Mardiya"
Kai ya d'aga had'e da fad'in "Wannan Hakane"
"Mardiya tayi amfani da yardar da na Mata ta cutar dani" gyara zama tayi kana Tace "Bayan na gama secondary school, ina burin Shiga School of nursing Amma Abba yaki ya fi so sai na yi aure in yaso na cigaba da makarantar, Already dama ina da saurayin da yake son Aurena Mai suna Bashir, Bashiir mutum ne mai bala'in kishi, Kuma yana yawan fad'in shi idan ya auri mace ya same ta ba a budurwa ba zai rabu da ita"
Ma'aruf yace "Ina sauraron ki"
"To akwai wani d'an unguwar mu , Kama sanshi sunan sa Usman ana Kiran sa da Usu"
"Eh na gane shi"
"Akwai wata rana Mardiya ta shigo gidan mu ta zo take min labarin sa, akan yana da kirki Kuma yana Sona, sai nace Mata kina da shirye me wallahi an fa Riga da ansa ranar biki na Nan da yan satikai Kuma kike min maganar wani, sai Tace min "Ai ba a d'aura ba tukunna ai ansha yin hakan"
Nace Mata "Bana so ayi hakan akai na gaskiya kima bar maganar Nan kawai."
sai ta Ciro wasu kud'aden da ni ban San adadin su ba, Wai Usu ne yace a bani, babu yadda batayi da ni ba naki karb'a, a haka ta maida masa, ba shine na farko kuma ba shin na karshe ba tana yawan kawo min maganar sa Duk da na nuna Mata Bana son hakan.
Sau dayawa takan kawo min kud'i da turaruka akan shi yace a kawo min ban tab'a sa hannu na karb'a ba, tunda bana son sa bazan so abin hannun sa, akwai wata rana ana saura 5 days da bikina tazo gidan mu nace "Mardiya ya batun lalle ne, wa Kika Sanni wacce ta iya, don Gaskiya ina so a fitar Dani"
Tace "Eh akwai wata mata da take yi gidan ta bayi da wani nisa sai muje a Miki,Amma fa sai munje Mun tambaye ta,ta San da zaman ki"
"To yaushe kike ganin zamuje?"
"Zuwa gobe,idan Baki da abin yi"
"Okay zan fad'a wa Mama Sai muje,zan ma Kira Isha sai muje tare"
"Ki bari ranar lallen sai muje tare da Isha d'in tunda yau ai tambayar ta zamuyi ko?"
"Eh to da Wannan ma, Allah ya Kaiimu goben" Nan muka cigaba da hirar mu, washe gari Bayan sallar azahar sai ga Mardiya ta shigo gidan mu,dama na sanarwa Mama inda zamuje tana zuwa na Sanar da ita zamu fitan, ta min a Dawo Lafiya Kuma tace Kar ka na dad'e,muka tafi, napep muka hau wani gida d'an madaidaici muka nufa, kusa kan mu mukayi muka Shiga ciki Bayan mun Shiga har parlor muka zauna.
Bayan Mun Zauna ne naga wani Saurayi ya fito daga shi sai gajeren wando da singlet, Ya mana Sannu kana ya wuce, Yana fita nima na miki na Fara masifa ina fad'in "Dama Nan gidan zaki kawo ni, gidan maza, kince Nan gidan mai lalle ne Amma Banga mace ko d'aya ba tunda muka Shigo" hannu na ta rike Tace "Haba Meerah Nan gidan Mai lallen ne wallahi tana ciki shi Wanda ya wuce d'an tane fa" Kan na bata amsa wata budurwa kamar sa'ar mu ta fito Hannun ta d'auke yake da drinks da ruwa ta Shigo da sallama, tace "Sannun ku da zuwa,tana wanka zata fito yanzu" sai ta fice, jin hakan sai naji hankali na ya d'an kwanta, sai na samu wuri na zauna.
Mardiya da kanta ta zuba min a kofi na karb'a nasha Sannan ta d'auki d'ayan ta bud'e ta zubawa kanta ta Sha, nace Mata "Big cola ne fa, ai da baki bud'e wani ba"
Sai tace min "Eh Wallahi kan ne ba dad'i kin sanni da shirme" girgiza kaai kawai nayi na shanye Tass, kasantuwar ni masoyiyar coca cola ce.
Tunda na Sha Wannan naji idanuna sun fara rufewa tun daga Wannan lokacin na manta kaina ban San a Ina nake ba Kuma ban san a wani Hali nake ciki ba, ji nayi na farka a razane d'ago kaina da zanyi na gan ni a kwance a jikin Usu, a razane na Mike nayi kokarin d'aga kafana naji sun min nauyi kallon kafan nawa nayi naga jini na bin kafana.
Usu kuwa Kallo d'aya yamin ya kawar da kansa a kaina hakan ne ya tabbatar min da Usu ya min fyad'e, kuka na fara yi ina ja Masa Allah ya Isa shi da Mardiya bazan tab'a yafe musu ba, hijabi na d'auko Nasa ina tafiya da kyar har na fita bakin fate napep na Tara ya kaini gida, ina Shiga gida naci sa'a Mama na d'akin ta hakan yasa na Shiga ban d'aki na gyara jikina.
Fitowa ta Kennan daga ban d'akin Mama ta Shigo d'aki na, ganin irin tafiyar da take ta tsaya Kallo na Tace "Me ya same ki a kafa na ga kina limping?"
Cikin inda Inda nace "Mun dan yi accident ne a hanya na sai na d'an buga kafa na"
Tace "Subhannallah Baki ji ciwo Sosai bako?"
"Eh d'an bugewa nayi kuma nasha magani"
"sannu Allah ya sauwaka, Ita Mardiya fa babu abinda ya same ta" ji nayi kamar na fashe da kuka da naji ta anbaci sunan ta amma nayi kokarin dannewa nace "Eh babu abinda ya same ta nice kadai na d'an buge"
"toh Allah ya tsare na gaba"
Na amsa da "Ameen" sai ta fice.
Kwana nayi da zazzab'i chemist d'in unguwar mu na nufa na sayi magunguna nasha shine na samu zazzab'in ya d'an sauka, washe gari kuwa da mamaki na ina kwance a d'aki na ga shigowar Mardiya da Wannan Yarinyar da ta bamu abin Sha.
Mikewa nayi saye cike da takaici nace "Ke me ya kawo ki gidan mu? Ke don ke karamar Mara kunya ce har kin iya tako kafar ki Cikin gidan mu har cikin d'akina?"
Mardiya tace "Kiyi hakuri Wallahi ban San gidan su Usu bane"
Murmushiin takaici nayi nace "Ke d'ince baki San gidan su Usu ba? Bayan gidan su Usu a unguwar nan yake? Mardiya kin cuce ni kin lalata min Rayuwa kin ruguza min tanadin da na dad'e ina yi,laifin me na Miki? Wallahi tallahi bazan tab'a yafe Muku ba"
Wacce suka shigo tare ce tayi duguwar tsaki Tace "To sai me in baki yafe ba, kar fa ki d'auka Mun Zo neman yafiyar kine, munzo gidan ku ne don muga yanayin da kike ciki"
Ji nayi kaina Yana juyawa na rasa abinda yake min dad'i cikin kuka nace "Dan Allah me na muku me na muku"
Mardiya Tace "Wallahi babu abinda Kika Mana, Kin san ance mutunci ya fi kud'i but to me kud'i yafi mutunci, 5 mil ba wasa, zuwa yayi ya same mu, Akan mu taimaka Masa ya cimma burin sa Akan ki, kin San ke d'in akwai kayan Jin dad'i " dariya sukayi suka yi tafi kana ta d'aura da fad'in "Ya mana tayin 5mil each ni ko ina ganin Wannan kud'in bazan bari su wuce ni ba"
Ji nayi kukan ma na kasa yi ina kallon su baki a bude nace "Yanzu akan kud'i? Akan kud'i Kika min Haka kefa kawatace?"
"mtssw Wannan kuma ke ta shafa na samu kud'i na babu abinda ya Sha min Kai, Kuma idan Kika kuskura kikace Zaki Kai karan mu, ina mai tabbatar miki da sai Bashiir yaji labari, Kuma idan yaji kema kin San ba zai tab'a auren ki ba"
Ayrah dariya ta Shiga yi Tace "Sunan wani abu wai fanko, anyways kar ki damu baza mu fad'a Masa ba , Amma idan Kika kuskura muka ji maganar nan a wani wuri sunan ki Sorry, Kinga Nan" wayarta Ciro a jaka ta nuna min Video d'ina da na Usu Ashe sunyi Mana video yanda yake lalata dani, ta d'aura da fad'in "Nasan Mardiya baza ta rasa number sa ba zamu tura Masa"
Mardiya Tace "Idan kunne ya ji?" Had'e da rike kunnen ta, Ayrah ta karasa mata zancen nata da "Jiki ya tsira" suka yi dariya had'e da barin d'akin na dad'e a tsaye agun kukan da nake yi ma na kasa yi.
Zama nayi na had'a Kai da gwiwa ina kuka Jin an turo kofar ne na yi shiru had'e da d'ago kaina don ganin Wanda ya shigo ina ganin Isha ce ta nufeta da gudu na fad'a jikin ta ina kuka, Allah sarki Isha kawar arziki Nan ta zaunar dani tayi tayi ta rarrashi na, Bayan na fad'a mata abinda aka min har ta fini Shiga tashin hankali, tashi tayi akan zataje ta sanarwa su Mama don a bi min hakki na, na hanata sannan na fad'a mata dalili na da farko taki Amincewa bayan hakurin da nayi ta bata ta fasa fad'a musu ba don ta so ba.
Ana saura kwani hud'u bikina Bashir yazo gidan mu, ina ganin yanayin sa, sai da naji gaba na ya Fad'i dama a parlor baba muke Hira Bayan Mun gama gaisawa sai nace "Kana Lafiya kuwa,naga fuskar ka wani irine"
"Lafiya na Lau,akwai maganar da nake so muyi dake ne"
Na amsa Masa da "ina sauraron ka"
yace "so nake ki rakani wani wuri yanzu"
Zaro Ido nayi nace "Yanzu da daren nan? A a gaskiya Ni ba inda zanje Mama ba za ta bari na fita ba yanzu"
Murmushin gefen baki yayi yace "Amma Kuma kin iya zuwa 'dakin samari ko?"
Cikin rashin fahimta nace "Ban fahimce ka ba"
Yace "Kar ki rainawa kanki hankali don wallahi kinyi kad'an ki rainan hankali" wayan sa ya ciro ya nuna min Video nan, kuka na fara yi ina fad'in "Wallahi ba da sani akayi ba" Amma yaki yarda da magana ta mikewa yayi yace "A Daren nan Nima ina so ki bani abinda Kika bashi in ba Haka ba goben Nan zan turo a karb'a min kayana da na kowo gidan ku"
Durkusawa nayi a akasa da gwiwowina ina rokon sa "Dan Allah Bashir Kar ka min haka, Dan Allah da wanne zanji Dan Allah ka rufa min asiri."
Yace "Idan kina so na rufa miki asiri kiyo yadda nace kawai" ganin dagaske yake hakan yasa na share hawayena na Mike had'e da fad'in "Bashir idan baka fasa aure na ba kai ba d'an halak bane, kayi Duk abinda zakayi Amma Ni bazan bika"
Cike da mamaki yace "Oh haka kikace, kinje ki ba wa wani ni da zan aure ki ne baza ki bani ba?"
"Tunda aure na zakayi sai ka jira idan aka d'aura auren sai na baka kaina Amma wallahi bazan tab'a aikata abinda kake so na aikata ba"
Yace "Allah ya sauwake na had'a jini na da Yar iska karuwa"
"uhmn naji na gode Amma Allah Shaida nane ban a hayyacina aka yi hakan ba"
"Dallah gafara makaryaciya inda fyad'e aka miki ai da kin fad'a a gida ko ni Nan bazan bari ba, bare ma karya kike da son ranki akayi hakan"
"Ban fad'a wa kowa bane sabida sun tsoratani Akan zasu nuna maka, shiyasa na yi shiru"
"Makaryaciyar banza, Ni zaki kalla ki fad'awa hakan an gaya miki ni yaro ne, Wallahi Meerah idan baki biya min bukatata ba zan fasa auren ki"
"Sai akace maka Ni d'in wawiyace ko? Oh in baka kaina ka yi yanda kake so dani sannan kaki aure na, Ni ba mazinaciya bace, sannan na tabbata bani da zunubi a agun mahaliccina, sabida haka kazo ka karb'i kayan ka mtssw" tafiya nayi na barshi a gun baki a bud'e shikan sa yayi mamakin yanda akayi ban amince da bukatar sa ba Duk da dama niyarsa ko da kuwa nayi abinda yake so bazai aureni ba.
Bayan na Shiga gida Isha na Kira na Sanar mata da yanda mukayi da Bashir, Isha cike da mamaki Tace "Bashir ya bani mamaki, insha Allah, zai had'u da dai dai shi"
Cikin Muryar kuka nace "Isha yace zai fasa aurena Dan Allah yazanyi ina tsoro Kar ya sanarwa iyayena"
"Kar ki damu, inshallah Allah na tare dake" Nan tayi ta rarrashina, daga bisani ta katse wayar.
Washe Gari
Da safe Bashir ya turo magabatan sa, gidan mu Akan a maida Masa kayan sa, Baba na jin dalili a take hawan jinin sa ya tashi Mama ta Shiga tashin hankali a gurguje aka kaishi asibiti, Bayan ya farfad'owa yayi kuka har ya tsine min Albarka, Albarkacin Mama ita kadaice ta yarda da magana ta.
Baba yafi shekara baya kulani ni kuma ban gaji da bashi hakuri ba duk da ba saurarona yake ba, bayan wasu watanni nayi wani rashin lafiya kamar bazan tashi ba, sanadin rashin lafiyar Nan ne Baba ya saurareni har ya fahimci komai yayi da na sanin fushin da yayi dani sannan ya kudiri aniyar sai yasa an Kama su.
Amma mama ta hana a fad'in ta idan akayi hakan tamkar an tona min asiri ne, dakyar ta shawon Kan Baba ya bar maganar, Bayan na samu sauki ne yasa na Shiga school if nursing, tun daga Wannan ranar da zaran mijin aure ya fito Sai a same shi a sanar dashi Kuma na tabbata aikin Mardiya da Ayrah ne.
'dago Kai tayi tace "Ma'aruf kaji abinda Kanwar ka tamin sabida son zuciya irin nata" ta karasa maganar tana kuka.
Ma'aruf Banda ambaton Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un babi abinda yake yace "Mardiya Ashe haka kike? Innalillahi am finding it Very difficult to believe my ears"
Isha Tace "Ya fa Riga ya wuce dan Allah"
Cikin Muryar kuka Tace "Hakika nayi abubuwa da dama Wanda ban tab'a da na sani ba sai yanzu Wallahi nayi na dama Dan Allah ku yafe min"
Isha Tace "Ni baki min komai ba, Meerah kikayiwa Kuma Insha Allah zata yafe miki"
Mardiya Tace "Isha kema na miki laifi kawai dai baki sani bane"
Isha cike da mamaki Tace "Laifin me ni Kuma Kika min?"
*ina masu son koyon humra da kwalacha na jiki da kuma kwalacha na gashi da turaren wuta da kuma kyaran jiki na uwar gida har amarya akan naira #250 kawai, duk mai bukata ya tuntube ni a wannan number 07053599651*
_____________________________
Please comment and share
Milhaat ce
Yar Terewa
[7/6, 1:26 PM] Miilhaat: 🍃 *DANGIN UBANA*🍃
Story & Written
By
Milhart
Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne.
*🌍MANAZARTA*
*WRITERS ASSOCIATION📚🖊*
*M. W. A*
*Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.*
Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️
*BISMILLAHIR RAHAMANIN RAHIM*
Page
49&50
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._
```Continuation..........``` kallon Yayan ta Mardiya tayi kana ta sunkuyar da kanta kasa tace "Tun ranar da na ganki a cafeteria da Haisam na gane ki, sabida nasha ganin hotunan ki a wayan Meerah, Ayrah ta nuna min tana son sa nice na zugata mukaje gun Boka aka asirce shi, sannan ta bini akan muje mu tona naki, Haisam bazai tab'a son wata ba in har Wannan layan na kasa"
Isha Mikey tayi cikin Muryar kuka tana ambaton sunan Allah tana fad'in "Mardiya why? Mardiya me muka miki haka da kike son ganin mun wulakanta?"
Kai a kasa tace "Meerah Qawata ce tun muna Yara dake unguwar mu d'aya ke Kuma kawar Tace a makaranta, Meerah tana samun Duk wani gata da jin dad'in Rayuwa iyayen ta sunfi nawa karfi bayan hakan Kuma suna sonta sosai kasantuwar ita kadaice Yar su shiysa da Usu ya Zo min da bukatar sa na amince sabida nasan Dole iyayen ta zasu tsane ta, maganar ki da Haisam Kuma hoton ku na gani ke dashi a wayar Meerah sai naji na kamu da son sa ganin irin Soyayyar da kukewa junan ku nasan bazan tab'a samun Soyayyar sa ba, shiyasa na yi kokarin raba ku, duk Wanda ya ganku zai gane Kuna son junan ku Amma, Haisam bai gane ba shiyasa mukayi amfani da wannan damar wurin rabaku,amma Wallahi tallahi ban san Shirin rabuwa take dashi ba plan d'inta ne da mahaifinta Wanda ni ban sani ba, Amma a yanzu nayi na dama kuma na miki alkawarin yau d'in Nan zanje na cire layan Nan"
Cikin Muryar kuka Tace "Kin cuce ni kin cuci masoyina bazan tab'a yafe miki, a dalilin Kune na kamu da ciwon zuciya, sannan a dalilin kune Yayana Yana chan yana kwance Rai a hannun Allah, bazan tab'a yafe muku ba"
Durkusawa mardiya tayi ta had'e Hannayen ta wuri gudu alamun roko Tace "Dan Allah kuyi hakuri ku yafe min, wallahi alhakin kune yake ta bina gashi na gama makaranta sama da 3 years Amma babu Wanda ya tab'a zuwa gidan mu da sunan yana Sona, in ko an min zancen Soyayya to jikina suke so Dan Allah kuyi hakuri ku yafe min"
Meerah itama mikewa tayi a tsawace Tace "yafiya? Har kina da bakin neman yafiya a wurin mu? Shin zakiyi iya Dawo min da budurcina da kimata da na rasa a dalilin ki?" Isha ta d'aura da fad'in "Shin Zaki iya Dawo min da Yayana? Zaki iya sa ya tashi? Ko Kuma zaki iya bani lafiya" Cikin tuhuma suke mata maganar.
Meerah Tace "Baza ki iya bako? To kamar yadda baza ki iya Dawo da wa'an nan abubuwan da muka rasa a dalilin ki ba Haka baza mu iya yafe miki ba" riko hannun Isha tayi da niyar barin d'akin har sun Isa kofar fita, Ma'aruf yace "Isha please " a hankali suka juyo suna kallon sa, ya karasa inda suke yana matsar kwalla yace "Nasan an zalin ce ku, har abada abinda kuka rasa baza su Dawo ba, Dan Allah ina rokon ku, ku yafe mata on my behalf, and please Isha Kar abinda Kanwata ta aikata a gare ki ya sa ki janye maganar aurena dake"
Murmushin gefen baki tayi kana Tace "It can never happened"
Cikin rashin fahimta a d'an kid'ime yace "What? Isha please Kar kice baza ki aure ni ba Dan Allah"
Girgiza Kai kawai tayi ta fice Meerah na ta bi Bayan ta yana Kiran sunan su basu juyo ba bare su saurare shi ya dad'e a tsaye a gun ya rasa abinda ke Masa dad'i d'akin shiru yayi Banda sautin kukan Mardiya babu abinda kake iya ji a parlorn, cike da takaici ya kalle ta Kiran sunan ta yayi da d'an karfi "Mardiya!!!
A d'an razane ta d'ago kanta had'e da mikewa jikin ta na kyarma cikin rawar murya Tace "Na...naaa..... Na'am Yaya"
Cike da takaici ciza leb'en sa yayi yace "Are you happy now? Kinji dad'i ko? A dalilin ki na rasa masoyiyata"
"Wallahi yaya ban sani ba, ban San itace wacce kake so ka aure ba da ban....... "
A tsawce ya katse yace "Da bakiyi me ba? Oh sai kin San cewar zan aure ta ne tukkunna kisan abinda ya kamata? Who gave you the right to mingle in someone's life? Me suka miki? Nace me suka Miki?" Ya karasa maganar cikin tsawa har Saida ta razana ta jaa da baya a tsorace cikin Muryar kuka Tace "Yaya please" daka mata tsawa yayi ya nuna ta da 'dan yasa yace "This will be the last day da zaki sake kirana da wannan sunan Ni ba Yayan ki bane, daga yanzu na yanke ki daga jikina" ya Kama hanyar fita da gudu ta karasa inda yake ta rike kafafun sa tana kuka had'e da bashi hakuri, hankad'e ta yayi da kafar sa ta buge bakin ta a Kan tiles d'in dake gun Nan da nan bakinta ya Kumbura ganin ya fice ta bi Bayan sa cikin sauri.
Wurin motar sa ya nufa ya shige ganin tasa hannu ta bud'e motar zata Shiga a tsawace yace "Kul Kar ki soma Wallahi Kika kuskura Kika Shiga min mota sai na karya ki kinji na gaya miki" marfin motar ta rike ta sandare tana kallon sa tsaki yayi ya sa hannu ya ja marfin motar sa da karfin gaske ya rufe ya had'a da yatsanta , wani Kara ta saka har da ya tsorata, da sauri ya fice daga motan, hannun ta ya cire ya na mata sannu had'e da hura mata hannun (Nace Allah sarki jini kennan duk da yana fushi da ita amma ya damu da lafiyar ta) yana tuna abinda tayi ya ture ta had'e da rufe marfin motar sa ya zaga ya shige ya sa wa motar key Mai gadi ya wangale Masa gate,Mai gadi yana masa sannu da fitowa Amma bai kalle sa ba bare ya amsa,ficewar sa kawai yayi.
Mai gadi girgiza kai yayi had'e da fad'in "Anya Lafiya kuwa?"
Sai ya hango Mardiya a tsaye tana kuka ta rike hannu ta tana kallon raunin da Yayan ta ya ji mata, da sauri ya karasa inda take yana mata sannu ganin jinin da yake zuba a hannun ta, yana mata magana bata kulashi, hanyar fita tayi Yana kallon ta har ta fice, tab'e baki yayi had'e da fad'in "Tooooh Allah shi kyauta."
Da sallam ya shigo parlor kallon da take Masa ne yace "Mama Lafiya kuwa kike min irin wannan kallon?" Ma'aruf keyiwa mahaifiyar sa Wannan tambayar.
"Ina fa Lafiya ina ka baro min yarinya, Kun fita tare Kuma ka Dawo kai kadai"
Shiru yayi a zuciyar Kuma yace "Kash Ma'aruf ka kwafsa kasan Dole sai an tambaye ka inda take" a karo na biyi ta Kuma cewa "Ina magana kayi Shiru Ina take?"
"Umm... Ummm" Muryar ta ya jiyo a ta Bayan sa tana fad'in "Gani Nan Mama"
"mtsww dama kuna tare Kuma shine ina tambayar ka kayir Min shiru"
Shiru yayi baice mata komai ba, mardiya inda Mama take ta nufa ta zauna a gefen ta, idon Mama ne ya sauka a hannun ta da yayi jajir jini yana d'an sauka a hankali cikin tashin hankali Tace "Subhannallah Auta me ya same ki?"
"Mama na....."
Charafff ma'aruf ya kase ta da fad'in "Wurin rashin hankalin ta man, ta datse hannun ta a marfin mota"
Hannun ta rike tana mata sannu Tace "Amma shine Kuka Dawo gida baka kaita asibiti ba? Haryanzu fa jini yana zuba"
Yace "itace fa, Babu yanda banyi da ita ba muje Taki wai in muka dawo gida zata sha magani shiyasa na kyale ta"
Mardiya kallon sa tayi cike da mamakin karyar da yake,ganin tana kallon sane hakan yasa ya mata wani irin muguwar Kallo,da sauri ta kawar da kanta.
"idan ita bata da hankali kaima baka dashi Kenan? Maza ka d'auke ta kuje asibiti"
Ba don yaso ba ta fita tabi Bayan sa, ta tarar ya Shiga mota har ya tada ta, ta bud'e gidan baya zata zauna a tsawace yace "Ni d'in driver kine da Zaki zauna a baya don gidan ku?"
Jiki na rawa ta Dawo gaba, tana zama Bai jira ta rufe kofar ba ya fizgi motar, Mai gadin gidan nasu ya bud'e musu gate suka fice, babu Wanda yayi wa d'an uwan sa magana har suka Isa wani clinic tare suka Shiga yasa aka wanke mata had'e da sa bandage, ya biya sa hakkin sa kana suka fice.
"a gaskiya Isha wannan shawarar da Kika yanke bata yi min ba Sam" Meerah kewa Isha Wannan maganar.
Isha kallon ta tayi da kamar baza ta tanka mata ba sai Kuma tace "Koh?"
Meerah ta amsa da "Kwaraai ma kuwa"
"To ni yamin"
"Uhmn Isha Kenan, ya kamata ki gane wani abu Mardiya daban haka ma Ma'aruf daban, so please kar laifin wani ya shafi wani please"
"Dole ya shafe shi sabida kanwarsa ce, Akan
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 24