Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Abba Gana Nihla" Sai a lokacin Abba yayi magana, "ya Usman biki kuma?" Usman yace "emana, to tsayawa zamuyi muyita kallan ku" Murmushi kawai yayi, baisan dalili ba haka nan yakejin dadin zamansu a kujera daya, jiyake Kamar suci gaba da kasancewa ahaka Ruwan dake ajiye a table din gabansu yadauka ya tsiyaya a glass cup yanasha, hakanne yabawa Nihla damar matsawa gefe can qarshan kujerar, domin kuwa ba qaramin takura ta yayi ba Wayartace tayi qara, Kamar hadin baki dagashi har ita suka kai dubansu kan wayar, yau ma cin karo yayi da irin sunan da yagani kwanaki Wato ❤my Yusif ❤ Wani irin haushi ne ya kamashi, Wanda shi kansa yarasa dalilin jin hakan,daga farouq har Usman da Aliyu Abba suka zubawa ido suna kallan yanayin sa Nihla kuwa hamdala tayi cikin ranta, ta miqe zata shige daki domin amsa wayar, saida taje tsakiyar falon ta tsinci maganarsa Kamar almara "please kid'an kawomin lemo a kitchen" Cak taja ta tsaya, ita batayi gaba ba, ita batayi baya ba, wallahi ranta yabaci, Dan me dukda datake zaune baice taje tadauko masa ba, saida yaga zata shiga daki ta amsa waya, tayi tunanin su ya Usman zasuce tarabu dashi taje tayi wayarta, amma saitaji shiru, tome suke nufi? Ita zasu hadewa kai subi bayan dan'uwansu? 🤔 Cikin taqaici tayi hanyar kitchen din,takawo masa lemon ta ajiye, Usman sai kallan fuskarta yake ko zaiga yanayin ta amma sai yaga fuskarta Babu yabo Babu fallasa, shi kokadan baiji haushin abinda Abban yayi ba, domin kuwa yagama gane dan'uwan nasa kishi yafara batare daya saniba, shikuma gaskiya bazaiso ace mace Kamar Nihla tasake kubce musu ba, musanman ma yanzu dakomai yaji 🤣 Bayan ta ajiye lemon ko kallansu batayi ba, tashige cikin dakinta, wayar ta wullar akan gadon tareda dafe kanta 🤦🏻‍♀️, me wannan mutumin yake nufi da ita ne? ❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️ Zaune suke suke afalon Diyana gaba dayansu, dukansu Kallanta suke tana basu labari, cikin damuwa taci gaba da cewa "idan na zauna afalo koda yaushe bashida wajan zama sai qarqashina, ga aiki, kullum saiya sakani aiki Dan masifa, narasa yaya zanyi, har gara wani lokacin Momy tana masa magana, amma wallahi rannan dasu ya Usman sukazo dukansu qyaleshi sukayi, kuma suna gani fa ankirani ne awaya " Dida tace" to Nihla me kikeso suce miki?, lemo yanema ki kawo masa, kinga ai bazai iyu suce karkije ba, babu girmama wa aciki, Inda wani abu yace daban, dole zasubi bayanki " Tace" to zaman dayake a wajena fa? Shikuma me zakice? " Diyana tayi Murmushi tace" ai zama wannan kawai ni abinda na fahimta yana gyara kansa ne kawai, ada ma kowa yana cewa Nihla Nihla bare kuma yanzu daya ga abubuwa sun qara baiyana ai dole Yazauna a qarqashinki "🤣 Nihla tace" to aikuwa zandena zaman falon, bare yazo yananiqe min " Ilham tayi Murmushi tace" keda abokinki " Harararta Nihla tayi tace" kimin shiru kiji da abinda yake jikinki, wai Dan Allah idan kin haihu ma sunan wazaki sane? Dafatan nizaki saka " Ilham tace" hum wallahi ingaya miki yace Ya Abba zaisa, in mace ne kuma Anty aysha " Yatsina fuska tayi tace" Abba de Abba de, narasa meya musu duk suka daukakeshi haka" Ilham tace "aikinfi kowa daukakarsa, keda kikace yana nan daram acikin ranki kina sonsa" Wata irin dariya tayi tace "um da kenan, da kika sani yarinya, wallahi yanzu nafi qarfin sa" Diyana tace"gaskiya kam, wallahi kija ajinki dakyau, yagane da da yanzu ba daya bane" Dida tace "Allah sarki ya Abba, nikam wallahi tausayi yake bani, ko'ina yarinyar dayace yanaso din Dafarko?" Ilham tace "nikam dukda abinda yamiki abaya, wallahi zanso ace kin aure shi, kin auri abokin mijina, muci gaba da zumuncinmu, Nihla ki auri ya Abba Dan Allah, shi ubangiji yanason bayinsa masu hakuri, duk danasan cewa abune Mai mutuqar wahala hakan" Diyana tace "waiku cewa yayi yana sonta?, Nikaina nasan ya Abba yahadu babu qarya, yakai na mijin dakowacce mace zatayi Burin ace ta samu, to amma kutuna abinda yamata mana" ta kalli Nihla tace "wallahi koya dawo kinuna masa mata sunada daraja" Nihla tace "yawwa Diyana, fada musu de" Haka sukai ta firarsu cikin jin dadi, kasancewar haduwa tana musu wahala ❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️ Ahankali kwanaki sukaci gaba da shudewa, Abangaren Dida, tunda tasamu ya Fawaz ciwon cikin sa yalafa tadena damuwa, sabgarta kawai takeyi, domin kuwa itade tana kunya bazata iya masa komai akan haka ba, cikin Ilham kuwa yaqara girma tana nan haihuwa yau ko gobe, babu wanda yakai Aslam murna saboda yasan cewa kwana kusa zai zama uba Yau bataje makaranta ba Inda take service, ta dade tana bacci dasafe sai wajan goma da rabi tatashi, doguwar riga ce a jikinta ta bacci amma me kauri, rigar batada hannu, sai hula datasa akanta, tana hamma tafuto falon anan taga Momy itada wani da alama likitane sun futo daga dakin ya Abba, yanayin Momy ta kalla kawai tasan Babu lafiya saboda yanda jikinta yayi sanyi,kuma hakan baya rasa nasaba da abinda likitan yafada mata, sallama sukai da Doc din sannan tajuya zata koma dakin nasa, Nihla tace "Momy lafiya?" "wallahi Abba ne baida lafiya Nihla" Tace "subhanallah, Allah yabashi lafiya Momy" tafadi haka tana kokarin juyawa dakinta Momy ta kalleta da mamaki tace "yayanki baida lafiya, amma kina kokarin juyawa daki? Ba zakizo ki ganshi ba?" Turo baki tayi gaba alamar shagwaba, Sannan tabiyo bayan Momy suka shiga dakin nasa, yau ne karo na farko data shigo dakin Tun bayan barin ta gidan, gaba daya dakin saiya koma mata sabo saboda ansauya komai nasa Yana kwance yana bacci, dagashi sai wando three quater, da vest fara qal ajikinsa, kallonsa Nihla tayi, faffadan qirjinsa gashine kwance, sai Dan qaramin bakinsa daya fara bushewa, ko menene yake damunsa oho? Kallan Momy tayi tace "Momy ai bacci ma yake, bari naje nayi wanka kafin yatashi" tafadi hakanne kawai danta gudu, saboda bata fatan ace yafarka yaganta a dakinsa Abinda bata saniba kuwa shine idonsa biyu, kawai yana kunyar hada ido da Momy ne, tayaya zai iya Kallanta bayan fama dayayi da ciwon ciki Tun cikin dare kuma yau doc yazo yace yakamata ayi masa aure saboda sha'awa datake damunsa, tayaya zai iya hada ido da Momy? Momy tace "a a, ai hakuri zakiyi da wannan wankan, nasa Adala tahada masa Tea, zanje na karbo, ki zauna karya farka shi kadai kozai nemi wani abu" 🤣 Wannan karan kam, ran Nihla baci yayi, harta kasa boye hakan akan fuskarta, Momy ma taga yanda yanayin ta ya sauya amma haka tayi shiru tafice daga dakin, taga alama Nihla har yanzu yarinya ce, yanda takejin ta aranta Kamar su Usman Babu yanda za'ai tadinga Hadata Da Abba Dan wata manufa, itace ta haifi Abba amma dole zata nuna masa kuskurensa akan abinda yayiwa Nihla abaya, amma hakan ba zaisa tazuba musu ido tana kallansu suna zaman doya da manja ba, koba komai dukansu yaranta ne, babu wanda zata nunawa banbanci acikinsu, tana wannan tunanin ta qarasa cikin kitchen din Shiru Nihla tayi tana tana zaune akan bedside drower, ko Inda yakema bata kallo, shima yana jinta a gefensa amma bai bude idoba, asali ma jiyayi bugun zuciyarsa yana qara sauya wa, kuma yarasa dalilin hakan, yasan cewa a dole take zaune dashi, saboda yanda yake ganin tsanarsa qarara acikin idonta, yasan kozai mutu bazata kulashi ba Ahankali wata dabara tafado masa, bari ya gwada, yasan idan yayi hakan dole zata ambaci sunansa, sannan tabashi kulawa Ahankali yafara motsi tareda yatsina fuskarsa, cikin alamun ciwo yace "wayyo Allah nah.... Momy... Momy Zan mutu..." Cikin sauri Nihla ta kalleshi, amma abin mamaki ko sunansa bata kamaba tace "subhanallahi, sannu" 🤣 Haushi yakama Abba, waime yarinyar nan take nufi ne? Murqususu yaci gaba dayi Kamar gaske, duk ya rikice Kamar bashi ba, handle din dakin da aka kama za'a bude yasa Nihla tayi tunanin Momy ce zata shigo, kuma tasan fada zata mata tace tana ganinsa ta qyaleshi, hakan yasa cikin sauri tatashi tadawo gefensa tazauna tana cewa "Sannu, sannu" Jinta akusa dashi yasa yatashi Ahankali Yazauna, sannan yazuro qafafunsa qasan tiles din dakin yamiqe tsaye zai shige toilet, yana Miqewa kuwa mararsa ta murda agaske, cikin azaba yadawo Yazauna, baisan lokacin da yadora kansa akan kafadarta ba, hannunsa kuwa yana kan cinyarta, gaban Nihla yahau luguden faduwa, itafa tarasa gane Inda ya Abba yadosa, meyake nufi hakane? Ahankali yaji maransa tadena ciwo yabude idonsa, amma me? Saiya kasa dauke kansa daga kan kafadarta, yanda ya kwantar da kan nasa hakan yabawa idonsa damar hango cikakkun nashanunta farare tas, cikin ransa yace wallahi natane Babu qari, but ya'akayi yarinyar nan takoma hakane cikin shekara hudu? Turo dakin Momy tayi tashigo hannunta dauke da cup din Tea, ganinsu ahaka yasa ita kanta gabanta yafadi, anya Abba kuwa bason yarinyar nan yakeba? Me Abba yake shirin janyo musu? 🙆🏻‍♀️ Haka de takawar da tunanin aranta, takawo masa Tea din tace "gashi Abba, tashi kasha Tea" Ahankali yadago kansa daga kafadarta, cikin dabara ta matsa can gefe dashi tana hamdala aranta, Tea din ya karba yafara shan ahankali, cikeda shawaga yace"Momy zafi " Tace" nifa Abba dama ba rashin lafiyarka ba kadinga langabewa mutum kenan, kaiba qaramin yaro ba amma kadinga shagwaba, kuma wannan gashin na qirjinka ka zauna ka askeshi Dan Allah"🤣 Dukda yana jin jiki, saida ya danyi murmushi kadan, yasaci kallan Nihla, sai yaga kanta a sunkunye batama kallansu Saida Momy tabashi magani yasha sai runtse ido yake alamun bayaso, sannan suka futo daga dakin itada Nihla ❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️ Yau Tun safe tatashi da matsananciyar naquda, daqyar ta'iya kiran Aslam dayake wajan aiki, yana jin yanayin muryarta yasan ba kalau ba, haka yadawo gida suka tafi asbiti Tayi doguwar naquda sai cikin dare ta haihu lafiya, tahaifi danta namiji Mai kamada ita sak Tun asuba labari ya'isa family house cewa Ilham ta haihu, dasassafe kuwa asbitin yacika sosai da yan'uwa, Nihla kam tafi kowa murna, gata da ihlam haka suke zaune a dakin, sai wajan la'asar sannan suka dawo gida, amma Nihla sai dare tadawo agajiye, hajiya Na'ila bataga ta zamaba, tunda akai haihuwar tayi kane-kane akan komai, ko kara bata yiwa hajiya Abida ba, Wato Maman Ilham 😃 Ita kuwa hajiya Abida abin ma bai wani dameta ba tunda ana kula da yarinyar ai shikkenan, ita dadi ma taji, tasan cewa hakan alama ce ta Ilham din tana zaune da sirikarta lafiya Bayan kwana bakwai aka radawa yaro suna Abubakar Wato Abba, suna kiransa da lil Abba Da yamma ta shirya tsaf cikin riga da siket na leshi, Mai launin dark blue da sirkin fari, qananun kalba ne akanta, da kanta ta tsara kwalliya taci daurin dankwali Mai kyau, ta tattare kalbar tata tadaureta abaya, wayarta ce take qara taqi dauka, su Dida ne suke kiranta Tun dazu, tasan kuma bazai wuce suce basu ganta ba Saida ta shirya tsaf sannan tayafa mayafin ta Dan ma dedeci tafuto falo, hayaniyar su ya Usman take juyowa a dakin ya Abba, tace to wannan yaushe sukazo, gefenta ta kalla taga wata waya qirar iphone tayi Murmushi tadauka tace may be ta ya farouq ce, tana daukar wayar kai tsaye tatafi camera tadinga yin Selfie masu shegen kyau, sai Style take qarawa tana yin pictures din, saida tagama sannan ta ajiye wayar ta qwalawa Momy kira Sai gata tafuto daga dakin ya Abba ita dasu ya Usman ashe ma tare suke, suna futowa farouq yace "kai kai kai, ina zakije haka Kamar Wanda zakije wajan gasar sarauniyar kyau?" Murmushi tayi, tace "ya farouq gidan suna Zan tafi" Ya Usman yace "gaskiya wannan wankan nawa ne" Murmushi tayi batace komai ba, Aliyu kuwa baiyi mata magana ce kawai de yana murmushi cikin ransa yana yaba kyawun surar yarinyar Shikuwa Gogan abakin kofar dakin nasa ya tsaya hannunsa zube cikin aljihun wandonsa, yana qare mata kallo Bece dasu komaiba, yatsani yaga tanayiwa mutane murmushi saboda yanda take yin mugun kyau, musanman ma yanda dimple dinta suke futowa Fuskarsa adaure Babu alamun wasa yake kallanta, amma yakasa cewa uffan Momy ta kalleta tace "masha Allah, yanmatan Momy kinyi kyau sosai, bari na gyara miki daurin dankwalin naki" Nihla ta tsaya Momy kuwa ta qara gyara mata daurin, sannan tayi mata sallama tatafi ❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️ Gidan suna yayi albarka sosai, Mazawaje family duk sunje, iyayenne mata kawai basujeba, saikuma 'yan'uwan mahaifiyar ta suma duk sunje sosai, maijego tana shiga cikin kayaiyaki na alfarma itada Baby Har dare yayi anata hidima sannan mutane suka Dan rarragu, duk wannan abun da ake jikin Dida asanyaye yake, sai bayan mutane sun watse ne da daddare Nihla take cewa "Dida meyake damunki ne Tun yamma kinyi shiru" Tace "tunanin ya Fawaz nake, ina tsoron karyaqi shan ma ganinsa" Diyana tace "Dida kina shagwaba ya Fawaz wallahi, koda yake soyaiya ce, rannan ma munyi waya da mum take cemin tabawa driver yakawo miki jakar ki tunda kintafi Babu sallama" 🤣 Murmushi tayi kawai Ilham tace "kice anaji da yayan nawa, toki sakarwa dan'uwana jiki de yamore ehe" Diyana tace "um, nikam danba qara, Tunna farko bansake yarda ba" Nihla tace "waiku Dan Allah miye hakan, kawai saiku dinga yin wannan firar agabana, salon ku lalatani" Dida tace "kwana nawane kema Nihla, ai Kamar yaune" Diyana tace "ke gwauruwa waye zaizo yadauke ki ne? Kingani ya Adam zaizo, kuma Dida ma nasan ya Fawaz zaizo" Tace "nikam driver, dama shiya kawoni" Itama Diyanan tace "wai kina nufin ya Abba ba zaizo yadauke ki ba?" "ya Abba fa kikace, ashe kuwa saide na kwana anan, keni fa ko magana bamayi, kowa harkarsa yake agidan nan infada miki" Ilham tace "haba Nihla, ya Abban kine fa, kudena Dan Allah" Itade Nihla shiru tayi tanajin su suna zancen su ta qyalesu, taga alama Ilham ta Manta cin mutuncin dayayi mata ❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️ Fira suke sunata kwasar daria amma shi yana zaune akujera shi kadai ya zubawa wayarsa ido, farouq Tun dazu ya lura kwata-kwata hankalin Abba yanakan wayarsa, ko kallansu Babu kawai ya qurawa waya ido Ahankali yatashi yayi kitchen Kamar gaske 🤣 Soyake yaga menene yadauke hankalinsa haka, daya dauko Ruwan da niyya yazo wucewa ta bayan Abba,karaf idonsa yasauka akan screen din wayar Abba, pictures din Nihla ne, kuma da kayan data fita dashi dazu da yamma ne, toya akai Abba yasamu pictures din? Yaushe yayi mata? Dama sun fara shiri shida itane harya fara yimata photo awaya? Ganin Babu me bashi amsa yasa ya tsaya yana kallan Abba dayake kallan pictures din daya baya daya, idan yashiga cikin guda daya saiya dade yana kalla sannan zai sake zubawa nagaba ido Momy data lura shurun nasa yayi yawa tace "Abba na lafiya de ko?" Kafin Abba yayi magana farouq dayake bayansa a tsaye yace "lafiya Momy, yana ganin abinda yake rayuwa tare dashi ne acikin gidan" Cikin sauri ya juya ya kalli farouq, Dasauri yasaka wayar aduhu, sannan yasakata cikin aljihun wandon jeans dinsa, Innalillah... Baiso farouq ya kamashi yana kallan pictures din yarinyar nanba, kada yayi tunanin wani abu, ahankali yamiqe tsaye yace "Babu komai Momy" Farouq ya kwashe da daria ganin yanda qanin nasa yayi fuska Kamar bashi ba, yace "idan tayi tsami maji" Momy kam bata gane komai ba, danhaka tashare su, haka sukaci gaba da firarsu sannan sukai mata sallama kowa yatafi gidansa Shima Abba compound din gidan yafuto, Momy kuwa daki tashige tana waya da Daddy akan matsalar Abba da likita yafada mata, yace ta bari idan yadawo gida saisu yi masa magana Yadade a compound din yana kallan get din gidan, Agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa ya kalla kasancewar akwai yalwar hasken fitilu agidan yaga goma saura, zagaye yafarayi awajan hannunsa daya yana cikin aljihunsa, har zuwa wani lokaci kuma Yaqi komawa cikin part din nasu, Agogon yasake kalla afili yace "why bata dawoba har yanzu?" Gashinan anyi dayawa, dafatan zanga Comments, facebook readers ina godia sosai da sosai 🙏 Amnah El Yaqoub ✍️ [7/5, 12:37 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️ {Romance&Friendship luv} Writing by Amnah El Yaqoub Like my page On facebook 👇 https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493 37&38 Babu me bashi amsa, haka yadinga zagaye wajan har saida ya hango maigadi yana bude get alamun itace suka dawo, sannan ya juya cikin sauri ya koma ciki Ita kuwa Nihla bata lura dashi bama, ana sauke ta tashigo part din nasu, kai tsaye dakin Momy taje ta sanar da'ita dawowar ta sannan tatafi dakinta tayi wanka, tafara shirin bacci Har shigowar ta falon yanajinta, sai a lokacin ya kashe wutar dakinsa shima ya kwanta ❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️ "Doctor magunguna na sun qare inaso kahada min wasu" cewar Fawaz Doc yadubeshi yace "to Alhamdulillah gaskiya naga ana samun cigaba" "hakane kam, but wani lokacin inajin raina yana baci haka kawai, kuma cikin raina inajin inason nasha qwayar ko kadanne" Murmushi Doc yayi "hakane, dama dole zakaji haka, amma kaci gaba da hakuri, kana kai zuciyarka insha Allah zuwa nan gaba kadan zakaji tafita daga ranka ma gaba daya" "ina fatan haka Doc, domin duk abinda mata ta bataso nima banaso, banason bacin ranta ko yayake" "masha Allah, kanason matar nan taka Fawaz, dukanku kunason junanku,amma bansan wacce irin soyaiya ceba wannan, duk yanda kake sonta bazata iyama abinda kakeso ba, domin ta cetoka daga halaka" "mekake nufi Doc?" "matarka takirani rannan da alamun ma Kamar tana kuka, tace bakada lafiya inzo, nafada mata cewa maganin ai yana wajan ta, tabaka haqqin ka kawai, kai tsaye tacemin bazata iyaba" Murmushi Fawaz yayi "ai tanada kunya Doc nima nasan bazata iyaba, kuma ni hakan datayi ya birgeni, inason mace Mai kunya, nikuma gaskiya kunyar tunkaranta nake da wannan abun, bansan ta Inda zan fara ba, please ko zaka bani wasu magungunan Wanda Zan dinga sha duk lokacin dana jini cikin wannan yanayin " Dariya likitan yayi" lalle, ina Ruwan laila majnun, Wato ahakan batayi laifi awajan ka ba, kuma kai bazaka iya kai kanka wajantaba, lalle Fawaz irinku kadanne Awannan zamanin, to maganar gaskiya bazan baka kowanne irin magani ba, inzaku nemi haqqin junanku ku nema, idan bazaku nemaba shikkenan, amma kanada aure kanada mata bazan baka wani magani ba, wannan ai sai yarinyar ta rainaka ma tace baka iya mata komai " Murmushi Fawaz yayi " tace komai ma Doc, amma ni bazan iyaba " Likitan yayi shiru yana kallan Fawaz, ikon Allah kenan, Awannan zamanin? 🤔 ❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️ Tun bayan dasukai magana da Doc. Ya tattara maganarsa ya watsar yaci gaba da sabgarsa, har Tsawon sati daya, zaman su da Dida kuwa komai lafiya, yau Tun safe yakejin cikin sa yana murdawa, haka yatashi yafita, Dida na daki sai dirin motarsa taji, wajan wani abokinsa yaje, abokin na ganin Fawaz cikin damuwa ya tambayeshi meyake damunsa, nan take yafadawa abokin nasa, murmushi abokin yayi yace "dadina da gobe saurin zuwa" Yatashi yaje daki yadauko masa wata kwalbar wine yace "abokina baka taba shan wannan ba, kasha ta, zakaji dadi, damuwar ka zata kau nan take" Fawaz ya karbi kwalbar giyar nan yariqe, idan ya tuna cewa Dida bataso sai yaji jikinsa yayi sanyi, uwa uba shi duk shaye shayensa baitaba shan giya ba, to amma kuma idan ya tuna cewa damuwar sa zata kau saiyaji gara hakan " Memakon yasha anan sai yatafi da ita gida, yana zuwa falo kuwa Dida tafuto daga daki zataje kitchen, kallan farko tayi masa ta hango rashin gaskiya awajan sa, taga sai boye hannu yake, bata zurfafa bincike ba tayi masa sannu da zuwa tawuce kitchen, shima cikin sauri yashige dakinsa, yadauko cup ya tsiyaya giyar aciki, Yazauna zai fara sha kenan taturo kofar dakin tashigo, abinda tagani agabansa ne yasa gabanta yayi mugun faduwa, giya? Dasauri taje tadauke gaba daya, ita dama tunda taga shigowarsa tasan cewa akwai abinda yake boye mata, cikin bacin rai tace "ya Fawaz miye hakan? Menene wannan?" idanunta suka cika da qwallah Shiru yayi yakasa bata amsa, ita kuwa ta tsareshi da ido tana jiran amsa Kallanta yayi sannan Dasauri yayi kasa da idonsa, cikin rashin gaskiya yafara yimata magana " Dida... kiyi hakuri, wallahi ba laifi na bane, wani abokina ne..." Kafin ya qarasa ta tareshi tace "to laifin waye?ya Fawaz Dan Allah yaya kakeso nayi da raina ne eh? Kai yaro kullum zamu dinga magana akan abu daya shekara da shekaru?" Hawaye yazubo mata, tasa hannu ta goge, sannan tadauke kwalbar giyar da wadda yazuba akofin, ta miqe zata futo daga dakin cikin fishi Dasauri yatashi ya fusgota jikinsa, ya rungumeta tabaya, tsayawa tayi cak, hawaye yana zuba a'idonta, Tun tana na hawaye harta dawo yi abaiyane, shi kansa yasan cewa bai kyauta mataba, amma yaya zaiyi? Kansa yadora akan wuyanta yayi shiru kuma yariqe ta gam ajikinsa, Ruwan dataji yana Saukowa daga wuyanta yana shirin shiga cikin rigarta ne ya tabbatar mata da cewa kuka yake Saikuma jikinta yayi sanyi, tadena nata kukan tanajan zuciya, cikin hawaye yace "kiyi hakuri, bazan qaraba, Allah abokinane yabani, bansan yaya zanyi ba Dida, ina cikin damuwa, cikina kullum ciwo yake min" Nan take Dida tafara tunani, karfa garin kunya tasa mijinta ya koma ruwa, bayan tasamu daqyar yadena shan komai, yanzu inda yasha giyar nan tasan cewa alhaki yana kanta, kuma dalilin ta ne yasa mijinta bayan shan qwaya ya koma shan giya, dolen dole zatai kokarin raba ya Fawaz da wannan abokin nasa duk da batasan ko wayeba Cikin kunnanta yake mata magana Kamar rad'a yace "kiyi hakuri kinji, Dan Allah Karki sake tafiya kibarni" Ajiyar zuciya tayi tace "toka cikani natafi, abinci Zan dora mana" Cikin shagwaba yace "um um kibarshi, nasan sake guduwa zakiyi kibarni" Girgiza kanta tayi, taga alama Jan magana kawai yakeso, ita zataje tabarshi Awannan halin salon yasake fadawa cikin shaye shaye, kokarin janye jikinta tafara yi shikuma yariqe ta gam, hannunsa takama tadaga masa su sama zata fita daga dakin, shikuma yakai mata wani irin ruqo, sai jin hannunsa tayi akan kirjinta, zaro ido tayi tana ganin Inda hannunsa yake, shi kansa yayi mamaki, amma memakon ya janye hannun nasa saiyayi shiru, laushin dayaji ne yasa yakasa dauke hannunsa daga wajan, baisan lokacin daya fara shafawa ba, amma hannunsa gaba daya rawa yake 🤣 Wani irin yanayi ta tsinci kanta aciki Wanda bata taba tsintar kanta aciki ba, cikin sanyin murya tace "ya Fawaz kabari Dan Allah, ni wani iri nakeji" Yace "um um, nima haka nakeji" Jikinta tafara janyewa, cikin sauri yaqara riqota, yaci gaba da abinda yake, wannan karon kam shiru Dida tayi, harga Allah tanajin dadin abinda yake mata, Dan haka tayi shiru tabarshi, daqyar ya'iya dago kansa ya kalleta, abin mamaki sai yaga Dida ta lumshe idonta, murmushi yayi, gaskiya in hakane yadade yana cutarsu gaba dayansu, cikin rad'a yace "akwai dadi?" Ahankali ta daga masa kanta Yasake cewa "kinaso in cigaba?" Nanma Dida batayi magana ba kawai de tasake daga masa kanta, yana ji ta amince kuwa ya dauke ta cak, ya juya kan gadon sa da ita, kayan jikinta yafara cire mata, ahankali tabude idonta, mamaki ya kamata, tayi tunanin akan zaici gaba da kayan ta a jikinta, amma sai tayi shiru Tana ganinsa yana kokarin cire nasa kayan tayi sauri ta rufe idonta, batasan lokacin daya gamaba sai jinsa tayi a jikinta, yasaka hannu ya balle mata breziyar jikinta, saida yagama kallan qirjinta tsaf yana ganin ikon Allah, sannan yadora bakinsa akai yafara sha, salon yanda yake mata ne yasa tarasa nutsuwarta, batasan lokacin data kai hannunta kansa ba, ta riqoshi sosai Saida Fawaz yayiwa Dida charge sosai yanda bazata taba iya masa musu ba sannan yafara neman hanya, daga haka na futo nabar musu dakin ❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️ "maryam ga wannan kyautar danaso nabaki Tun ranar nan dakike min kuka, kuma Wanda nace yasiyo min bai kawomin da wuri ba" Kallan hannunsa Diyana tayi cikeda mamaki, wata yar qaramar akwati ce da awarwaro aciki manya guda uku na gold, cikin murna ta karba tace "ya Adam duk nawane wannan?" "yes naki ne, kawo hannunki nasaka miki" Babu musu tabashi hannun, yazura mata awarwaron, sunyi mata kyau sosai Tace "ya Adam nagode, nagode sosai" "nine yakamata nayi miki godia maryam, saboda kyautar dakikamin, maganar gaskiya banyi tunanin haka Zan sameki ba, amma ina Mai qara baki hakuri akan hakan, kiyafemin" Hararar wasa ta watsa masa tana shafa abin hannun nata Murmushi yayi yace "yanzu ya za'ayi? Nayi hakuri fa maryam" ya qarasa maganar yana kashe mata ido daya Cikin shagwaba tace "ya Adam Allah ni gaskiya bazan iyaba, duk wahalar daka bani haka bai isaba" Daria yayi yace "a a, nide bai isaba, please maryam" Shiru tayi masa, hakan yasa yafara aika mata da saqonni, amma yanda taji na farko wannan ma haka taji, banbancin kadanne, domin kuwa yauma taci wahala ❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️ Zaune suke afalo shida Aslam, takardu ne ahannun su suna cikewa, sun baje a kafet din falon, yayinda sautin tv din falon yake tashi Ahankali Cikin sauri

Chapter 14 of 24