takeyi su k’araso dan ta lura tabon goshin Jalila ya warke da alamun tana buk’atar wani kuma daman tun ranar da Ya Jaafar ya sumar da Hudan take adduar Allah ya kawo abinda zai had’ata fad’a da su!.
Ita kuwa Jalila ko da ace taje ma ba ta kan Sakina take shirin zata bi ba, tun ranar da taga Hudan da Arshaad take ji kamar ta mak’ureta, Yarinyar da bata yi makaranta ba wata kuchaka da ita amma wai itace har zata yi saurayin da ya fi nata?!
Shiyasa so take kawai ta isa wajen ta samu ko da marin Hudan ne tayi atleast ta san hakan zai rage mata rad’ad’in da take ji a ranta….
Gashi su Umma suma sun gama tunzurata! Ji take kamar ta fashe….
Ganin dai da gaske Umma fad’a zata yi da Sakina ne ya sanya Anty Zainab ta sha gabanta ta rik’e hannayen Jalila sannan ta cewa Umma “haba! haba dan Allah, abun har ya kai haka? Y’ar cikin ki fa! ai girma sai ya fad’i.
Ku zo muje d’aki kuji, dan Allah.”
Shiru Umman ta d’anyi tana kallon su Sakina tana huci sai kuma kawai ta juya a fusace ta shige d’aki.
Sai da Anty Zainab ta dakawa Jalila tsawa tukunna ta wuce tayi d’aki tana mai dannawa Sakina zagi!.
A d’akin su Mama kuwa! Mama har zata fito amma sai Ummu tace mata “ta rabu dasu kawai! In dai Sakina ce daidai take dasu.”
Dan haka suka zauna suka ci gaba da tattaunawa….
Sai da Anty Zainab tayi da gaske tukunna ta iya lallab’a Umma da Jalila suka hak’ura Danna k’ad’an ba sun d’au zafi!k’arshe ma Umma cewa tayi “in taci gaba da zama a cikin gidan, zuciyar ta zata iya bugawa, dan haka suka fita tare da Anty Zainab, aka bar Jalila.
Ko kallon inda suka bi Sakina bata yi ba, dan ita har mamakin Anty Zainab d’in take idan taga tana biyewa su Umma. So take yi ta fita a gidan shiyasa ta cewa Hudan tazo ta rakata ta karb’i kud’i a wajen Ummu suje gidan kitso, dan su Umma suna fita Jalila ta sake fitowa ta zauna a tsakar gidan tana wani ciccin magani kana gani ka san neman bala’i take yi.
Har Sakina ta mik’e zata je d’akin Maman sai Hudan tace “dan Allah su zo su tayata tsefe kanta sai su tafi tare, ba zata iya tsefewa ita kad’ai ba.”
Sakina ce ta dawo tana cewa “Huda Allah ya nunamin ranar da zaki koyi tsefe gashinki da kanki”
Da d’an k’arfi Sakinan ta kuma cewa “Dan ma dai Arshaad d’in naki mai kud’i ne, nasan y’an aiki a ciki harda mai yi miki tsifa zai nemo, idan bayanan ta dinga tayaki, In kuwa yana nan na san shi zai dinga yi miki dan yadda yake nacin son nan naki ba zai bari ki sha wahalar komai ba.”
Ta fad’i hakan tana mai kunce d’ankwalin dake a kan Huda wadda take cewa
“Allah Sakina za muyi fad’a dake ni daina ki daina, banaso.”
Ai kuwa kamar yadda Sakina taso haka maganarta tayi tasiri a kan Jalila, dan har wani huci taga tanayi daga nan inda take a zaune.
Haka nan Sakina tana dariyar mugunta ta hau tsefewa Huda kalbar kanta da suka sauk’a har chan gadon bayanta.
Jalila tana zaune tana kallon su…tabbas ta san tanada kyau dan ana yawan gaya mata
sannan tafi Hudan manyan idanuwa amman idanun huda sunfi nata kyau nesa ba kusa ba dan ita nata idon ba cycle baneba irin dogayen nan ne sannan farare tas kuma kamar tana jin bacci, gata da dogon hanci ga bakinta mai kyau d’an k’arami. Ta san a iya fuska ma Hudan ta fita…maganar kalar fata kam ba’a magana, ta san ita ba bak’a baceba amman ba zata tab’a had’a farinta dana Hudan dayake da sirkin yellow yellow, kuma mai d’aukar ido, ba.
A kyauwun sura kuwa, Hudan a iya yanzu ta kusan kamo ta tsayi duk da ta grime ta, dukda cewa k’irjinta yafi na Huda cika a yanzu amma ta san ko tak’i Allah ba zata had’a hips d’inta dana Huda ba dan Hudan ta fita nesa ba kusa ba dan idan ta juya tana tafiya zaka d’auka wata shahararriyar budurwa ce.
Jalila bata gama sarewa ba sai da ta kalli gashin Hudan da Sakina ke tsefe mata y’ar kalbarta guda biyar har ta kusan gamawa, Gashin bak’i k’irin, gashi har gaban gashinta ga wani saje da takeda shi mai mugun kyau..
Tsayawa Jalila tayi tana kallon gashin dukda ba yau ta fara ganin gashin Hudan ba amman tabbas ta san ya Kara tsayi kwana biyun nan, tana zaune amman kamar zai tab’o k’asa! Bata san lokacin data sa hannu ta shafa nata ba, wanda ya wuce kafad’arta da kyar, d’aurin ta na ture kaga tsiya ta gyara dan ji tayi gaba d’aya ranta ya dagule!
Tabbas a yanzu idan taje wa Arshaad d’inma ba kula ta zai yi ba, ahaka ma bai ga gashin Hudan ba, gaskiya tun kafin ya gani ko ruwan batir ne sai ta kwara mata a gashin wallahi…..
Da sauri ta muk’e ta shige d’aki jin Sakina na cewa “bara inje In d’akko mike ribbon da comb sai in gayawa Ummu In taho mana da kud’in kitson.”
Jalila tana shiga batayi wata wata ba ta d’aga k’asan kayan ta inda take da wani ajiyeyyen almakashi, ai kuwa ta d’auko tayi waje da sauri, ta b’oye a k’asan zaninta.
ji tayi Hudan na cewa Sumayya “dan Allah ta d’auko mata hijabin ta a cikin kayanta”.
Cike da murmushin mugunta tayo inda take zaune kamar zata wuce, tana ganin d’aga labule da shigar Sumayya d’akin Mama ta k’araso inda Hudan take da sauri ta kama gashin kamar zata ribbon!!
Ita Huda da farko dake bata ga tahowarta ba ta d’auka Sakina ce, sai da taji an damk’i gashin da k’arfin sannan ta juyo zata cewa Sakinan baki taje mini ba zaki sa ribbon d’in? Kawai suka had’a ido da Jalila…..
Ai kuwa a take ta fara k’ok’atin kwace kanta, amma kafin ta kufce tuni Jalila ta zaro almakashinta ta daidaita gashin Hudan da iya k’arfinta ta yanke shi kitt!!!!!
Iyakar wanda ta bar mata wanda za a iya had’awa ayi parkin ne kawai, shima kuma jelar sai dai yayi kamar bindin kaza!
Hakan yayi daidai da fitowar Sakina da comb da ribbon a hannunta dan Ummu cewa tayi “su bar kitson sai gobe suje da wuri yanzu yamma tayi”
Huda da sauri ta juyo tana kallon k’asa jin abu ya fad’i, wani razanannen ihu tayi sakamokon ganin gashinta wanwar a k’asa! ita abun ma mugun tsoro ya bata shiyasa
ta shiga shafa kan tana wani irin kuka….
Jalila bata ga k’arasowar Sakina ba sai wani mugun mari n da taji ya sauk’a a kan kumatunta, kafin ta yunk’ura Sakina ta rufeta da duka ta koina….dukda tazarar shekarun dake a tsakaninsu yau kam Jalila ta daku a hannun Sakina dan k’arshe ma ihu Jalilan ta fara tana neman taimako.
Su Mama jin abun yayi yawa dan su duk a tunani su su Umma sunan nan, sanin halinsu yasa suka k’i fita kar su fita su Umman su had’a dasu a fad’an Yara
Shiyasa har Sumayya data shigo d’aukar hijabi suka hanata fita. Amman ihun Jalila daya k’arashe ko Ina lungu da sak’o na gidan ne ya sanya sanya suka fito.
Turus!!! Haka suka ka suka tsaya sakamokon ganin gashin Huda a tsattsaye, ga uban tulin gashi a k’asa tanata k’ok’arin tattarewa tana d’aurawa a kan cinyarta tana kuka, gefe guda kuma ga Sakina a gefe sai jibgar Jalila take yi da iya k’arfinta.
Kafin su k’arasa tuni Ya Junaidu wanda shigowarshi kenan yayi saurin yin kansu Jalilan. Da kyar ya iya kwatar ta a hannun Sakina amman fa ta fasa mata hanci har da baki, ta yi mata jina jina!
Su Mama ne suka hau tambayar ba’asi, nan Sakina ta hau kwararo musu jawabi iya abinda ta gani…
Junaidu ji yayi da ma bai kwaci Jalila ba ji yake kamar ya juya yaci gaba da dukanta tun bama da yaga yadda Hudan take kuka ba abun tausayi,
juyawa yayi kan Jalilan a fad’ace har zai fara magana
kamar kuma wanda ya tuna wani abun sai kawai yace mata “wuce ki shige d’aki”
Tana tafiya ya juyo ya kalli Hudan, wadda take mishi kallon ‘ya yau bai shigar mata ba!’ Gashi kuma abunda aka yi mata yau d’in ma yama fi na kullum…
Da sauri ya d’auke kanshi ya juya ya nufi hanyar d’akin shi ba tare da yace musu komai ba.
Sakina ce tace “Kinga irinta ko!! Saboda Allah ai atlest ya kamata ko fad’a ne yayi mata.”
Mama da Ummu kuwa sarai sun san dalilin da yasa Junaidu yayi hakan, dan labarin abinda ya faru shekaran jiya Mama take bawa Ummu sukaji ihun Jalila!
Shiyasa ba tare da sunce komai ba, suka tattare gashin kawai, suka d’aga Huda suka yi d’aki da ita tanata faman kuka.
Sai da suka rarrasheta da kyar! Aka samu bacci ya kwasheta tukunnan suka tafi bayan Ummu ta tabbatarwa da Mama kafin ta tafi gida sai taje ta samu su Baaba Talatu
kuma daga nan zata fad’a musu zancen makarantar da su Hudan zasu tafi, ta san ko su zasu yarda dan yanzu kam abun na su Umma ya zama hauka k’arara!! Dole a d’auki mataki sannan kuma Hudan tayi nesa da su……
Tanata fad’a baki da kumfa haka ta tusa k’eyar su Sakina suka tafi.
Ita dai Mama tayi shiruu! Dan tama rasa bakin yin magana.
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
24
Successfully, Kaka da Baba Talatu suka amince da batun makarantar Huda, Kaka shi ya sanar wa Madu wanda shima bai hana ba bai kuma ce taje ba kawai dai ya jinjina kai alamar ya ji kuma ya fahimta.
Kaka ne ya yanke shawarar Hudan ta tafi gidan su Ummu tayi koda sati ne, bayan ya kira Baba da Umma da Jalila yayi musu fad’a sosai!! Sannan ya cewa Jalila “tunda y’ar daba take son ta zama kuma iyayenta sun kasa tsawatar mata to ta tabbata tana gama ssce d’inta ta fito da Miji idan ba hakaba to zai bada hotonta a masallaci duk wanda ya zo kuma shi zata aura koda kuwa gurgu ne!.”
Jalila kuka wiwi haka suka baro gidan Kaka, Umma sai mita take yi wai ‘anyi son kai!’ Idan ba haka ba dan maiyasa ba a yiwa Sakina fad’an dukan da ta yiwa Jalila ba?!.
A Daren ranar da su Ummu suka koma gida suka samu takardun Sakina itama har sun zama ready..
Duk wani preparation na exams d’in yi suke dan Arshaad har wata lesson teacher ya d’auko tayi musu isashshen lesson ranar asabar da lahadi wanda da farko shi yaso yi musu lesson d’in amman sai aka tura shi wani aiki Abuja sai monday da yamma tukunna zai dawo.
Sakina tana fahimtar lesson d’in sosai amman Hudan kam sai dai godiyar Allah,
matsalar da aka samu shine ita lesson teacher bata jin Hausa ita kuma Huda turancin sai a hankali.
Sai da ya zamana
duk abinda lesson teacher ta fad’a sai an mata translating da Hausa! Duk k’ok’ari da hak’uri irin na matar sai da ta k’ule a cikin kwana biyun.
Da kyar Hudan ta tsinci iya abubuwan da zata iya tsinta ranar Litinin kamar yadda aka fad’a Baban Sakina da Ummu suka kaisu makarantar domin su zana jarabawar.
Hudan har kusan kukan murna tayi da taga jarabar tasu zab’i ka tik’a ce! Saboda daman adduar da take ta yi kenan.
Sai dai kuma duk da hakan
da kyar da sid’in goshi ta iya amsa question biyar a cikin guda d’ari biyun da take tunanin ta gane wanda hakan ya d’auketa sama da awa d’aya.
Tayi kokari wajen ganin ta amsa ragowan dan bata so ace ta fad’i jarabawar nan tana mugun son tayi karatu a rayuwarta amman kwata kwata sai ta kasa.
Har kuka tayi a exams hall d’in, bata ankara ba taji ana cewa “20 minutes remaining!!” idan ta fahimta sauran minti ashirin kenan a tashi! Hakan ya sanya
kawai ta rufe idanunta ta karanto sunayen Allah ta nemi nasara da sa’a sannan ta d’aga pencil d’inta ta fara sheding, duk shed d’in da zata yi sai ta kira sunan Allah tukunna ta tik’a…
Haka tayi daga Ar Rahman zuwa As Sabboor, ta sake dawowa Ar Rahman a haka har ta gama wanda yayi dai dai da fara amsar takardun nasu.
Sai da ta tofe takardarta da addua tukunna ta bayar invigilator d’in yana ta tsokanarta.
Kasancewar y’an hall d’in su Sakina sun rigasu shiga yasa tana fitowa suka had’u da Sakina a k’ofa tana jiranta.
Sakina na ganinta ta k’araso da murnarta tana cewa
“Hudan jarabawar tayi sauk’i ko? kinga duk abinda malamarnan ta koya mana kusan duk sun fito, kamar ta sani.”
Da mamaki Hudan ta kalleta kafin tace “Tab! Ni fa biyar kawai na gani irin wanda tayi mana, a maths d’in kuma naga irin wannan mai kamar triangle d’in wanda kika sake koya min da daddare dayawa amman duk sun chanja nambobin.”
Lumshe ido Sakina tayi a hankali sannan ta bud’e, kafin tace mata
“Ai numbers d’in kawai suka chanja, kin dai yi ko?”.
Hudan bata b’oyewa Sakina ba ta gaya mata yadda tayi..
Jikin Sakina duk sai yayi sanyi amman gudun kar ta sace mata guiwa ya sa kawai tayi ta bata kwarin gwiwa.
Suna shirin wucewa aka ce “kowa ya tsaya akwai d’an guntun orientation da za ayi musu, babu isheshshen lokacine amman da it’s sopposed to be for weeks..”
Haka nan suka d’unguma aka fara orientation d’in. Ita kam Huda zuciyarta duk a dagule, bare ma da aka fara orientation d’in nan ta sake ji makarantar ta shiga ranta, duba kuma da abunda ta rafka a exams d’in duk sai hankalinta ya sake tashi.
Sai da aka yi rounding up sannan suka kama hanyar inda su Ummu suka yi parking, Hudan har da y’ar kwallarta,
da kyar Sakina ta d’an lallasheta ta bata kwarin guiwa tukunna aka samu hankalinta ya d’an kwanta.
Suna zuwa nan ma Ummu da Baban Sakina suka shiga tambayarsu, ita dai Hudan k’arshe ma kuka ta saka, dan gani take yi kamar har ta fad’i ne, sai da su Ummu suka yi ta bata baki tukunna ta hak’ura tayi shiru.
A haka dai duk jikinsu yayi sanyi jin Hudan bata yi wani abun kirki ba, suka k’araso gida.
D’aki suka wuce ita da Sakina sai da suka yi wanka suka shirya suka yi waya da Mama sannan suka fito suka ci abinci suka d’an yi hira da kallo sama sama isha nayi kowa ya nufi gado.
Ranar Hudan bata yi bacci ba kwana tayi tsayuwar dare tana rok’on Allah yasa suci jarabawar nan…
Washegari ma da safe haka ta tashi duk jiki ba kwari har dare, kamar jiya yau ma bata yi bacci ba, kwana tayi tana sallah..
Haka ta kasance kullum, itama Sakina daga baya tayi joining d’inta a sallar daren, a haka aka yi sati.
Ranar litinin da yamma sai ga Arshaad ya zo.
Su bama su san yazo ba, suna falo suna kallo, sun gama waya da Mama kenan! Wayar Baban Sakina ta shigo layin Ummu, d’auka tayi suka yi magana bayan ta ajjiye ta kalli Sakina da Huda tace “kuje Babanku yana son ganinku, Arshaad yazo da result d’in jarabawar da kuka yi.”
Da kyar gabansu yanata fad’uwa suka iya mik’ewa suka nufi d’aki, bayan sun d’auko hijabansu suka tafi parlourn Baban Sakinan.
Sakina ce tayi sallama aka basu izinin shiga, ita ta fara shiga sai Hudan a bayanta kansu a k’asa suka gaida Arshaad.
Cikin kulawa ya amsa yanata satar kallon Huda wadda ta kusan yin fitsari a wando tsabar fargaba! So take kawai taji me za a ce.
Baban Sakina ne ya mik’a musu takardun yace “ga results d’inku”
Da kyar Sakina ta iya mik’ewa taje ta amso sannan ta dawo kusa da Huda ta mik’a mata d’aya… har rige rigen bud’ewa suka hau yi.
Hudan tana bud’ewa taga 149/200 sai kuma daga chan k’asa anyi stamping ‘PASS’ da green rubutu!
Sai da ta kalli sama sai taga sunan ba nata bane ashe takardar Sakina ce. Murna ta hau yi dan taji dad’i duk da fargaban rashin ganin nata amman atleast Sakina ta wuce.
Ita kuma Sakina tana bud’ewa taga sunan Huda, da sauri Hudan ta lek’o, bata san lokacin data ce
“Kaiii!! nawa ne kuwa?”
Da taga 185/200 itama an mata stamping ‘PASS’.
Ai kuwa da sauri suka rungume juna a wajen suna dariya suna maimaita kalmar “Alhamdulillah” Hudan har da kwallarta a ranta tana aiyyana
“Yanzu kenan itama zata yi karatu kuma a wannan makarantar y’an gayun data gani zata je tayi karatunta.”
Wani irin farin ciki ne ya lullub’e Arshaad a ransa yace
“So she’s this happy and it’s all because of him? Ai kuwa
In shaa Allah he will make it his life’s mission to keep her happy.”
Ya ji dad’i sosai dan bai san lokacin da shima ya fara murmushin ba. Tabbas Yarinyar tana son karatu, he wonders why iyayenta basu barta tayi ba, ko saboda halin babu ne maybe shiyasa….
Maganar Baban Sakina ce ta katse mishi tunani…
Godiya ya sake yi mishi kafin ya juya ya cewa su Hudan
“murnar ai ta isa haka ko? Ko godiya fa baku yi mishi ba.”
Nan suka had’a baki suka ce
“Mun gode, Allah ya saka da alkhairi.”
“Ameen, ba komai.”
Kawai yace dasu daga nan
Baban Sakina yace su tashi su tafi.
Sai da suka fita Arshaad yace “akwai interview d’in da ake zuwa ayi kuma du, amman dai shi ba wani issue bane tunda sun riga sun yi passing wannan.”
Godiya Baban Sakinan ya k’ara yi mishi.
Bayan Arshaad d’in ya
sanar dashi date na interview d’in ya wuce.
Successfully, suka je suka yi interview d’insu daga nan kuma aka fara preparation d’in tafiya.
Baban su Sakina ne yayi yayi musu provision da komai da komai har books, da farko Asrshaad yaso yi amman ya hanashi kwata kwata.
Sai a lokacin kuma Shuwa taji labarin tafiyar Huda da Sakina makaranta. Ita dai bata cewa Mama komai ba tunda daman ai ta dad’e da cire harkar ta a ranta amma Ummu kam ta sha fad’a! Wai “taje ta had’e kai da y’ar uwar ta sun b’oye mata abu, kuma Baban Sakinan da Mijin mama yayiwa rashin mutunci shine yanzu ta tura shi yake yiwa Maman abu salon wani abun ya sake faruwa ta jawowa kanta matsala a
Auranta!” harda cewa “ta raba Huda da Sakina dan ita tana da nata asalin.” Haka nan dai tayi ta mita.
Ita dai Ummu hak’uri tayi ta bata, sannan tace “Kaka ne yace Hudan taje gidanta ta d’an zauna”
Tukunna Shuwa ta d’an sauk’o.
Sai ranar lahadi tukunna Ummu ta bar Huda tazo gidansu..
Washegari da safe ta saka sabon uniform d’inta ta shirya tsaf sai a lokacin Mama taji kuka ya zo mata, itama Hudan kuka tayita yi ahaka Ummu da Sakina itama data shirya suka zo suka samesu.
Da kyar suka lallashi kansu sannan Ummu ta kai Huda da Sakina d’akin Umma dan su yi mata sallama.
Kasa b’oye bak’in cikin su suka yi, tun ba ma da sukaji sunan makarantar ba!
Ita dai Ummu bata bi ta kansu ba ta sanya suka yi musu sallama suka fito suka tafi.
A gate d’in makarantar suka had’u da Arshaad da k’anwarsa Aaima wadda tana ganinsu Huda ta dinga jansu a jiki kamat sun shekara da sanin juna.
Duk wasu formalities aka yi aka gama sannan Aaima ta sanya aka taya su kai kayansu hostel, sunata kuka ita tayi ta lallashinsu ta jasu suka tafi.
Su Ummu da Arshaad ma suna ganin shigewarsu suka juya suka wuce bayan doguwar godiyar da suka yi ta jera mishi, shi kam abun ma sai ya fara bashi kunya..............
Bayan shekara uku!
After 3 years (present day).
Yau Monday kuma yau su Hudan za suyi graduating.
Arshaad tare da Aaima suka zo, su suka fara zuwan ma su Huda dan sun riga su Ummu ma zuwa.................
Bayan an kai su Sakina makarantar shekaru uku da suka wuce Aaima ce ta tsaya a kansu especially Huda har
personal lesson take yi musu.
Tana son Yaran ba kad’an ba, ranar graduation d’inta kam sunci kuka, da kyar suka warware daga baya suka yi friends.
Daga nesa ta hango su cikin graduation gown d’insu sun yi kyau sosai sun zama y’an
mata sun yi fresh hasken
fatar su ya k’ara fitowa.
Basu lura da ita ba saboda duba wayar da suka ara domin kiran su Ummu da suke ta k’ok’arin yi, dan sunga har an kusan farawa amman shiru basu k’araso ba.
Sai da Aaima ta k’araso ta dafa kafad’ar Huda, tukunna
suka lura da ita.
Ai kuwa da sauri suka yi hugging d’inta suka hau murna, nan shima Arshaad ya k’araso, da murmushi a kan fuskarsa yake bin Hudan da kallo… Dukda cewa duk visiting yakan zo ya ganta amman yau d’in sai yaga gaba d’aya ta chanza, tayi wani kyau kamar yayi irin shekaru d’innan bai ganta ba.
Sakina ce ta fara gaidashi sannan itama Hudan ta sunkuyar da kanta ta gaidashi
dan ita har ga Allah yanzu wata kunyar shi take ji saboda tun lokacin da zasu fara zaman extension da yazo kawo musu books da abubuwan buk’ata yake gaya ‘yana sonta’ shikenan har yau bata iya ko had’a ido da shi.
Murmushi yayi ya amsa gaisuwar yana mamakin kunya irin ta Huda.
Sallamar da su Ummu suka yi ne ya juyo da hankalinsu..
Tun da suke zo makarantar sau biyu taje gida hutu a lokacin tana ss1, bayan nan a gidansu Sakina take hutunta kuma Mama bai fi taje sau d’aya ba dan ko visiting Baba hanata zuwa yake yi.
Shiyasa yau take ta adduar Allah yasa azo da ita, ranar farin ciki ya kamata ace tana kusa da ita.
Ai kuwa tana d’agowa da Maman suka fara had’a ido, ba tayi wata wata ba ta tafi da gudu ta fad’a jikinta, ji tayi kawai kuka ya sub’uce mata
Itama Maman harda y’ar kwallarta amman sai tayi saurin sharewa….
Sai da ta cewa Hudan “zata koma idan bata yi shiru ba”tukunna tayi shiru ta goge hawayen ta tana mai sauk’e tagwayen ajiyar zuciya.
Aaima ce ta fara matsowa ta gaida Mama dan ko ba’a fad’a mata ba ta san itace mahaifiyar Huda, daga nan
ta gaida Baban su Sakina da Ummu sannan ta hau tsokanar Sumayya tana cewa “ta zama y’a mata” ita kuma Sumayyan tana murmushi tana cewa “bata so” daman sun saba.
Sai da Sakina ta k’arasa dai dai gaban Arshaad ta tsaya tayi snapping fingers d’inta tukunna yayi firgigit! Ya kawar da idanunsa daga kan Mama da ya kafe da idanu, sannan yayi saurin juyo da hankalinshi kan Sakina yana murmushi.
Kallon da yaga Sakina tana yi mishi tana kuma waiwayawa tana kallon inda taga yana kallo ne yasa shi cewa
“Itane Maman Huda??”
Murmushi Sakina tayi sannan tace “Ai ni na d’auka wata kake kallo, baka ga har na had’e rai ba? Ashe Mama kake kallo.”
Ta k’arashe maganar tata tana murmushi.
Shima murmushin yayi sannan yace “kina tayata kishi bayan ita ko kishin nawa batayi, I don’t even think ma tana sona!”
Yayi maganar yana langab’ar da kai yanayin kalar tausayi.
Dariya Sakina tayi sannan ta d’an matso ta sa hannunta ta kare bakinta ta gefe kamar zatayi rad’a, tace “Kar ka damu zan yi maka campaign mai zafi!”
Dariya yayi yace
“Woow!! really? tnx sis, you are the best!”
Yayi maganar yana yi mata tumbs up.
Dariya tayi tana d’aga kanta alamar ‘eh’ sannan at the same time tana d’aga girar ta,
hakan yasa gaba d’aya suka kwashe da dariya, sannan
tace mishi zo muje ka gaisa da surukarka, yau ne had’uwar ku ta farko so you better act decent!”
Dariya kawai yayi, sannan ya bi bayan ta suka k’arasa inda su Maman suke tsaye.
Sai da ya d’an russuna sannan ya gaida Mama.
Cike da kunya ta amsa dan tunda ya nufo su Ummu tace mata “ga Arshaad”
Su ummu ma cikin ladabi ya gaida su suka amsa mishi da kulawa.
Daga nan suka d’unguma gaba d’ayan su suka yi hall d’in da ake taron bayan sun gaggaisa cikin mutunta juna…
Suna zuwa kamar su kad’ai ake jira nan aka fara gudanar da programs of event, Hudan aka kira ta bada speech wadda in mutun yaji kalar turanci da accent dining Hudan sai yace ba ita bace ba.
Bayan ta gama aka fara
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 19 Chapter of 32