mata kallo, shekaru sun ɗan ja, ta girma yanzu, amma tsaf da ita, tana samun kyakywar kulawa.
Ya dubi ɗanlami ya ce "Ɗan uwa, kuma a haka ba ta da lafiya?"
Yaya ɗanlami ya ce "Babu lafiya, wasu lokutan dai hankakin yana dawowa, wasu lokutan kuma sai ciwon ya dawo tayi ta shirme. Amma a hakan nan da take, za ta yi wanka, tayi shara tayi kwalliya ga shirin dutse nan ma gashi ka ganta tana yi, likita ne ya ce a samo mata abun da zai din ga ɗebe mata kewa.
Ka ga yanzu tafi sati ba ta yi magana ba, ba ta duka ba ta zagi, kaga daga mutuwar mijinta, ga rabata da ummi, ta zo ta haihu ɗan ba rai, tayi jijjiga depression yakamata sai kuma dai ta samu matsala gaba ɗaya.
Ban taɓa tunanin wani daga dangin baban ummi zai biyomu ba, dan mun yi alƙawarin ba zamu sake zuwa ba, irin jafa'i da mugun bakin da mahaifiyar ku tayi wa ƴar uwarmu, ya sanya muka ce gara mu yanke alaƙa da ku kawai".
Dr. Yayi ajiyar zuciya ya ce "Tun da na ɗauki yarinyar nan, nake fafutukar neman ina ku ke, ni ban san garin nan ba, ainihin in da kuka zauna aka aureta, mun je aka ce ba kwa nan, abubuwa dai duk ba su yi daɗi ba, sai fatan Allah ya kyauta".
Mama da yaya maryam da suke gefe suka amsa da amin, dan maryam ta zo gida yau, babu tsammani suka ga kawu yahaya.
Maryam ta ce "To ya ummin take? Ba ka zo mana da ita ba?"
Ya girgiza kai ya ce "Ba yanzu ba, ummi na nan a jami'a".
Yaya maryam ta ce "Dan girman Allah, ummin?"
Yayi murmushi ya tashi ya ƙarasa gaban ta ya zauna yana kallonta, ba tare da ta ɗago ba tayi murmushi ta ce "Baban ummi"
Ya ce "Na'am".
"Jigidata da ka tsinka mini nake gyarawa"
Sunkuyar da kai suka yi cike da jin kunyar abun da ta faɗa, dan tafi sati ma ba magana.
Yayi murmushi ya ɗebi dutsen da take ta shiryawa ya ce "Gaskiya ban kyauta ba, ki haɗa wata maza".
Ta sake yin murmushi ta ce "Da na san zaka dawo, ai da na yi kitso, an yi mini lalle, kaina ba kitso, bana son kitso tun da ka tafi bana son kitso" tayi maganar tana cire hular kanta, gashin kanta baƙi wuluk ya bayyana.
Yaya maryam zata yi magana, ya ɗaga mata hannu tare da girgiza mata kai, ya ce "To tun da na dawo yanzu sai ayi ko?".
"Ba zan yi ba, tun da ka tafi ka bar ni, ka ƙi ka dawo, Iya ta ƙwace mini ummi, ɗa na ya mutu ka ƙi ka zo ka ganni kuma bani da lafiya" tayi maganar tana kuka wiwi.
Ya ce "To ki yi haƙuri, ki yi haƙuri ba zan sake tafiya naƙi dawowa ba"
Ta riƙo hannunsa ta na cigaba da kuka ta kwantar da kanta a hannunsa ta ce "Baban ummi"
Ya amsa mata da "Na'am"
Ta ɗaga kanta ta kalleshi ta ce "Ka je ka karɓo mini ummina, Iya ba zata din ga yi mata wanka ba, ko idan yamma ta yi ta saka mata kayan sanyi, ba ta son ummi, dan Allah baban ummi ka karɓo mini ummi, kaga katifata ta ishemu ni da ita, idan ka sai mana gida sai in dawo gagarawa ko?"
Ƙura mata ido yayi, cike da matsanancin tausayinta, lallai yana daga horon da za ka yi wa uwa, ka rabata da ɗan ta, duk da tana cikin hauka, amma ba ta manta da ƴar ta ba.
Yayi ajiyar zuciya ya ce "To shikenan, ki daina kukan ya isa haka, mayar da hularki, kiyi haƙuri" ta ɗauki hularta ta saka.
Ta ja bakinta ta sake yin shiru.
"Zan kawo miki ummi in sha Allah, amma ba yanzu ba".
Yaya maryam ta ce "Saboda me? Abun da ta daɗe tana jira kenan, ka taimaka".
Ya ce "Ina da dalilina, kuyi haƙuri dan Allah"
"To amma mu ai ka bari muje in da take".
Kawu yahaya ya ce "Da ina da ƙudurin rabaku da ummi, da ba zan neme ku ba, ina da hujja mai ƙarfi sosai.
Zan cigaba da shiga lamarin nemawa mariya magani in sha Allah, komai zai daidaita kuma zai wuce".
Ba haka suka so ba, amma ba su san takamaimai menene dalilinsa na ƙin haɗa su da ummi ba.
***
Hangen dala ba shiga birni ba, domin kuwa inteesar tayi zaton soyayyar da suka sha da sagir a waje, ita za aje a cigaba da yi a gidan, sai abun da take so shi zai din ga yi mata, amma ina.
Ya nuna mata shi namiji ne, mage mai kwanciyar ɗaukar rai, a gida ta saba ba abun da take yi, ummi ce take komai. Yanzu kuma ya ce shi ba zai ɗauki ƴar aiki ba.
Dan haka sai komai ya din ga bata wahala, asubar fari zata tashi ta haɗa masa breakfast, gashi su yi ta faɗa dan abincin nata ba daɗi, ga almubazzaranci kamar ba mace ba.
Ga rashin kunya da rashin iya magana, gashi ɗan uwan mata, yana da tarin yayye da ƙanne mata, ga uwarsa mai shegen sanya ido. Sai ƙannensa su zo gidan su fi sati, gasu manya duk sun girmeta, su yi ta yi mata rashin mutunci, idan tayi magana su ce za su yi mata dukan tsiya.
Abun duniya ya damu inteesar, ta dawo gida tana kuka, ta gayawa mamanta.
Farida a zatonta zata iya maganin abun, ta kira Sagir tana masifar dan me ba zai tsawatarwa ƙannensa ba?
Ya ce mata ba zai iya ba, baya son ya saɓawa mahaifiyarsa.
Abu kamar wasa aka fara jamb, kawu yahaya ya turawa inteesar kuɗi, ya ce taje tayi jamb, a nema mata admission.
Amma sagir ya ce ba yanzu ba, sai ta haihu, domin kuwa a lokacin ma laulayi take yi.
Kawu yahaya bai matsa ba, farida ta din ga masifar dan me ba zai dage sai inteesar ta fara makarantar yanzu ba?
Ya bata amsa da "Yanzu ya fi ni iko da ita, shiyasa tun tana ƙarƙashin ikona, na so ta fara makarantar, yadda bai isa ya hana ba, amma ku ka dage, dan haka ni ba abun da zan ce".
***
BAYAN WANI LOKACI!.
Kasancewar tsakiyar damuna ne, an ɗan kwana biyu ba a yi ruwan sama ba, dan haka ana tafka zafi, ga uwar rana da ake ƙwalawa.
Tamkar ba ita ranar ke duka ba, haka take tafiya sannu a hankali, tana ratsa layukan unguwar, sannu a hankali take tafiyar, tamkar tana tausayin ƙasa, kamar mai rangji haka take tafiyar kamar tana tausayin ƙasa.
Ta cikin niƙabinta take kallon dogon layin, tare da lissafa sauran tafiyar da ta rage mata, ta isa in take fatan zuwan.
Layin shiru, sai lokaci lokaci, ababen hawa ke giftawa, manyan gidajen layin ko ina a rufe.
Ƙarar babur ta ji, kasancewar gefen hanya take bi, ya sanya ko a jikinta, dan ko waiwaya wa ba ta yi ba, ashe layin da yake gabanta yake ƙoƙarin shiga.
A ɗan fusace ya ce "Ke, kurma ce ne? Sai mutum ya tureku, ace bai kyauta ba, ba ki ji ina horn bane?"
Ta tsaya cak, ta ɗan ja wasu seconds, sannan ta juyo ta kalleshi ta cikin niƙab, sai dai ba ta ce komai ba.
Maimakon ya wuce ya tsaya ya ji me za ta ce, idan rashin kunya za ta yi masa, ya ƙare mata ta tas.
A hankali ta ce "Sorry, ga hanya wuce" tayi maganar tana ɗan ja baya ta bashi hanya.
Fuskar ta a rufe da niƙabi, amma muryarta ce ta saka shi ƙara kallonta.
"Malama idan zaki ware murya ki ware, da na bugeki ai ba zaki maƙale murya ba".
Ta ce "Ikon Allah, me muryata kuma tayi maka, ai na ce ka yi haƙuri ka wuce"
Tsaki yayi ya ja babur ɗin sa ƙirar lifan, ya yi gaba.
Ita kuma ta yi ajiyar zuciya, ta cigaba da tafiya.
A ƙofar ƙaton gate ɗin gidan ta tsaya, mutum biyu ta tarar sanye da uniform na security, suka dubeta suka ce "Gurin wa zaki je?"
Ta ce "Habu baka gane ni ba?"
Jin muryarta ya sanya shi cewa "Ahha wata sabon gani, ke dama kina duniyar nan?"
Ta ce "Ina nan mana, ya aiki ya kwana biyu?".
"Alhamdilillah, gaba ɗaya tun da ƙawarki ta bar gidan nan muka daina ganinki"
"To ai gashi na zo wanke laifina yau, ina fatan mami na nan?".
Ya ce "Eh tana ciki"
Ta ce "Yauwwa na gode" ya buɗe mata ƙaramar ƙofar gate ɗin, ta shiga ciki.
Ɗayan ya kalleshi ya ce "Ka barta ta shiga? Baka kira hajiya bilkin ba, kuma ba ta ɗaga niƙabinta ba".
Habu ya ce "Ai ƴar gida ce, ƙawar maryam ce, tun da tayi aure ne ta daina zuwa".
Ya ce "Ok, na so ta ɗaga niƙabin naga fuskarta, muryarta tayi mini daɗi".
"Ji ɗan wahala, ka sani ko yanzu tayi aure, ka shiga hankalinka".
Ummi kuwa sashin mami ta nufa, fasalin gidan yana nan yadda yake, amma yanayin fentin da aka sassauya masa da wasu abubuwan zaka san arziki ya fi na da.
A falo ta tarar da mai aiki, duk da ƴar bata san ƴar aikin ba, suka gaisa sannan ta tanbayeta ko mami tana nan.
Mai aikin ta ce "Eh, tana falon sama"
"Ki ce mata ummi ce ta zo" mai aikin ta jinjina kai ta nufi ƙafar benen ummi kuma ta zauna.
Bai kai mintuna biyar ba, mai aikin ta saukko, ta ce wa ummi ta shiga.
Ummi ta tashi ta bi bayan ƴar aikin.
Da sallama ummi ta shiga, mami ta waiwayo tana cewa "muryar wa nake ji ne haka? Gaskiya koma nayi fushi"
"Tuba nake mami"
Sai dai tana zagayowa, ta tarar da na kan babur da ya kusa tureta da lifan, yana zaune ya barbaje ƙafa a kan centre table, sai yanzu ta gane a in da san shi.
Sai da ya ɗan sake ɗaga kai ya kalleta shi ma.
Nan suka gaisa da mami, mami nata mitar ummi ta ɗauke ƙafa ta daina zuwa tunda maryam ta bar gidan.
Ummi ta kalleshi ta ce "Ina wuni?"
Ya basar ya ce "Lafiya ƙalau"
Mami ta ce "Laaa ka amsa kuwa? Kema meyasa ki ka gaishe shi? Ƙaninku ne fa, ƙanin maryam ne Raihan ne.
Kai kuma ka amsa kamata yayi fa ka gaisheta" ya wani basar.
Ummi ta ce "Ƙyaleshi mami, ai dama su Allah ya bawa girman" tayi maganar tana ɗaga niƙabin fuskarta.
Sai yanzu shima ya ganeta, ranar saukarsu da maryam a makaranta.
Mami ta ce "Ya wani je ya tara gemu, yafi kowa girma kai ka ce wani babba ne, ni wannan gemun ina tantama idan ba mai ya shafa ya fito ba, dan ga gemun nan dai, amma hankali da saura".
Ummi ta yi murmushi ta ce "Girma ya riga hankali kenan" sai da ya ɗan buɗe baki jin abun da ummin ta faɗa.
Mami ta ce "Eh mana, ya makaranta ummi?".
Ummi ta ce "Mami makaranta muna jiran result"
"Masha Allah, lokaci ba wahala har kin gama ummi, Ubangiji Allah ya sanya alkhairi, to ya batun aure kuma? Ko invitation ki ka kawo mini?".
Ummi ta sunkuyar da kai, tayi murmushin yaƙe ta ce "Tukuna dai mami"
Mami ta ce "Ya salam, Allah ya kawo nagari ummi, yanzu fa maryam kusan shekarar ta bakwai da aure, ke kuma shiru duk ƴan islamiyyar ku sun yi aure, saura ke, amma kar ki damu komai lokaci ne"
Ummi ta ce "To mami, bari na yi alwala dan Allah"
Mami ta ce "To shikenan ba damuwa, je ki yi"
Ummi na tashi raihan ya kalli mami ya ce "Dan Allah mami fisabilillahi meye na tambayar invitation ta kawo miki? Da shi ta kawo miki ai ba sai kin tambaya ba, kin ce shekarar maryam bakwai da aure ita ba ta yi ba, kin dawo kin ce tayi haƙuri lokaci ne, kamar fa kin mari mutum ne kina sane sannan ki ce yayi haƙuri".
Mami ta ce "To uban tsari, ai da tausayi yakamata ace ita ma ta tashi haka, in da take tana shan wahala, matar yayan babanta ke wahalar da ita, shiyasa nake tambayarta ko auren ne ya zo, ta huta".
"Matsalarku kenan mata, kune maƙiyan kanku, ladan ake rubutawa mace idan ta azabtar da ɗan wani? Kuma duk tausaya matan da ki ke, tun da dai ba ki samo mata mijin nan ba, ai sai ki yi mata addu'a, is like an insult at times, ka tambayi mace maganar aure, ni idan mace ne faɗa za ayi da ni"
Mami ta ce "Kai,tashi ka je mini aike na uban tsari".
"To ɗaukko kayan, ki haɗo da kuɗin shan mai".
"Duk kuɗin da babanka yake baka, sai ka damfareni dan zan aikeka, to ba zan bayar ba".
Ya kashingiɗa ya ce "Mami idan kina son aiken nan a kan lokaci, ki bayar da cin hanci " tashi mamin tayi tana hararsa.
Hakan yayi dai-dai da fitowar ummi, fuskarta a jiƙe da ruwa, gaban gashinta duk a kwance, gashin girarta ma tamkar za su haɗe.
Fararen idanuwanta suka bawa brown ɗin ƙwayar idonta fitowa sosai da sosai.
Ƙwayar idonta yake son kalla, domin tabattar da kalarta, sai dai bata bashi damar hakan ba, dan mayar da niƙabin ta rufe fuskarta, ta tayar da salla.
Mami ta dawo falon da ATM ɗinta, tana yi wa Raihan kashedin ya je ya dawo da wuri.
Ya karɓi ATM ɗin yaƙi tashi, ummi ta idar da sallar, tayi Addu'a ta cewa mami za ta tafi, tashi yayi ya riga ummi fita.
Mami ta ce sai ta tsaya ta ci abinci, amma ummi ta ce sauri take yi.
Ta ajiye wa mami kyautar kwalbar turaren humra.
Kuɗin motar da ta bawa ummi ma, ƙin karɓa ta yi, kuma da ganinta ka san tana buƙata amma mursisi taƙi karɓa ta tafi.
A babban falo ta tarar da shi, yana taje sumar kansa.
Har zata fita ya ce "Ki tsaya mu tafi tare na ajiyeki ko a titi ne"
Ummi ta girgiza kai ta ce "A'a na gode sosai, zan ƙarasa" bai kuma ce mata komai ba ta fito daga falon.
Ta fita harabar gidan, hakan yayi dai-dai da fitowar wata babbar mace, ta sha ado da lace blue, hannunta da wuyanta duk gold.
Wani matashi yana biye da ita, kai da ganinsa ka ga ɗan shaye-shaye.
Da sauri ummi ta ƙarasa in da matar take, ta ɗaga niƙabinta ta durƙusa ta gaisheta.
Matar ta faɗaɗaɗa murmushinta ta ce "Ummi yau kece a gidan, ba dan Allah yasa na fito ba tafiya zaki yi bamu gaisa ba?"
"Ba haka bane hajiya, a gurguje na shigo ne, kusan kullum ta hanyar nan nake bi, shiyasa na ce yau dai bari na shigo"
"Eh amma zaki tafi bamu gaisa ba ummi, ya gida ya makaranta?"
Ummi ta amsa da Alhamdilillah.
Hajiya ita ce uwar gidan mami, tun lokacin maryam na nan, tana son mu'amala da ummi saboda nutsuwarta, amma ummi ta janye jikinta ta daina zuwa gidan ma, saboda ba a ga maciji, tsakanin mami da Hajiya.
Ummi ta gaida Salim da suke tare da hajiya, ya amsa mata sama-sama.
Hajiya ta ce "Ummi kin yi aure ne?" Ummi ta girgiza mata kai.
"Ai da kin yi aure ban sani ba, sai mun yi faɗa".
Kamar an jefo shi, ya dafo kafaɗar hajiya yayi ƙasa da murya ya ce "Ku daina yi wa mutum irin wannan tambayar babu daɗi"
Hajiya ta yi murmushi ta ce "To babban mutum".
"Biki zaki je kenan?"
Ta ce "Eh, ƴar set ɗinmu ke auran ɗa"
Raihan ya ce "Shiyasa ki ka sha kwalliya, kamar ƙawar amarya mu ga jakar" ya karɓi jakar hajiya ya zuge.
Ya girgiza kai ya ce "Allah sarki Alhaji, an ɗebi kuɗinsa za aje ayi liƙi, to nima bari na ɗebi rabona" ya zura hannunsa ya ɗebo kuɗi ya zura a aljihunsa.
"Raihan abun har da gori, sai ka gayawa duniya kuɗin babanka ne"
Yayi dariya, ya ce "A dawo lafiya"
Ummi ma ta ce "Hajiya bari na tafi, a dawo lafiya "
Hajiya ta ce "A'a ummi, shigo mu fara aniyeki, sai mu ƙarasa wurin bikin"
Ummi ba za ta iya jayayya da hajiya ba, dan haka ta ce "To na gode"
Har ummi ta juya zata bi su ya ce "Eh ba shakka, ba zaki hau babur ba sai mota shikenan ai".
Lokacin suna Islamiyya, Maryam bata da aiki sai bayar da labarin Muhammad Raihan, barkwancinsa da kuma tsokana, tsokanar ma irin mai cika cikin nan.
Dan haka ummi ba ta waiwayo ba, tayi murmushi ta bi bayan su Hajiya.
Ayshercool
08081012143
Whats app only please 🙏
*CUTARWA!*
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
P22
FOLLOW ME ON WATPAD VIA THIS LINK.
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
Masu neman free books ɗina, da free pages duk akwai a kan watpad account ɗina. Irinsu
Abduljalal
Wata kissar sai mata
Wuta a masaƙa
Cutarwa
Ƙanwar maza
Gaba da gabanta
Aƙidata
Ruɗin ƙuruciya
Zaku iya samun paid pages ɗin a Arewabooks @ayshercool7724. Ko ku tuntuɓe ni kai tsaye ta lambar wayata.
08081012143.
And also don't forget to subscribe my YouTube channel via this link.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ayshercool.
PAID ADVERT!.
Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi.
Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku
Oll types of Turaran wuta
Sandal
Halut
Irik
Difur
Gab Gab
Kajiji
Habil
Nabak
Humra
Kulakcha
Dilke da kalta
Kayan
Garan jiki
Muna turara
Kaya
Kujerar garan jiki
Kannada
Madarorin turare masu kamshi
Man garan gashi
Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche
Ku nememu a wan nan no 08065728702 08025453921
*TALLA!TALLA!TALLA!*
*INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*.
*BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU*
*MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA*
BRIGHT PENS A SHIRYE MUKE, WURIN KARƁAR TALLACE TALLACENKU CIKIN FARASHI MAI SAUƘI.
22
Raihan ya nufi in da babur ɗin sa yake, ya ɗauka ya fita daga gidan.
Suna tafe suna taɓa hira da ita da Hajiya, duk da ta kasa sakin jiki da hajiyar sosai, saboda yadda take matuƙar jin nauyinta.
Har kan layinsu suka kai ta, ummi ta yi ta musu godiya, sannan ta sauka ta nufi gida.
A harabar gidan ta tarar da Abdul hannunsa riƙe da waya. Yana ganinta ya tsaya yana jiran ƙarasowarta.
"Yaya ummi ina ki ka shiga ne?".
"Na ɗan biya wani wuri ne, meyafaru?"
Maama sai faɗa take yi, intee ce aka dawo da ita, wai ta kuma yin ɓari, zasu tafi asibiti zata bar miki sallahu baki dawo ba.
Ummi a ranta ta ce 'Ga kausar a gidan, ita ba za a bar mata sallahun ba'
A zahiri ta ce "Subhanallah, ubangiji Allah ya bata lafiya".
Ya amsa da "Amin, Allah ya taimake ki sun tafi, yanzu na dawo daga kaisu, kafin su dawo na san ta huce ba za ta yi miki faɗa ba".
Ummi ta ce "Haka ne, bari na yi sauri na shiga ciki"
Ta ƙarasa ɗakinta, ta yi wanka a gurguje, ta canza kaya ta saka hijjabinta na zaman gida, ta nufi kitchen.
Ta tarar da noor tana wanke-wanke a kitchen.
"Mama aiki ki ke yi haka?"
Noor ta ce "Eh, rage miki aikin nake yi, na san a gajiye zaki dawo, na ɓoye miki abincinki a ƙarƙashin dining, kar a cinye ba ki ci ba" tayi maganar cikin iyayi.
Ummi ta yi murmushi ta ce "Na gode sosai mama, bari na je na ci abincin, in zo mu ɗora abincin dare"
Noor ta ce "Kije ki yi bacci ma ki huta, zan yi miki greating kayan miya, na yi miki mopping"
Murmushi ummi kawai take tana kallon noor, soyayyarta da noor gamon jini ce.
Bayan magariba Rayhan ya dawo yana zaune a falon mami, yana ta bawa ƙannensa umarni, duk barkwancinsa idan yana nan basa wani sakewa saboda akwai dealing.
Mami na zaune a gefe tana cin abinci, tana kallon citruss.
Ya kalleta ya ce "Mami kin san ina ta yi wa baƙuwar ɗazu kallon sani, sai daga baya na tuna a wurin saukar su Maryam na san muryarta, dan ban ga fuskarta ba ranar"
Mami ta ce "Auu wai ummi, yarinyar kirki".
Ya ce "Tana da tarbiyya sosai tun ranar da na ganta a wurin saukar nan, tubarkallah idonta mai kyau, ban taɓa ganin irin idonta ba".
Mami tayi dariya ta ce "Kaga iskancin da su maryam suka din ga yi mata suna Islamiyya, saboda fatarta da idonta, duk in da maryam ta zauna sai ta bayar da labarin baƙin ummi. Gashi uwar riƙonta na azabtar da ita, ai ainihin ƙawancensu ma, maryam ce ta ture ta, ta faɗi ashe ƙonuwa ce a cikin ta, ta dinga zubar da jini, uwar riƙon ta ƙonata da dutsen guga a ciki, shima da ƙyar ta gayawa malaman ƙunar duk ta jagwale"
A razane raihan ya tashi zaune, ya ce "Ta ƙonata da dutsen guga fa ki ka ce?"
"Wallahi kuwa, maryam ta ce kusan kullum cikin kuka ummin take, kuma bata magana sai ta ga dama, duk yadda za ayi da ita, ba zata faɗi ga abun da yake damunta ba, sai kuka".
Ya murza goshinsa a hankali ya ce "Mami kuma babu wani abu da ki ka yi, ki taimaka mata a wannan lokacin?"
"Rufa mini asiri, ai yanzu ba a wannan shishshigin, na so dai na din ga taimaka mata financially, amma yarinyar nan ba a bata kyauta ta karɓa, halint sai ita"
Ya dinga kaɗa ƙafarsa a hankali yana tunani, gaba ɗaya kalar ummi ba mai hayaniya bace, hasali ma fuskarta kalar tausayi ce.
To wani laifi za ta yi wa mutum, har a ƙonata da iron a ciki, ita kuwa wannan wace irin azzaluma ce.
Labarin da mami ta bashi tana dariya, bai ga abun dariya ba a ciki, na cewa yara na tsokanarta saboda tana da duhu da kuma ƙwayar idonta, meye a baƙar fata duk halittar Allah ce, kuma idanunta meye aibunsu, ai abun a hukunta su ne a wancan lokacin, ga child abuse a gida, makaranta ga takura daga abokan karatunta, Allah ka ɗai ya san the hardship she goes through.
Dan bai manta yadda Maryam ke bashi labarin abun da ake yi wa ummi ba, da yadda take kwatanta masa baƙinta, sai duk iya ƙoƙarin sa wurin gano muninta shi bai gani ba.
Fuskarta kawai yake hangowa, ko ɗazu da suka yi faɗa kan ya shigo bashi da gaskiya, amma ta bashi haƙuri, komai nata simple ne.
Ya miƙe tsaye ya ce "Mami sai da safe, bacci nake ji" yana gama maganar ya fita.
***
Ko da farida ta dawo sai da ta ci wa ummi mutunci, duk da ta san ummin wurin aiki take zuwa, domin kuwa bautar ƙasa take a lokacin a wani gidan jarida, daily news.
"Maama dan Allah ki daina yi wa anty ummi faɗa, ba gashi nan duk mun gama yi miki aikin gidan ba".
Cikin tsawa ta ce "Idan ina magana ki na saka mini baki sai na yi ball dake" tayi maganar tana nuna noor da yatsa.
Ta mayar da idonta kan ummi ta ce "Dan kan ki, gaba ɗaya kin mayar mini da yarinya fitsararriya mara ɗa'a kamar ke, zaki haifa ne kema. Sakwara zaki daka, da jar miya, kije Abdul ya kai ki asibiti ki kai wa inteesar ki kwana da ita asibiti, kausar ta dawo gida".
Daga auren inteesar zuwa yanzu, tayi ɓari ba adadi, dan kamar har mijin nata ya fara ƙosawa da hakan.
Ummi ta je kwana da ita, ta tarar ana yi mata ƙarin jini, duk ta rame, ƙannen mijin suna zazzaune, suna ta hirarsu ko a jikinsu da halin da take ciki, kausar ce a kusa da ita a zaune, ita ma kuma danna wayarta take yi.
Ko da ta ga ummi ta wani haɗe rai ta yatsine fuska ta ce "Dan wulaƙanci, tun kan mu taho asibitin nan ake jiranki, amma ki ka ƙi dawowa kin bar mutane da yunwa, kuma kin san dai ba iya cin abincin sayarwa muke ba"
Ummi ta ja wuri ta zauna ba tare da ta kulata ba, suka gaisa da ƙannen mijin inteesar.
Babu kunya suka ja kwanon sakwarar nan suka buɗe, suka ci abin su, suka gama suka ƙara gaba.
Sai da inteesar ta yi sati a asibiti, ummi ce ke sintirin kai abinci da ɗawainiyar kwana da ita, amma duk basa gani sai rashin mutunci da hantara, gashi idan ta kwana kan wani yazo daga gida ta koma ta shirya ta tafi in da take SIWES, sai ta makara sosai da sosai.
Idan ta je wurin aiki, shima ayi ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 54