Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ki" Ma'isha ji tayi kamar zuciyar ta zata buga,ganin irin kallon da Mummy take Mata tana son gane wani abu tayi kirkirerren Murmushi Tace "Nifa na d'auka Yaya is not serious about her" "Dama kinsan tane?" "Eh na santa ita ma a school d'in mu take course d'insu d'aya da yaya" "Kina so kice min course mate d'insa ce" "Eh to kusan hakanne Amma fa ba aji d'aya suke ba,sune zasu Gama a shekarar Nan" "Oh Masha Allah, Yayan naki Kinga na manta kije ki kirashi yazo yaci abinci" Ta Mike Kenan ta hango shi Yana saukowa hannun sa a manne a kunnen sa yana waya Yana dariya,Zama tayi Tace "Gashi Nan ma" "Okay" Sai da ya gama wayar yazo ya ja kujera had'e da fad'in "Barka da Dare Mummy" "Yauwa Barka son,yanzu nake ce mata ta Kira ka sai ga kanan,waya ake tayi haka da surkuwa ta?" Murmushi yayi kawai baice mata komai ba, Ma'isha tace "Yaya ina wuni" "Lafiya Lau princess, pharmacists of the house ya na ganki haka? Baki da lafiya ne?" "Bacci na wuni yi Yaya" Mummy Tace "Wai wuni naga Bayan la'asar Kika dawo" Uhmn kawai Tace ta cigaba da cin abincin,ci kawai take Amma bata jin dad'in abincin Sam kasantuwar bakin ta Duk d'aci,mikewa tayi ta ajiye plate d'in a kitchen kana ta wuce d'akin ta ba tare da tace musu komai ba. Haisam yace "Mummy Amma baki lura kamar princess na cikin damuwa ba?" "Gata Nan dai nima na lura da hakan Amma na tambaye ta Tace min bakomai" Mikewa yayi yace "Bari naje naji ko mene ne." Bai jira yaji amsar ta ba ya haura sama da sauri, tun daga kofar d'akin yaji tana ta dariya, a hankali ya tura yaga tana waya Zama yayi tana kallon sa Amma Bata kashe wayar ba,ta d'auki kusan 5 minutes Kan ta katsewayar da fad'in "Sorry Love zan Kira ka yanzu" Haisam ji yayi wani abu ya tokaresa a wuya Ma'isha Tace "Am sorry yaya wallahi Ma'aruf ne yake ta bani dariya" Cikin rashin Jin dad'in maganar nata yace "Waye ma'aruf?" "Saurayina man Yaya Wanda yake zuwa gidan Nan" "Oh that guy? Ni ban San sunan sa ba" "Ma'aruf sunan sa" "Ban San me Kika gani a jikin sa ba Ni Sam bai min ba" "Yaya saurayin nawa ne bai maka ba? Aiko shi nake so Kuma zan aura" "Hmm lallai gani nake Sam baku dace ba" Ma'isha wayanta ta bud'e ta Shiga gallery ta Mika Masa wayan had'e da fad'in "have a look" Karb'a yayi ganin hotunan da suka d'auka tare sauran selfies ne sauran Kuma d'aukan su akayi suna dariya a wurare da dama,sauran gun wurin cin abinci ne da ice cream Rai a 'bace ya Mika mata wayan yace "ba laifi maybe ranar kallon tsoro na Masa,Kuma yana sonki?" "Eh Mana sosai ma yana sona ga alamu Nan, hotunan Nan da ka gani ai sun Isa ka gane hakan" "Hakan.......yanzu auren sa zakiyi?" "Eh insha Allah,daddy ma yace na fad'a Masa ya turo don Yana so a had'a ayi rana d'aya" "Me za'a had'an" "My wedding and yours" Mikewa yayi yace "Yayi kyau" Ya fice Isha kuwa d'aga kafad'a tayi irin halin ko in kula d'in Nan ta Kira Ma'aruf ya katse kana ya kirata suka cigaba da wayar su. Haisam kuwa Yana Shiga d'akin sa ya kasa tsaye ya kasa zaune ya rasa dalilin da yasa yaji duk ya damu baya son Ma'isha ta auri gayen Nan, dafe kansa yayi yace "Maybe ko don gayen baya burgeni ne?" Ya kuma bawa kansa amsa da "Hakanne ma?" Wayar sa ya d'auka kamar zai Kira Aysha sai kuma ya fasa ya kashe wayar gaba ki d'aya ya kwanta dakyar da makyar kyasa bacci ya sace shi. *Washe Gari* Karfe hud'u na yamma,Daddy da Abba suka shirya don zuwa gidan su Aysha , Haisam ke Jan motar yayin da Abba ke gefen sa daddy Kuma yana baya suna tafiya suna Hira har suka Isa. Kasantuwar an san da zuwan su aka musu iso cikin gidan,Amma Haisam a mota ya zauna ya kira ta a waya suna ta Hira daddy da Abba suka gabatar da Kan su,shima Dad d'in Aysha da kannen sa maza biyu suka gabatar da kan sun,sun fahimci juna sosai kasantuwar Daddy sa nannen mutum ne, sannan basu 'boye musu asalin Haisam ba gudun Kar wani abu ya gifta suce an musu karya, Bayan sunji bayanin su Daddy suka amince da had'in tunda yara suna son junan su babu 'bata Lokaci suka amince da bukatar su, hakan yasa aka sa ranar aure Nan da wata biyu, drinks ne Niki Niki a gaban su daddy da namomin kaji Amma basu tab'a komai ba suka fice. Haisam na ganin su Daddy yace "habibty ganan su Daddy sun fito zamuuyi waya anjima" Cikin muryar Shagwab'a Tace "Bazan ganka ba Kenan?" "Zan dawo anjima insha Allah, bari Muji yanda sukayi tukunna" "Insha Allah,Mai dad'i ne sabida dad yasan ina son ka,Kuma yana son abin da nake so" "To Masha Allah,I'll call you later." ya katse wayar. Su dad kuwa har jikin mota suka raka su daddy hakanne ya tabbatar Masa da cewar bashi da sauran matsala,ai kuwa suna fita a gidan daddy ya Sanar Masa da and ranar bikin Nan da wata biyu, Haisam farin cikin da yake ciki ya kasa 'boyewa, gidan Abba Suka nufa Umma taji dad'i ta wani 'bangaren wani 'bangaren Kuma bata ji dad'i ba Sam,sabida kullum burinta shine Haisam ya auri Ma'isha tayi wa Abba korafi yayi saurin dakatar da ita akan ba a yi wa d'an yau auren Dole. Shiri suka Shiga yi duka family Ma'isha ma ba'a barta a baya ba,idan tana cikin Mutane ta nuna tafi kowa farin ciki yayin da idan tana d'akin ta Kuma taci kukan ta,son ranta idan ta gama ta wanke fuskar ta. Yau saura sati d'aya bikin Aysha da Haisam, Ma'isha da Meerah na gani zaune a cikin Masallacin asibiti da alama sun idar da sallar ne "Isha kiyi hakuri Dan Allah, Rana ita yau fa auren su,kema sai da nace miki ki tura Ma'aruf Amma kinki har karya fa kikayi wa Daddy cewar Ma'aruf baya Nan Bayan kuma yana Nan,ban San dalilin ki nayin hakan ba" " Dalili d'aya ne kema kin sani,Haisam nake so ba Ma'aruf ba" "Na sani amma ai Haisam d'in aure zaiyi ko?" "Eh Ana gama auren sa zan fad'awa Ma'aruf ya fito" "Ikon Allah,to Allah ya nuna Mana" "yanzu Meerah ya Haisam aure zaiyi fa ko? Kuma wata zai aura bani ba?" Ta fashe da kuka Mai cin raai har Saida sauran staffs d'in suka Fara kallon su rarrashin ta Meera keyi sai da tayi mai isarta ta Mike Kenan ta yanke jiki ta fad'i sumammayi. ____________________________ Please Comment and share Mihaat Ce Yar Terawa 🍃*DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhaart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* ```Kungiya d'aya tamkar da dubu.Masu Nazari da Aiki da Ilimi, Burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma Nishad'antar da masoyan ta.🤙🏻``` https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa ____________________________________ *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM* Page 39&40 _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._ _Continuation........._ Cike da fargaba da tsoro suka chiccibeta suka kaita A&E (Accident & Emergency) Nan da Nan likitoci sukayi kanta, kwata kwata bata numfashi da taimakon Oxygen ta fara numfashi, Haisam kuwa yazo wucewa ne don duba patient d'insa ya hango meerah na ta aikin kuka, da sauri ya karasa inda suke ganin Isha ce a kwance bata motsi ya birkice Yana tambayar su "Me ya same ta ne?" Wurin Meerah ya nufa Yana tambayar ta "Meerah what Happened to her? Me ya same ta? Please ki Sanar dani" Cikin kuka Tace "Yanke jiki tayi ta Fad'i" Likitane ne ya juyo yace "Dr Haisam, itace sister d'inka ko?" Cikin rawar murya yace "Eh itace" "To ya akayi kuka bari har ciwon zuciya ya kamata?" Zaro Ido yayi yace "What ciwon zuciya dai? But how comes?" Kafad'ar sa ya d'aga had'e da fad'in "I don't know, thank goodness ma ta samu kulawa cikin gaggawa da an rasata Kai ma kasan irin wannan lokaci d'aya mutum yake mutuwa ko Kuma ya kamu da mutuwar 'barin jiki" Haisam dafe kan sa yayi ya jaa da baya ya jingina da bango yana kallon Ma'isha da haryanzu oxygen na hancin ta, d'an bubbuga shi likitan yayi kana ya fice dashi da sauran nurses d'in. Kallon Meerah yayi yace "Dan Allah ki Sanar dani me ke damun Princess nasan kisan komai a kanta sabida kinfi kusanci da ita fiye da kowa" Kai a kasa tace "Ni ban san komai ba, babu abinda na sani" Girgiza Kai kawai yayi ya Koma kusa da ita ya zauna ya sanya hannunta a cikin nasa Yana ta kallon ta, sai yamma ya tuna bai Kira su Mummy ba, Nan ya kirasu ya Sanar dasu, ba dad'ewa Mummy da Daddy suka zo, mummy na ganin halin da yarta ke ciki ta Shiga rera kuka dakyar daddy ya samu ya rarrashe, a takaice dai Ma'isha a haka ta kwana bata farka ba ta kwana ta wuni tana bacci, sai yamma lis ta bud'e idon ta haisam da kanshi ya duba ta, ya mata alluran da ya kamata, aiko ta sake komawa bacci. A takaice dai Ma'isha Kwanan ta uku a gadon asibiti, sai da ta d'an Samu sauki aka sallame ta, a cikin Yan kwanakin Nan ta rame ta lalace Kamar ba ita ba, kuka kuma sai abinda ya karu,mummy da daddy sunyi rarrashin sunyi fad'an Amma taki fad'a musu, mummy Tace "Ma'isha idan baki fad'an min damuwar ki ba wa Zaki fad'awa umm? Ki duba kiga yanda kika lalace fisabilillahi baki kyauta wa Kanki ba wallahi" "Mummy nifa ba abinda yake damina" "Idan babu abinda ke damin ki me ya kawo miki ciwon zuciyar?" "Uhmnn mummy ciwo ne kawai daga Allah ba wani abinda yake damina" "Toh naji kukan da kike Kuma fa? Ki duba abincin Nan da sadiya ta kawo miko tun na safe baki ma tab'a shi ba" "Zanci Mummy" "A gaskiya Ma'isha bana Jin dad'in ganin ki a haka Dan Allah........ " Sallamar da akayi ne ya katse ta amsawa tayi had'e da kallon kofar don ganin wane ne, Murmushi Umma tayi Tace "Ameerah kece?" "Eh Mummy ina wuni?" "Lafiya lau ya gida ya su maman naku?" " Suna lafiya sunce a gaishe ku da maie jiki" "Allah sarki muna amsawa , sannu Ameerah Allah ya biyaki sai faman wahala kike " "Aaaa haba Mummy nida Isha ai Mun Zama d'aya nima idan hakan ta same ni nasan zata min fiye da hakan,fatan mu shine Allah ya bata lafiya" "hakane Allah ya bar zumunci" "Ameen Mummy" "Please kiyi Mata magana ta fad'a miki abinda ke damin ta, Kuma taki cin abinci, rabonta da abinci tun jiya da dare" "Kar ki damu mummy zataci insha Allah" Mummy fita tayi ta barsu da ga ita sai Isha, plate da d'auka tasa abincin d'an dai dai ta ajiye Sannan ta zaunar da ita ta Shiga bata a baki ba musu ta karb'a. Cike da kulawa Tace "Haba Isha, Isha so kike ki kashe Kanki?wannan fa ba alkawarin da Kika d'aukan min ba Kennan, kin zabi ki mutu Kennan?" "uhmn zan mutu idan kwana na ya kare,kema kin San da hakan ko?" "Amma kuka ai gangancin kine zai saka ki rasa ran naki tun kwanakin ki bai kare ba, wallahi Isha na gaji da ganin ki a Haka, a gaskiya lokaci yayi da zan fad'a Masa da dasu mummy" "Meerah please ki tuna alkawarin, Duk Wanda ya karya alkawarin to ba Makawa alkawari zata cishi, kin fiso a rasa rayuka biyu ne?" "Ban gane a rasa Rayuwa biyu ba, wa Dawa Kenan?" " Ni da Ya Haisam, wallahi farin cikinsa matters allot to me, bazan juri ganin sa a cikin damuwa ba, moreover ba Sona yake ba" "Shima Kuma bazai tab'a jin dad'in abinda kike Shirin aikatawa ba, ko da ace baya sonki na tabbata zai so ki Nan gaba" Maganar Meerah a kunnen Haisam ya sauka, turo kofan yayi ya shigo gaisawa sukayi kana Meerah ta Mike Tace "Zan wuce asibiti dama nazo  na duba jikin nakin ne, sai gobe zan dawo insha Allah, Allah ya baki Lafiya" Suka amsa da ameen tayi ficewar ta, tana fita ta nufi gun motar ta Muryar Haisam taji yana kiranta a hankali ta juya tana jiran sa. Karasowa yayi yace "Meerah wane ne Wanda Ma'isha take so?" In a serious tone yake tambayar ta, mamaki ma ya bata don ita ta manta ranar da ya Kira Ma'isha da sunan ta in bata manta ba tun suna school, ajiyar zuciya tayi Tace "like I said to you ban sani ba ni kaina taki ta fad'a min, sai anjima Kar na makara" ta shige motar ta har ta fice daga gidan Haisam na tsaye yana nazarin maganar ta a bayyane yace "Dole na sanarwa su Mummy sabida jinin ta sake Hawa yake Yi" Ya shige ciki ai kuwa Yana shiga har d'akin mummy yayi zama yayi ya Sanar mata da halin da Ma'isha Ke ciki tace "yanzu Isha dama akan na miji ne ta kamu da ciwon zuciya?" "Wallahi mummy Ni kaina abin mamaki yake bani" Daddy ne ya shigo Zama yayi Bayan sun gaisa ta Sanar mishi da halin da Isha take ciki Murmushi irin tasu ta manya yayi yace "Habae biri yayi kama da mutum, Dole mu nema Mata farin ciki ta samu abinda take so, koma wane ne zan Nemo shi sanan Nan da sati uku za a d'aura musu aure" "Haba alaji ko waye fa kace idan Kuma ba mutumin kirki bane fa?" "I trust my daughter baza ta tab'a son abinda bayi da kyau ba." Uhmnn kawai mummy Tace Haisam yace "am in full support Daddy Dole a nemo shi ko ina yake don wallahi idan bata Samu abinda take so ba zamu iya rasa ta" Daddy yace "Insha Allah, zan mata magana." Mummy ta ce "Amma ya kamata a bita a hankali gudun kar rashin Lafiyan nata ya kuma tashi ya kamata ace tana samun kulawa ne" "kar ki damu insha Allah zan San yanda zanyi ta fad'a min." Mikewa daddy yayi ya nufi d'akin ta babu yanda baiyi da ita ba ta fad'a masa Tace Masa "Babu wanda nake so Daddy." Matsa mata yayi Sosai daga bisani ta fashe da kuka daddy ransa a mugun 'bace ya bar d'akin. 'Dakin mummy ya nufa ya tarar haryanzu Mummy da Haisam maganar suke,hushi yake Yana fad'in "Taki ta fad'a min,ban san wani irin taurin kai Isha take da shi ba,tana chan tana kuka don kawai na bukaci ta fad'a Mana gaskiya" Mummy mikewa tayi Tace "Ka gani ko Alhaji,sai da fad'a maka mubi ta a hankali" tana kai Nan ta fice da sauri tayo d'akin Isha. Haisam shima mikewa yayi yace "Daddy kawarta fa tasan komai" Kallon sa yayi kana yace "Wacce kawarta Kenan?" "Daddy ai kawarta d'aya ce Ameerah,I over heard them suna maganar sa but na bita ta fad'a min Taki ta Sanar dani" "Ta kwana gidan sauki,Ni zan same ta da kaina kasan inda zamu same ta?" "Eh har gidan su na sani,Kuma Nurse d'in mu ce" "Shikenan idan Allah ya kai mu gobe sai muji" "Allah ya Kaiimu" sai ya fice. Mummy na Shiga d'akin Isha ta tarar da ita kuka take Sosai rungume ta tayi tana rarrashin ta amma Taki yin shiru, ganin Kamar numfashin ta na kokarin tsayawa ta shiga kwalla wa Haisam Kira, Haisam kuwa dama yazo fita ne yaji irin kiran za take masa, da gudu ya dawo ya Shiga d'akin, Daddy da sadiya suka shigo a tare. Duk kanta suka nufa Haisam kuwa Bayan ya duba ta d'akin sa ya Koma ta d'auko first aid box ya fara duba, Duk abubuwan da yakamata yayi Mata kana ya mata alluran bacci, mummy kuwa kuka take Sosai daddy na rarrashin ta, sadiya kuwa tausayin Ishan ce ya kamata sai matsar kwalla take, sabida Isha ta kasance tana kyautata Mata. Haisam ne yace "Mummy!! daddy!! Ya kamata mu bar ta ita kad'ai ta samu damar bacci, mummy Dan Allah ki daina kukan hakan Nan, Kar kema ki jaa wa kanki wata matsalar please." Hannun ta daddy ya rike suka fice daga d'akin,sadiya tafita, Haisam kuwa kallon ta ya tsayayi na d'an wasu lokuta kana ya fice daga d'akin. A hanyar sa ta fita ya jiyo Muryar Umma da Abba a parlor da sauri ya karasa Bayan ya gaida su ya Mika hannu ya d'auki kannen sa wata Aaima da Aymana,  mummy dai haryanzu kukan take Umma hankalin ta tashi yayi ganin mummy a Haka, cikin Muryar kuka Tace "Dama jikin Daughter yayi tsanani har hakane? Nifa tun a asibiti da na ga har munyi Hira na d'auka taji sauki Sosai." Ajiyar zuciya daddy yayi ya Sanar Mata abinda yake damin ta dama sun 'boye Mata Tace "Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un, Ciwon zuciya a d'an karamin shekarun Nan nata? Kuma akan na miji? Dan Allah wane ne shi? Ni zanje na durkusa har gaban sa ya aure ta" ta fashe da kuka, cikin Muryar kuka Mummy Tace "Bamu San shi ba, Taki fad'a mana Wanda take so" Daddy yace "Yanzu kukan da kuke me zai amfane mu dashi? Dan Allah da wanne zamuji?" Tsaki yayi ya fice daga gidan, Abba ma yabi Bayan sa, a garden suka zauna suna ta tattaunawa har Abba ya bukaci da a d'aga auren daddy yace "A a Abdul baza a d'aga auren Nan ba" "Amma Yaya ka duba halin da isha ke ciki, shi Karan kansa baya cikin hayyacin sa" "Uhmn bikin Nan fa saura 4 days, 4 days kawai me zamuce wa jama'a?" "Amma Yaya Ana uzuri ko?" "Eh Ana uzuri, Amma baza a d'aga bikin Nan ba, ranar jumma'ar Nan za'a d'aura auren. Abba ganin Daddy dagaske yake hakan yasa ya bar maganar suka Fara maganar kasuwancin su, Haisam kuwa Zama yayi dasu mummy Yana Basu hakuri had'e da wasa da kannen sa, sun girma sai wayo idan sukayi wata maganar zakace fad'a musu akayi, dab da sallar magrib Abba ya Shigo akan su koma gida. Umma ta kekashe Tace babu inda zata je anan zata kwana sabida ta kula da Ma'isha, Dole daddy ya hakura, Daddy ne yace "To kaji, kaima sai ka kwana anan, tunda gidan babu kowa baza ma kaji dad'in gidan ba." Murmushi yayi irin nasu na manya yace "To ya na iya da garen da ba wuya? Dole nima na kwana" Daddy ne ya maida kallon sa ga Haisam yace "Toh masu kanne taso muje Masallaci" suka wuce. Sosa keya Haisam yayi ya bi Bayan su. Ma'isha sai da gari ya Waye kana ta farka, mikewa tayi ta Shiga ban d'aki ta wasa ruwa    kana ta d'auro alwala Sannan ta Shiga jero sallolin da ake binta, Bayan ta idar ne ta sauko parlor Jin muryar su Mummy a dinning room ne ya sa ta nufi gun, da sallama ta karasa inda suke ta jaa kujera ta zauna dukkanin su kallon ta suka Shiga yi cike da mamaki Umma tace "d'azun Nan fa na leke ta tana bacci, Amma gashi ta fito." Abba ne cike da kulawa yace "Daughter ya jikin naki?" Ta amsa da "Sauki Alhamdulillah" Daddy yace "Sannu daughter" Ta amsa da "Yauwa nagode Daddy." Mummy mikewa tayi ta shafa kanta had'e da tab'a wuyan ta Tace "Jikin naki da d'an zafi har yanzu" "Uhmn da sauki mummy" Haisam kuwa gyaran murya yayi yace "Princess ya jikin naki? Da fatan bakya jin komai yanzu?" Kirkirerren Murmushi tayi kana tace "Eh bana jin komai , sai Kaine da yake d'an sarawa kad'an kad'an" "Allah ya sauwaka, shima zai daina a hankali." Duk suka amsa da "Allah yasa" Kallon Mummy Ma'isha tayi Tace "Mummy nima a Samin abincin" Jika na rawa ta sa mata abinci, kallon ta suka tsaya yi Murmushi tayi Tace "Dan Allah ku daina kallo na haka sai ku sa na kware." Haisam yace "Ai Dole ne mukalle ki, Duk da Yan kwanaki kikayi bakya cikin mu, ji muke Kamar shekara kikayi" ya maida kallon sa ga su Umma ya d'aura da fad'in "Ko ba Haka ba" Umma ta amsa da hakane, dariya sukayi suna ta hirar su, dukkanin su sunji dad'in ganin Ma'isha a haka. Sai da aka Fara kiraye kirayen sallar azahar ,Duk mazan Suku fice zuwa Masallaci, Bayan sun idar da sallar kuwa asibiti suka nufa, Haisam office d'insa ya bud'e musu suka zauna kana ya fita, bai wani dad'ewa ba suka ya Shigo Meerah kuwa na biye da shi. Har kasa ta durkusa ta gaida daddy ne yace "Tashi ki zauna" Yana nuna mata kujerar dake fuskantar su, Bayan ta zauna ne ya Fara magana yace "Meerah nasan Daughters bata da kawar da ta wuce ki, sannan nasan kin San sirrukanta Dan Allah ina so ki fad'a min abinda Kika sani game da Wanda take so" Kai ta d'aga ta kalle shi kana ta maida kanta kasa Tace "Daddy ban sani ba, ban San Wanda take so ba" Abba yace "Please ki fad'a Mana gaskiya nasan Dole Akwai abinda Kika sani akai" Meerah har cikin ranta take so ta Sanar dasu gaskiya Amma idan ta tuna alkawarin da tayi wa Ma'isha sai ta fasa Tace "Abba da na sani wallahi zan fad'a Muku" Haisam ransa ya yi mugun 'baci cikin 'bacin Rai yace "Wallahi karya take Daddy, da kunne na fa naji lokacin da suke maganar Amma yanzu Kuma don ta Raina Mana hankali tace bata sani ba" Daddy yace "Son calm down" Abba yace "Kinji ko Ameerah, Dan Allah ki fad'a mana wane ne, kece kad'ai zaki taimaka Mana wajen sama wa zuciyar ta abinda take muradi" Shiru tayi tana matsar kwalla, a tsawace haisam yace "Shegen taurin Kan tsiyane da ita, ranar babu yadda banyi da ita ba Akan ta fad'a Min Amma taki, na rantse da Allah idan wani abu ya sami princess...... " Daddy ne ya d'aga Masa hannu yace "Ya Isa , ya Isa " mikewa yayi ya kalli Abba yace "Mu tafi ko?" Abba Rai ba dad'i ya mike yana girgiza Kai, Sai da suka Isa kofar fita, Abba ne ya juyo ya kalle ta yace "ki yiwa girman Allah ki ceci rayuwar Isha wallahi tana cikin wani matsanancin hali dan Allah ki fad'a mana gaskiya wane wannan wanda Isha take so a ina yake kuma d'an waye?" Cikin Muryar kuka Tace "Wallahi ban sani ba,da na sani da na fad'a Muku" Girgiza Kai Daddy yayi yace "Allah shi kyauta" suka fice Haisam Rai a 'bace yace "Tirrr da qawa irin ki, Wallahi ko kaffara bazan yi ba kin San komai" "Ya Haisam ban....... " A tsawace yace "Get out of my office" a tsorace tayi hanyar fita sai da ta kusa fita yace "Kuma ki sani idan wani abu ya same ta kece sila" cikin kuka ta fice. Tana fita shima ya fita, rufe kofar office d'in yayi ya nufi gun su Daddy dake tsaye a jikin motar sa suna jiran sa , hakuri ya basu Duk suka shige motar suka koma gida, Bayan ya ajiye sune ya koma office don cigaba da aikin sa. Daddy da Abba ganin Isha na walwala hakan yasa suka d'an ji dad'i, ta wuni cikin farin ciki sai fara'a take,Nan suka Cigiba da shirye shiryen biki, Isha kuwa Duk lokacin da ta Shiga tashin hankali sai ta Rika ambaton '''la'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu Minal zalimin''' hakanne yasa ta ji sauki abun Sosai. Rana bata karya sai dai uwar d'iya taji kunya, yaune ranar da Haisam da Aysha suke jira,

Chapter 11 of 24