raba gifts sai da ta karb’i hud’u!!Best in English
Physics
Most decent da
most beautiful.
Sakina kuma ta karb’i
Best in maths
Most popular da
Da gift d’inta na social prefect da aka had’a mata.
Mama dai sai share kwalla take yi sunata murna.
Bayan nan akayi pictures da ragowan abubuwa daga nan kowa ya watse.
A waje ma sai da Aaima ta sake yi musu kowa
da kowa
Sannan tace sai Huda ta tsaya anyi mata da Arshaad, da kyar
ta tsaya kuwa dan sai da ma ta fakaici idon su Mama taga sun d’an juyo sun basu baya.
Haka nan cikin farin ciki suka nufi gida.
A gidan su Sakina suka yada zango.
Arshaad a falon Baban su Sakina suka tsaya, a nan aka kai musu ruwa da abinci suka ci.
Su Hudan suna cikin cin abincin suma Baban Sakina ya shigo ya cewa Hudan “taje falonshi” sannan ya nufi hanyar d’akin shi. Sai da Ummu ta sake maimaita mata tukunna ta mik’e kamar munafuka tana jan Sakina tana kallon Mama wadda ta d’auke kai tayi kamar bata ji su ba.
Sai da suka je d’aki suka chanzo hijabai sannan suka nufi falon….
Babu yadda Sakina bata yi da ita akan ta fesa turare ta shafa powder ba amman fur tak’i! Haka suka fito Sakina tana ta faman b’alla mata harara ita kuwa Hudan sai dariya take yi. Suna zuwa dai dai k’ofar falon kuwa bayan sun bud’e Sakina
tasa duka k’arfinta ta turata ciki sannan ta juya da gudu tana yi mata dariya itama…
Cike da kunya ta d’an juyo tana kallon Arshaad wanda shima dariyar yake yi mata dan ya san wannan aikin Sakina ne.
Turo baki tayi kafin tace
“Ya arshaad kana gani ta turoni kuma baka ce min sannu ba kake min dariya?”
Murmushi yayi kafin yace
“Nasani ko tirjiya kika yi? Kika ce ba zaki zo wajena ba shiyasa ta turoki?”.
Sake turo bakin tayi.
Ganin haka yasa yayi saurin kama bakin nashi da y’an yatsun shi yana dariya k’asa k’asa, kafin yace “Afuwan wifey! Zo ki zauna tou nayi
shiru ba zan sake cewa komai ba.”
Yayi maganar yana mata nuni da gaban kujerar da take facing d’inshi.
Da sauri taja gaban hijabinta ta rufe idanunta sannan tazo ta zauna a wajen da ya nuna mata ta sake sunnar da kanta k’asa.
Tafi minti uku a haka jin shiru yasa ta d’ago kanta a hankali a tunaninta ko wani abun yake yi a waya amman tana d’agowa sukai ido biyu dashi da sauri ta kuma sunkuyar da kanta.
Murmushi gefen baki yayi kafin yace “Hudan”.
“Um”
Tace.
“Hudan”
Ya sake kiranta.
A hankali tace
“Na’am”
Sai da ya d’an yi jim!
Tukunna yace
“Pls ki cire wannan hijabin daga idonki, I want to talk to you about something that is very important, kinji”.
A hankali ta d’an jashi sama, face d’inta ya fito.
Ajiyan zuciya ya sauk’e kafin yace “Last time da naje wajen ki a school!
I told u what i feel towards you amman baki ce komai ba har yanzu.
Inaso in san matsayina
dan i think is about time da ya kamata in san where i stand ko?”
Yayi maganar yana d’an lek’o fuskarta.
Shirun da tayi ne yasa yace
“Um? Please don’t say you need more time Hudan, Allah kad’ai ya san what I’m going through!
Ko menene just say it, in ma bakya sona ne ki fad’a min zan d’auki k’addara.”
A hankali yaji tace
“Ya Arshaad nifa ban ce bana sonka ba.”
Zuciyan shi har wani bugawa take yi, cikin k’aguwa da son jin amsar ta yace “Does this means kina sona?”
Murmushi tayi sannan ta d’aga kanta alamar ‘eh’
“Alhamdulillah”
Taji ya furta tare da sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya
kafin ya sake cewa “zaki aureni right?”
Murmushi tayi sannan ta d’aga kanta still alamar ‘yes’
Kunyace taji tana shirin nutsar da ita shiyasa ta tashi da sauri ta fice a falon, tana jinsa yana cewa “No pls wait bamu k’arasa ba”
amman ta fice cikin sauri….
Arshaad ya kusan 1 hour a parlourn shi kad’ai a zaune yanata murmushi da day dreaming na yadda rayuwanshi zai kasance tare da Huda.
Yanata plans shi kad’ai
kala kala, bai san lokaci ya ja har haka ba!
Kiran sallar la’asar ne ya fargar dashi, gashi yanada meeting d’in gaggawa a company wanda Granpa ya turo mishi d’azu akan za suyi su biyu @5pm! Bai san akan menene ba.
Da sauri ya d’au wayar shi ya buga kiran Aaima yace “ta sameshi a mota yanzu yanzu.”
A gurguje Aaima ta yiwa su Mama sallama, dan taji kamar Yayan nata yana cikin sauri ne.
Tana zuwa kuwa ta fad’a motar yaja suka fita daga gidan…
Gudun da taga yana yi ne ya sanya ta tambayeshi
Nan yake ce mata “Granpa ne yace mishi ya sameshi a office bai san mai ya fari ba.”
“Allah yasa lafiya.”
shine abinda Aaima ta fad’a sannan ta jingina da jikin kujera ta lumshe idanunta ta fara tunanin Auwal…
Yau kwana biyar kenan bata gansa ba kuka ko ta kirashi baya d’auka! Daman kwana biyun nan rashin mutunci yake ji dashi, dan kawai yace tayi mishi abu tak’i yi! Ita wani abun na Auwal sai take ganin kamar iskancine amman friends d’inta na nile su ce mata suke yi ‘hakan wai wayewa ce, its a normal thing and dan yana sonta ne shiyasa yake demanding, inda iskanci ya so yi to da ba zai na demanding peck da kisses ba, he would have ask for something different!’.
To ko dai tayi mishi kawai tunda ba wani abun bane ba, dan ita dai har ga Allah
Allah ya d’aura mata son Auwal, bama ta san wanne irin so take yi mishi ba! She don’t ever want to see him angry,
besides she is in level 2, tana ganin yadda mates d’inta suke kula da samarin su......
Maganar Arshaad ce ta katse mata tunani jin yana cewa
“Wai tunanin me kike yi ne haka?”
Cikin fad’a.
Firgigit!! Ta bud’e idanunta.
K’ura mata ido yayi sannan a hankali yace “anjima around 9, ki sameni a parlourna.”
“To”
kawai tace, sannan ta bud’e k’ofar ta fita, binta yayi da kallo har ta shige sannan ya nufi mosque d’in jikin estate d’in yayi sallah, yana idarwa ya d’anyi addua, sannan ya fito ya shiga mota ya nufi office....
Yana zuwa bai tsaya b’ata lokaci ba ya nufi hanyar office d’in da yake mallakinsa a cikin building d’in dan Granpa yace mishi “a nan zasu had’u”
kuma kamar yaga d’aya daga cikin motocin da Granpa d’in yake hawa a parking lot shiyasa a
gaggauce ya dinga amsa gaisuwar securities da wasu ma’aikatan da suke ta gaidashi yana mai k’arsawa office d’in nasa.
Key ya zaro zai bud’e k’ofar amman yana d’aurawa yaga ashema k’ofar a bud’e ne hakan ya bashi tabbacin Granpa ya rigashi k’arasowa kenan!! Agogon hannunshi ya kalla yaga ya k’ara 5 minutes akan time d’in da yace masa ya sameshi.
Ajiyar zuciya ya sauk’e kawai yayi ‘bismillah’ ya tura kai ya shiga.
Yana shiga ya hango Granpa a kan kujerar shi ya juya baya.
Sai da yayi addua sannan ya k’arasa inda yake…
D’an gyaran murya yayi sannan cikin girmamawa ya gaidashi.
Ba tare da ya amsa gaisuwar tashi ba yace “I’ve waited for you, for six minutes!”
Arshaad zai yi magana Granpa ya katseshi ta hanyar mik’o mishi wasu takardun. Karb’a
yayi ya fara dubawa……
Cikin no nonsense voice d’inshi yaji Granpa d’in yana cewa “3 days ago mun samu embezzlement, ko kuma in ce theft from an insider, munyi ta bincike da ni da Auwal at long last mun gano waye!”
Dai dai nan idanun Arshaad suka kai kan abunda takardar ta k’unsa!
Gabanshi ne ya hau fad’uwa babu k’akk’autawa!
Naira miliyan dubu d’ari tara ne suka b’ata! Kuma shine yayi signing, gashi kuma a d’ayan takardan an nuna ya shiga personnel account d’inshi!.
Da sauri ya d’ago ya kalli Granpa a mugun firgice yace
Grandpa, i don’t know anything about this! Maybe mistake ne ko kuma someone is trying to frame me, amman wallahi i have no clue......”
Kura mishi idon da yaga Granpa yayi ne ya sanya shi yin shiru.
Cikin kakkausar murya Granpa yace “Who’s trying to frame you?
Um?
Ni ko Auwal?
Use your words!
Dan mune muka yi binciken, just the two of us!.”
Shiruuu, Arshaad yayi ya sunkuyar da kanshi k’asa.
Granpa yaci gaba da cewa
“For your information nayi suspending Auwal d’in kanshi for a week!
Did you know wat he did??
I ask him to investigate, and after he finds out kai ne b’arawon he hid it from me! Bawan Allah n nan was even trying to pay back the money from his own pocket duk dan kar in gane kaine mu samu matsala da kai….”
Da k’arfi Arshaad ya runtse idanunshi, har ga Allah Auwal fa ya fara kaishi mai’ura da makirce makircensa!
Shi da yake a matsayin MD amma wai yana yi mishi bak’in cikin treasurer d’in da aka bashi! For wat!??
Sai kace ba y’an uwa suke ba?
Maganar Granpa ne ya dawo dashi daga tunanin daya fad’a
jin yana ce mishi “take this!”
Hannu Arshaad yasa ya karb’a jikinshi duk yayi sanyi.
Mik’ewa Granpa yayi ya gyara suit d’in jikinshi, sannan ya fara tafiya yana dogara sandarshi, sai da ya kai bak’in k’ofa ya juyo ya kalli Arshaad
Sai a lokacin yaga bai ma duba takardarba, yana nan tsaye yadda ya barshi ya lumshe idanuwanshi…
Bud’e k’ofar Granpa yayi sannan yace mishi “the door is open and ranar Monday zamu fara zaman kotu da kai!”
Da sauri Arshaad ya kalleshi sai kuma ya hau duba takardun hannunshi, ta farkon takardar kora ce ta biyun kuma takardar sammaci ce!.
Da sauri ya k’araso gaban Granpa yace “Granpa pls i ....”
“OUT!!”
D’in da Granpa yace mishi da k’arfi ne ya sakashi saurin yin shiru dan yaga alamar kamar ran Granpa ya soma b’aci dan haka kawai sai ya yanke shawarar tafiya….
Jiki a mugun sanyaye ya sa kai ya fice daga office d’in!
Yana fita yaga Granpa ya d’aga sandarsa ya buga a jikin k’ofar dai dai inda glass d’in da aka rubuta sunanshi yake ‘Muhammad Arshaad Yahaya MT’
Nan take sunan ya tarwatse ya zube a k’asa.
Da sauri Arshaad ya juya ya fara tafiya da sauri….
Bai tsaya a ko ina ba sai a bakin motarshi, yana zuwa ya
bud’e ya shige ya kunna ya bata wuta…
Ikon Allah ne kawai ya kaisa gida, saboda uban gudun da yake zubawa.
Yana yin parking ya fito ya nufi gidansu Auwal..
A parlourn farko yana shiga ya hango shi a bakin kitchen da cup yana kurb’a da waya a hannunshi!
Gadan gadan yayi kanshi yana zuwa ya zuba mishi naushi!
Auwal bai ga shigowar mutum bama, kawai naushin da aka yi mishi yaji wanda yayi sandiyyar fad’uwar waya da cup d’in dake hannunshi da kuma fashewar hancinshi.
Jikin bango ya kama dan sauran kad’an ya shima d’in ya zube k’asa! Sannan da sauri ya d’ago dan ganin waye…
Suna had’a ido da Arshaad kawai ya kwashe da wata mahaukaciyar dariya har da rik’e ciki!
Arshaad bai kula shi ba sai da ya barshi ya d’an tsagaita
tukunna yace masa “why? And how do you do it??”
Murmushin gefen baki Auwal yayi sannan ya lakato jinin da yake bin hancinshi wanda ya sauko har kan k’irjin shi, kallon jinin yayi kafin ya gogawa Arshaad d’in a daidai kan kirjinshi wajen heart d’inshi, sannan yace
“Na tabbatar zafin da nake ji a face d’ina da jinin dana zubar bai kai wanda kake ji anan ba”
Buge mishi hannu Arshaad yayi kafin yace “ I don’t have time for this, just tell me, me nayi maka haka? What do you want from me?”.
Murmushi Auwal ya sake yi kafin yace “Yanzu kam i want nothing from you, a time d’in da nake neman abu a wajenka ai k’in yi mini kayi.
Kai ka san waye ni bana mantuwa kuma bana yafiya!
Zaka iya tuna ranar da Khadija tazo wajenka akan kayi mata signing ka k’i yi!?
A time d’in I called you Arshaad a whole me ina a matsayin MD nace maka kayi signing d’innan, I’ll explain later amman saboda taurin kai irin naka da kuma son kayi proving wasu silly principles d’inka ka k’i yi! A whole me ace wai in saka ka kayi abu amma ka
k’i yi! Who do you think you are??”
Da mamaki Arshaad yake kallon Auwal, kafin yace
“Yanzu saboda wannan ne kake son lalata mini image da carrier da future d’ina gaba d’aya?
Auwal Granpa ya kai ni court!! I’ve been sued by my own family for theft!! wanne company ne kake tunanin zasu bani aiki da wannan pent d’in da kayi mini??”.
Gyara tsayuwanshi Auwal d’in yayi kafin yace
“Actually Arshaad maganan court was my idea, although ban fad’awa Grandpa direct ba
kawai dai na bashi labarin wani Abokina da yayiwa mahaifinshi haka shikuma Mahaifin nasa ya kaishi court! That’s all i said i was hoping yayi same thing to you, and look! He did!!”
Ya fad’a yana murmushi kafin ya ci gaba da cewa “Arshaad!!you should have known me by now, bana son shishshigi…actually akwai abubuwan da kayi mini dayawa a company d’innan, tun dawowarka da aka baka position d’inka shikenan ka saka mini ido dayawa, I’m the MD bai kamata ka dinga bin al’a’mura na ba amman kwanaki har investigation ta k’ark’ashin k’asa kayi mini.
Duk wasu abubuwan da kake yi ina sane da kai.
I warned you twice amma baka ji ba!
A tsarina bana maimaita magana sau uku…
Da Khadija ta zo, na kiraka nace kai signing mata, ko nawa ne zasu fita ta acc d’in company Ina ruwanka??
amma still u refuse.
On a serious note Arshaad nayi tolerating Dinka more than yadda nake tunanin zan iya ma.
And you should stop saying wai nayi tarnishing image naka akan small thing cos this is not a small thing to me, remember i hate nonsense, and small thing su suke komawa manya shiyasa nayi deciding in yi dealing with you now!.”
Yana gama fad’in haka ya juya har ya d’an yi gaba sai kuma ya sake juyowa yace “sai mun had’u a court, i‘ll make sure na kawo wasu takardun da zasu sake girgiza ka!!
Don’t underestimate the power of your MD, wannan ma ina baka san ya aka yi suka fito ba ko?”
Bai jira jin me Arshaad d’in zai ce ba ya ci gaba
“A daa abokin fad’a ne da kai! Yanzu kam you’ve made an enemy that too a powerful one so be afraid!!”
Yana gama fad’in haka yayi hanyar sama ya kyale shi a wajen….
A hanyar main k’ofa na shigowa ya hango Mom da alamun yanzu ta shigo amman tabbas taji komai dan da mugun mamaki take kallon shi, d’an takowa tayi tana lek’a inda Arshaad d’in yake taga bai juyo ba har yanzu,
Yana ganin ta matso kusa dashi da alamun tausar shi zata yi a take ya b’ata rai yaja d’an gajeren tsaki kafin k’asa kasa ciki b’acin rai yace
“What a terrible timing u have! duk inda ake abunda bai kamata ki sani ba sai an ganki a wajen!!
Anyways it’s on u, cos I’m not gonna change or do anything for you. Kece kika ce inyi k’ok’ari nayi winning MT and that’s wat i’ve been trying to do.”
Yana gama fad’an haka ya wuce yayi hanyar stairs d’in side d’inshi.
Mom bata so Arshaad ya ganta a wajen, amman shock d’in da Auwal ya bata ya sa ta daskare a wajen ta kasa matsawa…
Gaba d’aya kullum Auwal sake rainata yake yi kamar kashin gindinshi, why?.
Tana a haka har bata san Arshaad d’in ya k’araso ba, sai muryarshi taji yana gaisheta.
Da kyar ta iya amsawa tana tunanin yadda zasuyi da Mammy idan case ya fito…ta san Mammy k’awar ta ce amma yadda take son Arshaad ko uwarta fad’a suke yi da ita akansa…
Amsawa tayi cikin basarwa da nuna kamar bata ji conversation d’inshi da Auwal ba.
Arshaad kam bai ma wani lura ba ya wuce dan duk jikinshi a mace yake, sannan har ga Allah bai san ta ina zai fara zaman court da Granpa da Auwal ba!!…
Mom kuwa ta dad’e a wajen tana lissafin nemo yadda zata b’ullo wa alamarin, ganin bata da wata mafita ya sanya kawai ta hak’ura ta wuce d’akinta tana mai jiran k’arasowar Mammy dan ta san tana hanya muddin zancen yaje kunnenta.......
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
25
Jiki a mace haka Arshaad ya shiga gida, bai tarar da kowa a parlour ba, dama kuma hakan yake hoping dan ya san in dai Mammy ta ganshi a wannan situation d’in to sai ta fahimci yana cikin matsala, kuma ta dinga tambayar shi kenan, shi kuma a halin yanzu baya buk’atar yin magana ma, he just need rest, peace and quite!.
A haka ya k’arasa side d’inshi ya wuce bedroom, yana shiga ya fad’a kan gado rigingine yayi pillow da hannayenshi ya lumshe ido ko takalmin k’afarsa bai cire ba.
Ya dad’e a haka, tukunna ya zaro wayarsa daga aljihu ya shiga contacts ya fara scrolling, yana zuwa kan ‘bff’ yayi dialing da alamun daman number yake nema…
Bugu uku a na hud’u aka d’auka!
Wata murya very calm cike da jarumta da dad’in sauraro mamallakinta yayi amfani da ita wajen cewa
“Assalam alaika!”
Nannauyar ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e kafin yace
“Ameen, wa alaika assalam. Ya aiki?”
“Alhamdulillah, wats up!?”
Aka ce daga d’ayan b’angaren.
“A lot!”
Shine abinda Arshaad yace, sannan cikin nutsuwa ya hau kwararo mishi bayanin yadda suka yi da Granpa da Auwal d’azun, da kuma zancen shiga kotu!…
Shiruuu, kowannen su yayi bayan Arshaad ya gama bayani. Chaan!! daga d’ayan b’angaren akace ,
“I’m coming home this Sunday, in sha Allah.”
Da k’arfi Arshaad wanda a take yaji kusan 70% na damuwarshi ya kau, yace
“Really?? Woow!”
Sai a lokacin ’ASLAM’ yayi murmushi, sannan yace
“Yeah really, Bro. I was planning nayi surprising naku gaba d’aya, but naga u need something to brighten up your mood, so i have no choice but to tell u.”
“U really did brighten up my mood kam.
Allah ya kawoka lafiya and i also have a surprise for you.“
Cewar Arshaad.
“Ok, sai na zo d’in in sha Allah.”
Cewar Aslam, har zai kashe wayar sai kuma yace “karfa ka gayawa kowa, remember it’s a surprise.”
“Yeah i won’t, i promise.”
Shine abunda Arshaad yace yana murmushi.
D’an tattaunawa suka yi akan case d’in da Auwal ya had’a, bayan sun gama
Arshaad yayi mishi godiya sannan yace “bara ya barshi ya ci gaba da aiki.” Dan ya san maybe abunda yake yi kenan ya tsayar da shi.
Shiruuu, Aslam yayi bai kashe ba kuma bai yi magana ba….chaan! Ya sauk’e ajiyar zuciya sannan yace “how is she??”
Lumshe ido Arshaad yayi a hankali, sannan ya bud’e su kafin yace
“She’s fine, sai ka dawo.”
Fahimtar da Aslam yayi k’ok’arin hanging up Arshaad yake son yi yasa da sauri yace
“No, pls wait!”.
Shiruu, ne ya sake biyo baya chan Aslam d’in yace
“Tayi maganata? Did she ask about me?
Dan Allah ka gaya min gaskiya.”
Gaba d’aya zuwa yanzu Arshaad ya fara regretting kiran sa d’in da yayi!
Wani yawu mai mugun d’aci ya had’iye da kyar kafin yace
“A’a!
Amman tana.....”
‘Kit!!’ yaji an yanke kiran…
Da k’arfi Arshaad ya runtse idanunshi tare da damk’e hannunshi kamar zai yi boxing!
Ya fi minti biyar a haka tukunna a hankali ya fara bud’e idanuwan nashi da suka sauya kala tukunna ya samu ya iya janye wayan daga kunnenshi…
Yana mugun jin tausayin Yayan nasa, da ace yana da yadda zai yi to da ko nawa ne zai biya in iyakar kud’in shi kenan to zai biya ya yaye mishi wannan damuwar!.
Duk fad’in duniyar nan ko wajen Mammy yaje bata samo mishi solution d’in problems d’inshi amma minti goma yayi yawa Aslam zai nema mishi solution d’in matsalar shi ko wacce iri ce.
But shi gashi matsala guda d’aya tak! Wadda ya taso ya ganshi a cikinta sam ya kasa taimaka mishi…
Gaba d’aya Arshaad sai ya fara jin haushin kanshi…
Haka nan ranshi babu dad’i yana zaune har aka yi kiran sallar Magrib!
Toilet ya wuce yayi alwala, ya fice zuwa masallaci..
Bai dawo d’akin ba sai da yayi Sallar isha.
Yana shiga ya fad’a toilet bai dad’e ba ya fito d’aure da bathrub kanshi yana digar ruwa da alamun wankeshi yayi…
Tsadaddun mayuka da turarrurruka yayi amfani dasu wajen shafe jikinshi, sannan ya nufi wajen kayayyakin shi ya d’auko wani three quarter wando cream colour, da wata armless riga itama cream mai ratsi ratsin red a jiki ya saka, kayan ya mugun karb’ar shi,
yayi kyau sosai.
Bai damu ya tsaya taje sumar tasa ba, ya d’auko wayar shi.
Kunyar kiran Ummu yake yi amman ba yadda zai yi, tun d’azu yaketa daurewa akan ya bari sai gobe su had’u amman ya kasa.
Dialing number Ummu yayi yana adduar Allah yasa Sakina ce zata d’auka ta yadda cikin sauk’i zata had’ashi da Huda.
Adduar shi kam bata amsuba dan ana d’aukar wayar ya gane Ummu ce
“Assalama alaikom, Arshaad ya gida.”
Ummun tace
“Lafiya Alhamdulillah Ummu ina wuni.”
“Lafiya k’alau ya su Maman ka?”
“suna lafiya kowa lafiya.”
Sai kuma yayi shiru, kafin yace “ya su Sumayya?”
Nan take Ummu ta gano shi, hakan yasa tayi murmushi kafin tace “Sumayya lafiya k’alau, su Huda kam da Sakina d’azu sun bi Mama datazo tafiya sai jibi zasu dawo.
Kana da number Maman ko?”.
Kamar yana gabanta haka ya hau sosa kai, yana sunkuyar da kai sannan yace
“Eh, ina da shi.”
Murmushi ta sakeyi sannan tace “to a gaida mutan gidan Arshaad, mun gode sosai.”
“Tam zasu ji, in sha Allah sai da safe.”
“Mu kwana lafiya.”
Ummu tace, sannan ta kashe wayar, tana murmushi da mamakin kunya irin ta Arshaad !
Shi kam wannan shi ya cika cikakken bafulatani, ta san sarai ba zai tab’a kiran Mama a yau ba, tunda ya lura ta gano shi, talkless of ya nemi magana da Huda.
Mikewa tayi ta nufi kitchen ta d’auko tray ta isa dining….
Tun d’azu take jiran Baban Sakina ya fito suci abinci, amma yana dawowa a sallah ya shige ciki har yanzu shiru. Dan haka ta d’aba musu abincin ta d’aura a tray ta wuce d’akin shi.
Sai da tayi knocking ya bata izinin shiga tukunna ta shiga da sallama.
A kan gado ta hangoshi ya kwanta rigingine, yayi
pillow da hannunshi d’aya d’ayan hannun kuma ya dafe goshinsa da shi.
Kan tebur d’in d’akin mai d’auke da kujeru biyu da suke d’an gefen gadon kad’an taje ta ijjeye sannan ta dawo bakin gadon kusa dashi ta zauna.
A hankali ya juyo ya kalleta kafin ya k’ak’alo murmushi sannan ya mik’e ya zauna ya kamo hannunta duka biyu a nashi hannayen bayan ya gyara zama ya fuskanceta.
Itama murmushin ta mayar masa sannan tace “kazo muje kaci abinci.”
Bai musa mata ba ya mik’e suka nufi inda ta ajjiye abincin…
Sai da suka gama ci sannan tace “Me yake damunka? Naga kamar kana cikin damuwa.”
B’oyayyiyar ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace “ba komai, aiki ne kawai, an ma yi settling. Kawai dai ina wasu y’an lissafe lissafe ne.”
Ummu kwata kwata bata gamsu da amsar daya bata ba, amman gudun ja inja da zargi a tsakaninta da Mijin nata yasa kawai ta kawar da zancen ta kawo wata hirar..
Sun d’an jima suna hira kafin yace mata “D’azu Arshaad ya same ni akan yana son ganin Mahaifin Huda.!”
Da sauri Ummu ta d’ago tana kallonshi.
Ganin hakan yasa yaci gaba da cewa “Ban b’oye mishi ba, na fito na fad’a mishi cewa ‘an samu matsala tsakanin kakanninta na wajen uwa da mahaifinshi dashi kanshi Mahaifin nata, yanzu dai Huda a hannunmu take.
Nayi matuk’ar mamaki da Arshaad ya gaya mini cewa ‘iyayensa zasu amince da auren ko da babu Mahaifinta!’.”
Murmushi Ummu tayi kafin tace “Ai fa Baban Sakina ba koina ne aka taru aka zama d’aya ba! Inaga shi nasa dangin in dai suka bincika suka ga tarbiyyar Yarinya kuma suka tabbatar babu wani mugun abu a kanta ai dan dai fad’an iyaye ba sai sunbi diddigi ba, shiyasa yace maka ba matsala, danginshi basu da zafi kenan tunda kaji ya fad’a maka hakan!”
Jin yayi shiru yasa Ummu ta sake cewa “Ko?”
“Um, yes! maybe.”
Shine abunda Baban Sakina yace da alamun hankalinshi baya gareta…
A hankali ta d’an matso ta sake cewa “Kayi bincike sosai ko, i mean a kan shi Arshaad d’in.”
“Eh, nayi sosai, ba wata matsala fa.”
“Alhamdulillah” shine abunda Ummu tace sannan ta cigaba da cewa “ina so ma inje wajen Maman shi, inyi mata godiya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 32