tana fad'in "Tabbas karya ya miki"
A razane ta Mike jikinta na kyar ma Tace "Mamy dama... dama kina Jin mune?"
"Kwaraai Yanzu ke Ayrah kin kyauta wa Kanki Kenan? Ashe dama abinda kuka aikata Kenan ko da yake Banga laifin ki ba kina amfani da abinda mahaifin ki ya d'aura ki a Kaine, to bari na fad'a miki gaskiyar maganar, mahaifin ki shi ya kashe Yayan sa, sannan ya kwace komai da komai nasa........ " Nan ta Sanar da ita komai da komai harda yadda ya aika a kona Haisam da mahaifiyar sa.
Ayrah Zama tayi a kasa, kasa motsi tayi sai hawayen dake gangarowa daga fuskar ta bakin ta rawa ta ma rasa me zata ce, Mardiya ce ta karasa inda take tasa a hannu ta d'aga ta ta zaunar da ita a kan gado fashewa tayi da Kuka tana fad'in "Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un me na aikata wa kaina, me nayi na Shiga uku"
Tsaki Mamy taja Tace "Kuka ba? Baki ga komi ba tunda kin biye wa ubanki zaki ji dashi" tana Kai Nan ta fita, Mardiya ce tayi ta rarrashin ta tana Jin jina lamarin tabbas mahifin Ayrah abun tsorone.
Ayrah tun daga Wannan ranar ta Shiga tashin hankali mara misaltuwa tundaga wannan ranar take kiran layin Haisam Amma baya Shiga tayi kuka tayi kuka har ta godewa Allah.
Yau ta kudiri aniyar ko ta halin Kaka sai ta ganshi, har asibitin da yake aiki taje aka tabbatar mata da bayi da lafiya, jiki ba karfi ta fita a hanyar ta ta fita sukayi kicibus da Farukh.
Farukh na ganin ta ya kawar da kansa Kamar bai tab'a ganin ta , da sauri ta bi Bayan sa tana Kiran sunan sa baiyi niyar kulata ba ganin yadda take kiran sunan da ya ja attention d'in Mutane yasa ya tsaya, kallon ta yayi kana ya kawar da kansa had'e da fad'in "Lafiya kuwa kike ta bina?"
"Am Lafiya lau dama Kaima anan kake aikine?"
Kallon ta yayi yasa hannu a aljihun wandon sa kana yace "umm umm a specialist nake, tambayar Nan ce ta sa Kika tsayar Dani?"
Jiki a Sanyaye Tace "A a dama ina Kiran layin sa ne baya Shiga shine nazo neman sa aka ce min bayi da lafiya me ya same sa ne Haka?"
Ciza leb'en sa yayi cike da takaici yace "As if you care ta ina ruwanki da lafiyar sa bayan burin ki Kenan? To Haisam ya Shiga comma a dalilin ki kinyi farin ciki ko? Mtswww" ya tafi ya barta a tsaye a gun baki a bud'e.
Ta dad'e a tsaye a gun kana ta wuce gidan su mardiya ta sanar mata da halin da Haisam ke ciki "tab wai yanzu a dalilin ku, a gaskiya Wallahi Allah bazai bar ku ba, idan kuma ya Rasa ransa a dalilin ki kema kin Zama Kamar mahaifin naki"
"look mardiya nasan mahaifina ba mutumin kirkii bane ba, Amma that's not give you the right to disrespect him kin gane ko"
"Am sorry am sorry abun ne ya dameni, yanzu mene ne abinyi?"
Cikin Muryar kuka Tace " I don't know, I don't know am in a mess Wallahi, idan Haisam bai yafe min ba Nima bazan yafe kaina ba"
"kiyi ta istigfari Sannan muyi fatan Allah ya bashi Lafiya, kin san fa Allah ba ya yafe laifin wani wa wani"
"Ba Wannan ba, asirin Nan nake so a karya shi, don kin San Boka yace bazai tab'a daina Sona ba har ya mutu sai dai idan Mun tone abinda muka binne"
"Ta kwana gidan sauki sai muje mu cire shi"
"Shikenan hakan za'a yi zamu had'u gobe Insha Allah"
Ta Mike kana ta Tace "Ni zan tafi sai anjima Amma Banga Mama ba bata nan ne?"
"Eh sun fita da Ya Ma'aruf"
"Oh Ya Ma'aruf d'in kin Nan yaki aure ki had'a ni dashi Mana"
"Taaab d'i"
" Me na wani tabd'i?"
" umm babu babu muje na raka ki" a zuciyar ta Kuma Tace "Allah ya sauwake mu had'a jini da ke"
Har jikin motarta ta raka ta, sai da taga fitar ta ta koma cikin gida.
Ma'isha tundaga Wannan ranar kullum a asibiti take kwana take ta wuni idan ta koma gida to dalili ne Mai karfi dake a kwai bathroom na staffs hakan yasa ta kanyi wankan a Chan Amma ta fiye yi a gida, Bayan likitocin dake kula dashi ita kadaice ake bari ta Shiga kansa Nan ma sai ta sa wani irin rigar Wanda baya Kara dama an tanadar dashine sabida Shiga ICU sannan suna da takalmi na musamman idan ta Shiga takan d'auka wa Umma hoton sa ta tura mata ko kuma in taje gidan ta nuna Mata.
Duk sanda ta Shiga gunsa idan ta fito Sai tayi kuka, ga Nan mutum amma ba Hali yayi magana.
Kwan a tashi asarar Mai Rai, wasa wasa Haisam ya kaie shekaru har biyu bai tab'a motsi ba.
Daddy,mummy da Ma'isha ne zaune a parlor, gyara Zama Daddy yayi yace "Daughter na Kira ne don ina so muyi wata muhimmiyar magana"
"Toh daddy ina sauraron ka"
" Yaron Nan Ma'aruf magabatan sa sun Zo nema Masa auren ki Amma nace sai na ji ta bakin ki tukunna, kina son sa?"
Ma'isha ji tayi gabanta na duka uku uku baki na rawa Tace "Daddy aure Kuma?"
Mummy Tace "Eh Mana Ma'isha so kike mu zauna mu zuba miki ido kina abinda Kika ga Dama? Isha idan ma bacci kike ki farka kina neman kusan shekaru 29 a duniya Amma har yanzu kin kasa fidda miji Kuma bawai kin rasa mane ma ba"
Cikin Muryar kuka Tace "Mummy ni gaskiya ban shirya aure yanzu ba"
Mummy Tace "Kana ji ko Alhaji, kana ji ko? Yarinyar Nan so take ta jaa Mana zagi a gari shiyasa tun farko nace ba sai kaji ta bakin ta ba asa rana kawai"
"Hakane Hajiya sai yanzu na fahimci abinda Kika hango sabida haka Isha zan sa ranar auren ki da Ma'aruf Nan da 2 weeks ki Fara Shiri" Yana Kai Nan ya mike ya Shiga d'akin sa Mummy ma ta Mara Masa baya suka barta a zaune a gun ta rasa me ke mata dad'i abin duniya Duk ya bi ya ishe ta.
____________________________
Please comment
Vote
And share
Milhaat ce
Yar Terawa
[7/6, 1:26 PM] Miilhaat: 🍃 *DANGIN UBANA*🍃
Story & Written
By
Milhart
Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne.
*🌍MANAZARTA*
*WRITERS ASSOCIATION📚🖊*
*M. W. A*
*Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.*
Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️
*BISMILLAHIR RAHAMANIN RAHIM*
Page
45&46
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._
_Continuation........._ jiki ba karfi Isha ta fita, asibiti ta nufa Wanda shine ya zame Mata wurin wuni da Kuma Kuma kwana ko da kuwa ranar aikin tace ko ba ranar aikin ba achan ta ke Zama, Bayan ta Isa asibitin ne ta tarar da Meerah ta tashi, Isha hannun Meerah ta rike suka fita waje suka zauna a inda ba hayaniya Sosai Tace "Meerah ina cikin matsala Ina cikin tashin hankali"
"Kwatar da hankalin ki ai ko baki fad'a ba na fahimci hakan a tattare dake, Amma me ya Faru?"
"Uhmn Daddy ne Wallahi"
"Me ya sami Daddyn?" Cike da kulawa Meerah ke mata tambayar.
Isha Tace "Daddy wai aure zai min Nan da 2 weeks"
Murmushi tayi had'e da fad'in "Alhamdulillah Kai Amma naji dad'i Wallahi"
Wani irin Kallo ta mata Meera cikin rashin fahimta Tace "ikon Allah Wannan mugun kallon fa, nifa ina Taya ki murna ne"
"Zaki taya ni murna ne only if am happy with it"
"what do you mean if you're happy wi.....? Hold on kina so kice min bakya son auren ne, nasan Babu Wanda daddy zai aura miki a yanzu da ya wuce Ma'aruf"
"Bana farin ciki gaskiya Kuma eh Ma'aruf d'in ne"
" Meyasa bakya farin ciki?"
"Sabida bana son auren nan ke Kanki kin San Wanda nake so ba Ma'aruf ba, and yanzu fa Dole zasu min" ta karasa maganar tana matsar kwalla.
"Isha Kenan ke ma kin Samu zakiyi auren Amma Ni Kuma fa tunda na rabu da wannan d'an iskan shiru babu Wanda naga ya kwanta min"
"Uhmnn kefa issue d'inki daban nawa daban, yauwa that reminds me, ya maganar Farukh ne Kam?"
"Wai kina nufin Abokin Ya Haisam"
"Eh Mana Akwai wani Bayan shine"
"Yana nan kin San ya dage sai dai ya turo gidan mu"
"Then what are you waiting for? Then ki turashi Mana"
"Banfa Gama sanin wane ne shi ba tukunna so Ina bukatar lokaci gaskiya"
Zaro Ido Ma'isha tayi Tace "Wani irin sani kike bukata yau kusan 3 years Kennan fa da kwanciyar ya Haisam Kuma tun lokacin kuka fara Soyayya, ke dai kice bai miki bane kalas"
"Ba haka bane kin San ai gayen ya had'u ban San meyasa na kasa bashi dama ba"
"a gaskiya ki cire Duk wani kokonto Wallahi Yana da kirkii Sosai"
"To Shikenan inshallah zan duba na gani, Amma seriously Isha Kar ki tashi hankalin ki Akan maganar auren Ma'aruf Wallahi yana sonki"
"nifa bana son shi kin fi kowa sanin hakan, Haisam nake so kuma sho zan cigaba da so"
"Haka zaki zauna kina jiran ranar da Haisam zai farka? Kin San ranar da zai farka ne? Kibe abinda su mummy sukace shine kad'ai kwanciyar hankalin ki"
Ajiyar zuciya tayi Tace "Hakane I always have faith in Haisam will wake up sooner or later but it seems like...... " Kuka ne ya ci karfinta ta kasa karasa maganar dake bakin ta, Nan Meerah tayi ta rarrashin ta, sai da tayi ta bata baki har hankalin ta ya kwanta suka rabu.
"Mamy Dan Allah horon yayi yawa Dan ki yi hakuri ki yafe min"
Kallon ta tayi kana Tace "Ayrah na fad'a miki ba sau d'aya ba sau biyu ba, baza ki tab'a samun sakin fuska daga gareni ba har sai Haisam ya farka sannan ya yafewa miki, nifa baki min laifi ba"
"Toh Mamy tunda ban miki laifi ba Dan Allah ki daina maltreating d'ina nifa 'yar kice"
Mikewa tayi Rai a mugun 'bace Tace "Ni ce ma nake Maltreating d'inki? Oooookaaay wata kin samu dama ina kula ki shiyasa kike fad'a min magana son ranki ko? Tashi ki fice min daga d'aki, Kuma ko da wasa na sake ganin kafar ki a d'aki na sai na karya miki su."
Ganin yanda mamy take mata fad'a ta tsorata matuka,Bata tab'a ganin ta a Haka na, hakan ne yasa ta fice da gudu tana kuka, Kanwar Tace ta bi Bayan ta tana tambayar ta "Aunty Ayrah Dan Allah ki fad'a min me ya Faru kullum cikin kuka kike"
'daga kai tayi ta kalle ta kana Tace " Babu komai" tasa hannu tana shara hawayen ta cike da kulawa Tace "Haba Aunty sai dai in baza ki fad'a min ba, na rasa dalili Duk sanda kuke tare da mamy sai kinyi kuka ko wani laifi Kika Mata ne?"
Kai a kasa Tace "Eh Nabila, nayi mata laifi kuma ta gindaya min wasu sharud'a Kan ta yafe min"
"To ai ni a gani na abu mai sauki ne tunda kin San abinda take so kiyi, sai ki aikata hakan"
"Uhmn lamarin Nan ya wuce tunanin ki, Amma ki tayani da addu'a insha Allah komai zai dai daita"
"Allahu yasa"
Ta amsa da "Amiin."
Ma'isha Bayan ta baro asibiti gidan Umma ta nufa, Bayan sun gama gaisawa Umma tace "Amma yau Kam zaki kwana mana ko? Kannen ki suna tambayar ki"
"Eh Umma kwana zanyi ina Twins d'in suke ne ma ban gan su ba?"
" Sun tafi islamiya"
"Haka Auta fa?" (Auta shine d'an da Umma ta Haifa Bayan kwanciyar Haisam zuwa yanzu yaron na da shekaru biyu a duniya da Yan watanni, sunan sa Aayan, amma suna kiransa da Auta).
Umma ta amsa da "Yana bacci kin San shi da son bacci"
"Wallahi yafi mishi ai, Ni da zan samu hakan ma ina so"
"Uhmn daughter Kenan, ki dai bi abin hankali ko da yake yanzu da sauki ma tunda kin kwana biyu ciwon ki bai tashi ba"
"Hakane Umma abin ne sai a hankali, gashi Daddy na son d'aura min wata damuwar Kuma"
Gyara Zama tayi tana kallon Isha tace "Me kuma ya Faru?"
"Umma Daddy wai aure zaimin Nan da sati biyu"
"To me abin tashin hankali anan ai dama tare da na Yayan ki za'a had'a rashin lafiyan naki ne yasa aka d'aga, ma'aruf sunan saurayin naki ko?"
'dan tab'e Baki tayi tace "Eh"
"Amma Isha me aibun sa naga yaron na da nitsuwa tunda yasha zuwa gidan na ganshi"
Cikin Muryar kuka Tace "To Ni Umma yaushe ni zan Sami abinda na ke so ni Wallahi bashi nake so ba, Ya Haisam nake so kuma shi nake so na Aura"
Umma Tunda Isha ke magana Baki a bud'e take kallom ta Muryar Mummy suka ji daga bakin kofa tace "Biri Yayi kama da mutum, Ashe dama Soyayya kuke da Yayan naki?"
Wuri ta samu ta zauna Umma tana mata Sannu da zuwa ta amsa a gaggauce kana ta maida hankalin ta ga Isha dake kuka tace "Isha dama kina son Yayan ki? Kika cuci Kanki Kar dai ma shine Wanda a dalilin sa Kika kamu da ciwon zuciya?"
Kai ta d'aga alamun eh, Umma Tace "Haba Isha Amma baki kyauta Mana ba, Kuma kin cuci Kanki"
Cikin kuka tace " Umma ya kuke so nayi ne? Baku ga yanda Yaya yake sonta bane? Idan ma ya sani babu abinda zai Canza tunda ba Sona yake ba"
Umma Tace "Ai mune gaba daku Isha da kin sanar damu da Duk Wannan bai faru ba, Kuma da Yayan naki Bai Shiga comma ba"
"uhmn Umma Kenan, zafa ku raba su ne kuma yana sonta yanzun ma ai rashin natan ne yasa ya Shiga comma, Kinga da ko an gudu ba lallai bane a tsira."
Mummy Kam shiru tayi tana Jin tausayin Yar tatan chan sai ta ce "Idan bakya son Ma'aruf d'in zan fad'a wa mahaifin ki a kyale ki kawai"
Umma tace "A kyale ta Kamar yaya? Kina nufin ta cigaba da zama haka tana jiran babu?"
Cikin rashin fahimta mummy Tace "Ban gane babu ba?"
"Babu man Haisam da shi da Babu ai duk d'ayane, gaskiya to me a bar yarinyar nan tayi auren ta, wa yasan ranar da zai farka?"
Mummy Tace "Haba Dan Allah meyasa kike fad'in hakan, Haisam fa d'anki ne"
"Isha ma 'yata ce" kallon Isha tayi Tace "Daughter kiyi auren ki kiyi fatan hakan shine alhairi a gare ki dake da Haisam d'in baki d'aya"
Kirkirerren Murmushi tayi Tace " Shikenan Umma nagode Sosai Kuma na amince da auren Ma'aruf d'in"
Umma Tace "Masha Allah, Allah ya miki Albarka"
Ta amsa da "Ameen."
Girgiza kai mummy tayi tace "To dama Nazo ne muyi list na abubuwan da ya kamata mu saya mata in yaso zuwa next week sai muje turkey, muyi sayayyan a Chan"
Umma Tace "Ai a gani na ba sai munyi list bako?"
" Gara dai ayi kin San Akwai mantuwa"
"Eh hakane Kam" Nan suka shiga listing kayan d'aki da kayan kitchen d'in Isha mikewa tayi Tace "Nikam zan Shiga bacci nake ji" ta shige ciki abinta ba tare da taji abinda zasu ce ba.
Kwanciyar ta ke da wuya Ma'aruf ya Kira wayar ta da Kamar ba zata d'aga ba har dai da ya kusa yankewa ta d'aga bayan sun gama gaisawa yace "Am sorry Isha na tura gidan ku ba tare da sanin ki, Isha na gaji da ganin ki a haka ina sonki kuma ina tausayin ki sabida halin da Kika tsinci kanki a ciki"
Tashi tayi ta zauna Tace "Bangane kana tausayin halin da na tsinci kaina a ciki ba?"
"Uhmn Isha Kenan na Riga na San komai, Meerah ta Sanar dani halin da kike ciki and please Karki yi fushi da ita ko ranki ya 'baci a Kan hakan nine na takura ta Akan ta fad'a min Nan ma da kyar ta Sanar dani irin Soyayyar da kikeyiwa Yayan ki since from day one na fahimci hakan daga gare ki na d'auka Soyayya ce ta jini, Amma Dan Allah ina so ki bani dama na Shiga rayuwar ki ko da kuwa bazan iya maye miki gurbin sa ba zan kwatanta baki kulawa iya bakin karfina"
"Lallai Meerah wato shine ta je ta gaya maka ko zamu gamu"
"Yi hakuri ban sanki da fad'a ba"
"a a yanzun ma ba fad'a zanyi ba"
"Yauwa nasan nayi dace ai"
Murmushi kawai tayi yace "Isha Aurena da ke is in two weeks da fatan kina farin ciki da hakan?"
"Hmm eh"
"Dan Allah dagaske kike?"
"Eh dagaske nake"
"Kai Alhamdulillah ya kamata mu Fara Shiri ko?"
Murmushi tayi kana tace "Eh"
"Masha Allah, yanzu kina ina?"
"Ina gidan Umma"
"Okay ina zuwa yanzu Amma da Kanwata zamu Zo"
"To Shikenan sai kunzo d'in"
Bayan sallar la'asar yayi horn a mamakeken gate d'in gidan Abba, mai gadi bai tsaya 'bata Lokaci ba ya wangel musu gate d'in sabida zuwa yanzu yasan Ma'aruf da Kuma gun Wanda yake zuwa, Kamar kulluma kud'i ya zaro a aljihun sa ya Mika Masa kud'i ne sun kai kimanin naira dubu biyar murna ya Shiga yi yana kwararo Masa addu'a.
Kiran ta yayi akan sun iso, Yar aikin gidan ta aika ta Shiga dasu parlor bakin, kana ta kai musu abin sha da snacks bayan yan Mintuna ta Shigo bakin ta d'auke yake da sallama, Ma'aruf da Kanwar sa a tare suka suka amsa sallamar.
'dago kanta tayi don ganin wacce take sallama, ai ko tana ganin fuskar Isha ta Mike zumbur, Isha ma tayi mamakin ganin ta, Ma'aruf mikewa yayi yace "Ya dai Kun san juna ne dama?"
Kirkirerren Murmushi Isha tayi Tace "Eh kamar nasan fuskar Nan a wani wuri" shiru tayi tana kallon ta don tuna inda tab'a ganin ta, Yayin da ita Kuma jikinta sai rawa yake duk ta rasa sukunin ta, gani take kamar Isha tasan Duk Shirin su.
Muryar Isha ta tsinkayo tana fad'in "Yauwa kawar Aysha ko? Ko ince Ayrah?"
Murmushi kawai tayi bata ce komai ba Isha Tace "Zauna Mana" zama tayi kanta a kasa Isha Tace "Rankashidad'e Kai ma ka zauna Mana" Zama yayi yana kallon yadda yanayin kanwar tasa ya canza, Isha tace "Ya kike ya kwana da yawa da fatan dai an sami abinda ake so" Jin hakan tayi saurin d'ago Kai tana kallonta Isha ta d'aura da fad'in "Ina nufin an fita da result Mai kyau?" Ta maida kallon ta ga Ma'aruf Tace "kasan lokacin su suke bin mu a school"
Ajiyar zuciya yayi yace "Ai ni Duk kun tsoratani ne"
" Me abun tsoro anan don kawai Mun San juna"
"To baki ga yadda Mardiya bta sauya ba?"
"Oh dama sunan ta Kennan ai ban sani ba, ikon Allah Kenan back then ina ga sau d'aya ko biyune muka had'u dake ashe zaki Zama sister in-law na"
Mardiya da tun d'azu ta kasa cewa komai kirkirerren Murmushi tayi kana ta amsa da "Allah Kenan"
Wayar Isha ce ta fara ruri picking tayi Tace "Haba Dan Allah, to ki Shigo parlorn baki man muna ciki" ta ajiye wayan Ma'aruf yace "Wane ne?"
Ta amsa da "Meerah ce"
Ya amsa da "Oh okay"
Bata d'au lokaci Mai tsawo ba ta Shigo bakin ta d'auke yake da sallama, Zama zatayi ta kalli fuskar Mardiya Tace "What me ya kawo Wannan munafukar gidan Nan?"
Duk su ukun suka Mike suna kallon juna Meerah Tace "Isha me ya kawo Yar iskan yarinyar Nan gidan Nan?"
Murya na rawa Tace "Dama kin santa ne?"
Wani irin mugun kallo ta mata sama da kasa Tace "Nasan ta mardiya Kenan, itace wacce nake baki labari Wanda suka Shiga tsakani na da Bashir da kawarta Ayrah"
Kallonta mardiya Isha tayi Tace "Tirkashi to ai nima itace kawar Ayrah da sanadiyar ta Yaya na ya Shiga comma"
Ma'aruf Duk ya rikece ya kasa fahimtar inda maganar su ta dosa cikin rashin fahimta yace "Wai me ke faruwane Kun sani a duhu?"
Meerah Tace "Ni zan fitar da Kai daga cikin duhu ko Kuma ince zan kunna maka haske,in dai Wannan yarinyar kanwar kace Wallahi Sam bakayi dacen kawa ba sabida wannan da kake gani tafi bakar macijiya mai mugun dafi"
Isha Tace "Please Meerah maganar nan ta wuce, please kiyi hakuri ki manta komaai dan Allah"
"Isha ke Shaida Ce kin San halin da suka sa na shiga, Duk duniya zan iya yafe komai Amma banda abinda Sukayi min"
Ma'aruf yace "Isha please Kar ki hanata Dan Allah, Meerah Sanar dani me Kanwata ta Miki?"
Mardiya kuwa duk da AC da ke d'akin bai hana jikinta jikewa da zuwa fa, sai rarraba idanu take, juyawa tayi da niyar fita daka Mata tsawa ma'aruf yayi yace "Dawo Nan"
Jiki Sim sim ta dawo ya nuna mata kujerar dake gaban sa yace "Zauna anan" sai da ta zauna ya maida kallon su ga Meerah da Isha yace "Please ku zauna, Meerah ki Sanar dani abinda ya kamata na sani"
Kallon Kallo Meerah da Mardiya suka shigayi wa juna.
Ana wata sai ga wata shine mene ne wannan abun da Mardiya tayiwa Meerah?
Ku cigaba da bibiyata, don Jin yanda labarin zata kasance.
_____________________________
Ina Jin dad'in comments d'inku Group d'in Dangin Uban dama sauraun groups d'in, bana samun damar yi muku reply Amma ina gani sannan hakan na faranta min Rai nagode Sosai Allah ya bar Kauna.
Please kuyi min sharing sannan ku cigaba da Sharhi ni Kuma na Rika yi muku typing
Milhaat Ce
Yar Terawa
[7/6, 1:26 PM] Miilhaat: 🍃 *DANGIN UBANA*🍃
Story & Written
By
Milhart
Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne.
*🌍MANAZARTA*
*WRITERS ASSOCIATION📚🖊*
*M. W. A*
*Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.*
Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️
*BISMILLAHIR RAHAMANIN RAHIM*
Page
47&48
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._
_Continuation......._ Ma'aruf ganin sunyi shiru ya Kuma cewa "Meerah kinyi Shiru, Ina sauraron ki, Dan Allah ki Sanar dani Kar ki boye min komai"
Ajiyar zuciya Meerah tayi kana Tace "Na San ka San kawancen dake tsakani na da Mardiya Bayan Isha bani da wata kawa da ta wuce
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 13 Chapter of 24