Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yake 'boyewa? Anya Adnan baida sa hannu acikin 'batan Ayrah kuwa? Mtswww ko ma mene ne zan bin cika" ta d'auki wayarta ta Fara latsawa. Bayan ta Dawo daga gun aiki ta tarar da su Umma, abba, Daddy, Isha, Mummy da Twins Sannan da Auta suna dinning suna cin abinci suna Hira, manta jiki tayi tana kallon su, ganin yanda suke farin ciki basu da wata damuwa, tsanar Isha ne ya sake ninkuwa a zuciyar ta. "You don't deserve to be happy, yayana ya rasa ransa Amma ko kad'an abun bai dame ki ba, hankalin ki kwance dake da ahalin ki, to wallahi Ni zan Zama sanadin rushewar farin cikin Nan tunda Ayrah ta kasa, Allah sarki Mummy da Daddy, Ina kewar ku sosai Yaya kasance kana son farin ciki Isha sama da komai a duniya Amma Bata damu da Kai" magana take a zuciyar ta tana matsar kwalla, batayi aune ba sai jin murya Umma tayi Tace " 'yata kin Dawo?" Had'e da dafe kafad'ar ta. Umma kallon fuskar ta tayi, cike da tausayi tasa hannu ta share mata Tace "Ki daina Kuka Mardiya, nasan is not easy ki d'auke mu tamkar family d'inki kinji, ki cigaba da musu addu'a kinji" Girgiza Kai tayi cikin Muryar kuka Tace "Nagode Umma" ta fashe da wani irin kuka, Umma rungume ta tayi tana rarrashin ta, Suma kallon su suke suna jin tausayin ta Amma Banda Haisam ya rasa dalilin da yasa ya ji bai yarda da yarinyar Nan ba, cigaba da cin abincin sa yayi hankali kwance, Roku hannun ta Umma tayi har dining table kaita ta jaa mata kujera ta zauna , sannan ta karb'i jakanta ta ajiye mata daga gefe, plate ta d'auka ta sa mata abinci sannan Tace "kici abinci" ta shafa kanta kana ta koma mazaunin ta, shiru wurin yayi baka jin komai sai Karan cokula, abincin take ci Amma Sam bata jin dad'in da, taci Kad'an kana ta mike had'e da fad'in "Nagode, bari na shiga ciki" Mummy Tace "Ki samu kiyi wanka sannan ki Dawo ki same mu a parlor ki daina zama ke Kad'ai" cike da kulawa take maganar, Murmushi Mardiya tayi had'e da fad'in "to mummy." Bayan ta Shiga d'akin ta ruwa ta watsa duk jikinta a Sanyaye , Bayan ta gama ne ta zauna a bakin mirror tana shafa mai, karar wayar ta taji tana ringing, ta duba don ganin wane ne, number ta gani ba suna, tsaki tayi bata d'aga ba an Kira har a karo na uku kana ta d'aga ta Kara a kunnen ta ba tare da tace komai ba daga 'dayan 'bangaren akace "Assalamualaikum" Murya kasa kasa ta and da "wassalam" " Barka da war haka Hajiya Mardiya" Jin an Kira sunanta ta d'an d'aga girar ta kamar yana kallon ta Tace "Yauwa barka dai" tana son gane ko wane ne. "Suna na Abdallah, abokin Adnan" Yar karamar Murmushi tayi had'e da fad'in "Oh Abdallah barka kana lafiya, ya gajiyan ku na d'azu Nagode fa" Shima Murmushin yayi yace "Bakomai, da fatan kina Lafiya?" "Alhamdulillah" "Ya aikin? An taso ko?" "Eh" "Allah ya taimaka dama na Kira ne naji lafiyar ki" "Allah sarki Nagode sosaiii" "Goodnight" Ta amsa da Night. "Ayrah Wai meyasa kike da shegen taurin Kaine?" A tsawce yake maganar kallon sa tayi sama da kasa kana ta kawar da kanta, ajiyar zuciya yayi ya Saira kansa ya lura idan ya mata da zafi bazai tab'a samun kanta ba. Durkusawa yayi a gaban ta ya hard'e Hannayen sa alamun roko kana yace "Ayrah Dan Allah Dan Annabi give me chance na tabbatar miki da cewar ina son ki, so na Haki ka" Kallon sa tayi kana ta murmusa Tace "Naji zan amince da hakan Amma ina da sharad'i" "Ina sauraron ki just name it and Ni zan yi miki shi" Mardiya na Gama shafa mai simple duguwar Riga ta Sanya a Jikin ta kana ta fito parlor kamar yadda mummy ta umurce ta, hirar su suke hankali kwance, sunayi suna dariya. Wuri ta samu ta zauna had'e da fad'in "Mummy na d'auka Kun koma gida fa" Murmusawa Mummy tayi kana Tace "A a yau muna nan, Umman ku ta kafa ta tsare akan dole mu kwana" "har naji dadi zamu Sha Hira kam" Isha ta ce "Sai kace dama tana hirar" " Ina yi man, gashi nazo ayi Dani" "toh you're welcome" Haisam zaman ta a gun duk yasa yaji ransa ya lalace mikewa yayi had'e da Mika yace "Nikam zan kwanta, bacci nake ji, sai da safe" Duk suka amsa da Saida safe, Kallon Isha ya tsaya yi ita ma kallon sa take gira ta d'aga Masa alamun ya dai? Sai da ya tabbatar hankalin su Mummy baya kansu kana murya kasa kasa yace "I Love You" rufe fuskar ta tayi da tafin hannun ta tana Murmushi, Mardiya kuwa duk abinda suke Akan idanun ta, tsaki tayi Wanda yasa Haisam yayi saurin kallon ta, wani irin Kallo ya mata Wanda yasa tayi saurin kawar da kanta, tana jin kirjin ta na duka uku², Isha ta lura da sauyawan fuskan nasa, cikin sanyin Murya Tace "Ya Haisam what happened?" Murmushi yayi mata Kana yace " Nothing ki hau online" Yana Kai Nan ya haura sama bai tsaya jin me zata ce ba, bin Bayan sa tayi da Kallo, kana ta maida kallon ta ga Mardiya wacce ta manta kanta tana kallon Haisam d'in, Isha da d'an karfi Tace "Duk maita Mutum wannan halittan ya fi karfin sa" sai kuma tayi kamar ba ita tayi ba, Abba yaji abinda Tace Sarai Amma bai gane da wa take ba, kawai ya batsar. Mardiya kuwa hararar Isha tayi had'e da mikewa Bata ce musu komai , Babu ma Wanda ya San ta bar gun Isha kuwa Tace a ranta "sai nayi maganin Yar iska dani kike zancen" Datan ta ta bud'e suka cigaba da chat d'insu da Yayan ta, Yana nuna Mata shi sam Baya son zaman Mardiya a gidan, Isha da itama ranta a 'bace yake da Mardiyan sai ta danne 'bacin ran natan tana ta bashi hakuri. "Ayrah kinyi shiru? Fad'a min mene ne sharad'in naki?" "Na'amince zan aure ka" Wani uban tsalle Adnan yayi yana Fad'in "Yessssssss!!! Yaja yes d'in sabida tsantsar farinciki, ita kanta Ayrah abinda Adnan d'in yayi ya bata dariya, sai taji ya burge ta, matse dariyar tayi Tace "Not so soon, Kar kayi farin ciki tsaya kaji sharad'ina tukunna" Zama yayi a gefen ta Yana kallon ta yace "Uhmnn, ina jinki" "Zaka barni na koma gida daga nan sai muyi auren mu" Murmushin gefen baki yayi kana ya mike yace "Zaki koma gida Amma Nima kiji nawa sharad'in" Tana kallon sa don Jin me zai ce. _______________ Toh fans me kuke ganin Adnan me zai bukata daga gare ta? Ina jiran amsoshin ku. Please comment and share fisabilillah. Milhaat Ce Yar Terawa 75&76 '''Continuation.........''' sai da ya Kai bakin kofa yasa hannu ya bud'e kofan kana ya waigo ya kalle ta, Murmushi yayi yace "Zaki Koma gida a matsayin Mata ta, idan kin amince ki same ni a d'akina, and kir ki wani damu da batun waliyi, Zanyi handling na komai" ya fice kana ya rufe Mata kofar , duk da ya fita Amma baki a bud'e take kallon kofan, tana mamakin karfin Hali irin nasa. Zama yayi yana jiran ta Amma shiru har bacci yayi awun gaba dashi, alarm d'insa ne ya buga na karfe 5 ,jaan wayar yayi ya kashe kana ya Shiga ban d'aki ya d'auro alwala ya tada sallah , Bayan ya idarne ya Koma baccin Sa. Ayrah kuwa kasa bacci tayi tana ta kuncewa da tsakawa ta rasa abinda zatayi, sai da taga wuri ya fara haske ta shige ban daki tayi alwala, Bayan ta idar da sallah, zaune take Akan prayer mat d'in haryanzu dai maganar Adnan ke Mata yawo a kwakwalwar ta, Bayan ta gama tsakawa da warware a bayyane Tace "Zan amince na aure ka, Amma da zaran na fita anan dole ne ka sake ki, in Kuma kaki kotuce zata rabani da Kai" Kofar d'akin sa ta nufa, ta kwankwasa kofar had'e da kusa Kai ciki, duk zaman ta a gidan bata tab'a zuwa d'akinsa ba, daga d'akin da take sai kitchen, baccin Sa taga yana yi, ta koma da niyar fita Muryar da taji yace "Ina Zaki?" Cikin Muryar bacci ya mata tambayar Nan. "Na d'auka bacci kake" "Umm yanzu na farka Shigo Mana" Kujeran dake gaban Mirror ta ja ta zauna a kusa dashi kana Tace "Nazo muyi magana ne" Zama yayi yana d'an goge idanun sa da yatsunsa kana yace "Ina jinki" Shiru tayi kanta a kasa kana Tace "Na'amince zan aure ka, Amma Dan Allah Kar ka cutar Dani" hawaye fal a idanun ta, hannu yasa ya share mata kana yace "Insha Allah, I will never guv you the chance to regret, Is a promise" Murmushi tayi, shima ya maida mata mikewa yayi da d'an saurin sa ya shige ban d'aki karar ruwan da taji ne hakan yasa ta gane yana wanka ne, Zama tayi tana jiran sa, tana jin ya fito ta sunkuyar da kanta, ta cigaba da wasa bda yatsun ta, abun ma dariya ya bashi, me bata sani a Jikin sa ba? Sai da ya gama Shirin sa tsaf yace "Muje muyi breakfast ko?" Ta amsa da toh, had'e da mikewa tayi gaba yabi bayanta, yau tare sukayi girki, sunayi suna Hira abin birgewa kamar wasu amarya da ango, ko da yake sun kusa su fad'a lambun ma'aurata. Bayan sun gama karyawa ne, ya fita da niyar tsara komai na yanda za'a d'aure auren sa da Ayrah, hakan kuwa akayi bai dawo ba har sai da ya tabbatar an sa ka ranar d'auren su Nan da sati d'aya hakan kuwa akayi,dama ba wuya a wurin Allah muddin an sa Rana, a yau aka d'aura auren Adnan da Ayrah Akan sadaki dubu d'ari. (Oh Ni Milhat jikar Mutum hud'u, Adnan ya d'aura auren da masoyiyar sa ba tare da iyayen sa ko iyayen ta sun sani ba, yayi hayan iyaye ba tare da Wanda ya d'aure ya sani ba, Ko ya zasu wanye? Mu cigaba da zuwa). Adnan ya sa an yi Masa video don ya tabbatar wa da Ayrah cewar an d'aura musu aure ta Zama mallakin sa, Allah sarki Ayrah a duk sanda aka d'aura wa yarinya aure tana samun kula ta musamman a gun dangin ta, za a rako ta har d'akin ta ana nuna mata so da Kauna sannan su rabu cikin kuka da kewar juna, Amma kashhh ita ta samu aka sin hakan, video d'in da yayi shine shaidar auren su, tayi kuka sosai Adnan tun yana rarrashin ta har ya daina ya fita ya bar mata d'akin ma gaba ki d'aya. Tun daga wannan ranan Ayrah kullum cikin kuka take,shi Kuma Adnan baya gajiya da bata hakuri a haka har ta sake Jiki dashi ta bashi dama Yana nuna mata irin soyayyar da yake mata,yana Kuma saka ta tana Kara son shi,duk da cewar tana kokarin taga ta 'boye,Amma masu iya magana sunce shi so baya 'buya. Haisam ta samu sauki sosai har ya Fara fita gun aiki,farin ciki da kwanciyar hankali Kuma sai dai ace Alhamdulillah,Isha na samun kula sosai musamman ma gun Umma da ta hana ta fita ko ina,idan ta fito to tare da Haisam suka fita Nan ma idan suka dad'e Umma tayi ta Kira Kenan Kira Kan Kira. Shirye shiryen Biki Meerah ake yau saura kwanaki Uku, events Kam sun Sha shi,sunyi friends day,bridal shower da dai sauran isha ba a barta a baya ba duk da ba wani Abu take ba sai dai ta zauna tana kallon su. *Ranar Biki* Farukh ne zaune da Haisam da sauran abokan sa suna shiri zuwa gun d'aurin aure sai tsokanan sa suke musamman ma haisam da dama sarkin tsokana ne,wayar Farukh ce tayi kara har da bazai d'auka ba sai Kuma ya zaro wayar a chaji ,sakon da ya shigo wayar sane yasa shi tsuman tsaye,Nan da Nan hawaye suka cika idanun sa,Kallo d'aya Haisam ya Masa ya Gane ba lafiya,hakan yasa ya mike ya nufi inda yake kafad'ar da ya dafa had'e da fad'in "Ya dai ango Lafiya kuwa ga na ganka Haka?" Farukh Mika Masa wayan yayi ba tare da ya Ce Masa kala ba, Haisam da d'an saurin sa ya sa hannu ya karb'a. Yana ganin abinda faruk d'in ya kalla zaro ido yayi dq d'an karfi yace "whaaaaatttt!!!! Hakan yasa dukkanin abokan su hankalin su yayi ta Dawo kansu,d'akin shiru yayi baka jin motsin komai sai Karan AC da kumma TV dake aiki. _________________ Please comment and share Milhat ce Yar Terawa 77&78 Continuation.......'''  'daya daga cikin abokan sune yace "Ya dai Guys? Lafiya kuwa?" Murmushi Haisam yayi had'e da fad'in "Good" beyi aune ba sai jin karar an rufo kofa, farukh ne ya fita Yana mugun sauru.     Haisam ne yace "Ku cigaba da shiri bari muzo" Bin bayansa sa yayi, har ya bud'e marfin motar yaji Muryar Haisam "Farukh ina zaka?"     Cike da tashin hankali Farukh yace "zanje ne na dakatar da auren Nan, I can't marry Meerah, Ashe dama haka Meerah take? Duk irin soyayyar da nake mata Amma ace da abinda zata saka min Kenan" ya karasa maganar Yana kuka, Haisam kwace key d'in motar yayi ya zaga ya Shiga gun zaman driver, farukh kuwa kallon sa ya tsaya yi ya kasa motsi, Haisam lekowa yayi yace "bamu da Lokaci Shiga muje"     "Ina zamu?" "Idan munje zaka gani" Tada motar yayi Mai gadi ya wangale musu gate suka fice daga gidan, gudu sosai haisam keyi sai da ya Isa inda yake son zuwa kana ya tsagaita gudun, a bakin gate d'in ya tsaya ba tare da ya Shiga ciki ba, wayar sa ya d'auka ya Shiga yayi dialling number, duka biyu ta d'aga da sallama, kai tsaye yace "Ki fito ki same ni ina waje, and please ke Kad'ai zaki Zo." Ya katse wayar ba tare da yaji amsar da zata bashi ba.     Farukh ji yayi kansa Yana mugun sarawa, ji yayi duniyar tana juya Masa, ji yake kamar ya fasa auren Amma wani 'bangare na zuciyar sa tana matukar kaunar Meerah.    Isha ce naga ta fito, ta nufo su da d'an kuttun cikin ta, Bayan motar Haisam ya bud'e Mata, ta Shiga ta zauna kallon su take tana Jin gaban ta mugun Fad'uwa sabida yanayin da ta ga Farukh a ciki, murya na rawa Tace "Ya Haisam Lafiya?"     Wayar Farukh d'in dake hannun sa ya Mika Mata, tana kallon video ta rike baki tana ambaton sunan Allah.                "Inna lillahi, wannan videon a ina kuka same shi?" Da sauri Farukh ya waigo ya kalle ta yace "Kin San da videon dama?" Kai a kasa ta amsa da Eh.       Farukh baki a bud'e yake kallon ta wasu sabbin hawayene suke gangarowa daga idanun sa yace "Kin sani fa Kika ce Isha? Amma kuma baki Sanar dani ba? Na d'auka ina matsayin Yayan kine kamar yadda kike Kirana Taya za a ce kin San halin kawar ki Amma ki bari na aure ta, Bayan kin San ita d'in ba alhairi ce a gareni ba"     Isha cikin kuka tace "Tabbas Meerah tayi kuskure da ta 'boye maka, duk da nasan tayi hakan ne gudun Kar ta rasa ka kamar yadda ta rasa Bashir"       "Ban gane ta rasani ba, me kike nufi da hakan?" "Wallahi ko kaffara bazanyi ba nasan wannan aikin Mardiya ne, ita kadaice zatayi hakan, Mardiya da kake gani ya Farukh, babu abinda baza ta iya ba don ganin ta 'bata Meerah, na rasa dalili Haka kawai ta d'auki Karan tsana ta d'aura mata, 8 years ago there where friends, Amma........ Nan ta bashi labarin yanda akayi mata fyad'e da yanda  suka mata video da Kuma yanda suka mata barazana sannan suka rabata da mijin da zata aura a satin da Za'ayi bikin su.     Ajiyar zuciya tayi Bayan ta gama bashi labarin, Jikin sa ne yayi sanyi , kallon Haisam yayi yace "Dama kaima kasan da maganar?" "Eh not long ago, bayan na farfad'o Isha take Sanar dani, nifa ko shiyasa duk na tsani yarinyar nan wallahi, bana son ta kwata kwata, Dole ma ta bar gidan Nan yau d'in Nan"     "A a Ya Haisam Kar kayi haka Dan Allah su Umma baza suji Dad'i ba" "Amma Princess Kinga dai abinda tayi ko? Kika San mene ne Shirin ta na gaba?"     " Ban sani ba , Amma inshallah ta Allah ba tata ba" Shiru yayi baice mata komai ba.     "Ya Farukh" ta Kira sunan sa cikin sanyin Murya. Had'a Hannayen ta tayi wuri guda alamun roko Tace "Dan Allah, Dan Annabi, Kar kace zaka fasa auren Meerah wallahi tallahi ba laifinta bane ba, Bata San komai akai ba, wallahi duk sharrin Mardiya da Ayrah, idan kace ka fasa auren ta zuciyar ta zata karye Dan Allah" ta karasa maganar tana kuka sosai kamar ranta zai fita,haisam hankalin sa yayi mugun tashi,don shi idan akwai abinda ya tsana shine yaji ko ya gani Isha na cikin damuwa bare ma ace tana kuka.    Murmushi gefen baki Farukh yayi yace "Ki daina kuka Isha, bazan fasa auren ta ba, hasali ma labarin da Kika bani ya sa naji ina bukatar na rayu da ita zan goge Mata wannan bakin tabon da aka Mata, Kuma zan miki wani alkawari sai Nasa an d'aurte wallahi wallahi bazan tab'a kyale ta ba" Murmushi Haisam yayi yaji dad'in maganar abokin Nasa,su isja sarkin kuka Kuma Aka cigaba da kuku.     "Ya Salam Princess,kukan Nan fa na mene ne,inace ya fad'a miki baza a fasa auren ba,meyasa Kuma kike kuka,kin San fa bana son kukan ki"     Cikin Muryar kuka tace "Ya Haisam, Dole nayi kuka ina tausayawa rayuwa tane dana Meerah,tun tasowar mu,bamu samun abinda muke so,idan mun gama da wannan matsalar sai wata ta 'bullo" ta karasa maganar tana kuka Mai sauti, Haisam rarrashin ta ya Shiga yi yace "Ma'isha"      Cike da mamaki ta d'ago tana kallon sa,don a iya zaman su dashi bata tab'a ji ya Kira sunan ta ba,idan ma ya Kira to ta manta, Murmushi yayi kana yace "Ni Haisam na miki alkawari zan share duk wata kunci da damuwar da kike ciki,kawai dai wannan d'an nawa na cikin ki ne yake katse min hanzari" ya karasa maganar kamar zaiyi kuka Isha kuwa hakan dariya ya Bata,tana kuka had'e da dariya.     Farukh yace "Wa yace maka namiji ne?" "A jikina nake Jin hakan" "Mtsww dallah malama ka tada mota mu tafi ya fa rana na ce, nasan suna chan suna jiran mu"    Dariya Haisam yayi ya kalli Isha kana yace "Princess ki Shiga ciki ko,zan Zo na d'auke ki anjima,kin San Umma Tace Kar na bari ki kai la'asar so ki kasance cikin shiri" Ta amsa da toh, had'e da bud'e marfin motar, Farukh ne yayi saurin fad'in "Dan Allah ki kwantar da hankalin ki auren da Meerah babu fashi sai dai idan mutuwa nayi, Sannan please bana so ki fad'awa Meerah ko ki nuna Mata cewar an turo min wani abu,ita Kuma wannan Kanwar zanyi maganin ta"       Dariya sukayi dukkan su, Haisam yace "me Kuma kanwa?" "Kanwa mana,kanwa uwar gami had'a su kasa rabasu"     Dariya suka Kuma yi cikin dariya Haisam yace "Princess jeki suturun sa ba karewa zaiyi ba" ficewa tayi ta shige,ai kuwa Isha na Shiga, Meerah na ganin ta ta fahimci akwai matsala,Jan ta tayi suka keb'e tana tambayar ta dalilin da yasa ta ganta a haka,Isha Tace Mata bakomai,ganin Meerah ta nace yasa Tace Mata marar ta ke mata ciwo,ta Mata sannu sannan suka Koma cikin kawayen nasu.     Dubbanin Mutane ne suka shaida Auren Dr Farukh Sani Usman da Ameerah Murtala, cikin mutanen kuwa harda Daddy da Abba.      Mardiya ne kwance akan gado,tana taunar chewn gum wata iriyar dariya tayi,Zama tayi Tace "waima taya Za'ayi kiyi aure  Ni banyi ba? Dr Farukh? Hmm kyakkyawan saurayi haka bai dace dake ba Sam dani  ya Dace,na tabbata duk inda yake yanzu yaga sakona" ta Kuma fashewa da dariya.    Muryar Umma taji tana Kiran sunan ta kanta amsa har ta Shigo kallon ta Umma tayi Tace "Lafiya ke da waye?" Murya na rawa Tace "Ummmmmm....waya nake"    "Ok ,ya naga baki shirya ba baza ki bikin bane?" " Wani biki Umma,Bayan an fasa bikin?"     " Wani bikin ne aka fasa? Bayan tun karfe 11 aka d'aura aure" Zumbur ta Mike Tace " No no inaa bazaiyu ba, wahala na ya tashi a banza Kennan?"   Umma Tace "Ke Lafiyan ki kuwa?" Shan jinin jikinta tayi ta zauna ta ce " kaina ke ciwo Umma,sai kun Dawo" wani irin Kallo Umma ta mata har ita mardiyan ta tsargu,ta fice abinta,tare da mummy zasuje tana jiran ta a parlor tana Isa parlor sukayi tafiyar su. Ciza leb'en ta tayie kana Tace "wato Farukh ya auri Meerah? Ko dai baiga sakon bane? Anyways idan ita Meerah ta tsira, Ma'isha baza ta tsira ba muje zuwa, wallahi sai na ga Bayan ku,I'll disgrace you to extend that you'll be ashamed of yourselves." Ta kwanta ta cigaba da danna wayanta tana jinra duk ba dad'i.     Umma da Mummy  dasu akayi bud'an Kai da kamu,a ranar amarya ta tare a gidan angonta.Allah ya bada zaman lafiya amiin.           *After 4 months* Malam Hassan duk wasu raunuka na jikinsa sun warke Amma sabida tashin hankali da ya Shiga ya had'u da shanyewan 'barin Jiki, duk wani kud'i da ake kashewa Faisal ne yake bada su, yayin da Mamy har ta cire Rai da ganin Ayrah, kullum sai tayi kuka.      "Mamy nifa na gaji da 'bata kud'i na Akan wannan mutumin" Faisal ke wannan maganar Kama hab'a mamy cike da mamaki tace "Kaci gidan ku" had'e da masa dakuwa.      "Yanzu  Kai Faisal rashin hankalin naka ya Kai haka? Ubankane fa duk lalacin sa, ni na d'auka kayi Dana sanin abinda ka aikata Ashe ba haka ba, ka godewa Allah ma da ya kowa abun da sauki da yanzu Ana irga kwanakin da ka mutu, daba don Allah yasa yaran basu da gata ba wallahi na tabbata da yanzu baka raye"      "Mamy dama tun chan kwanakin mutuwa ta basu yi bane, Kuma wallahi ko kad'an bana Dana sanin abinda na aikata, Ban so hakan ba, naso da shi d'in ne ya mutu ko hankali ya zai kwanta"     Tasss Tass Mamy ta shafa Masa maruka har sau biyu, rike kuncin sa yayi Yana matsar kwalla.    Mikewa Mamy tayi Tace "Ka fice min daga gani Kar Kuma na Kuma ganin ka anan, Kan kazo ka karasa min shi"        Faisal kwallon mahaifin sa yayi da yake kallon su, cike da hawaye a idanun sa, Murmushin Takaici Faisal yayi kana yace "Mamy mari na kikayi? Akan mutumin da bai damu dake ba, mutumin da bazai San mutuncin ki ba? Shin kin San irin bakin cikin da muke ciki da ni da Yan uwana Akan irin abubuwan da yake aikata Amma ke sabida.......... " Shiru yayi ya kasa karasa maganar kallon mahaifin nasa ya Kuma yi ya fice yana matsar kwalla.       "Zainabu!!! A hankali cikin sanyin Murya taji ya Kira sunan ta, da sauri har kafarta na hard'ewa ta nufi inda yake tana tambayar sa "Malam wani abun kake buka ne?"     Kai ya girgiza mata alamun a'a cikin Muryar sa Wanda baya fita mai kyau yace "Da baki mare shi ba sabida

Chapter 22 of 24