da sarawa ta sa hannu ta share hawayen da ya zubo mata!
Juyowa tayi da niyyar d’auko kwano a kwando suka had’a ido da Huda wadda take kallon ta tana zubar da hawaye…
Wani tausayinta ne ya lullub’e Mama lokaci guda!
A b’angaren Hudan ma hakan take.
Da sauri Mama ta zo ta giftata ta wuce ta fice daga kitchen d’in
Dan kallon fuskar Yarinyar sake narkar mata da zuciya yake yi..
Tana fita itama Hudan ta juya ta bi bayanta.
Duhun! Da ta fara gani ne ya sanya ta d’an tsaya ta dafe kanta…
A hankali ta fara jin wani irin jiri yana kwasarta kafin daga haka taji jinta da ganinta da k’arfin jikinta sun d’auke lokaci guda ta tafi ta sulale a tsakar gidan ta fadi!! Kamar matacciya!.
Da k’arfi Huda tace “Maamaa!!!”
Sai kuma ta yi kanta da gudu tana kuka......
Kuka take yi tun k’arfinta tana kiran sunanta amman ko motsi bata yi ba.
Ganin hakan yasa ta sake gigicewa ta rikice ta rasa ma ta Ina zata fara!
Tana shirin mik’ewa sai ga Ya Ja’afar ya shigo…
Da gudu ta k’arasa inda yake tace “Ya Ja’afar napep dan Allah ka nemo napep mu d’auki Mama a kaita asibiti dan Allah Ya Ja’afar..”
ta hau rirrik’esa tana mishi magana duk ta gigice..
Kallonta yayi ya kalli inda Maman take.
Kamar wanda zai yi abun arzik’i haka ya k’arasa inda Maman take kwance…
Dai dai setin fuskarta ya d’an yayyarfa hannunshi (kamar wanda zai kore mata sauro)
A hankali ya d’ago ya kalli Huda wadda take kuka kamar ranta zai fita yace
“Wannan ai napep ba zata yi aikin komai ba!
Sai dai a d’auko makara!! ayi mak’abarta da ita.
Kallifa ko uffan bata ce mini ba!
Bafa ta motsi.”
Cikin kuka Hudan tace Ya Jaafar asibitin dai!
Ka nemo mai napep ka taya ni d’aukar ta
Zata farfad’o in shaa Allah suma tayi.”
Banza yayi da ita ya juya ya nufi kan baranda sannan yace “bara in d’an rintsa In farka sai munje in yi mata sallah a mik’ata!.”
Sai a lokacin Huda ta lura da yadda yake tafe yana tangad’i!!!
“Na shiga uku yau!”
Tace tana wani irin kuka…
Ko myafinta bata tsaya d’auka ba ta fita da gudu gidan da yake a jikin nasu dake suna da mota su wai ko zata samu a tayata a taimaka mata su mik’a Maman asibiti.
Sai dai kuma tun kafin ta k’arasa ta hango k’atoton padlock mak’ale a k’ofar gate d’in gidan wanda hakan
yake nuni da ba kowa ma a gidan kenan!.
A rikice ta juya ta koma cikin gidan tana shiga ta tarar Ya Ja’afar har yayi bacci..
K’arar wayarta ta jiyo a d’aki sai a lokacin tunaninta ya bata kawai ta kira Arshaad.
Tana shiga ko bi ta kan misscall d’in bata yi ba ta hau kiranshi babu k’akk’autawa…..
MT & co.
A lokacin
Aslam ya je office d’inshi kenan
Granpa kuma
ya saka shi wani aiki
na gaggawa….
Duk ya rikice hakan yasa ko wayarshi bai tsaya d’auta ba ya wuce wajen da ake sarrafa turarurrukan wanda yake nan a gefen building d’in da yake d’auke da offices bayan ya cewa Aslam d’in ya jira shi a office d’in nasa nan da kamar 20 minutes zai dawo…
Yana fita ko 1 minutes bai yi da fitar ba wayarshi ta fara k’ara!
Aslam, kamar zai bishi da wayar sai kuma yayi tunanin ‘bara kawai ya jira har ya dawo sai ya bi kiran kawai’
Ganin yadda aka jera mishi kusan 20 misscalls a jere ba hutu ne ya sanya ya yanke shawarar kai mishi wayar kawai, dan ya san dole its important!!
Yana d’aukar wayar wani kiran yana sake shigowa tare da wani message da alamun yanzu aka turo!
“Life support ❤️”
Haka yaga sunan b’aro b’ari ya fito a akan screen d’in.
Ko ba a gaya mishi ba
Ya san Huda ce!
A hankali ya lumshe kyawawan idanuwanshi ya bud’e su kafin ya maida wayar kawai ya ajjiye ya koma ya zauna yayi shiruuu….
Ganin tanata kira still babu k’akk’autawa ne ya sanya ya mik’a hannu ya d’auki wayar a karo na biyu
Yana d’auka kiran yana tsinkewa dan haka ya samu damar ganin sak’on data turo ta notification bar!
“Ya arshaad Mama ta suma ba kowa agidan sai mu biyu ka taimakamin Dan Allah kazo mu kaita asibiti!”
Da mugun k’arfi yaji k’irjin shi ya buga!
Tsintar kanshi kawai yayi da mik’ewa tsaya ya fice daga office d’in gaba d’aya bayan ya ajjiye wayar a kan tebur.
Ko takan wayar Arshaad d’in bai sake bi ba!
Ya isa inda motar shi take ya shiga ya bata wuta ya fice daga companyn da gudu…
Babu nisa tsakanin company d’in da gandun albasa hakan ya sanya ya samu damar k’arasawa acikin mintuna k’alilan!
Yanayin parking ya fito da d’an gudu ya shiga gidan kanshi tsaye…
A tsakar gidan ya hango su
Hudan tanata k’ok’arin d’aura Mama a bayanta tana kuka
amman ta gagara!
Tanajin shigowar mutum ta d’ago idanuwanta tana kallonshi…
Shima itan yake kallo!
Wani sabon kuka ne ta ji ya kufce mata mai k’arfi ba tare da ta shirya ba!
Da sauri ya k’arasa inda suke yana kallon ta yana jin yadda k’irjin shi yake bugawa…
Da kyar ya iya ce mata
“Muje”
Sannan ya durk’usa da niyyar d’aukar Mama.
Zabura!! Yayi bai san lokacin da yace
“Anty Maryam!!!”
da d’an k’arfi, ba…
Sai kuma ya sago yana kallon Huda wadda take yi mishi kallon mamaki..
Mayar da dubanshi yayi a fuskar Mama yana yi mata kallon kurilla
Kana ganinshi ka san a firgice yake!! Cike kuma da mamaki
sannan kanshi a d’aure yake.
D’agowa ya sake yi ya kalli Huda!
Sai
kuma ya sake maida idanunsa akan fuskar Mama…..
Cikin kuka Hudan tace
“Ya Aslam dan Allah mu je
kar wani abun ya sake samunta…
Wani yawu mai d’aci ya had’iye kafin a hankali still idanuwanshi suna a kan fuskar Maman ya sanya hannu ya d’auketa yayi waje da ita….
Ita ma Hudan kanta a d’an d’aure yake….sakamokon jin yadda ya kira sunan Mama lokaci d’aya kuma har da
‘anty’ wanda ko lokacin da su Jalila suna Yara ta san ba anty suke ce mata ba!
Sanann bata tunanin ko Ya Arshaad ta tab’a gayawa sunan Mama balle tayi tunanin ko shine ya fad’awa Aslam d’in!.
Bata wannan take ba yanzu ta
Lafiyar Mama take dan itace abun dubawa!
Dan haka ta kawar da tunanin gefe…
Tana ganin sun fita itama
da gudu ta koma ta d’au mayafinta ta d’auko y’an kud’ad’en da suke dashi ta zuba a jakar Maman ta d’auko mata purse d’inta data bari a kitchen tasa a cikin jakar ta fito daga gidan
Lokacin Aslam har ya saka Maaman a Bayan mota yana gyara mata ruffin mayafinta daya d’an zame kad’an.
Ganin ya juya ya shiga mazaunin driver ne ya sanya itama ta bud’e motar ta shiga baya ta zauna ta d’aura kan Mama akan laps d’inta tana shafawa tana kuka....
Basu kaiga k’arasawa asibitin ba taji yace
“Assalam alaikom,
Abba Ina wuni!
Dan Allah duk abunda kake yi ka bari kazo emergency yanzu akth…
Ba zan iya bayani a waya ba
Dan Allah Abba ka zo
Dan Allah.”
Shiru taji ya d’an yi kafin ya sake cewa
“Ok tam
Nagode.”
Ita dai Huda mamakin Aslam take yi yadda duk ya rikice
Da kuma yadda ya kira sunan Mama!
Sannan yanzu taji ya kira wani ‘ABBA’ yace ya samesu a akth!
A hankali a chan k’asan zuciyarta tace
“Waye ABBA???”.
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 32 Chapter of 32