tuno lokacin da ya ɗaukkota daga gagarwa a wahale, ba sutura ga ciwo, ko ba komai ta samu alkhairi a dalilin riƙonta da yayi
A ranta ta ce "Allah sarki kawuna, baba ya tafi amma ya bar mini Allah, Allah kuma ya bani kai, Allah ya kula da kai da zuriyarka".
Duk da ba ga saba baccin mota ba, gajiya ta sanya wani irin nannauyan bacci yin awon gaba da ita.
"Mamana tashi mun zo" a hankali ummi ta motsa tare da buɗe idonta, har suka fito daga cikin motar, ba ta iya cewa komai ba, sai bin wurin da kallo.
Ƙofar wani gida suka tsaya, dr. Ya ciro wayarsa ya ɗan daddana ya kara a kunnensa ya ce "Gamu mun zo"
Wani matashin saurayi ya leƙo ya durƙusa ya gaida dr. Sannan ya ce su shiga.
Suka shiga cikin gidan, ummi ta zubawa dattijon da suka tarar a tsakar ido, yana zaune a kan buzu, da Alƙur'ani bugun warshi a gabansa.
Dattijon ya miƙe tsaye yana yi musu maraba, tare da bin ummi da kallo, ba ta ɗaga niƙabin fuskarta ba, sai dai ta shagala da kallon sa ta san shi, amma a ina? Ta kasa tunawa.
Yayi musu jagora har wani matsakaicin falo, yana ta yi musu sannu da zuwa.
Suka gaisa da dr. Ummi ta gaishe shi, ya amsa mata cikin kulawa, sai dai bai tambayi wacece ba, kuma ya kasa daina kallonta.
Dr. Ya ce "Ina mutuniyar kuwa?"
"Wai sun fita barka a nan bayan layi, jikin ne ma ya ɗan motsa, amma Alhamdilillah mun gode Allah, bari azo a ɗora muku girki, ai bamu san zaku zo ba"
Dr. Ya ce "Ai alƙawarin da na ɗauka na zo cikawa, zuwan babu cikekken shiri, bari mu yi salla kafin su dawo".
Ya ja dr. Suka fita, bayan nuna wa ummi banɗaki, tayi alwala ta yi salla, ta nemi wuri ta kashingiɗa tana hutawa, saboda gajiyar da tayi.
Ummi ta ɗan jima a zaune, sannan dr. Ya shigo, shigowar ta sa yayi daidai da shigowar matashin da ya yi musu iso, ya kawo musu nono mai sanyin gaske, da nama fal malam ya ce a kawo musu da ruwa, dan azo a ɗora sanwa.
Ummi dai ta kasa sakewa ta ci, dr. Kuma sai hira suke yi da malam.
Dr. Ya ce "Malam ba ka ganni da baƙuwa ba ne? Baka tambayeni wacece ba"
Malam yayi murmushi ya ce "Tun da baka gaya mini ba, bai kamata na yi shishshigi ba ai, na ma zata ko mai ɗakinka ce, shiyasa ban yi magana ba, kuma na ganta sanye da niƙabi"
Dr. Yayi murmushi ya ce "Aishikenan, mama malam ne fa, baki gane shi ba?"
Ummi ta ce "Na sanshi amma na manta a ina?"
"To ki cire niƙabin ko zai gane ki"
Ummi ta jinjina kai tana ƙoƙarin cirewa, aka yi sallama.
Bayan matar farko ta biyun ma tayi, a nan take ummi ta daskare, ƙirjinta ya buga da ƙarfin gaske, ta ji tamkar numfashin ta zai bar ƙirjinta, wata irin tsuma ta ji ta fara yi, amma ta gaza motsawa.
Malam ya ce "Daga zuwa barka kun yi zamanku, gashi kun yi baƙi tafiyayyu daga kano"
Ta ce "Baban ummi ne?"
Malam ya ce "Eh shi ne, tun da shikaɗai ki ka sani a kanon ba"
Shigowa suka yi tare, tana riƙe da mayafinta a hannu, hannunta kamar amarya an yi mata lalle yayi jawur.
Ba ta kalli baban ummi ba, kai tsaye ummi ta zubawa ido, yayin da ummin ma ta zuba mata ido, tana jin yadda ƙirjinta ke lugude. Gaba ɗaya suka zuba musu ido, kai tsaye ta nufi ummi ta zauna a gabanta, tana cigaba da kallon ummi ta niƙabinta.
Ta miƙa hannu a hankali ta ɗaga niƙabin ummin, tayi tozali da fuskar ummin da a duniya bata ganin kyan komai, kamar yadda take ganin kyawun wannan fuskar.
A gigice ummi ta yi mata wata irin runguma ta fashe da matsanancin kuka, saroro mariya tayi, ta kasa taɓa ummi sai hawaye da ya fara zuba daga idonta.
Mama ta miƙa hannu tana faɗin "Ki yi mata a hankali ba ta da cikakkiyar lafiya"
Mariya ta buge hannun maman da ƙarfi, ta ruƙunƙume ummi, tana wata irin ajiyar zuciya kamar za ta fita daga hayyacinta.
Ta miƙa hannu ta warware mayafinta, ta lulluɓe da ummi da shi, ta ɗaukko mafici kuma tana yi mata fifita tana kuka.
Sai a yanzu suka gane wacece, malam ya sunkuyar da kai yana hawayen tausayin ƴar sa.
Ya zura hannu a aljihunsa ya ɗaukko wayarsa, ya kira Maryam a waya da kuma yaya ɗan lami.
"Ummina, kina cin abinci kuwa? Naga duk kin rame, iya tana yi miki wanka? Ko dai zazzaɓi ne a jikinki?" Tayi maganar tana ɗora hannu a goshin ummi.
Wasu irin jijiyoyi suka ɗaɗɗaga a goshin ummi, wani irin riƙo take yi wa mariya, tana jin kamar an sanyata a wata ni'ima.
Sun fi mintuna talatin a haka, sun ƙi sakin juna, mariya sai kakkare ummi take yi, kar wani ya taɓa mata ita.
Dr. Yayi gyaran murya ya ce "Yau na cika alƙawari ko?"
Ta jinjina masa kai, tana kuka ta ce "Wallahi ba zan taɓa yafe wa iya ba, Allah ya saka mini zaluncin da ta yi mini, ta ƙwace mini ummi bayan ba son ta take yi ba, ta ce ni na kashe mata ɗa, kalli yadda duk ummi ta rame, haka zan kwanta in yi ta mafarkin ummi tana kuka, tana cewa na zo na tafi da ita"
Ta ɗago ummi tana goge mata hawaye ta ce "Ki daina kuka kin ji ummana, ba zan sake bari a mayar da ke wurin iya ba, na san ba ta sonki ba ta ƙaunarki, ban san me ki ka yi mata ba, wallahi ba zan yafe mata ba, yaya ɗan lami yaƙi dagewa ya karɓo mini ƴa ta, kullum sai na yi kuka saboda ummi, yaya maryam ma ta hantare rannan wai kamar nikaɗai ce me ƴa, ki daina kuka kin ji ummina, da kaina zan din ga yi miki wanka, ina baki abinci, katifata zata ishemu mu din ga kwana tare, ba zan sake bari a kai ki wurin iya ba kin ji mamana"
Ummi ta ƙura mata ido, yadda mama ke wannan surutan daga wannan zuwa wancan tare da kasa gane ummi ta girma yanzu, ya tabbatar wa da ummi cewar mariya bata da lafiyr ƙwaƙwalwa.
Ta miƙa hannu ta ɗaukko ledar pure water, ta buɗeta ta saka wa ummi a baki tana faɗin "Na san ƙishirwa ki ke ji ummi, sha ruwa kin ji"
Babu wanda tausayin ummi da mariya bai kama a wurin ba, uwa kenan duk da ciwon ya motsa ba ta hayyacinta, amma hakan bai hanata gane ƴar ta ba, duk da shekarun da suka shafe basu haɗu ba.
Dr. Yayi gyaran murya ya ce "Alhamdilillah ala kulli halin, na gode Allah da ya sanya ummi da mahaifiyar ta suka haɗu, ba tare da ta Allah ta kasance ba. Ummi na yi miki laifi, kuma na yi muku duk da ina godiya da fahimta ta da ku ka yi.
Ummi ban ƙi sada ki da mahaifiyarki dan baƙanta miki ba, a lokacin da na ganota, tana cikin halin larura sosai, ba komai take ganewa ba, na yi fargabar haɗuwarku ba za ta yi daɗi ba, idan ku ka haɗu ta kasa gane ki, abu na gaba kuma ina tsoron halin da ki ke ciki, ya sanya ki ƙi zama ki dawo wurinta, alhalin kina tsaka da karatu, dan duk wanda yake ruwa, ko takobi aka miƙa masa zai kama, dan haka a matsin nan da ki ke, duk da kasancewar ki mai biyayya, zaki iya bujirewa ki zaɓi dawo wa gaban mahaifiyarki, ba tare da kin yi acheiving wani abu ba.
Wanda a lokacin babban burina da fatana, ki samu nagartaccen ilimi, da zaki iya tsayawa da ƙafafuwanki, ina fatan zaki yafe mini daga ke har mahaifiyar ki" yayi maganar a sanyaye.
"Ai dama kai na yafe maka, baka cuceni ba, amma iya iya iya, ban san me na yi mata ba, amma za ta maimaita a gaban Allah, amma wallahi ba zan yafe ba, na ji labarin azabtar mini da ummi ta yi, amma yaya ɗan lami ka ƙi dagewa ka karɓo mini ummina"
Dr. Ya ce "Haba maman ummi, ki yi haƙuri abun da ya wuce ai ya riga ya wuce, ki yi haƙuri dan Allah" yayi maganar yana haɗa hannayensa.
"Ai kai na ce na yafe maka, tun da ka kawo mini ummi, kuma kana saya mini magani da abun da nake so, har yaya ɗan lami na yafe muku, amma ban da iya da wanda suka ci zalin ummina, bani da abun da zan gani na tuna da bashir sai ummi, amma ta ƙwace mini ita dan ta wulaƙanta ni"
Dr. Ya ce "Ba gani a gabanki kina kallona ba?"
"Yaya Yahaya ne fa ba Bashir ba, na gane ka yau" yayi murmushi ya fahimci memoryn na ta yana yi yana seizing ne.
Sun sha mamakin yadda ummi ta girma, ummi kuma kallon mamanta take yi, kamar ba ita ta haifeta ba, haryanzu shar da ita, gashi gaba ɗaya ba sa kama, sai kaɗan, kamar ya da ƙanwa ba uwa da ƴa ba.
Dangin mama kamar su cinye ummi, a yamamcin nan suka din ga zaryar ganin ummi, sai dai ta ɓoye ummi a bayanta, kowa ya zo sai dai ya hango ummi daga nesa wai kar a ɗauketa a mayar da ita wurin Iya.
Ummi ta ga ƙauna da soyayya, mariya ta din ga zuba mata hira, wata tana ganewa, wata ba ta ganewa, ummi space take son samu, ta kira raihan a waya ta sanar masa.
***
Raihan yana zaune a falon hajiya Aisha yana kaɗa ƙafa, yana danna wayarsa cikin damuwa, ya kasa samun ummi a waya.
Falon ta shigo cikin takunta na ƙasaita, ta samu wuri ta zauna ta kalli raihan ta ce "Kai, babanka ya kasa samunka a waya, yana ta ƴar murya a lallaɓoka ka koma fa"
Raihan ya gyara zamansa ya ce "Wallahi ko dan saboda Alhaji ban so na taho ba, mami ce taƙi tsayawa ta fuskance ni, na rasa yadda zan yi da ita wallahi, taƙi fahimta ta kuma anty rakiya ce take zigata"
"Kai dalla can, na kirata mun yi magana da ita, ba abun da za ta sake yi a kan maganar, ita ba a auren aka aureta? Mu ba auren zumunci ake a danginmu ba, babanka shi ya fara karya mana wannan ta'adar, ya aurota daga nan kowa ya samu ƴancin yin hakan, sai yanzu ita kuma ta ce ba za a auro wata ba?"
Raihan ya ce "Abun kuma har da gori?"
"Eh an yi mata gorin, da ai ba ayi ba, siyama na nemanka wai ka je ta girka maka menene oho mata"
Yayi murmushi ya ce "Nifa yanzu abincin
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 35 Chapter of 54