Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ce ba ita ba, and wannan matar Itace matar da take Kawo Mana abinci a 'boye ba tare da Mijinta ya sani ba, sannan itace matar da take kullar miki dani a lokacin da babu Wanda yake tare da ke, ta d'auki risk da dama akaina, shin Umma laifin wani na shafan wani dama?" Ya karasa maganar cikin sanyin Murya. Shiru Umma tayi , Jikin ta ne yayi sanyi tabbasa mamy mutunce ta taimaka musu da ita da 'danta a lokacin da basu da kowa basu da komai, kosan da ta sayar a baya ma Itace ta bata jarin, tana cikin wannan tunaniin ne ta ji an Kama Mata kafa da sauri ta kalli a kasa, ganin Mamy tayi ta zube a gaban ta, tana kuka Tace "Dan Allah maman Yara kiyi Hakuri nasan an cutar dake, nasan Hakurin da zan baki bazai Canza komai ba, but please find a place in your heart to forgive and believe me, Wallahi I know nothing about this, hatta ita Ayrah ma bata San komai ba, you know how Hassan is he a very manipulative human being, yayi manipulating d'inta ne Wallahi bata San komai ba Yanzu haka maganar da nake miki ayrah ta 'bata kusan watanni hud'u kenan bamu San inda take ba ko ta mutu ko tana raye bamu sani ba, babban tashin hankali na ace ta mutu bamu gana ba sabida nayi fushi da ita tsawon shekarun Nan da muka rasa Haisam, Akan sai ya farka na yafe mata gashi ya farka and she is nowhere to be found" ta karasa maganar cikin kuka. "Tabbas ni shaida ce, Mamy bata kula Ayrah, Wanda hakan ba karamin tada Mata hankali ba" duk suka kalleta, sai Kuma tayi shiru kamar ba ita tayi maganar ba, Haisam kallo d'aya ya mata ya gane ta, ya dad'e Yana kallon ta kamar Mai son gano wani abu, sai Kuma ya kawar da kansa. Umma hannu tasa ta d'ago Mamy suka rungume juna, Umma na fad'in "Kiyi Hakuri Maman Yara, da na kasa fahimtar ki na manta duk abubuwan da suka faru a baya, na rasa madafa, Ina cikin tashin hankali" " Ko kad'an Banga laifin ki ba, Amma Dan Allah ki yafe min" "Allah ya yafe Mana duka" Duk suka Masa da amin Amma fa Banda Mardiya da take ta taunan chewn gum tana latsar wayarta. Duk wuri suka samu suka zauna, kasantuwar d'akin babba ne ya d'auke su, Hira suka Fara yi harda Mummy, cikin hiran ne suka yanke shawarar zuwa ganin Jikin malam hassan, Mummy, Umma da Mamy suka fita,suna fita Haisam ya Koma Kan gadon sa ya kwanta suna Hira da Isha,daga bisani sukayi shiru baka jin komai sai karar chewn gum d'in da Mardiya ke tauna. Suna cikin wannan yanayin ne faruk da Meerah suka shigo, Isha na ganin Meerah da d'an saurin ta Mike ta rungume Meerah, Meerah d'an ture ta tayi tana fad'in "Kaaai mai ciki zungurina fa kike da tumbin ki" sai a sannan mardiya ta d'ago kai ta sauke Akan tumbin Isha, zaro Ido tayi tana kallon Isha, Meerah da ta lura da kallon da take mata Tace "Allah ya sauke ki lafiya mu samu Ma'aruf junior" Mikewa tayi tana kallon Isha cikin Muryar kuka Tace "Ciki? Ciki kike dashi Isha? Cikin Yayana?" Duk lokaci Guda ta jero mata tambayoyin Nan, Murmushi Isha tayi kana Tace "Uhmnn eh" mardiya Rungume Isha tayi ta fashe da kukan farin ciki. _________________________ Please comment and share Milhaat ce Yar Terawa [8/15, 8:02 PM] Miilhaat Writer✍🏻: 🍃 *DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIN RAHIM* Page 71&72 _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._ ```Continuation.......``` Isha Murmushi kawai take ta kasa bata amsar tambayoyin ta, mardiya sakin Isha tayi hawayen fal a kwarmin idanun ta, Tace "Allah ya sauke ki lafiya" Duk suka amsa da Amin, Farukh ne ya zauna kusa da Haisam musabaha sukayi, sannan ya tambaye shi ya Jiki, hiran su suke hankali kwance, yayin da Meerah da Isha ma tasu hirar suke, Mardiya kuwa ta yi saye tana kallon su kamar gunki, kallon ta Farukh yayi yace "Hajiya ki zauna Mana" kamar dama jira take ta koma mazaunin ta Jiki a Sanyaye. Farukh yace "Baby ya Kamata mu tafi fa, kin San akwai wuraren da bamu je ba tukunna" Mike wa Meerah tayi fuskar ta d'auke yake da Murmushi, kallon ina zakuje Isha take Mata, hannu tasa a jakar ta ta cire IV (invitation card) ta zaro su dayawa bata San Guda nawa bane ma ta Mika wa Isha had'e da "fad'in tare ya Kamata mu raba, amma Kuma kina tare da patient, ga wa'annan ki bawa Wanda ta dace" Kallon kati Isha tayi tana Murmushi Tace "Kai Masha Allah, katin yayi kyau, ikon Allah baikin saura 1 months" ta karisi maganar tana kallon Meerah, Murmushi tayi Tace "Eh." Gyaran Murya Haisam yayi kana yace "Amarya to ni ina katin nawa ko baza a gayyace Ni bane?" Yar karamar dariya tayi kana Tace "Ai sai dai kayi gayya ba dai a gayyace ka ba" Faruk yace "You're right kaifa babban abokin angone" " Isha Kuma babbar kawar Amarya ba, an bata Amma Ni ba'a bani ba" a Shagwab'ance Haisam yayi maganar kamar karamin yaro. Isha dariya ma ya bata ta Mike ta Mika Masa Tace "Gasu Nan Yaya" Meerah Tace "Bakwa gajiya da drama, to ai Ishan ba nata bane na bata ne don tayi gayyar ta itama" " To Nima a bani tawa" ai kuwa da sauri Meerah ta Sanya hannu a jaka ta miko Masa masu yawa, dariya ya shigayi had'e da fad'in "Ni Wallahi zolayar ki nake, Allah ya nuna Mana ranar" Suka amsa da Amin. Mardiya kuwa ji take kamar ta Burma musu huka, ta tsani taga Meerah na cikin farin ciki duk da ta kasance kawarta ce tun na yaranta, mardiya irin mutanen ne masu bakin hassada da Kuma kyashi. Meerah da Farukh suka nufi hanyan fita, sai Meerah ta juyo kamar tayi mantuwa, inda Mardiya take ta nufa,ta zaro kati d'aya ta Mika mata had'e da fad'in "Be my guest" kallon katin ta tsaya yi kamar Mai tunani kana tasa hannu ta Karb'a, ta mata Kirkirerren Murmushi da duk Wanda ya gani yasan a iya fuskane kawai, Meerah da Farukh sukayi ficewar su. Shiru d'akin yayi sai kara IV da Isha take ta kallo, Haisam yace "Ya dai Princess?" "Me ka gani?" "Naga sai kallon katin kike tayi, ko dai.....? " " Ko dai me?" " Baaaa......buuu" yace babun yana jaan sa, girgiza Kai Isha tayi ta mike had'e da ajiye IV d'in a Kan kujerar da ta tashi, yace "Ina zaki?" "Toilet, alwala zanyi" Yace "oh" ta shige toilet ba tare da ta ce masa komai ba, shiru sukayi kowa da abinda yake tunani ransa, Haisam tunani yake Akan yadda zai kula da Isha ya gyara dukkanin abun da ya 'bata ya sani da ace baiyi na'am da Ayrah ba da Yana Nan tare da ishan sa, idan bai zame mata farin cikin ta ba Tabbas Hakkin soyayyar ta (sunan book d'ina na gaba *HAKKIN SO*) bazai barshi, a Yanzu ya shirya zama da Isha ko ta halin Kaka ne,sabida yana matukar kaunarta, a ranar da ta gaya masa cewar tayi aure kwana yayi baiyi bacci wani irin wutar kishi ne take tashi a zuciyar sa, Amma daga bisani yace haka Allah yaso. Mardiya kuwa tunani take ta ina zata bullo wa al'amarin Auren Meerah sai ta gama da ita tukunna ta Dawo Kan Isha da Haisam, baza ta tab'a bari Isha tayi farin ciki ba in ta kuskura Tace zatayi aure. (Oh ni milhaat ina mamakiin karfin Hali irin na Mardiya, ita idan baza ta samu Abu ba to gara kowa ya rasa, muna da ire iren mardiya a cikin al'umar mu Wanda they can even do worst ya Allah ka Shiga tsakanin mugu da na gari, Amin). Bayan Isha ta fito daga toilet ta kalli Haisam da ke kallon sling na d'akin yayin da Mardiya kuwa tana kallon kofar d'akin, dukkanin su sunyi nisa a duniyar tunani, gyaran Muryar da Isha tayi ne yasa duk suka kalleta ta, a lokacin ta d'auko prayer mat ta shimfid'a, ta hau kai ta tada sallarta. Haisam ma sauka yayi daga Kan gadon ya nufi toilet din shima da niyar d'auro alwala, mardiya wayan Haisam ta hango a Kan gado a hankali ta Mike tasa hannu ta d'auka tayi sa'a ba password hakan ba karamin dad'in ya mata, sai da ta ji motsin Haisam na kokarin fitowa tayi saurin ajiye wayar a mazaunin sa Takoma ta zauna, Isha taji motsin ta Amma kasantuwar ta juya mata baya bata ga abinda take ba. 'dayan prayer mat d'in ya d'auka ya shimfid'a ya tada sallar. Su Umma kuwa suna shiga d'akin da Malam Hassan yake, Umma har kusa dashi taje tana Masa ya jiki ya kawar da kanta ya juya mata baya, Nabila har kasa ta duka ta gaida su Mummy da Umma suka amsa ba yabo ba fallasa, ganin Wanda suka Zo gaishe sa bai kula su ba, sukayi hanyar fita, Mami Tace "Dan Allah ku d'an zauna Mana,wurin shiru duk muna cikin kewa" Ba musu suka zauna suna hiran sama sama,Nabila kuwa tana ta chatting a wayar ta. Isha Bayan ta idar da sallan ta zauna tana azkar d'in da ta Saba,Bayan ta shafene ta d'auki sallayar ta nad'e kana ta ajiye shi a mazaunin sa,ta koma ta zauna. Haisam Bayan ya idar da sallar shima ya zauna Yana Addu'oin,ya dad'e Yana rokon Allah yafiya da Kuma biyan bukatunsa na alhairi,yaji shigowar su Abba da Daddy,ganin yana Addu'oin ne Suma suka d'aga hannu a tare suka shafa, fuskar su d'auke yake da Murmushi,gaishe su yayi suka amsa,Isha ma haka, Mardiya kuwa bata ma San da Shigowar su ba,Daddy ne ya mata magana Amma bata ji ba bare ma ta bashi amsa. Mikewa Isha tayi ta d'an tab'a ta,a d'an razane Tace "Na'am.. " Isha Tace "Su Daddy na miki magana Amma baki ji ba" Murya na rawa Tace "Sannun ku da zuwa ina wuni" A tare suka amsa da Lafiya,Abba yace "Mardiya ki rage yawan tunani gudun Kar ki cutar da kanki, kullu nafsin za'ikatul maut,ko wani rai sai ya d'an d'ani zafin mutuwa muma tamu muke jira,Kiyi ta musu addu'a,Kuma Kinga mutuwar shahada sukayi, insha Allah chan yafi musu Nan kinji" tunda ya fara magana kanta a kasa, tana matsar kwalla,su duk a tunanin su maganar da Abba yake ne yake sata kuka,ita Kuma kukan Nan na haushin Isha ne,ita duk ta d'auki tsanar duniya ta d'aura Mata,gani take kamar ita ta kashe Mata ahalin ta,cikin Muryar kuka Tace "Nagode Abba, Insha Allah zan kiyaye" "Yauwa Allah ya miki Albarka" ta amsa da Amin. Daddy ne ya tambaya ina su Mummy suke, Isha Ce ta shaida musu cewar sun je duba Jikin Malam Hassan, kwatancen d'akin suka sa aka musu suka fice a tare, suna fita Mardiya ta Mike tayi hanyar fita Isha Ce Tace "Ina Zaki?" A zuciyar ta Tace na tsani shisshigi wallahi, Amma a bayyane Tace "Wurin aiki, karfe shida ya Kamata na koma bakin aiki" "Amma this is just 4:03 ki d'an jira su mummy Mana tunda tare kuka Zo" "a a akwai abinda zanyi before lokacin yayi, idan su Umma sun shigo kice musu na wuce gida" ba ta jira amsar Ishan ba ta fice, tana fita Haisam yace "kema akwai nacin tsiya Wallahi" "Me Kuma nayi Yaya?" "Oho ba'a sani ba" Murmushi kawai tayi ta cigaba da dannan wayarta, Bayan su Abba sun Isa d'akin Malam hassan suka gaisa da mamy sannan Nabila ta gaida su, har suka gama tsayuwar su malam Hassan bai kula su ba. Gani suke kamar baya son kula sune Amma shi Kuma kunyace da Dana sani take daminsa , ji yake kamar ya tsaga kasa ya Shiga, shiysa yake pretending cewar baya magana ne. Sallama suka musu, Daddy ne yasa hannun a aljihun sa ya ajiye musu kud'i masu yawa yace a sayawa Mara Lafiya lemo. Mami ta masa godiya sosaiii suka fice. 'dakin Haisam suka nufa Umma na ganin Isha a zaune Haisam kuwa sai sharar baccin Sa yake, Umma Tace "Isha kina Nan haryanzu baki wuce bakin aiki ba?" "Eh Umma" "Why?" "Umma hutu na d'auka har sai na haihu, ina wahala sosai wallahi" "to in ko hakane kin daina Zama akan Haisam d'in Zaki koma gida sai kiyi ta hutawan" "A a Umma Dan Allah, to idan ta tafi wa zai kula Dani?" Baki a bud'e suke kallon sa Umma tace " ja'iri dama ba bacci kake ba?" " A a Yanzu na farka, Dan Allah Umma ku bar Isha anan" "Lallai Haisam, kai ko tausayin ta ma baka ji?" Kallon Isha yayi sai ya maida kallon sa ga Mummy alamun kisa baki Mana, Murmushi Mummy tayi tace "Maman Yara ayi Hakuri a barta ta kula da Yayan ta" Umma dariya mummy ta bata data Kira ta da Maman Yara , sunane da suke Kiran junan su ita da Mami, Abba yace "To tunda Tace zata iya a barta Mana, ko ya kace Yaya?" Yana maganar Yana kallon Daddy, Daddy yace "eh a barta kawai" Umma Tace "Kuna biyewa yaran Nan Wallahi, Shikenan nayi shiru tunda kunfi karfina" duk sukayi dariya. Daddy ne ya fara magana, "Son Bayan kwanciyar da kayi ajiyar ka da ke wurina nayi amafani dasu wurin gina maka asibiti, sannan na zuba maka ma'aikata aciki Ana gudanar da aiki yanda ya Kamata, a gaskiya Haisam ka samu aboki na Kwarai, da taimakon Farukh ne komai ya tafi dai dai tun Bayan wannan lokacin shi yake kula da komai, a halin Yanzu asibitin yana d'aya daga cikin manyan asibitocin da ake ji dasu a garin gombe, sannan na gina maka gida, na zuba maka dukkanin abubuwa na more Rayuwa" Mikewa Haisam yayi ya rungumi daddy yana kuka kamar wani karamin yaro Yana ta Nagode Allah ya saka, daddy Murmushi kawai yake Yana d'an bubbuga Masa baya alamun rarrashi, Umma ma godiya ta Shiga Masa, tana Kara godewa Allah da Ma'isha sabida itace silar komai, shiysa take matukar son Isha, fiye da ka yadda take son Haisam d'in, Abba yace "Kan mu shigo, mun biya gun Dr Ali yace anjima da Yamma za'a sallame ka" "Alhamdulillah dama Wallahi na gaji da asibitin Nan, Yamma tayi ai Abba" Duk dariya sukayi. Suna cikin maganar ne sai ga shigowar Dr Ali, Bayan sa biye yake da wata nurse hannun ta Kuma rike yake da patient file, Bayan sun gaisa ya Shiga Duba Haisam, Bayan ya gama ya rubuta Masa magunguna da za'a saya ya mikawa Ma'isha had'e da fad'in "Pharmacists a samawa patient magani" Karb'a tayi tana dariya tace "Ai na samu hutu" " Yet ke staff d'inmu ce" Charafff Haisam yace "She was dai, don Canza mata wurin aiki zanyi" girgiza Kai Isha tayi Dr Ali yace " Fatan alhairi" sai ya fice nurse din tabi Bayan sa. Tattara kayan su Umma da Mummy suka farayi Isha ma bata zauna ba da ita ake had'awa su Daddy da Abba Kuma suna Kai kayan mota, farin cikin da Umma take ciki bazai misaltu ba yau Bayan shekaru 4 d'anta zai Koma gida, har kuka Saida tayi mummy na ta aikin rarrashin ta. Bayan sun gama kai tsaye gidan Umma suka nufa Haisam zai zauna a gunta Kan ya gama murmurewa, Isha dama already tana gidan Umma, Ni ko nace Anya zaman Isha, Haisam ga Kuma mardiya zaiyu kuwa a gida d'aya? Muje zuwa. Mardiya Bayan ta koma gida ta shirya cikin doguwar rigar atamfamfar ta, Atamfa less ne, brown an Masa Flowers da kallan ja da yellow sannan less d'in Jikin farine hakan yasa tayi Rolling da d'an figegen gyale fari hannun ta Kuma rike yake da labcoat d'ayan hannun ta Kuma fashion bag d'intane shima fari Sannan takalmin ta ma fari, a gogon hannun ta take Kallo sai Kuma tayi Tsaki , a bayyane Tace "wannan Wace irin Rayuwa ce, a gaskiya zan d'auko mota na tun d'azu nake ta jiran abun Hawa Amma babu." Wata dankararriyar mota ce tazo ta faka a gaban ta, ta kawar da Kai Jin an Kira sunan ta Yasa ta kalli Wanda taji ya Kira sunanta Tace "Laaaa Adnan" Murmushi yayi yace "Mardiya manyan gari ana ganin ku dama?" Itama Murmushin tayi Tace "Gashi kuwa" "Hakane, ina zaki ne haka?" "Gun aiki ina ta jiran napep Amma ban samu ba" "Hoop In Mana mu rage Miki hanya" Ba musu ta bud'e gidan baya sabida daf take da yin latti,jaan motar yayi yace Mata "Wani asibiti kike aiki?" "Specialist hospital" "Okay " Babu Wanda yace komai sai chan yace "Wannan abokina ne sunan sa Abdallah" "Barka" Shima ya amsa da yauwa barka,nan suka fara hirar yaushe gamo,suna Isa specialist hospital har ta bud'e marfin motar Tace "Baka tambayeni mutuniyar ka ba?" Sai da yaji kirjin sa ya fara duka uku² cikin rawar murya yace " Wa Kenan?" "Ayrah Mana" "Ummmm...... Ya take ne? Tayi aure ko?" " Wai kana nufin baka ji abinda ya same ta?" Gyara zama yayi ya waigo Yana kallon ta kana yace " A'a me ya same ta?" _______________________ Please comment And share Milhaat ce Yar Terawa [8/17, 1:06 PM] Miilhaat Writer✍🏻: 🍃 *DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIN RAHIM* Page 73&74 _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._ ```Continuation.......``` Ba Adnan Kad'ai ba hatta Abdallah sai da yaji zufa na sassafo Masa, Adnan kuwa wani abu ya ji ya bi ta makoshin sa ganin irin kallon tuhuma da take masa, Dakyar ya aro jarumta yace "Umm umm bani da labarin komai" Ajiyar zuciya tayi kana Tace "Ta 'bata ba a San inda take ba" Gyara zama yayi kamar Bai San komai ba yace "Whatttt!!!! Da d'an karfi kana yace "when, how? Yaushe hakan ta faru,taya ma za'a ce ta 'bata sai kace Yar tsana?" Ya maida kallon sa ga Abdallah kana yace "kana Jin wani zance ko,wai ta 'bata kamar babyn roba?" "Wallahi da mamaki Kam" "Umhn to maganar da ake ma ta kai 4 months ba a San inda take ba" Adnan yace "Ashhha abu baiyi Dad'i ba, Allah ya bayyana ta" Duk suka amsa da Amin. Ficewa tayi daga motar Bayan ta bawa Adnan Number wayar ta, Motar ya tada suka Kama hanya, Abdallah ne yace "Abokina I think is high time fa da zaka bar yarinyar Nan haka ta koma gida, ina gudun abinda zai biyo baya gaskiya" "I wish zan iya hakan, I wish zan iya cire ta a Raina I wish lokacin da ta nemi mu na shirya na amince da duk ba a Zo Nan ba" " Bar maganar wish wish d'in Nan ka bar yarinyar Nan haka ta koma gida" "Bazan iya" Yana maganar ya maida hankalin sa kan tukin da yake. "Ka fahimce ni Adnan, wallahi idan asirin ka ya tonu abun bazai Mana kyau ba sabida duk abinda ya shafe ka Nima ya shafe Ni" " Nima ka fahimce ni, wallahi Allah ina son yarinyar Nan har cikin Raina" "Ita Kuma Tace Bata son ka just let her be" "Kana ganin idan na barta ta tafi zata rufa min asiri ne?" Shiru Abdallah yayi na Yan sakanni kana yace "No, I don't think so" "Good that's my point, ina so na jefi tsuntsu biyu da dutse d'ayane you understand what I mean?" " Yeah I do, Allah ya shige Mana gaba" "Ameen" " But fa ina son kawartar Nan Wallahi" Kallon bana son rainin hankali Adnan ya Masa kana yace "To wani sabon iskancin naka xaka Fara Kenan" "A a wallahi tallahi sonta nake Kuma da aure" "Hmm lallai fa" " Kana ganin zata amince kuwa?" "Can't tell, but try your luck" Bai Kuma ce masa komai ba har suka Isa inda zasu. Mardiya ce zaune a office d'inta ta Lula duniyar tunani, ajiyar zuciya tayi kana a bayyane Tace "Meyasa nake ji kamar akwai abinda Adnan

Chapter 21 of 24