sunk’i gaya mata ne ,
.......Amman Abba Mahaifin shi ya tura shi honeymoon da amaryar sa Uk kuma ya tula mishi uban aiki!!
Bayan haka yace mishi sai nan da a k’alla shekara tukunna yakeso ya dawo, yayi magana mahaifinshi yace idan ya kuma yi mishi musu, sai sunyi shekara goma tukunna zasu dawo kamar yadda yayi da Maryam.
Sarai ya san me Granpa d’in yake son yi ‘so yake ya had’a shi fad’a da ita ta k’arfin tsiya’
Tunda ya san ko zuciyar gold gareta idan taji zancen tafiyar sai ta d’aga hankalinta.
Shiyasa ranar ya zo har kuka yayi a gaban Baba Bashir yace mishi kuma ya cewa Maryam tazo su sake guduwa tace babu inda zata tafi tabar su Shuwa suna fushi da ita.
Yana ganin kawai b’oye mata zancen tafiyar zai yi inyaso sai yayi k’ok’ari ya dinga zuwa duk bayan wata d’aya koda a b’oye ne, saboda baya so ta d’aga hankalinta ko tasa wani tunanin a ranta saboda daga haka ne Granpa zai yi nasara a kansu.
Gaba d’aya In ka ganshi hankalinshi a tashe yake
Baba Bashir ne yayi ta bashi baki, dakyar ya lallab’asa ya tafi yace zai yiwa Maryam d’in bayani, in ta d’an samu nutsuwa.
Saboda shi a ganinshi bai kamata a b’oye mata ba........
Baba Talatu tana cikin wannan tunanin suka k’araso gida.
Jikinta duk a mace dan har Maryam d’in saida ta lura da hakan.
Suna isowa d’aki ta d’au waya ta fara neman layin Abba, duk fushin da take yi dashi na k’in zuwa ya washe.
Ta gwada yafi sau nawa amman not reachable, hakanan ba yadda ta iya ba dan ranta yaso ba ta hak’ura.
Tun daga ranar ba Abba ba labarinshi tun tana b’oyewa har ta kasa, dan in ka ganta sai ka tausaya mata ga tsohon ciki har wata Takwas!! Amma duk wannan halin da take a ciki bai sa Shuwa ko Madu sun sauk’o daga fushin da suke yi da itaba, ko gidan Baba Bashir Shuwa ta daina shiga tayi saboda ita.
Bilkisu kam in zata zo wajenta sai dai tazo a b’oye!
Bilkisun ce ma take d’an kwantar mata da hankali,
duk abunda ya same su bayan ta bar gidan sai da ta fad’a mata har rashin lafiyar Madu da Ya Usman da rasuwar Malan da Inna….
Maryam kuwa taji ba dad’i daga jin labarin, tabbas dole kam suyi fushi da ita.
Amman rashin sanin ranar sauk’owarsu shike daganan mata hankali, ga Abba ya d’auke k’afa!! Wayarshi kuma bata tafiya.
Tsabar yadda ta d’aga hankalinta ne ya sanya lokacin haihuwanta bai yi ba amma ta fara labour gadan gadan!! Ga jininta yayi mugun hawa nan da nan duk ta kumbura ta fita a haiyyacinta…ganin ba zata iya haihuwa da kanta bane yasanya Likitocin yanke shawarar yi mata ‘C S’.
Babu irin kalar rok’on da Baaba Talatu bata yiwa Shuwa ba akan taje ta dubo Maryam kafin ayi aikin amman k’iri k’iri tak’i zuwa.
Haka aka shiga da Maryam aka yi mata aikin…
Ma sha Allah! It was successful, an ciro mata Baby girl k’atuwa mai kama da Mahaifinta sak!!! Tun a jinjirarta yana yin idanunta da eyebrows dinta na Mahaifinta ne exactly!! Shiyasa in dai ka san Abba to kuwa kana d’aukarta zaka san y’arsa ce.
Ranar Maryam taci kukan farin ciki, da kuma na tunanin mai yasa Abba zai yi mata haka a lokacin da tafi buk’atar shi?!..
Ya sha fad’a mata bashi da buri a rayuwarnan wanda ya wuce yaga babynsu shi da ita, abunda suka riga suka cire rai dashi gashi yau Allah ya azurtasu dashi….
Don haka ta cewa Bilkisu “ta nemo mata biro da takarda!! Idan wayarsa baya tafiya ai akwai letter.”
Haka kuwa akayi ta rubuta mishi cewa “ta haihu sun samu baby girl…
Tare da sunan asibitin da take.”
A lokacin ko sunan MT
Idan ka kira a garin Kano babu wanda bai sansu ba. Shiyasa ta bawa Bilkisu tace “taje k’ofar estate d’insu ta nemi alfarmar ganin Daniel daga nan tace masa ya had’ata da Abba Tana son ganin shi ko da na minti uku ne.”
A b’oye Bilkisu ta tafi, dukda itama a lokacin tsohon ciki gareta har na wata bakwai.
Ta kusan 2 hours tukunna ta dawo duk da cewa gidan babu wani nisa tsakaninsu.
Sai da su Baaba Laraba da Sadiya waenda suka zo ganin Baby suka tafi tukunna Bilkisun ta mik’a mata takardar da ta dawo da ita.
Da sauri Maryam ta karb’a ta fara karantawa..
Kafin ta k’arasa tuni fuskarta ta jik’e sharkaf da gumi da hawaye. Idanunta jazir!! Ta d’ago ta kalli Bilkisu dashi wadda itama ta lek’o tana duba rubutun cikin takardar!
Kai kana ganinsu ka san hankalinsu a tashe yake matuk’a!!.
Maryam tana so ta k’aryata amman ko a mafarki idan taga rubutun Abba sai ta gane
…….Naji kin haihu, congratulations to you a lone Maryam.
I choose to obey my Dad.
Ki reni Yarinyarki ke d’aya!
Don’t ever tell her my name..
Akwai sak’on da na bawa Madu ya baki wanda daga dukkannin alamu bai kai ga isowa gareki ba.!………….
Ta karanta sak’on nan ta kuma maimaitawa yafi so babu adadi, so take yi kawai ta gano ta inda zata ce wannan ba rubutun Abba bane ba.
Jikinta ba kwari da kyar ma take iya wasu abubuwan
amman haka ta fara k’ok’arin tashi, tace “wajen Madu zata je yau ko zai yankata zata je wajensa ta karb’i sak’on da Abba ya bayar yace a bata!! She needs some elaborations.”
Bilkisu ce take kokarin hanata tana cewa “Likita fa yace kar ta d’ago kanta karta zauna…”
Amma sam Maryam bama ta jinta….
Suna a haka Baaba Taraba da Baba Bashir da Madu suka shigo..
Tana ganinsu ta fashe da kuka abin tausayi.
Baabaa Talatu ce ta karb’i takardar hannunta ta karanta.
Ajiyar zuciya kawai ta sauk’e sannan ta mik’awa su Baba Bashir..
Bayan sun gama karantawa suma da d’an kokwanto akan fuskar su amman kawai sai suka share.
Baba Bashir ne ya fara magana, yace “Daman akwai maganar da muke so muzo muyi dake to gashi shi Abban ma ya riga ya fara fad’a miki.”
Takarda ya mik’o mata, ta sanya hannu ta karb’a kafin ta bud’e takardar Baba Bashir yace “Maryam duk abinda kikaga ya samu bawa to muk’addari ne daga Ubangiji.
Shekaran jiya da kika fara labour munje mun samu Mahaifin Mijin ki dashi kanshi Mijin naki wanda ya dawo daga tafiya, akan batun haihuwarki dan mun lura ma kamar bai ma san kina d’auke da ciki ba! Da muka je da farko mai gadi ne ya hanamu shiga
Sai da muka lallab’ashi tukunna ya kira wani Yaro da kayan sojoji ya nuna mishi mu
yace mu fad’a mishi me ke tafe da mu!
Hakanan, muka bashi sak’on muka ce yaje yace ‘iyayen maryam ne suka zo tana asibiti zata haihu, ana buk’atar jini kuma ana buk’atar Abba a wajen saboda wasu y’an cike cike.’
Munfi awa biyu a wajen a tsaye, daga k’arshe ko harabar gidan ba’a barmu mun shiga ba
Abba da Mahaifin shi suka fito.
Ko gaisuwar kirki bai bari mun yi ba, a take kawai Abba ya mik’o mana wannan takardar
yace ‘gashi dan Allah mu yi hak’uri, mu baki’.
Mahaifinshi bai bari sun koma cikin gida ba sai da ya tabbatar Abban ya fad’a mana abunda yake cikin takardar da bakinshi tukunna suka juya suka barmu a wajen.
Tsabar yadda jikin mu yayi sanyi munfi minti goma a tsaye a wajen tukunnan muka juya da nufin zuwa inda mukayi parking da niyyar tafiya amma
bamu kai ga shiga motocinmu ba mutumin nan ya sa aka sakar mana mahaukatan karnukan estate d’in nasa wai saboda mun dad’e mun tsaya masa a bakin estate bamu tafi da wuri ba!!! Tsabar wulakanci!.
Gudun ceton ran da muka hau yi ne ya sanya muka bar motocinmu a wajen sai da daddare tukunna Usman da Abokinshi suka je suka kwaso mana…
Maryam Dan Allah ki ha’ura da Yaron nan, wannan itace kawai alfarmar da nake nema ki yi mini.
Kalli nan gefen cinyata cizon kare ne! Maryam duk surukin da zai yi maka haka ba sirikin arzik’i baneba ba sirikin da za a so a ci gaba da rayuwa dashi da zuri’ar sa baneba…
Ki kyale mishi d’ansa, dan Allah .”
Ita dai Maryam, zuwa wanna lokacin ta daina ji ta daina gani
tun daga lokacin da Allah ya bata ikon karanta takardar ‘saki d’ayan’ da Abba yayi mata .....…..
BULAMA ✍️
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.
Visit > https://www.aihausanovels.com.ng
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.
Email > aihausabooks@gmail.com
******* FOLLOW US ******
Facebook: Ai Hausa Novels
Twitter: Ai Hausa Novels
Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels
WhatsApp Number: 08138873799
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************
So da Buri
Free Book
20
Kamar yadda Baba Bashir ya rok’eta akan ‘ta rabu da Abba’
hakan take k’ok’arin yi.
Dan ko da ace bai fad’a ba tabbas ba zata sake bi ta kan Abba ba, tayiwa kanta wannan alk’awarin! Ya ga soyayyar ta yanzu kuma zaiga fushinta
In sha Allah ko shine autan maza ta hak’ura da shi.
Abu d’aya ne wanda Maryam tayi domin Abba shine ‘sakawa y’arta suna Huda’ da tayi saboda shi, dan tun lokacin da take boarding school indai suna hira yakance “Idan Allah ya basa y’a mace zai saka mata suna ’Huda’ saboda yana matuk’ar son sunan, idan
kuma Namiji ne zai saka mishi ‘Aslam’. Zai barta ta zab’i duk sunan da take so a duniyar nan
amman lak’abin ya zama Huda ko Aslam.”
Da matar Yayanshi ta haifa mai sunanshi shiyasa ta zab’i lak’abin ‘Aslam’ yanzu kuma ta sakama Yarinyarta suna Maryam ana kiranta da Huda ba dan komai ba sai dan kawai
tasan ba a tab’a chanjawa tuwo suna….tanaso wannan ya zama last abu da zatayi mishi
a matsayin sa na Mahaifin Hudan..
Bayaga haka! Duk wasu memories na Abba k’ok’ari kawai take yi ta goge su, ta samu ta ciresa gaba d’aya daga kanta har abada….
A lokacin data dawo Sadiya shiri take yi da ita sosai,musamman ma data lura da yadda y’ay’anta suke son Maryam d’in da Bilkisu, idan zata tafi yawonta haka nan zata kwaso su ta kawowa Maryam d’in suyita wasa suna d’ebe mata kewa….dama ita Maryam tana da son Yara sosai suma suna sonta, musamman ma Jalila wadda a lokacin da Maryam ta dawo shekararta 1 yanzu kuma tana shirin rufe biyu..
Har sati Jalila takanyi a wajen Maryam, sunanta ta fara kira a duniya kafin ma na Mahaifiyarta! Tun tana ce mata ‘miya’ har ta fara ce mata ‘mama miya’ daga baya ta koma ce mata ‘Mama’ kawai.
Shak’uwa ce sosai ke a tsakaninsu, ana yayeta kuwa Maryam dukda a lokacin tsohon ciki gareta, haka Jalila ta dawo wajenta dan tak’i yarda da kowa sai Maryam d’in……
Yanzu kuwa da Sadiya taga auren Maryam ya mutu!! gashi ko idda babu a kanta, tun daga lokacin taje ta d’auke Jalila, su Junaidu suma ta hana su kula Maryam d’in sai dai suyi a b’oye.
Tashi d’aya Jalila duk ta bi ta rame kullum cikin kuka take tana cewa “ita wajen Mama zata tafi amman furr!! Sadiya ta hana. Dan zuwa wannan lokacin ko gidan taje ba kula Maryam take yi ba sai dai idan ita Maryam d’in ce ta kulata
tukunna za ta amsa da kyar
shima kuma ciki ciki take amsata ba tare da ta kalli ko inda take ba! Idan kuwa iyaka su biyu ne a guri tofa in Maryam zatayi mata magana sau goma ba zata kulata ba!
Duk akan Mijin da bata saniba shi tun lokacin da Maryam ta dawo yake ta addua Allah ya bashi ikon raba aurenta da Abba!
Ranar kuwa da Abba ya saki Maryam a gaban shi suna gama gudun famfalak’in karnuka bayan sun dawo gida
ya cewa su Madu idan ta fita idda shi har yanzu yana sonta!
Ranar da ta haihu kuwa shi so yayi ma a d’aura musu aure a ranar! Sai da su Baaba Talatu suka yi masa da gaske! Tunkunna ya hak’ura.
To yanzunma ya sake tada balli
Hakan yasa kawai su Madu suka yanke shawarar d’aura musu aure amman Baba Bashir yace “zai fara tambayar Maryam d’in tukunna, tunda ita yanzu bazawara ce basu da hurumin zab’a mata Miji.”
Shi dai Madu bai biye Baba Bashir d’in ba ya tashi ya fita yana mai ce masa “idan yayi fixing date ya fad’a masa zai bayar a sanar a masallaci!dan shi kam ya gama zab’awa Maryam Usman.”
A b’angaren Maryam kuwa duk yadda ta kai ga k’in Ya Usman bata isa tace ‘a’a’ ba a gaban Mahaifin shi wanda yayi mata gata!….Bai duba yadda ta gudu ta sanya d’anshi a garariba haka ya rik’eta kamar komai bai faru ba!
Shiyasa yana zuwa mata da maganar tashi d’aya ta amince nan take.
A cikin sati d’aya aka gama komai aka d’aura auren
Usman Bashir
Da
Maryam Muhammad Madu akan sadaki naira dubu ashirin lakadan ba ajalan ba.
Murna a wajen Ya Usman a wannan rana abun har sai da ya bawa wasu mamaki!!!
Sadiya kuwa daman b’oye musu auren akayi….
Ranar taje wajen Baba Laraba suna hira kawai taji ana d’aura aure a masallaci, tun a lokaci ta fara hauka kamar tab’abb’iya! Tana cewa “Maryam taci amanarta, dan haka wallahi sai ta koya mata hankali!.”
Tun lokacin take hauka kwata kwata ya ma k’i ta saurari kowa, babu yadda Baaba Laraba bata yi akan ta tsaya ta nutsu ba amman tak’i! Ko y’ar
kissar nan ma ta mata ita kam ta kasa kwatantawa.
Tsautasayi ya kaita bayan an kai Maryam ta shiga har d’aki kafin Ya Yaman ya shigo, wai sai ta yi mata duka!!
Ita kuwa Maryam ta tare ta!
Dambe suka fara gadan gadan
dai dai Ya Usman yana turo k’ofa ita kuma Sadiya tayi sa’ar kifawa Maryam mari a kan idanunsa!
A zuciye ya k’araso, sai da yayi mata Mari kwarara guda uku!! sannan ya k’ara mata da saki biyu daman ya tab’a yi mata d’aya!.
Hankali a tashe! Sadiya ta fara bashi hak’uri, ita kanta Maryam d’in ta tsorata dan bata yi tunanin wannan hukuncin a Sadiya
daga wajen Ya Usman ba duba da Yaran dake a tsakaninsu.
Ganin da Sadiya tayi ba zai saurareta ba yasa ta mik’e ta zari mayafi ta nufi wajen su Madu…
Duk inda aka bi aka duba babu aure a tsakaninsu! Idan ma zata koma to sai tayi wani auren, kuma da sharad’in ba na kisan wuta ba.
Tana gama idda wani gurgu ya fito mata.
A nan bayan layin su Amaryar sa take amman shi yana Sumaila da Matan sa biyu.
Bata wani damuba ta amince bayan ta fito k’iri k’iri ta gaya mishi auren kisan wuta take so suyi shi kuma ya amince.
A lokacin nuna mata yayi ya amince aka yi shirin komai, ranar da aka d’aura aure iyayenshi suka zo suka tafi da ita sumaila, bayan da farko ce mata yayi a kano zata xauna
dan kayan d’akinta ma d’akin daya nuna gefen na Amaryarshi a nan aka jera mata.
Haka nan ta tafi Sumaila ta bar kowa nata daga ita sai Jalila suka tafi.
Bayan sati biyu ya zo da kansa ya kwashe kayan jeren ta aka kai mata Sumaila aka jera wasu, dan kusan rabin kayan karshe sai siyarwa tayi saboda ba zasu shiga d’akin ba.
Sadiya bata tashi sanin Garbati yaudararta yayi ba sai ranar daya fito mata a mutum yace mata “shi fa ba zai saketa ba!”
Jalila ma data taho da ita cewa yayi “ba zai rikeba” haka nan tanaji tana gani aka karb’e Jalila aka dawo da ita gidan Babanta wajen Maryam bayan shi ga nasa y’ay’an guda goma sha takwas kuma duk ranar girkinta sai ta girka musu abinci ta basu…
Sadiya taci kuka ranar da aka karb’e Jalila kamar ranta zai fita! Ita kuwa Jalila murna ma ta dinga yi ta dawo wajen Maman ta.
Maryam duk wani kulawa haka ta had’a Yaran nan guda hud’u take basu kamar ita ta haifesu duka….Jalila ta taso da k’aunar Huda a ranta dan babu wadda takeso kamar Huda! Abu kad’an ‘k’anwata’ komai ita dai k’anwarta, ko abu taci a makaranta sai ta rago ta kawowa k’anwarta.
Lokacin da aka saka Huda a makaranta kuwa taga gata wajen Jalila da Junaidu wanda tun a lokacin Junaidun yake cewa “shi kam inama ana auran k’anwa to da zai auri k’anwarsu Huda” Gata kala kala ba wanda baya nuna mata, ita ma Jalila yadda take ji da Huda kamar tsoka d’aya a miya! In ka tab’a Huda to ko d’an gidan uban waye kai sai taje har d’akin uwarka da jibgeka…dan one thing about Jalila bata da kunya kuma bata da tsoro ko kad’an! Dan ma Mama tana taka mata burki.
Ya Jaafar ne kawai baya shiga harkar Hudan sosai, saboda shi daman chan akwai shi da son girma kuma miskiline na ajin k’arshe. Shekarunsa suna d’an yin sama ya daina yi musu dariya ma kwata kwata, ko
hira akeyi haka nan shi sai dai ya shige d’aki.
Shiru shirun sa ya fara damun Mama dan haka ta saka mishi ido, ai kuwa nan ta gano ashe yawan baccin da yake yi shaye shaye yake yi tuk’uru.
Hankalin Mama ba k’aramin tashi yayi ba dan a lokacin kwata kwata shekarun Jaafar 15 kuma koma ba dan ta shekarun ba shaye shaye ba abu bane mai kyau. Shiyasa ta dage ta tsaya tsayin daka da addua da komai da kyar aka samu ya shiryu ya daina.
Tsakanin Maryam da Ya Usman kuwa! Soyayyar sati uku kawai ya nuna mata bayan aure daganan ya birkice ta kasa gane kansa…
Haka kurum sai ya tisa ta a gaba wai sai ta fad’a mishi wa tafi so tsakanin shi da Abba!
Wasu lokutan a rana d’aya sai ya buka’ceta sau hud’u idan ya ga dama ko sama da haka a cewarsa ‘sai yayi wanda yafi na Abba yawa!’
Gaba d’aya waensu irin abubuwa yake yi marasa ma‘ana wanda sam ta kasa gane kanshi kwata kwata.
Tabbas Ya Usman yana sonta ta yarda da hakan amma wasu lokutan har hanata abinci yake yi wai yana so ta ji yadda yaji a lokacin data gudu ta barshi dan a wannan lokacin har kwana hud’u ya sha yi bai ci abinci ba…..
Hanyar gidansu Abba kuwa ko waye ata arean bata isa ta bi ta je ba, ko dubiya ne ko kasuwa taje in dai yaji labarin sun wuce ta hanyar gidansu Abba to sai tayi sati tana shan azaba a hannunsa. Babu abinda ya fi sosa mata rai kamar yadda Ya Usman yake nunuwa k’iri k’iri kaff a fad’in duniyar nan babu wadda ya tsana sama da Huda!
Haka kurum sai yayi ta kyarar ta yana hantarar ta, wani lokacin har duka!
Tun Hudan bata gane ba har ta gane, dan sai da ya zamana ko
muryarshi ne idan taji da gudu haka zata shige d’aki….
Hakan ya sanya hatta Jalila da Junaidu da suka fahimta suma sai daina kula shi,har sai da Maman ta gane ta bud’e musu ido tace “basu isa gaba da Mahaifinsu ba”, tukunnan
ba yadda suka iya suka sak’k’o amma idan yana yiwa Huda abu wani lokacin har kuka suke yi.
Lamarin Ya Usman ya kai idan gida akwai mai suna Abba to zai hana Maryam mu’amala da y’an gidan kwata kwata!
A cewarsa wai ‘da gangan take zuwa gidan saboda idan an kira sunan Abba ta dinga tuna Abba…’
Abubuwa kala kala dai…tun abin yana damunta har ta hak’ura ta rungumi y’ay’anta ta yaye lamarin shi a kanta.
A b’angaren Sadiya kuwa sai da tayi shekara 9 tana shan azaba a hannun Garbati, k’arshe ma rufe mata baki yayi ita da iyayenta suka daina neman saki a wajenshi, Allah ma ya taimaki Sadiyan bata yarda ta haihu a gidanshi ba saboda dama tace ‘bata ga guri ba!’.
Su Jalila sukan je su dubata su kai mata kayan abinci da zannuwa, da farko da Maryam suka fara zuwa amman tun zuwan farko da ta saka Yara suka yi mata ihu shikenan Ya Usman da yaji labari ya hanata zuwa kwata kwata.
Sai da zama ya Kare tukunna Allah ya karb’i ran Garbati a hanyar shi ta zuwa Niger (minna) ganin Mahaifiyarsa….
Yaranshi ne kad’ai suka yi kukan rashinsa amman matan sa da y’an unguwa har ga Allah murna suka yi domin kuwa kai tsaye zaka kira Garbati da mai mugun hali gashi duk wani hali na mugunta ya sani ya kware a kai.
Tana gama idda ta fara yiwa Usman zirya..
Haka kurum za taci kwalliya ta ta zo gidan wai ta zo ganin y’ay’anta! Shi dai Usman ba ma ya bi ta kanta dan yace ‘daman a rashin Maryam ne ya hak’ura ya zauna da ita!’.
Idan tazo gidan ta dinga habaice habaice kenan, ko
Jalila ba kulata take yi ba sai
Maryam tayi da gaske tukunna suke gaisheta, Jafar ne kawai yake biye mata.
Ana cikin haka aka yiwa Mijin Zainab transfer shima ya dawo Kano, lokacin Yaranta uku mata biyu Aisha (momy) da khadija sai auta muhammad, itama dayake malamar makaranta ce sai ta nemi transfer aka kaita makarantar mata ta nan gandu take koyarwa.
Ai kuwa tun daga nan duniya ta yiwa Mama zafi, domin kuwa k’awancen Zainab da Sadiya sake k’ulluwa yayi dayake itama Zainab d’in nan kusa Mijinta ya kama haya ba nisa, dan haka kusan kullum suna tare.
Haka nan za suzo gidan suyi ta neman ta da fad’a!
Ita dau ba kulasu take yi ba.
Bilkisu a lokacin Yaranta biyu
Itama ta kammala karatunta na law tana aikin ta!
Kowa dai da y’ar sana’ar shi ko wani means of samun kud’i dan hatta Sadiya business d’in kaya take yi, amma ita Maryam a duk lokacin da tace tana son yin karatu ko sana’a tashi d’aya Ya Usman zai ce “a’a!!
Salon tayi kud’i ta gujesa!.”
Ranar da abun ya isheta daman ko kayan sallah baya yi musu ita da Huda idan ka gansu kullum cikin tsumma, Baba Bashir da Baba Talatu ne suke dan k’ok’artawa suyi musu sai ko Bilkisu,
hakan yasa ta d’auki waya ta kira Baba Talatu tana kuka tana gaya mata.
Ashe Shuwa na gefen ta a lokacin suna tare
Baba Talatu batayi auni ba taji Shuwa ta karb’e wayar!
Maryam zata iya cewa ta manta rabon da taji muryar Shuwa amma maimakon magana mai dad’i sai kawai Shuwan ta rufeta da fad’a ko gaisuwarta bata tsaya amsawaba, tace hau fad’a tana cewa
“Ai ta riga tabar gini tun ran zane! Lokacin da su Zainab da Bilkisu suka yi nasu karatun a lokacin daya dace ai ita saurayi tabi, sai yanzu god’ai god’ai da itane zata wani ce tanaso zata koma makaranta??!.
Kawai ta zauna idan Usman d’in yaga dama yaayi mata to, idan kuma bai yi mata ba ta hak’ura, sannan tama daina k’ok’arin had’a kanta ‘jahila! mara aikin yi! Da su Bilkisu masu ilimi masu aikin yi dan indai tace haka zata yi to kuwa wahala zata sha!.”…
Tana gama fad’in haka ta kashe wayar.
Haka rayuwa taci gaba su Shuwa ko k’ofar gidansu har yau har gobe sun hana Maryam zuwa ballantana Huda, ko Bilkisu ta je gani idan emergency ya taso sai dai su had’u a waje ko a gidan Baba Bashir..
Sunce ‘ai tun ranar data saka k’afa tabi Abba suka cireta a matsayin y’arsu, su bama su da ita ba.…..
Ana haka rana d’aya kawai Usman Ya mayar da Sadiya aka d’aura aure.
Da farko su Baba Bashir sun so hanawa amman yadda ya nuna kamar idan bai auri Sadiya a ranar ba to tabbas zai iya mutuwa! Ne ya sanya kawai aka d’aura musu aure ta tare…
Tun daga wannan lokacin kuma Ya Usman d’in sai ya zamana kamar irin tsoron Sadiyar ma yake yi
,baya son ganin b’acin ranta baya iya hanata abu.
Tana dawowa gidan ta janye y’ay’anta duk wahalar su da Maryam taci ba ayi shekara uku ba gaba d’aya hankali Jalila ya koma kan Mahaifiyarta, tun bata kulata har ta fara kulata daga baya data gane uwar ta kuma sai ta fara yiwa Maryam rashin kunya da rashin mutunci kala kala tun bama data lura da Maryam d’in bata so
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 32