Aslam yace
“What plan?
Who are you planning on deceiving?
Parents d’inmu?
Ko su Yarinyar!
Dan dole sai an yi deceiving 1of 2 d’innan
tukunnan auren nan zai yiu.”
Ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e kafin yace
“I love her!
Sosai!!
Ba zan iya hak’ura ba Aslam.
Kar ka damu, nothing will go wrong!
In shaa Allah.”
Wanann karon a harzuk’e Aslam yace
“How will....”
Ganin ma ba shi yake kallo ba ya sanya shima ya juya yana kallon inda yaga yana kalla…
Ko ba a fad’a mishi ba, ya san itace Hudan!
Ya jima yana kallonta!! Kafin da kyar ya samu ya iya janye idanunsa daga kanta.
Tun kafin ta k’araso Arshaad ya bud’e k’ofar ya fita.
Sai bayan kamar 20 minutes haka tukunna Arshaad d’in ya bud’e motar ya lek’o…… a zaune ya ganshi ya kwantar da kanshi a jikin seat!
Ya lumshe idanuwanshi kamar mai bacci.
Murmushi yayi kafin yace
“Ka fito mana, ku gaisa.”
Jinjina kai kawai Aslam yayi alamar ‘to’ ba tare da ya juyo
ko ya bud’e idanunshi ba.
Ganin haka yasa Arshaad d’in komawa tare da maida murfin motar ya rufe.
….Sam ya fidda ran Aslam d’in zai fito dan kusan 30 minutes
kenan da yayi mishi maganar!
Gashi ya san suna sauri ne saboda sunada appointment da Khadija GF d’in Auwal ta company wadda ta yarda da kyar zata gansu a yau, around 6pm ba tare da Auwal d’in ya sani ba.
Haka yasanya kawai ya fara yiwa Hudan sallama bayan ya kalli agogon hannunshi yaga time.
Kamar zata tambayeshi ina bak’on saboda d’azu yace mata ba shi kad’ai baneba
kuma har cewa yayi bara ya lek’a yace ya fito su gaisa..
Amma kuma ganin bai sake yi mata maganar ba yasanya kawai tace “ya gaida Aaima”
Tana shirin tafiya suka ji k’arar bud’e motar…
Ya kusan minti d’aya tukunna
kawai yayi tsaki ya mik’e ya fito ya zagayo inda suke tsaye.
Murmushi Arshaad yayi ya kalli Huda wadda take kallon k’asa tana mamakin yadda k’amshin turarenshi ya karad’e wajen, daga fitowarshi dan gashi har ma yana shirin k’orar na Ya Arshaad daga gurin gaba d’aya..
Muryar Arshaad taji yace
“Dan milki kenan!
Don’t mind him.”
Sai kuma yace
“Hudan ga yayana ‘Aslam’.”
D’agowa tayi tana kallon wanda ya kira da Aslam…wanda shi kuma sam kwata kwata yak’i yarda ya kalli inda take, chan wani waje ma taga ya juya yana kallo….
A ranta ta hau rayawa
….kwata kwata basa kama da Arshaad, Arshaad ya fishi hasken fata, amma fa tunda take a rayuwarta bata tab’a ganin skin colour d’in da yayi mata kyau!! Kamar na Aslam d’innan ba.
Yafi Arshaad tsayi, dukda kuwa shima Arshaad a sahun dogaye sosai za a sakashi.
Yanayin fad’in k’ashinsu shima kusan d’aya ne amman Arshaad ya d’an fishi k’iba……
Gyaran muryar da Arshaad yayi ne, ya dawo da hankalinta gareshi..
Ganin yadda ya kafeta da idanu ne ya sanya ta yi saurin sunkuyar da kanta k’asa
A hankali tace
“Ina wuni Ya Aslam”
Jin bai ce komai ba ne ya sanya ta d’ago kanta ta kalleshi sannan ta sake maimaita abinda ta fad’a da farko tare da d’an d’aga murya..
Sai da ya sake had’e rai
tukunna yace “lafiya”
Ba tare da ya kalleta ba!.
Arshaad, sam bai ji dad’in yadda Aslam d’in yayi mata ba!
Ganin kamar itama jikinta yayi sanyi ne kawai ya sanya yace
“Baby, bara mu tafi.
We have somewhere else to go.
Sai mun yi waya, ko?”.
“To”
Kawai tace, sannan ta d’an d’ago tana kallon Aslam tana mamakin kalar miskilanci da mugun hali irin nashi.
Ji yayi kamar ance ya kalleta
yana juyowa kuwa akai sa’a itanma shi take kallo dan
haka idanuwansu suka sark’e cikin na juna! Wanda sai a lokacin ne taga kwayar idanunsa…
Da sauri kawai ya juya
ba tare da yace komai ba!
Ya nufi inda ya fito ya bud’e ya shiga ya zauna ya jingina kamar d’azu ya mayar da idanunsa ya lumshe.
Ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e kafin yace
“Ki gaida Mama da Sakina.”
daganan ya bud’e motar ya shige.
Sai da taga wucewar motar
tukunna ta shige gida ranta duk ba dad’i......
A tsakar gida ta tarar da Sakina da Mama sun shimfid’a taburma dake yau garin akwai zafi da alamun hadari ne ke had’uwa.
Mama na kwance kanta akan pillow tana bacci
Sakina kuma tana zaune a gefenta tana yi mata firfita.
Jiki a mace Huda ta k’arasa inda suke ta zauna
sannan tace “Ya jikin nata??”.
A hankali Sakina tace
“Alhamdulillah.
Ni na d’auka ma zaki shigo da Ya Arshaad, na san idan shi yayi mata magana watak’il yayi convincing nata ta tafi asibiti..”
Ajiyar zuciya Hudan ta sauk’e kafin tace “Naso in fad’a mishi, sai kuma naga kamar yana sauri ne..
Sannan ya zo da wani Yayan shi mai fuskar shanu! Sai wani ciccin magani yake yi kamar ance mishi gasar dambe za’ayi…”
K’arar wayar Mama ne ya katse musu maganar tasu.
A hankali Mama ta bud’e idonta ta mik’e zaune sannan
tasa hannu ta lalumo wayar tata a k’asan pillow
Har kiran ya tsinke.
Dannawa tayi ta kalla screen d’in, da d’an mamaki ta d’an ware ido sai kuma ta mik’e da sauri tayi hanyar d’aki tana danna wayar.
“Hmmm”
Sakina wadda ta bita da kallo tace kafin tayi k’asa k’asa da murya tana cewa Hudan
wadda itama hanyar da Maman tabi take kallo
“Nifa na yiwa Ummu message na fad’a mata.”
Shiruuu, Hudan tayi
sai kuma tace
“Ai gara, dan nima daaa har na fara tunanin In kira Baaba Talatu..”
daga haka tayi shiru bata sake cewa komai ba.
Ganin da Sakina tayi kamar ta d’anyi zurfi a tunani ne ya sanya tace mata
“Tunanin me kike yi?”
Tayi maganar tana tsareta da dara daran idanuwanta.
Sai da ta cire mayafin abayar jikinta ta ajjiye a gefe ta jaa pillown da Mama ta tashi a kai ta kwanta rigingine sannan tace
“Ya Arshaad zasu sake komawa wajen su Kaka
this time around ba shi kad’ai ba har da parents d’inshi!
Maganar aure!!
D’azun na bashi, go ahead.”
Murmushi Sakina tayi kafin tace “To ai Alhamdulillah!
Damuwar me kuma kike yi tou?”
“I don’t know”
Shine abunda Hudan tace
sannan ta mik’e ta zauna tace
“Allah dai yasa ragowar danginsa ba irin halinsu d’aya da yayan nan nashi da suka zo tare ba ne, dan in dai dukkansu haka suke to Ina ruwa!
I hope kowa a gidan ya zama kamar Aaima kuma i just hope I did the right thing about
amincewar da nayi da zuwan nasu wajen Kaka.
…Thats all.”
“Kamar ya ‘you hope you did the right??’
Are u having second thoughts?”
Shine tambayar da Sakina tayi mata tana kallonta.
“No!
Kawai dai…
Maybe I’m nervous ne inaga
or something like that.
Kinga manta kawai…”
Ajiyar zuciya Sakina ta sauk’e kafin tace “Meye halin yayan nashi!”
Kai tsaye Huda tace
“Bashi da kirki!! kwata kwata, gaskiya.
Kinga yadda ya dinga had’e fuska kamar ta shanu.”
Dariya Sakina tayi, kafin tace
“Fuskar shanu kuma?
Mummunane?”.
Da sauri Huda tace
“Nooo!
Not at all…
Dan ni kam i don’t think ma na tab’a ganin mutum mai kyan shi! Tun da nake, wallahi.
Kinga hancinshi kuwa?
Idanunsa daya kalleni sai da na tsorata! Farare kall!!
Sannan kamar an zuba ruwa a ciki irin kad’an d’innan, har fa
wani haske k’asan idon yake yi
kamar irin ya saka kwallin haske....”
“Yafi Ya Arshaad kyau kenan?”
Sakina wadda ta kafeta da idanu tayi mata tambayar.
Hudan bata san lokacin da tace “Nesa ba kusa ba, sosai....”
Sai kuma tayi shiru ta kasa k’arasawa, ta koma ta kwanta tana kallon sama.
Ajiyar zuciya Sakina ta sauk’e
kafin tace “Hmm”
Daga nan ta d’auki wayarta wadda taji tana k’ara alamun shigowar sak’o, nan ta hau dubawa…
Murmushi tayi kafin tace
“Ya Arshaad ne!
Wai In tura account number d’in da zai turo mana kud’in ankon bikin Khadijah.”
Da sauri Huda ta mik’e ta fisge wayar ta hau duba sak’on kafin ta dago tace
“Sakina dan Allah kar ki tura masa!
Ya tambayeni nace mishi mun riga mun sayi komai har mun d’inka.
Sakina ta bud’e baki zata yi magana kenan k’amshin turaren Jalila wadda ta fito tana waya ya katseta…
Da sauri ta juya ta kalleta, suna had’a ido Jalilan da gangan aka ce “Baby gani nan zuwa”
Tayi maganar yadda ta tabbatar za suji, tukunna tasa kai ta fice daga gidan.
Tab’e baki Sakina tayi tace
“Ba zama fa! Duniya kowa sai ya san Jalila anyi waya anyi saurayi!”.
Hudan, wadda ko kallon inda take ma ita bata yi ba ce
tayi dariya sannan tace
“Kinji Sakina!
Dan Allah kar ki turawa ya Arshaad accnt no d’in.
Kinga halin da Mama take ciki
kar mu b’ata mata rai kin san ta hana bata so!
Wallahi har da son inga na kwantar mata da hankali yasa nace Ya Arshaad d’in ya tura parents d’in nashi wajensu Kaka, a samu ayi komai yadda take so. Ko a samu hankalinta ya d’an kwanta, dan ko bata fad’a ba na riga na san jininta ne ya hau!
Tunda kika ga tanata yawan ciwon kan nan.
Kin ji, Dan Allah.”
Hudan ta k’arashe maganar kamar zata yi kuka.
A hankali Sakina tace
“Okay sis, shikenan in sha Allah ba zan tura ba.
“Tnx” Huda tace mata.
Sannan suka ci gaba da hira.
Suna zaune kusan minti bakwai haka
Ummu da Sumayya suka yi sallama suka shigo…
Ummu na hada ido da Huda (wadda take k’ok’arin mik’ewa dan ta k’arasa wajenta tayi mata oyoyo) ta sauk’e ajiyar zuciya kafin tace
“Ai da na d’auka kece mai zance a cikin mota mai uban tint ta koina har gaba da baya!
Tunani nayi akan ‘in fara shigowa tukunna
in na tabbatar ke d’in ce, har cikin motar zan je in fincikoki a gaban Arshaad d’in.”
Dariya suka yi ita da Sakina sannan suka k’araso sukayi huggin d’inta sannan Sakina tace
“Ummu ai kema kin san ba kalar yanayin training d’in da kuka bamu ba kenan!
Ya Arshaad d’in shima bai dad’e da tafiya ba.
Wadda kuka gani a mota yanzu kuma zak’ak’ura Jalila ce da zak’ak’urin saurayinta!”.
Da sauri Ummu ta buge mata baki….
Ita wallahi inda ace ma ta san jalilace a motar da ba zata tsaya jin k’arashen zancen ba.
Ai kuwa abinda Ummun take gudu sai da ya faru!
Dan haka nan tashi d’aya sukaga Umma ta banko k’ofa ta fito kamar an cillota…
Nan ta hau zage zage har da su cewa
“Bak’in ciki ake yiwa y’arta saboda anga tayi saurayin da yafi na Hudan…
Ita Huda ai har makarantar kwana aka kaita saurayin ya dinga zagayawa amma babu wanda ya tab’a cewa uffan!
Sai ita yanzu dan anga Jalila tayi goshi!!”.
Sakina kamar ta had’iye zuciya ta mutu tsabar bak’in ciki dan
k’iri k’iri tanaji tana gani Ummu ta hanata magana ta kad’a su suka shige d’aki gaba d’ayansu
bayan ga amsoshin bak’ak’en maganganu barkatai a kanta!.
Hakanan suka wuce suka bar Umma kamar wata tab’abb’iya tanata faman zage zage…
Suna shiga suka ga Mama zaune a bakin gado
Fuskarta da idanuwanta sun yi jaa! Ga kuma ragowan hawayen da suke silalowa.
Ganin su ya sanya tayi saurin saka hannu ta share hawayenta a karo na ba adadi.
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
33
Da sauri Ummu ta k’arasa inda take ta hau tambayarta
“Mai ya faru??”.
A hankali Mama ta share hawayen da suka sake zubo mata sannan tace
“Bilkisu, barin garin nan zan yi!! Na gama deciding.
Ba zan iya ci gaba da zama ba.”
Ummu na shirin yin magana
Mama ta katse ta ta hanyar ci gaba da magana
“Duk tsawon shekarun nan da aka d’auka….ina hak’uri, ina rok’on Allah yasa su Hajiya su sauk’o daga fushin da suke yi da ni amman har yanzu ace sam babu chanji babu wani sassauci daga ita har Abba Madu??
Abun yana damuna ba kad’an ba!
Saboda Allah idan ni nayi mata laifi
Ita Hudan meye nata a ciki?.
Yanzu fa naga kiranta
ina bin kiran ta d’auka ko gaisuwata bata tsaya amsawaba tace
‘Wai taga Khadijah ta warewa Hudan da Sakina ankon su,
In tabbatar na hana Huda zuwa saboda ba zata iya yiwa mutane bayanin wacece ita ba!’.”
Kuka ne mai k’arfi ya kufcewa Mama, cikin kukan tace
“Saboda Allah sai kace wata shegiya?…
Shiyasa kawai na gama yanke shawara zan bar garin nan inaga zaman da nake yi a kusa da su ne ya sanya har yanzun bamu daidaita ba!
Watak’il idan muka d’anyi nesa da su abun zai yi sauk’i in basa ganinmu akai akai!
Kuma nima har ga Allah hankalina zai fi kwanciya..”
A hankali Ummu ta d’an juyar da kanta ta share hawayenta
kafin ta juyo ta cewa Mama
“Maganar ‘barin gari’ bata taso ba Mama
Ki tuna fa barin garin nan da kika yi a farko shi ya janyo komai in the first place!
Ki kwantar da hankalinki
duk abinda kika ga yayi zafi
tou zai yi sanyi da izinin Allah.
Kiyi hak’uri wata rana sai labari……”
Cikin tausasawa da lafazi masu tsuma zuciya Ummu tayi ta kwantar mata da hankali..
Sai da taga ta d’an yi sanyi
sannan tace
“Yanzu alfarma d’aya nake nema a wajen ki ‘ki tashi mu tafi asibiti dan Allah’.”
Shiruu, Mama tayi, chaan! Ta d’auki wayarta ta kira Baba..
Sai tayi mishi 3 misscalls tukunna a kira na hud’un ya amsa.
Bayan sun gaisa ne take ce mishi “tanaso zata je asibiti, Ummu zata rakata.”
Ba tare da ya tambayi mai yake damunta ba yace
“A dawo lafiya, kar kiyi dare!.”
Daga haka ya katse kiran.
Shiruu, tayi still da wayar a kunnenta bata cire ba..
….Jiya har amai tayi a gabanshi amman bai damu ya tambayi me yake damun ta ba!
Kuma wai a haka ne yake cewa ‘yana sonta’…
Dafa ta d’in da Ummu tayi, tana mai cewa “mai ya ce?”
ne, ya dawo da ita daga duniyar tunanin data tafi
“Ba komai”
Kawai ta iya cewa sannan cewa Ummu “ta mik’o mata hijabinta a wajen kayanta”
daganan suka fito tsakar gidan...
Jikin Huda ba k’aramin sanyi ya sake yi ba dan kasa zama ma tayi a d’akin! Tun lokacin da taji bayanin Mama akan abunda Hajiya Shuwa tace ta juya ta fita, daga d’akin gaba d’aya! Sakina da Sumayya ma suka bi bayanta..
Kamar yadda ta shawo kan Mama da kyar haka nan itama Sakina tayi fama da Huda
dan da farko itanma cewa tayi ‘guduwar zata yi!’ Wai “tunda Mama ta haifeta bata huta ba har yau!
Maybe idan bata nan Maman ta samu sauk’in wasu abubuwan…
Ta gaji da ganinta cikin tashin hankali kullum.”
Sai da Sakina ta bud’e mata wuta daga baya ta dawo lallashinta tukunna ta saduda.
A gida suka bar su Sakina
Ita da ummu suka tafi asibitin
basu dawo ba sai wajajen k’arfe 10:00pm dan sai da aka k’ara mata ruwa
Jikinta yayi weak sannan jininta ya hau..
Da kyar ma asibitin suka barta ta taho gida da ragowar drip ukun da bata gama shanyewa ba bayan Ummu tayi musu bayanin ‘akwai wata nurse mai chemist a bayan layin su da zata na chanja mata (drip d’in) sannan zuwa gobe da yamma in shaa Allah za su dawo’.
Kamar kullum yau ma Ummu ce ta biya bill..
Kusan a tare Adaidaita sahunsu suka tsaya a k’ofar gidan da motar Auwal.
Sam Jalila bata lura da su Mama ba, da yake duk a rud’e take kuma tayi dare tsoronta kar taje Baba ya dawo ya nemeta bai ganta ba! Dan
bata san lokaci ya tafi haka ba
Sai ta kalli wayarta yanzun tukunna ta gani..
Shiyasa ta zo ta wuce su tanata sauri nik’i nik’o da ledoji ta shige gidan.
Kallonta Ummu tayi sannan ta kalli motar kafin tace
“Allah ya kyauta!”
Daga nan taci gaba da k’ok’arin taimakawa Mama ta samu da sauk’o daga napep d’in saboda har yanzu jikin nata babu kwari.
Suna shiga suka tarar Sumayya tayi bacci
Sakina da Huda kuma idonsu biyu sun yi tsuru tsuru da alamun hankalinsu ba a kwance yake ba dukda kuwa sun kira tace musu jikin nata da sauki....
A hanzarce bayan Ummu ta samu Mama ta kwanta ta cewa Sakina
“Maza ta tashi Sumayya Babansu yayi mata waya ya kusan k’arasowa, su samu su wuce.”
Kalar tausayi Sakina tayi kafin tace “Ummu dan Allah ki barni mana.
Kinga Mama bata da lafiya..
Itama Huda ba zata ji dad’in zaman haka ba.”
Nan itama Hudan ta saka baki suka hau rok’ar Ummu..
Shiruu, Ummu tayi
kafin tace “to muje ki yiwa Babanku bayani..
Gashi nan ma na san shi yake kirana.”
Tayi maganar tana d’aukar wayar ta kara a kunnenta..
Hakan kuwa akayi
Allah ya taimaka ya barta.
Sai da Ummu ta je ta samu mai chemist d’in tabbatar mata ‘gobe da safen dan Allah taje ta sauyawa Mama drip d’in kafin ta k’araso’ tukunna suka wuce ita da Baban Sakina da Sumayya........
Jalila tana shiga d’akin taga duhu, dan haka ta zaro wayarta ta d’an haska…
Ga mamakinta sai taga Umma kwance tana ta sharb’ar barcinta!.
Ajiyar zuciya ta sauk’e
kafin tace “Barka na, gobe idan ta tambaya sai ince da wuri na dawo..”
Sad’af!!sad’af!! Ta wuce ta ajjiye ledojin ta fara k’ok’arin kashe wayar gudun kar Umma ta farka tana yi tana d’an kallonta.
Sai dai kuma bata kai ga kashe wayartata ba taga Umman ta bud’e idanunta.
Nan take ta diririce ta hau kame kame “Au um Umma k kin farka? Na d’auka kin yi bacci mai nisa ne.”
“Zo nan Jalila”
Shine abunda Umman tace
tana mai mik’ewa ta zauna a kan gadon.
A hankali ta k’arasa kusa da ita ta zauna.
Kallonta Umman tayi ta sauk’e ajiyar zuciya kafin tace
“Jalila, amma kin dai san halin Babanku ko?
Ga waennan munafukan y’an bak’in ciki suma har sun fara k’ananun maganganu..
Nan gaba idan kin san za ki dad’e ki dinga fad’amin sai inyi k’aryar ‘nice na aikeki’ ko kuma ince kin yi bacci tuntuni.
Allah ne yau ya taimake mu lokacin da Baban naku ya dawo bai nemeki ba! Na san da sai mun gane kuranmu daga ni har ke
dan na san kowa sai yaji kanmu da shi, gashi gida ba mu kad’ai ba cike da y’an bak’in ciiki…
Da kyar ma na lallab’a na bud’e miki k’ofa bayan naji ya shiga wanka
Amman da har ya rufe.”
“To Umman mu, in shaa Allah.”
Shine abunda Jalila tace, had’e da sauk’e ajiyar zuciya dan
Ita har ga Allah tayi tunanin Umman zata yi mata fad’an da yafi wannan..
Umman har ta koma zata kwanta idanunta suka kai kan manyan ledojin da Jalilan ta shigo da su!
Dan haka ta mik’e.
Kallonta tayi sannan ta mayar da idanunta kan ledojin kafin tace “Ke kika shigo da su?”
Mik’ewa Jalilan tayi ta nufi inda ta ajjiye ledojin ta d’auko sannan tace “Eh,
shopping muka je
shiyasa ma muka yi daren.”
Tana fad’i hakan tana mai k’arasowa ta ajjiye ledojin a gaban ta.
Sauk’owa Umman tayi ta hau bubbud’ewa tana cewa
“Nifa daman k’amshin ne ma ya farkar da ni
Da farko mafarki na fara yi ‘inacin kaji’ sai kuma
na fara jiyo k’amshi a hankali a hankali harya zo yayi mini yawa…
Ashe d’an kirki ne ya had’o ko da su…”
Tana maganar tana bud’e ledojin one by one..
Ledar farko
Fresh milk ne masu sanyi
da chocolate masu mugun tsada da ice cream da popsicles birjik!
D’ayar ledar kuma kaji ne
an yayyanka ledarsu daban
sai k’aramin pizza da su shawarma da burger.
Ledar ice cream d’in Umma ta sake dubawa dan d’azu kamar taji wani abun a ciki bayan abunda idanunta suka gani,
ai kuwa nan ta zaro kud’i!
Tun kafin tace wani abun Jalilan tace
“Ni kinga ban ma san ya saka ba.”
Jinjina kai Umman tayi kafin tace “Hmm, Jalila ina hango waenda za a kwantar a emergency ranar aurenki!”
Tana magana tana juya kud’in.
Rabawa tayi biyu, ta d’auki rabi ta bata rabi..
Jalila kwata kwata hankalinta ba a gurin yake ba sannan
jikinta duk yayi sanyi shiyasa
ma bata wani damu ba, tasa hannu kawai ta karb’a
tana kallon Umma wadda ta mik’e taje ta ajjiye kud’in ta dawo ta zauna tana cewa
“Ai gobe mai kankat! Zan cewa malan Yusuf yayi mishi..
Yarinya burin mu ya kusan cika,
Allah ya kashe ya bamu.”
Daga nan ta janyo ledar kaji ta hau ci sannan ta b’alle marfin fresh milk tana ci tana korawa
da shi…
Daman yau bata wani ci tuwon dare ba dan har ga Allah tuwo ya ginsheta wallahi ko sunanshi bata so taji an kira.
Sai da Umma taci kusan rabi, ta shanye fresh milk roba d’aya, tayi gyatsa!! Tukunna ta juyo ta kalli Jalila wadda kwata kwata hankalinta baya d’akin kana ganinta ka san tunani take yi, ta k’urawa waje d’aya ido kawai tanata kallo!.
Magana Umma tayi mata taga bata kulata ba, kamar ma bata jita ba! Dan haka
ta kama k’afarta ta jijjiga
sannan da k’arfi tace
“Ke!!”
Firgigit! Jalila tayi ta juyo tana kallonta, itama Umman ita take kallo tana sake nazartarta kafin tace “Tunanin me kike yi haka??”
Ajiyar zuciya Jalila ta sauk’e
sannan tace “Umma nifa Auwal d’innan na kasa gane kanshi!
A iya fahimta ta fa kamar yana tunanin ni budurwar Arshaad ce.
Sannan Umma, kwata kwata zuwanshi na biyu kenan amman na fahimci d’an iska ne! Kinga ranar farko rike min hannu kawai yayi ko?
Amman, wallahi idan
na fad’a miki abubuwan da yayi mini yau ke kanki sai kince ‘kar in sake kulashi’.”
Kallonta Umman ta hauyi irin kallon k’urillar nan!
Kafin ta ajjiye robar hannunta tace “Kuma na ganki Garau!!”
Cike da rashin fahimta Jalila take kallonta…
Fahimtar hakan (Jalilan bata fahimce ta ba) da Umman tayi ne yasa tace “Hmm”
Kawai. Sai kuma ta sake cewa
“me yayi miki?”
Kame kame ta hau yi kafin tace
“Har da rungumeni yayi, sannan ya dinga.......”
Sai kuma tayi shiru.
Tsaki Umman tayi
sannan tace
“Iyaka wannan ne Ina??
Jalila naga alamar bakida labarin ‘Hudan! Ita har makarantar kwana aka fake da kaita.’ Ni na haifeki, inaso ki fahimci ba zan tab’a cutar da ke ba!
Yanzu duniyarnan ta chanza!
Kuma Yaron nan burinmu a kansa ‘aure’
Allah na tuba ko me ma yayi miki ai dai shi d’in ne zai aurenki a k’arshe ko?
Yanzu abinda nake so dake
‘Ki bishi a hankali kawai! Gudun kar ya sub’uce mana’
Ki bishi kawai a duk yadda yace!
Ki barni da shi, ni na san me zan yi.”
A hankali Jalilan tace
“Umma to ba yadda wai za ayi In auri Ya Arshaad? dole sai wannan?
Nifa shi nake so!”.
Cikin fad’e Umma tace
“Jalila wallahi zan ci buhun uban ki daga ke har Arshaad d’in!
Nace miki ki hak’ura da shi ko?
Ga hanya nan mafi sauk’i amman kin gagara fahimta?
Da me Arshaad d’in yafi wanann??.
Cikin katseta Jalila tace
“Umma shine a zuciyata da haka kawai ya fishi...”
Buge mata baki Umman tayi
kafin tace “Bara kiji in fito miki a mutum!!
Wallahi ba zan iya kokawar bin Malamai da masu kud’i ba!
Ba zai yiu inje in bada dubu talatin mai kud’i ya zo ya ajjiye dubu d’ari ko d’ari biyu sannan kiyi tunanin za ai mana aiki iri d’aya ba!
A nawa tunanin fa kenan, bansan ya naki yake a k’aramar kwakwalwarki ba.
Ki cire wata soyayya a ranki…
A zamanin mu ne muka bi soyayya, kuma gashi muna cin ubanmu!
Gata nake yi miki Jalila ki bari
mu nutsu waje d’aya mu yi abinda zai yiu, kar ki je kiyi saki reshe kama ganye!
Na dai fad’a miki.”
Tana gama fad’in haka ta mik’e tace mata
“Asubah ta gari
Bara in je
ki saki net dan yau akwai sauro .”
Daganan ta fice ta nufi d’akin Baba.
Jalila ta dad’e tana tufka da warwara daga k’arshe ta yankee shawarar tabi zab’in Umma!
Haka nan ta hak’ura da Arshaad ba dan zuciyarta tana so ba.
Ta zo kwanciya kenan kiran Auwal ya shigo wayarta!
Tana gani har ta tsinke bata d’auka ba!
Tabbas duk tsaurin idonta da rashin kunyarta yau ta had’u da kakanta!
Kuma kalli ba kunya ba tsoron Allah kiranta ma yake yi
Ita kam kafin ta samu ta sake iya had’a ido da shi ma
ai sai nan da kwana biyu ko uku ma..
Miss call d’aya ta samu daga gareshi daga nan bai sake kira ba!
Dan ba zai tsaya kuchaka kamar ta tana ja mishi aji ba!
Although ya san a d’an rikice take har yanzu wanda hakan ne ma ya sake tabbatar mishi da ‘Yarinyar sabon hannu ce!’
Ko banza ya san zai tsinci dami akala!
Amman dukda haka
zai yi sauri ne kawai yayi abunda zai yi ya gama ya kuma gano dalilin alak’arta da Arshaad daga nan ya had’a mishi bomb d’in da yaga ya dace dashi! Ita kuma ya wurga ta a dustbin! Tun kafin wani a cikin Abokanayen sa ya gano yana kula mace irinta…
Although, she’s beautiful,
tabbas tanada kyau, ta fanni daban daban wanda hakan ne
ma ya sanya ya d’an sake janta a jiki amman dai still ba zai bari Abokanayensa su ga yana kula a girl
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 28 Chapter of 32