wachan Abu ke ruling a tasa zuciyar"
"hahaha ki yayyafawa zuciyar ki ruwan sanyi Qawata Haisam da kansa zai nemi soyayyar ki, alkawarina ne wannan"
"Nagode Qawata"
Mikewa Tayi Tace "mu tafi ko?"
Cikin rashin fahimta mardiya Tace "Ina zamuje?"
"Gida Man"
"Lectures d'infa"
"na yafe" tana kaina ta fara tafiya,bakiea bud'e mardiya ke kallonta,ganin da Gaske take ta Mike ta bi bayanyanta da d'an sauri had'e da gudu, motar Aysha suka nufa,tada motar tayi suka bar cikin school d'in, dropping d'in mardiya tayi kana ta wuce gida,dage unguwar su d'aya hatta layin su ma d'aya hakan yasa bata 'bata lokaci ba ta isa gida.
Karfe 4:10pm
Bayan ta gama lectures ta tsaya jiran sa har sai karfe 6 da Yan mintuna ya Zo suka Kama hanyar gida, yana driving sunan sharar hirar su.
Chan Tace "Yaya Ayshan Nan a ajinku take ne?"
"a'a Yar aji d'ayane?"
"To how comes Kuka Saba?"
"Sabawa a hakan? It's just this Saturday muka had'u fa, itace ma ta karb'i number na"
"sabida me?"
"Wai so take na Zama Tutor d'inta"
"Tutor kuma, Kuma ya yarda Yaya?"
" So kike nace Mata bazaiyu ba? Nifa Musulmi ne itama haka so hakkina ne Akan taimakawa ko wani Musulmi tunda ina da halin taimaka Mata me zai Hana naki amincewa"
Iska ta hura Tace "Hakane"
"Amma irin tambayoyi Haka princess am I safe?"
Murmushin yake tayi Tace "You're safe Mana Yaya, kawai dai naga sai aikin kallon ka take Kuma bata ji dad'in bani abinci a Baki ba, nayi tunanin ma itace auntyn tawa"
Dariya yayi yace "Haba princess ai da kece Zaki Fara sanin hakan,ni ba Soyayya muke da ita ba,hasali ma ban tab'a zaman minti 30 da ita ba"
"Amma fa Yaya Na lura Kamar son ka take"
"ah haba Dan Allah?"
"Allah kuwa"
"Lalle d'an Ni d'in Nan?"
Murmushi kawai tayi yace "Well bani da wannan lokacin Yanzu idan na tashi soyayyar ma ke zansa ki nema min Matar aure"
" Kamar dagaske"
"Allah kuwa dagaske nake miki na rantse miki da kauyen kakana"
Dariya tayi sosai Harda tafi, a Haka suna Hira har suka Isa gida.
Har cikin ranta taji dad'i ko ba komai hankalin ta ya kwanta, tunda tasan ba sonta yake ba, Bata da sauran damu sai na soyayyar sa da fatan ya fahimci hakan.
Suna isa gida suka tarar da su Mummy da Umma shigowar su gidan Kenan Suma, bayan sun gaisa ta wuce d'akin ta Shima Haisam ya wuce nasa d'akin, dake dukkanin su biyu suna da assignment basuyi kallon da suka Saba ba, hatta chat d'in ma basuyi ba.
Haisam na zaune akan gadon sa yana browsing yaga shigowar Kira ba wayarsa kallon time yayi yaga Karfe 11:38pm a bayyane yace "Aysha da Daren Nan?"
Picking yayi ya Kara a kunnen sa daga d'ayan 'bangaren tace "Barka da war haka yallab'ai"
Murmushi yayi yace "Yauwa Barka dai Yallab'iya"
Yar karamar dariya tayi Tace "da fatan dai ba bacci Kake ma tashe ka ba?"
"umm umm ba bacci nake ba, assignment nake yi"
"Oh so sorry na dame ka,duk da ma na ce ka Zama Tutor d'ina kaki ko?"
"No Kar ki damu, ba ki nayi ba ai na fad'a miki idan kin shirya ki Sanar dani"
" To na shirya gobe idan Allah ya Kaiimu"
"To Allah ya Kaiimu"
Ta amsa da "Ameen ya Allah"
Yace "ya kike d'azu kawai Kika tafi ba sallama"
"Uhmnn gani nayi ka fad'a lambun soyayya baka ji baka gani"
Dariya yayi yace "Soyayya Kuma Ni d'in?"
"Eh Mana Kai da princess d'inka harfa abinci naga kae Bata, nace lallai kud'in masoyan asaline"
Girgiza Kai yayi Kamar tana gaban sa yace "Ni ba Soyayya nake ba"
"Kiyayayya Kake yi Kennan?"
"Hahaha a a, to Shima dai d'an uwan soyayyar ne, amma taya za'ayi nayi soyayya da Kanwata?"
Cikee da farin ciki tace " Au dama kanwar kace? "
"Eh kanwatace da me Kika d'auka?"
"Na d'auka budurwar ka ce"
"To ki ajiye Kanwata ce,ai Ni bank da budurwa ban ma tab'a soyayya ba"
"Na dai ji ban yarda ba"
"Allah kuwa trust me ba wasa nake Miki ba,sai dai idan ke zaki nema min Yanzu"
"A a idan Kuma na nema maka waccce Bata maka ba Kuma fa?"
"Zata ma yi insha Allahu"
"To Insha Allah zan nema maka waccce zata dace da kai"
"Da kuwa naji dad'i sosai"
Nan sukayi ta hirar su kusan na mintuna 20 kana ta Masa sai da safe suka sauke wayar a tare, kwanciyar ta tayi yayin da Haisam ya cigaba da abinda yake yi.
________________________
Ba na ganin comment d'inku
Please kuyi sharhi sannan kuyi sharing.
Taku a kullum
Milhat
Yar Terawa
🍃 *DANGIN UBANA*🍃
Story & Written
By
Milhaart
Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne.
*🌍MANAZARTA*
*WRITERS ASSOCIATION📚🖊*
*M. W. A*
```Kungiya d'aya tamkar da dubu.Masu Nazari da Aiki da Ilimi, Burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma Nishad'antar da masoyan ta.🤙🏻```
https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa
____________________________________
*Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.*
Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️
*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*
Page
23&24
*...............WASHE GARI*
Kamar kullum a tare suka shiga school tun karfe 7 na safe, Yau Haisam ya Riga Ma'isha Gama lectures hakan yasa ya zauna zaman jiranta a Mango garden na cikin School.
Kiran Aysha ne ya Shigo wayar sa, picking yayi da sallama daga d'ayan 'bangaren ta amsa da "Wa'alaikassalam yallab'ai kana lafiya?"
"Ina lafiya ke fa?"
"Nima haka"
"Masha Allah ka Shigo kuwa?"
"Eh na Shigo"
"Ok please kana ina ne nazo na same ka"
"Ina mango garden"
"Okay muna kusa ma gani Nan karasowa"
Ya Masa da " okay" ya kashe wayan.
Girgiza Kai Aysha tayi Tace "Qawata Kinga bawan Allan Nan, Yana da wani habit d'in da bana so wallahi"
"Me Kenan fa?"
"Bai tab'a Kirana ba tunda Amma idan na kirasa shi yake fara cutting call d'in which is very bad" ta karasa maganar kamar zatayi kuka.
Mardiya Tace "It's not a big deal qawata tunda in Kika kirasa yana d'agawa Kuma yana sauraron ki ai Shikenan Kuma Nan gaba da kansa zai Rika neman ki"
Huci tayi tace "Shikenan tunda kince Haka shiyasa a ko wani lokaci idan ina bukatar shawara Kai tsaye ke nake nema nasan zan samu solution"
" I will always be here for you Qawata,yanzu dai tashi kije ki same shi before it's too late"
Aysha tace "I thought tare zamu"
"A a kaaai, kamata ai daga ke sai shi zaki fi fahimta" ta kashe mata Ido d'aya,duka Aysha ta Kai Mata ta kauce.
Mikewa tayi ta Masa sai anjimu da jaddada mata idan ta gama zata kirata sai su koma gidan tare,tayi tafiyar ta, ba d'au lokaci mai tsawo ba kasantuwar LT d'in da take da mango garden ba nisa hakan yasa tayi saurin Isa inda yake.
Da sallama ta karasa inda yake bayan sun gama gaisawa Nan ya mata umarnin da ta fito da handouts d'inta, Nan ya zari d'aya ya Fara mata tutorial d'in sunfi awa d'aya yana mata, Amma fa hankalin sa na Kan wayarsa minti minti yake dubawa daga bisani Tace "Akwai abinda kake jirane? Naga sai faman duba time kake"
"Hmmm eh, Time nake dubawa kar princess tayi ta jirana karfe 3 zata gama lectures"
Tab'e baki tayi Tace "Wai dole Kai Zaka kaita gida ne?"
"Eh Mana to wa zai kaita in bani ba?"
Ganin yanayin sa ya canza tayi saurin fad'in "Lallai kana ji da ita sosai Naga karfe 2 yanzu da sauran time ai"
Yace "Eh gashi wayata ta kusa d'aukewa ba chaji Kuma na baro cable a gida Dana saka a mota, kar ta Kira bata same Ni ba"
Ta amsa da "Hakane"
Yace "Anyways mu cigaba ko?"
Ta amsa da "Toh"
Nan ya cigaba da Mata tutorial d'in, ganin hankalinsa yayi nisa a abinda yake koya Mata tasa hannu ta kashe wayar tasa sannan ta maida ta ajiye.
Sun dad'e a zaune a gun ya d'auki wayar sa ya Danna yaga a kashe tsaki yayi yace "Damn it!!!"
Tace "Lafiya kuwa?"
Yar karamar tsaki yayi yace "Wayar ta d'auke"
"In time ne bari na duba maka a wayata"
Yace "Yauwa please duba min."
Aysha na duba time taga karfe 3 da kwata Tace Masa "2:30"
Zaro Ido yayi yace "Wai tun d'azun Nan 30 mints kawai mukayi?"
Tace "Eh"
"Lallai time baya gudu"
"Ko dai ka gajine? Mu bari sai gobe?"
"A a kar ki damu mu cigaba kawai."
Murmushin kyeta tayi ba tace Masa komai ba ya d'aura daga inda ya tsaya.
Ma'isha tafi minti 20 tana jiran sa, Kiran wayarsa take Amma switch off sai ta tuna tana da Number Farukh ta shiga dialling har kusa yankewa ya d'auka cikin Muryar ta mai dad'in sauraro Tace "Ya Farukh ina wuni?"
Ya amsa da "Lafiya"
cikin Muryar bacci, Tace "Am sorry kana bacci na tashe ka ko?"
Yace "Eh wallah but kar ki damu ya akayi?"
"Dama na d'auka kuna tare da Yayana ne"
"A'a mun rabu tun d'azu da mukayi sallar azahar but yace min zaiyi wa Aysha tutorail but ki kirasa ki ji"
"Uhmn number a kashe, Amma Bakomai nagode sai anjima" ta katse wayar tayi ba tare da ta ji amsar sa ba.
Girgiza kai yayi yace "kishi kumallon Mata, Amma guy d'in nan don ya raina min hankali yace min ba Soyayya suke da Ma'isha ba mtss" ajiye wayar yayi ya koma baccin sa, Ma'isha kuwa Mango garden ta nufa dake tasan wurin zaman sa Kenan yawanci.
Tun daga nesa ta hango su suna zaune dai dai lokacin da Aysha take dariyan sunan wani scientist da ya fad'a dariya take sosai Shima ya fara taya ta a Fili Tace "Tutorial d'in kenan" har ta nufi inda suke sai Kuma ta Canza shawara ta koma, gate na makarantar ta nufa tana fita ta tari napep ta wuce gida, ita kanta taji ta wani iri sabida shine karo na farko da ta shiga napep sannan shine karo na farko data Koma gida ba tare da Yayan ta ba.
Kiran sallah da akayi ne Haisam ya Mike a zabure Aysha ma mikewa tayi tace "Lafiya?"
"Kamar kiran sallah fa nake ji?"
"Eh Kiran sallah ne"
Ajiye Mata handout d'in yayi da saurin ya bar gun ba tare da yace mata komai ba, baki bta bud'e ta tsaya kallon sa har ta daina ganin sa bata bar mamaki ba, wa'anda suke zaune a gefen su Kuma suka tsaya kallon ta, tsaki tayi ta wurga musu harara da sauri suka kau da kansu Tace "magulmatan banza kawai Mtssw" ta d'auki Jakarta da handout d'in da Haisam ya ajiye ta bar gun.
Ma'isha na Isa gida ta tarar da su Mummy suna part d'insu Umma, hamdallah tayi ta shiga d'akin ta wanka ta fara yi ta d'auro alwala bayan ta idar da sallah ta kulle kofar d'akin ta kana ta kashe wayarta ta kwanta taso yin bacci ta kasa ta dad'e a haka kamun bacci ya d'auke ta.
Haisam wurin motar sa ya nufa duk a tunanin sa tana jiran sa, ganin bata Nan yace "to ina tayi ne?" Sa hannu yayi a Goshen sa yana ta waige waige bai ganta ba sai Kuma yace "Maybe bata zo ba nasan dai zata jirani"
Daga bisani ya shiga Masallaci don yin sallah, har ya idar ya dawo Bata Nan Zama yayii a motar har wuri ta Fara duhu, tsaki yayi ya jaa motar yabar gun.
Yana shiga gida d'akin ta ya nufa ya tura yaji a rufe, d'akin mummy ya nufa ya ga bata Nan, da sauri ya fice ya nufi part d'insu da sallama ya Shigo a tsatsaye ya gaida su yace "Mummy Ma'isha fa?"
Cike da mamaki suke kallon sa Umma Tace "Lafiyan ka kuwa meya same ka Shigo a rud'e Haka?"
"Umma banga Ma'isha ba, na d'auka ta dawone Kuma ban ganta ba"
Mikewa Umma tayi Tace "Shirmen banza Kenan dama ta tab'a dawowa ba tare da Kai bane?"
"Umma wall....... "
Mummy ce ta katse shi da fad'in "Son kasan dai baza ta 'bata ba ko? Ka Kira wayar ta man"
"Wallahi mummy wayata ce ta d'auke to nafi sa ran ta kirani ne bata same ni ba"
Umma ce ta zaro wayar ta dake chaji ta Shiga dialling number ta Amma switch off kallon Haisam tayi Tace "A kashe"
Kallon ta kawai yayi ya ma rasa abin fad'i,kana ganin sa Zaka gane Yana cikin tashin hankali, Ya dad'e a tsaye mummy Kam kallonta ta cigaba dayi yayin da Umma sai safa da marwa take tana Kiran layin Amma haryanzu a kashe.
A tsawace Tace "To uban me kake jira anan? Kana ji an Fara Kiran sallar maghrib yarinyar Nan bamu San a wani Hali take ciki ba ka fita kaje ka Nemo min yarinya,Kuma wallahi kar ka kuskura ka ka dawo gidan Nan ba da daughter na ba kaji na Gaya maka."
jiki ba karfi ya Shiga d'akin sa , cable d'in wayar sa ya d'auko ya fice ya fad'a motar sa, wayarsa ya zaro daga aljihun wandon sa kana ya sa a chaji, zaro Ido yayi don ganin fuskar wayar tasa da kyau a bayyane yace "15 percent to ya akayi wayar ta d'auke?"
Tsaki yayi ya kunnata ya Shiga dialling number ta haryanzu a kashe, jaan motar yayi ya fita Masallacin unguwar su ya nufa yayi sallah, bayan sun idar ne ya Kama hanyar makaranta, duk inda yasan Ma'isha ke zuwa babu inda baije ba Amma Bata Nan, duk da cewar dare ne Amma Akwai student a school d'in.
Haisam hankali a tashe ya Shiga motar sa ya nufi gidan su Ameerah, Ameerah qawar Ma'isha ce tun a secondary school yakan kaita gidan idan sun gama hirar su ya koma ya d'auko ta, Kiran layin Ameerah yayi da yaw Isa kofar gidan su.
Mamaki ma abin ya bata sabida ba ya kiranta haka kawai sai da dalili, picking tayi bayan sun gaisa yake fad'a Mata yana waje had'e da tambayar ta suna tare da Ma'isha ta tabbatar Masa da rabuwar ta da ita yafi 2 weeks tun bikin kawar su da suka je yace "Ya Salam"
Cike da kulawa tace "Lafiya kuwa? Wani abun ne ya Faru?"
"Lafiya lau, sai anjima bari na wuce"
"Baza ka Shigo ku gaisa da Mama ba? "
"Zanzo wani lokacin ki gaishe ta" kitt ya katse wayar.
Ma'isha kuwa tana chan tana ta baccin ta, da sallati ta farka ta kalli agogon dake d'akin ta taga karfe 7 saura mikewa tayi ta watsa ruwa kana ta tayi alwala tayi sallah wani uban yunwa take ji hakan yasa ta nufi kitchen food flask ta bud'e, farar Shinfa ta gani ta bud'e d'ayan taga stew tsaki tayi Tace "Mutanen gidan Nan da shinkafa nifa in ba tuwo ba duk shirme ne" plate ta d'auko ta zuba, kujerar dake Kitchen d'in ta samu ta zauna sai da ta cinye abincin Tass har ta Kara tasha ruwa tayi hamdallah, tasa Kai zata fita suka ci karo da Mummy Tace "Sorry mummy ban ganki ba ne"
cike da mamaki mummy Tace "Ma'isha kece?"
"Eh Mummy"
"Yaushe Kika dawo?"
"Tun kan la'asar"
Mummy ta Shiga ta yarfa hannu Tace "Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un Amma Ma'isha Allah ya shirye ki,Ashe dawowa kikayi Kika sa Yayan ki wahalan neman ki yanzu ga chan Umman ku ta Hana shi zaman gidan na tace kar ya kuskura ya dawo ba tare dake ba Ashe kina Nan kina ta baccin ki"
Turo baki tayi tace "To ai mummy...... "
"Ai mummy me ke? Ki fita daga idona Ma'isha wannan wani irin rashin hankaline, me ya sami wayar ki mukayi ta Kira a kashe?"
"Kashe nayi" Kai a kasa Tana wasa da yatsunta.
"Ka jimin ja'irar yarinya ki tadawa mutane hankali ba gaira ba dalili, dama kije ki Kira shi yanzu, tun d'azu yaron Nan baya gida gashi tun safe bai sa abinci a cikin saba kuka tafi makaranta ke Kuma kina Nan kin zauna Kinci abincin ki in ba mugunta ba"
"Mummy kiyi hakuri Dan Allah, wallahi na Kira layin sa ban same shi ba Kuma na gaji da jiran sa shiysa,Kuma na dawo a gajiye shiyasa fa na dawo gida Amma kiyi hakuri please"
"Dallah gafara ki bani wuri ko na had'a kanki da ginin Nan Mara hankali kawai"
Ficewa tayi da sauri don taga alama mummy zata iya buga Kan natan ta dad'e bata ga 'bacin ran mummy irin haka ba, da gudu ta Shiga d'akinta tana matsar kwalla, tana kunna wayar shigowar kiran Haisam ne ya shigo.
Haisam a kishingid'e yake a cikin motar, parking motar yayi a kofar gida ya kasa shiga cikin gida don bai San irin masifar da zai Sha a gun sa ba, ta dad'e baiga umman sa a cikin irin 'bacin ran Nan ba.
Jin Kiran ya Shiga ya zauna cike da kulawa yace "Princess Lafiyan ki kuwa? Kina ina nazo na d'auke ki?"
Cikin sanyin murya Tace "Ina gida"
Cike da mamaki yace "Gida wani gidan? Yaushe Kika dawo?"
"Gida man Ya Haisam akwai wani gidane bayan namu? Kuma tun kan la'asar nake gida"
Kashe wayar yayi, yayi horn Mai gadi ya bud'e Masa, Yana Shiga ya kashe motar ya fita ba tare da ya Kai motar parking lot ba, ya shige cikin gida da sauri, d'akin ta ya nufa, kofar d'akin ya tura da d'an karfi ganin ta Akan gado ya d'an ji sanyi a ransa sai Kuma ya fice daga d'akin tana Kiran sunan sa yaki kulata.
*FEDERAL LOW-COST*
Ayra kwance take Akan lallausar katifan ta, da sallama daddyn ta ya shigo tana ganin sa ta tashi Tace "Sannu da zuwa daddy Ashe ka dawo?"
"Eh Yar daddy na dawo tun d'azu mummyn ki Tace min kina school, ya school d'in dai?"
"Lafiya Lau daddy"
"Komai normal ko?"
"Eh Daddy"
"Masha Allah, to ya maganar mu ta kwana? Da fatan kin Fara aikin da na saki?"
"Hmm daddy Kennan ka kwantar da hankalin ka alkawari na maka sai na Kai makiyin mu kasa ko ta wace hanyance Kai dai kawai ka tayani da addu'a"
"I trust you Yar daddy, I trust you shiyasa na saki wannan aikin sabida nasan Zaki iya but mind you kibi a hankali kar kaikayi ya koma Kan mashekiya"
"hahaha insha Allah ba za'ayi hakan ba daddy your girl is very smart"
"Allah ya dafa Miki"
"Ameen daddy nagode, Ina tsarabata?"
"Yana Nan Zo muje ki karb'a"
Cike da murna ta Mike ta bi bayan sa.
Bayan ta karb'o ledan da ya Mika ma ta ta nufo d'akin ta, ji tayi an Kira sunanta cikin sauri ta juya don ganin Wacce ke kiranta ganin mahaifiyar Tace tayi Murmushi Tace "Na'am Mamy"
"Zonan ina da magana dake" tana Kai Nan ta shige d'akin ta Ayra ma tabi bayanta.
__________________________
Please comment sharhi, ku duba yawan typing da nayi Amma wasu thanks kawai nake Samu please kuyi min sharri sannan kumin sharing.
Milhaat ce
Yar Terawa
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._
*DANGIN UBANA*🍃
Story & Written
By
Milhaart
Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne.
*🌍MANAZARTA*
*WRITERS ASSOCIATION📚🖊*
*M. W. A*
```Kungiya d'aya tamkar da dubu.Masu Nazari da Aiki da Ilimi, Burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma Nishad'antar da masoyan ta.🤙🏻```
https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa
____________________________________
*Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.*
Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️
*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*
Page
25&26
..................Da gudu tabi bayansa , ya nufi part d'insu da gudu ta Sha gaban sa "Yaya Dan Allah ka saurare Ni"
Kallon ta ya tsaya yi kamar zai tanka mata sai Kuma ya kauce ya Shiga cikin gida da sauri, d'akin sa ya nufa Yana Shiga ya sa key ya rufe kofar Yana ji tana Kiran sunan sa had'e da bubbuga kofar tana fad'in "Yaya Dan Allah kayi hakuri wallahi kuskure aka Samu, bazan sake ba"
Umma jin Karan buga kofa ta fito daga kitchen cikin sauri hannun ta d'auke da cokalin Miya alama tana girki ne, kofar d'akin Haisam ta nufa ganin Ma'isha na bubbuga kofar tana kuka Tace "Daughter lafiya? Ina Kika Shiga ne Kika tada Mana hankali iye?"
Cikin kuka tana share hawayen da ke sauka a kuncin ta Tace "Umma ina Nan fa tun d'azu"
"Ban gane kina Nan tun d'azu ba, bayan Haisam shi kad'ai ya dawo Kuma yana neman ki, hankalin mu ya tashi sosai sabida a tare kuka Saba dawo wa"
"Umma da na gama lectures nazo inda yake ajiye motar sa, nayi ta jiran sa ban gan sa ba, Kuma na Kira layin sa a kashe a tunani na wani abun yake na shiga neman sa kawai sai na ganshi da wata suna hi....... "
kukane yaci karfinta ta kasa karasa maganar dake bakin ta.
Umma ruko hannun ta tayi suka dawo parlor,zaunar da ita tayi ta sa ta a gaba tana kallon ta , ita ko Ma'isha kukan ta to ta Rai rawa "lallai abinda nake zargi ya tabbata Soyayya ce a tsakanin yaran Nan tunda gashi har kishi take" zancen zuci take
A bayyane Kuma gyaran murya tayi Tace "Daughter ki daina kuka wa ya gaya miki ana wa na miji kuka kiyo shiru ki daina kuka sai ya raina ki,kuma ma naga ai shi ya Miki laifi so shi ya kamata ya baki hakuri ba ke ba."
Cikin shesshekar kuka Tace "A'a umma Ni na Masa laifi, da ban jira shi ya gama abinda yake ba, ni nayi tunanin kashe wayar sa yayi Ashe ba chajine, Kuma ku ma na tada muku hankali Dan Allah kuyi hakuri" ta karasa maganar tana kuka Mai tsuma zuciya.
" Yi shiru daughter yi shiru tunda kin dawo ai Shikenan, duk tunanin mu wani abun ne ya same ki har shi kanshi Haisam d'in ya damu don yafi kowa ma damuwa 'bacin Raine kawai Amma zai huce ki daina kukan haka, zo muje kitchen ki tayani aiki."
Riko hannun ta Umma tayi suka nufi kitchen, Nan ta Fara Taya ta wanke wanke da sauran abubuwan da ya dace.
Haisam kuwa tunda ya Shiga cikin d'akinsa ban d'aki ya fad'a ya kunnawa kansa shower ba tare da ya cire kayan jikinsa ba, tsantsan 'bacin Rai da Jin haushin abinda tayine ya sa shi hakan, sannan ya kunna shower d'in ne don kar yaji kukanta, sabida bazai iya jure Jin kukan ta ba, Dole ne ya horata.
"Ayra kiji tsoron Allah ki fad'a min abinda kuke shiryawa da mahaifinki, Ayra Ina guje miki abinda zai je ya dawo"
"Uhmn Umma Kenan Amma kin San Daddy bazaiyi abinda zai cutar dani bako?"
"Hakane nasan da hakan Amma ina so ki fad'a min abinda kuke shiryawa"
"Mamy kiyi hakuri bazan iya fad'a miki ba , sabida daddy fa gargad'i yamin akan kar na kuskura na sanar da kowa Shirin mu"
" Amma ai ni uwarkice ina da hakki Akan ki"
"Shima Kuma yana dashi a kaina, please Umma ki fita daga cikin maganar nan, daddy yaki fad'a miki ne sabida yasan baza ki bada had'in Kai akai ba"
" Hakan shi zai tabbatar da tsiya kuke Shirin aikatawa, ina so duk abinda zakiyi a rayuwar ki sa tsoron Allah a zuciyar Ayrah, shifa rayuwar Nan gajera ce, mahaifin ki bazai tab'a fahimtan hakan ba sabida shi na mijine ciwon 'ya mace na 'ya mace ne"
Mikewa Ayrah tayi tare da fad'in "Kar ki damu Mamy nasan Kina Sona Baki son abinda zai cutar dani insha Allah Babu abinda zai sameni"
"Ayrah Ni ba take nake ba,
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 6 Chapter of 24