buk’atar lokaci….”
Shiruuu, Kaka yayi na y’an mintuna sannan yace
“To!
Amma tunda dai yace zai zo ya gaishe mu ba wani abun bane ba za a barshi ya zo d’in, maganar turo iyayen nashi kuma sai a jira in kin gama d’aukar lokacin naki ko?”
“To” tace.
Daga nan ya tambayeta ‘makaranta’ da kuma ‘gidan ba matsala ko?’
Nan tace mishi “komai Alhamdulillah….a taya su da addua result d’insu yayi kyau!”
Y’ar hira kad’an suka yi sannan ya sallame ta ta tashi ta tafi….
Tun kafin ta k’arasa d’akin Baabaa Talatu take jiyo hayaniya.
Da sallama ta shiga nan ta tarar ashe Hajiya Shuwa ce suke ta hira da Sakina kamar wasu k’awaye itama Baaba Talatu tana taya su.
Har k’asa ta durk’usa ta gaida Baaba Talatu dayake itace a farkon d’akin, cikin kulawa da sakin fuska ta amsa mata.
Nan ta k’arasa wajen Shuwa itama ta gaida ita amman ko alamun taji ma bata yi ba!
Maimaitawa tayi ta sake maimaitawa amman Shuwa tayi mata banza!.
Nan Baaba Talatu tace
“Taso ki zo ki zauna, zo ki bani labarin makaranta…”
Haka jikinta duk yayi sanyi taje ta zauna kusa da Baaba Talatu, tana zama basu wani jima ba Sakina tace “ta zo su tafi k’unshi kar a haye musu layi.”
Nan suka yi musu sallama suka fito.
A hanya sai da Sakina ta bata hak’uri akan halin Shuwa, tace “wata rana zata daina.”
Murmushi kawai Hudan
tayi tace “ba komai.”
Haka suka k’arasa wajen k’unshi aka tsantsara musu mai kyau Ma sha Allah, sai yamma suka koma gida a gajiye…
Hudan bata waiwayi wayarta da ta bari a gida tun safe ba sai dare shima dan zata haska tayi wanka ne kasancewar garin da zafi sosai.
Tana d’auka kuwa taga misscalls d’in Arshaad, da messages kala kala.
Sai da tayi wankan ta sannan ta kira shi, bai d’auka ba sai da
ya katse tukunna ya kirata.
Tana d’auka yace “in sun gama waya ta tura mishi number Sakina, dan yaga ita tata wayar bata da amfani.”
“Tou” kawai tace tana murmushi, sannan ta bashi hak’uri…
Hirarsu suka sha sosai Hudan kamar tana gabanshi sai rufe ido take yi, Sakina na gefe tana chatting tana ta tab’e baki k’arshe ma barcinta tayi ta kyale ta.
Washegari da yamma ya zo, da yaga k’unshi nata kamar ya cinye hannun, yace mata ‘yayi kyau!’ Ya fi sau ba adadi..
Dukda tace masa ‘Sakina ta d’auka zata tura mishi anjima
amma hakan bai yi nasa sai da shima ya d’auka da wayarshi…
Suna tsaye mota tayi parking a k’ofar gidansu, ita bama ta san Junaidu bane ba dan motar akwai tint..
Sai da ya fito tukunna ta ganshi!
Ai kuwa nan jikinta ya hau karkarwa…..
A tunaninta zai yi wani abun
amman ga mamakinta ko kallon inda suke beyi ba, yayi wucewarshi cikin gida kamar
ma bai gansu ba!
Juyowa tayi taga shima Arshaad d’in Junaidun yake kallo…har ma Junaidun ya shige amman bai bar kallon k’ofar ba, da alama kuma wani tunanin ya tafi…..
Sai da ta kira sunan shi sannan ya juyo ya kalleta!
D’an k’uraa! mata ido yayi
Kafin yace mata
“How are you related to him??”
Cikin nutsuwarta ta fad’a mishi yadda suke a gidan da kuna yadda kakanninsu suke!
Ajiyar zuciya ya sauk’e sannan yace “Hudan hope ba matsala dai ko?
Dan gaskiya na d’an tsorata kad’an! Tunda kinga shi na gida ne.”
Shiruu, tayi kaman tana tunanin wani abun sai kuma da sauri tace
“Yauwa, Ya Arshaad, wai kai ne kace ‘kar a sake barin shi ya shiga wajenmu In ya je, a school?”
Shiruu ya d’an k’ura mata ido sai kuma yace “Inji wa?”
Ajiyar zuciya ta sauk’e, wanda har sai da yaji kafin tace
“Daman tun jiya na fad’a mishi ‘k’arya me gadin mu yake maka, nasan ba zaka tab’a yin haka ba!’
Wai fa har da cewa kaje kanata fad’a! Ni kuma na san bama ka iya fad’a ba! Shiyasa tun a nan na gane sharrin me gadin ne.”
Murmushi yayi sannan yace “ni ina na iya wani fad’a, um?.
Jiyan kun yi magana kenan??
I mean da shi Junaidun.”
“Eh!”
Tace.
Shiru yad’an yi kafin yace
“Kin je gidan Kaka??”
A hankali tace
“Eh”
Bai yi magana ba itama bata yi magana ba. Chaan! Tace
“Ba wai ina son Ya Junaidu ba ne..amman gara komai ya d’an lafa tukunna...
…Nan ta zayyano mishi yadda suka yi da Junaidun jiya sannan ta k’ara da cewa
“Idan nayi haka ban kyauta masa ba, yayi mini halacci sosai, tun ina k’arama yake raino na, har Mahaifiyarsa yake sab’awa fa duk saboda ni, in dai kaji suna fad’a da ita to akaina ne!
Jiya naga b’acin ranshi sosai, kuma ban yi zaton ni yake ta jira ba har ga Allah!
Yanata plans ashe, ni duk ban sani ba.
Yanzu idan yaji na banzatar da shi despite abunda ya faru tsakanina da shi a jiya amma kawai na sharesa naje an saka ranana or something like that a yanzun, it’ll break him.
Dan Allah ka bani time abubuwa su d’an yi settling. In sha Allah nan da y’an wasu kwanaki, idan ya sak’k’o daga fushin I’ll talk and explain everything to him, daga nan sai ayi maganan mu.
Amman yanzu idan wani abun ya faru gani zai yi kamar i don’t even care about him!
Shiyasa ma jiya da naje gidan Kaka......”
…Nan ta fad’a masa yadda sukayi da Kakan!
Sannan tace
“Please Ya Arshaad don’t get me wrong, babu abunda ya chanja daga promise d’inmu, ba wai ina son Ya Junaidu bane, kawai Ina so ne in yi mishi halacci ko ta yaya ne, saboda abunda yayi min a rayuwa idan nayi mishi haka lokaci guda ban kyauta ba.”
Tunda ta fara magana Arshaad ya kafeta da ido ko kyaftawa ya kasa yi!
Sai da ta kai aya sannan yace
“1 question please”
Bai jira jin me zata ce ba yace
“If to say, let’s just assume..
Junaidu yace miki yana sonki tun kafin ki tafi school tun farko, zaki kula ni???”
Sunkuyar da kanta tayi sannan tace “Muna da issue sosai da family d’in Ya Junaidun, ko da ace na yarda Mama ba zata yarda ba.”
“Ba wannan nake tambayar ki ba!
Abunda nake son ji shine
‘A zuciyarki, ki cire family d’inshi, just assume kamar ma babu family d’in nasa a duniya!
Zaki iya aurenshi??
Do you love him?’.”
Shiruuu, tayi sannan tace
“Ya Arshaad ai kai zan aura yanzu, mun gama wannan maganan…”
Da d’an fad’a yace
“Still kin k’i kiyi answering question d’ina!
inda bana nan da.....”
Ganin yadda take kallon shi ne yasa yayi shiru…ya dafe kanshi, ya lumshe idanunsa for some minutes! Kafin ya bud’e yace “Sorry”.
A hankali tace “Ya Arshaad kai zan aura, please ka fahimceni…ba wai ina sonshi bane kawa...”
Da sauri ya katseta yana murmushi yace
“I understand dear, kawai dama i just want to check ko ‘you have feelings for him’ ne!
That’s what the questions are for…..”
Zata yi magana yayi saurin sake katseta, ta hanyar cewa
“Bara in tafi, ko?”
Yayi maganar yana murmushi!
Bai jira jin me zata ce ba kawai ya bud’e motar ya shiga ya d’aga mata hannu sannan yayi reverse tana kallonshi ya fice a layin….
Jiki a sanyaye haka ta koma cikin gida.
Ko hijabinta bata cire ba Mama wadda gama wayarta kenan da Kaka ta rufeta da fad’a! Kamar zata cinyeta d’anya..
Sannan tace “su tattara kayan su ita da Sakina gobe da sassafe su tafi gidan Ummu
Tunda ganin Junaidun da take yi ne yasa take k’ok’arin chanja ra’ayi.
Duk ranar data dawo cikin hankalinta sai ta dawo gidan ayi maganar aurensu ita da Arshaad!
In ma bata son Arshaad d’inne tou ta nemo wani
amman ba Junaidu ba!.”
Ita dai Huda karshe ma kuka ta saka. Ta rasa meyasa mutane suke yi mata gurguwar fahimta akan halaccin da take son yiwa Ya Junaidu.
Da kyar Sakina ta lallasheta tayi shiru, kamar zata kira Ya Arshaad amman kuma sai tace bara ta kyaleshi dan dukda bai nuna mata komai ba amma gani takeyi kamar ranshi ya b’ac .......
Washegari da safe da kyar Mama ta yarda suka tayata wanke wanke da girkin safe dan daa cewa ma tayi su tafi kawai, ita Hudan har mamakin Mama take yi…ko d’an motsi taji a hanyar d’akin Junaidu ko alamun za a fito nan zata ce mata ta tashi ta shige d’aki da sauri ko ta turata kitchen!
A haka dai har suka kammala aikin, ita bata ma yi wani aikin sosai ba dan k’arshe kawai Maman ma ce mata tayi ta shiga d’aki daganan bata sake kiran ta ba!
Suna gama breakfast lokacin Mama tana d’akin Baba tana aiki suka yi sauri sukayi wanka dan Sakina cewa tayi “wallahi ba zata fita fuska duk kwantsa ba”. Suna cikin shafa mai Maman ta shigo, tace su yi sauri su tafi ta mik’o musu kud’in mota.
Sakina ce ta amsa suka ci gaba da shiryawa a gaggauce dan Mama tsayawa tayi a bakin k’ofa tace ba zata tafi ba sai taga fitar su..
Sakina har hijabinta ta saka Hudan kuma tana cikin d’aura zani sukaji kamar jiniyar y’an sanda…
Kafin k’iftawar ido suka jiyo ta a kusa kusa, sai kuma da wani irin k’arfi suka ji an bugo k’ofar gidan!!!
Nan suka tabbatar gidan aka zo…
Hakan ya sanya Sakina da Mama saurin fita itama Hudan ta rarumi hijabinta ta saka ko ribbon da d’ankwali bata tsaya nema ba!
Tana fita jikinta ya hau karkarwa sakamokon sojiji da y’an sanda data gani sunfi ashiri dan taff sun cika gidan.
Kusan a tare Hudan da su Umma da Jalila suka fito..suma duk jikin su karkarwa yake yi ganin sojoji fuskar nan a murtuke, ga uban bundugu.
Wani a cikinsu ne ya k’araso gaban Mama, da kayan sojiji a jikin shi amman nashi ba kalar na ragowan ba ne, yana zuwa ya nuna musu id card d’insa kafin yace “Muna neman Junaidu Usman Bashir!
Mun samu order daga sama!
Here” ( yayi maganan yana nuna musu wasu takardu )
Yace “We have a search warrant and arrest warrant!”
Umma ce ta matso kusa da Huda, a hankali tace
“Me kenan??”
Kallonta Hudan tayi sannan ta juya ta kalla mutumin tace
“Sir, for what please?”
Hannu mutumin ya mik’a baya
nan wani ya taho da gudu ya bashi wasu takardu sannan ya sara mishi ya k’ame!
Takardan ya hau bincikawa, sai da yazo kan wata ta tsakiya tukunna ya zarota ya mik’awa Hudan..
Da sauri ta sa hannu ta karb’i takardun ta shiga karantawa…
Sakina wadda ta matso suke karantawa tare ce ta rafka uban salati sannan tace
“Sir this cannot be true he h...”
Bindigar da d’ayan ya saita mata a kai ne ya sanyata yin shiru lokaci guda!
Jikinta na mugun karkarwa.
Umma kuwa fashewa tayi da kuka tana cewa
“Me yayi ake nemanshi har da bundugu?
Ku fad’a mana dan Allah!”
D’akunan gidan mutumin ya yiwa ragowan sojojin nuni sannan ya basu order!
Nan da na suka shishhiga suka hau bincike…
Su Umma duk suna tsakar gida banda k’arar fashewar abubuwa da fad’uwa ba abunda suke ji…
Har kitchen da band’aki sai da suka duba amman babu Junaidu ba labarinshi.. basu samu komai ba.
Mutumin ne ya kalli Sakina yace “how are you related to him!”
Nan ta fad’a mishi sannan yace mata
“Akwai siblings d’inshi ko Mamanshi a nan?” (Duk da turanci).
Direct ta juya ta nuna mishi Umma…
Nan kuwa Umma ta sake rud’ewa ganin mutumin ya nufota tana cewa
“Dan uban ki me nayi kike nunani?”
Da gurbatacciyar Hausar shi yace mata “Ina wayanki?”
“Tana d’aki” tace, sannan jiki na rawa ta cewa Jalila “ta shiga ta d’auko!”
Ana kawo wayar ya karb’a ya mik’a mata sannan yace
“Ki kira Yaron ki, kice duk abunda ya kayi ya baro yazo yanzun nan, and kar ki bari ya zargi komai!
If not, sai na fasa miki kai da bindigar nan”
Jiki na rawa Umma ta hau kiran Junaidu bayan ya umarceta data saka wayar a handsfree….
Sai da ta kusan katsewa tukunna ya d’auka!
Daga muryarshi zaka fahimci bacci yake yi..
“Kana Ina?”
tace mishi.
Shiruuu, yayi. Chaan! Yace
“I don’t really know!
Ina zuwa, zan kira ki”
Har zai kashe tace “dan Allah duk inda kake kazo yanzun nan kaji??”
“To” kawai yace sannan ya tsinke wayar.
Minti talatin mutumin ya bayar, dan haka yana cika yace “Umma ta sake kiran shi”…
Misscalls biyar tayi mishi bai d’auka ba, tana shirin yin na shidda suka ji k’arar parking d’in mota! Bai dad’e ba ya shigo cikin gidan…
Kayan jikinshi ne na jiya da yamma a jikinsa, amman kamar harda jini jini sannan duk ya yamushe kamar wanda yayi kokawa.
Gabanshi ne ya fad’i dan daman tun a waje yayi karo da wasu sojojin, a tunanin shi ba gidan suka zo ba amma yanzu kam ya tabbatar gidan nasu aka zo.
Dan haka ya k’araso da wuri!
Yana zuwa yana k’ok’arin yiwa su Umma magana sojojin suka rufar mishi suka hau k’ok’arin datsa mishi ankwa!
Ganin haka yasa gaba d’aya suka fashe da kuka har Mama….
Da kyar Sakina ta iya tambayarsu ‘ina zasu kaishi?’.
Ba b’ata lokaci mutumin yace mata “K’irik’iri maximum security prison!”
Babu irin kuka da burgimar da Umma bata yi ba har waje amman haka aka saka shi a mota aka tafi dashi!
Duk ta tara jama’a.
Shi kam Junaidu yama kasa magana dan gaba d’aya kanshi a d’aure yake…
Da kyar su Mama suka ja Umma suka maida gida sannan Mama ta kira Baba da su Kaka ta gaya musu halin da ake ciki.
BULAMA ✍️.
So da Buri
Free Book
29
Kafin minti ashirin Kaka, Madu, Shuwa, Baaba Talatu, Baaba Laraba da K’asimu sun k’araso cikin gidan!.
Baaba Laraba sai lallashin y’arta take yi itama tana nata kukan.
Baba ne ya shigo a k’arshe daman shi ake jira, dan haka yana zuwa su Kaka sukace “ba b’ata lokaci, bara a bi sahun su…”.
Sai a lokacin tukunna Sakina tayi magana, tace
“Sun tafi da shi Lagos fa!”.
Wani uban ashaar!! K’asimu ya buga sannan yace
“Wai wannan wanne irin rashin mutunci ne!
Haka kurum sun zo sun tafi da Yaro, kuma bama zasu barshi a nan ba sun kama sun kaishi har Lagos!! Sai kace wanda akace yayi kisan kai!
Sun fad’a muku laifin da yayi??”.
Cikin Kuka Hudan ta share hawayenta sannan tace
“A jikin takardan cewa aka yi wai ‘sun yi fashi su uku a gidan cheif justice jiya kuma sun kasheshi sun kashe y’ay’an shi hud’u!”.
Salati tsakar gidan ya d’auka, gaba d’aya. Baba kuwa dab’ass!! Haka ya zauna a k’asa…
Da sauri Umma tace “wallahi k’arya ne, sharri aka yi mishi, Junaidu tun yana Yaro ko cinnaka idan ya cije shi baya kashewa ballantana mutum, wallahi k’arya ne.”
Kaka ne yace “Sadiya ki yi shiru, kowa anan ya san k’arya ne, abun da ya kamacemu yanzu shine addua sai kuma mu nemo lawyer mu fara k’ok’arin fitar da shi ko?
Tunda kunga har an tafi dashi.”
…..
Nan suka hau shirye shirye aka ware masu tafiya Lagos d’in, sannan suka kira Ya Jamilu (Yayan Baba) shima.
Kuma suka nemo lawyer sannan aka yi shirin tafiya…..
Gidan Ummu za su fara zuwa su tambayi Mijinta akan ya barta a tafi da ita tunda lawyer ce itama mai zaman kanta..
Hakan kuwa aka yi a ranar zasu bishi.
Sai da suka raba sauk’ar Al Qurani da addu’o’i a wajaje daban daban, sannan suka d’au azumi kaff d’insu, har Jalila wadda rabonta da azumi har ta manta wai tana da ulcer Umma kuwa ko da yaushe cewa take yi “ai Allah ma ya ga zuciyarta kuma shine ya d’aura mata rashin lafiyar”.
Baba, Madu, Ummu, Kaka sai d’ayan lawyern da aka tafi da shi ne suka kama hanyar Lagos, sai washegarin ranar tukunna suka samu kansu bayan sunyi settling a hotel d’in da suka kama lokacin
Ya Jamilu shima ya k’araso dan haka ba tare da b’ata lokaci ba suka nufi inda aka kaishi!.
A nan ran Kaka ya sake b’aci da yaga wajen da aka kaishi d’in! Shi da ba a gama tabbatar da laifin shi ba saboda Allah meyasa zasu kawoshi prison?!
Haka nan yayita fad’a su Ummu suna bashi hak’uri… da kyar yayi shiru suka nufi gate d’in..
Kalar binciken da ake yi musu duk wanda ya gani zai yi tunanin ‘sun zo ganin wani hamshak’in d’an ta’adda ne’. Kuma dukda haka cewa akayi “sai dai mutum uku su shiga ba zai yiu su shiga su duka ba!”.
Baba, Ummu sai d’ayan lawyer d’in da aka tafi da shi ne suka shiga, shi kam Ya Jamilu ID card kawai ya nuna musu ya wuce…
Bayan y’an gwaje gwaje aka kaisu wajen zama (chan gaba da parking lot) aka ce “su jira shi a nan”
Anfi 30 minutes tukunna aka fito da shi.
Daga nesa da ya taho basu gane sa ba sai da aka matso dashi aka zaunar, tukunna.
Kuka kawai Baba yasa yayi saurin tashi a wajen.
Mai tsaron da ya kawo shi ne ya had’asu ya bashi iya lokutan da yake dasu sannan yad’an koma gefe kad’an ya tsaya.
Ganin basu da isheshshen lokaci yasa Ummu tace
“Junaidu, how are you?”
Ahankali muryar shi baya fita sosai yace
“Alhamdulillah”
Ba tare da b’ata lokaci ba tace
“ya aka yi? Mai
ya faru? Me
ka sani?”.
D’an gyara zama yayi tukunna ya fara magana…..
“…...shekaran jiya da daddare ina d’akin Abokina.
Ba a Kano yake ba, a nan Lagos yake, amma yana da apartment a Kano d’in.
Shekaran jiyan ya kira ni yace mini ‘zai shigo gari amman a jiya zai koma kuma akwai wani aiki da za muyi akwai samu a ciki sosai!
In da hali yana son ganina sharp sharp’.
Nan da nan nace mishi gani nan zuwa.
Ina zuwa ba tare da b’ata lokaci ba ya hau yi mini bayanin business d’in..
..’Wake ne zamu kawo daga Taraba, ko wanne a kan 9k zamu siya amman idan yazo Kano zamu iya siyarwa a kan 23k!
Kuma kud’in mota dududu bai fi mu biya dubu arba’in ba dan ya san wani me mota da suke irin wannan harkar, sannan za a kawo mana buhu sama da d’ari, a mota daya!’.
Nan da nan na amince…
Muna cikin maganar wata ta shigo har d’akin ta kawo mana Lemo..
Ban kawo komai a raina ba
dan irin gidan hayan nan yake kowa da dakinshi, da band’aki mai kyau sosai,
compound dinsu ne kawai d’aya, and tsarin d’akin har da d’an mini kitchen a ta chan gefe da d’an k’aramin dining kamar dai na turawa.
Na san shi, bashi da sakewa da mutum bashi da saurin yarda in ba wai ya san ka sosai ba!
Yadda suke wasa da barkwanci da wadda ta kawo lemon yasa na gane ya santa sosai shiyasa na aminta ba sha…
Amman wani abun mamaki
sip d’aya kawai nayi wa lemon ko ciki na bana jin ya k’arasa shiga na fara ganin uku uku!
Daga nan ban sake sanin inda kaina yake ba.......
K’arar k’aramar wayata ce ta farkar dani daga wani irin bacci…
Mamakin d’akin da na tsinci kaina na dinga yi dan ban san inane ba!
Amman har da mukullin mota na a hannu na. Sai dai babu wallet d’ina kuma ba babbar wayata.
Yadda naji muryar Umma a waya ne ya sanya nayi saurin fitowa, ban ma san layin ba!
Gidane mai bene mai kyau sosai amman duk k’ofofin a bud’e da alama an bud’e mini ne dan in fita!.
Ina fitowa naga motata a parke, dan haka nayi gaggawar shiga na taho…
Sai da na fito titi tukunna na gane ashe a chan cikin Farawa nake.........
Tun lokacin da suka taho dani kwakwalwata take min flashin wasu abubuwa kamar mafarki
Amman na gane a shekaran jiya abun ya faru dan da kayan nan na jikina nake ganina!”.
Ajjiyar zuciya Ummu ta sauk’e sannan tace “suna interrogating d’inka ne?”
“Sosai ma!” yace, sannan yaci gaba “In fact sai sun dake ni ma idan na suma most in zan farfad’o ne memories d’in suke flashing…
Amman d’azu da safe around 8 sun kawo wasu takardu
har da flash!
Ina wajen suka ce a maidani ciki tou tun daga lokacin basu sake yi min komai ba.
D’ayan d’an sandan ne yake ce min wai ‘Allah ya taimakeni amman still in ci gaba da addu a’.”
Sauke ajiyar zuciya lawyer d’in da Ummu suka yi a tare bayan sun gama rubuce rubucen su!..
Tabbas this is a very serious case, kisan kai ga fashi, ko da ace bai yi komai ba in dai dashi aka je wajen to hukuncinshi d’aya ne da waenda suka yi aikin, wanda definitely ‘kisa’ ne!.
Maganar shi ce ta dawo da Ummu daga duniyar tunanin data tafi jin yana cewa
“Ummu na rantse da Allah gaskiya na fad’a miki duk maganar nan
Wallahi ban tab’a fashi ba, ballantana kisan kai, ko bayan rai na, ki fad’awa Hudan wannan maganar, wallahi ni ba d’an fashi bane ba!”
Yana gama fad’in haka ya fashe da kuka.
Tausayin shi ne ya sa Ummu itama ta fara hawaye..
Tabbas ta yarda da Junaidu to amman wannan k’atamurmurar Allah kad’ai ne zai fitar da shi!
Dan bama taga ta inda zasu fara neman evidence domin kare shi ba!.
Wani mutum sanye cikin suit da sojoji biyu a gefe da gefen shi ne ya tunkaro su.
Suna hangoshi Ummu tayi saurin goge hawayenta sannan suka mik’e tsaye.
Ba tare da b’ata lokaci ba ya cewa su Ummu su biyoshi sannan a mayar da Junaidu inda aka d’auko shi
..........
Bayan kamar 2 hours su Ummu suka fito suka tarar da su Madu a inda suka barsu.
Suna ganin su tun kafin su k’arasa wajen motar su suka iso garesu suka hau tambayarsu halin da ake ciki
D’ayar lawyer d’inne yace musu “su k’arasa mota za suyi musu bayani a chan..
Ganin basu fito tare da Junaidun ba gashi kuma sun k’i yi musu bayani ya sanya tun a nan jikin su Madu yayi sanyi.
Ko a motar ma Ummu da taa yunk’ura zata fara bayani sai kuma tayi shiru dan bama ta san ta ina zata fara ba!
Sai da suka k’arasa hotel d’in, bayan sun fiffito Kaka yace “su je garden, su tattauna a chan!”
Zama suka yi aka kawo musu d’an abun sha tukunna bayan sun huta Ummu tace
“Kaka Junaidu is innocent! duk da cewa na san duk mun san da hakan amma yanzu haka suma mutanen da kansu sun san cewa bashi da laifin komai.”
“Alhamdulillah”
Gaba d’ayansu suka furta
kafin Kaka yace “tou dan maiyasa suka kamashi saboda Allah? Sannan maiyasa baku taho da shi ba?”.
D’ayan lawyer d’in ne yace
“A jiya da suka zo suka tafi da shi basu san babu shi a laifin ba!
Asalima shine prime suspect saboda wayarshi da wallet d’inshi dake a wajen sannan bindigar da aka yi amfani da ita aka harbi mutumin da aka duba hannun Junaidu ne ya fito a jiki…
Babu kalar duka da horon da basuyi mishi ba amman shi dai magana d’aya yake maimaita musu, itace maganar daya fad’a mana d’azu ni da Ummu
‘He’s innocent!’
iya abunda ya faru da shi na gaskiya yake fada..
Shiyasa suka d’an saka kokwonta a lamarin.
Kuma tun jiya da daddare suka tsananta bincike a gidan mutumin…nan kuwa aka samu wata b’oyayyiyar camera a parlour wadda babu wanda ya isa ya ganta, dan su kansu sai da camera detector tukunna suka iya ganota a jikin chandelier!
Nan da nan kuwa suka d’auka suka turo nan.
D’azu muna tare da shi Junaidun, aka zo aka kira mu, a ofice d’in muka samu Ya Jamilu shima..
Ba tare da b’ata lokaci ba mutumin ya nuna mana video din......
…’Shi Junaidu a sume ma wasu mutane guda biyu da mask suka shiga da shi, bayan wasu k’arti biyar sun firfito da CJ d’in da Yaran shi sun d’add’aure,
ana shiga da shi d’ayan yayi mishi wata allura sannan ya hau yayyafa mishi ruwa yana marin gefen fuskarshi…
Da kyar ya farka sai dai kana ganinshi ka san baya hayyacinshi sannan suna mik’ar dashi tsaye ya koma ya sume…
Babu yadda ba suyi da shi ba amma yak’i farkawa.
Nan d’ayan wanda suka shigo dashi ya koma gefe ya fara waya, bama jin abunda suke fad’a kwata kwata saboda camerar babu voice.
Yana gama wayar ya d’auki video d’in Junaidu da parlourn ya turawa wanda muke tunanin ya gama waya dashi.
After some minutes aka sake kiranshi, yana gama wayar ya zo ya kama hannun Junaidu (bayan ya sakawa nashi hannun socks da leda) ya damk’e bindigar da hannun Junaidu wanda yake ta baccinshi..sai dai okaci zuwa lokaci ya kan d’an bud’e idanununshi sai kuma ya maidasu ya kulle…
Bayan sun damk’a mishi bindigar ba tare da b’ata lokaci ba suka saita kan CJ d’in suka harba daga nan ragowar suka harharbe Yaransa…
Da alama k’arar jiniya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 24 Chapter of 32