a shirye ta hau Fara’a! Sai a lokacin taga tayi murmushi tun jiya.
“Hmm” Kawai Jalilan tace
daganan ta koma kan kujerar d’akin inda ta ajjiye purse d’inta ta d’auka da wayarta tace
“Bara inje yana waje.”
“To d’an yi dariya mana Autata!
Haba mana..
Haka zaki fita kina fushi da ni?”.
Umma ta fad’a cikin sigar zolaya.
Murmushi kawai Jalilan ta iya yi daga haka ta sa kai ta fice daga d’akin......
A hargitse Anty Zainab ta shigo gidan sakamokon abunda Umman ta gaya mata a waya tana kuka…
Bata bi ta kan Hudan wadda ke sharar tsakar gidan ba ta shige ciki kamar zata hantsila, kai
kana ganinta ka san ba lafiya ba!
Tana shiga d’akin ta hango Umma zaune akan kujera tanata faman sharb’ar kuka!
Kamar jira take yi suna had’a ido da Anty Zainab ta sake sakin kukan da k’arfi.
Da sauri ta k’arasa inda take kafin tace “Haba mana Sadiya,
ba kuka za kiyi ba!
Tashi za kiyi a fara nemanta
In ta kama har gidansu shi Yaron sai aje.”
Cikin kuka Umma tace
“Ina na san gidan su Yaron?
Sai dai In Huda za a kira ta fad’i inda gidansu Arshaad d’in yake sai aje
Na san za a samu Jalila a wajen”
Gaba d’aya kan Huda d’aurewa yayi lokacin guda!
…Parker take nema a tsakar gidan bata samu ba
Chan ta hango wata a bakin k’ofar dakin Umman
dan haka ta k’arasa don ta d’auka!
Ba abunda kunnuwanta suka jiyo mata sai
“Inda gidansu Arshaad d’in yake sai aje
Na san za a samu Jalila a wajen.”
Da mugun sauri ta bar wajen kanta a d’aure..
Har ta kwashe sharar ta zubar ta wuce d’aki hankalinta sam baya jikinta…
A Chan d’aki kuwa cikin rashin fahimta Anty Zainab tace
“Arshaad dai saurayin Huda?”
Da sauri Umma tace “eh,
ai Yaron k’aninsa ne.”
Ajiyar zuciya Anty Zainab ta sauk’e kafin tace
“D’an gwada sake kiranta muji
ko zata d’auka!”
Cikin kuka Umma tace
“Tun shekaran jiya fa wayar a kashe!
Yau kuma da safe a kunne amman nayi mata miss call yafi dari biyu bata d’auka ba.”
A hankali Anty Zainab tace
“Tou ko Baba zamu gayawa?
Lamarin nan bafa lalle mu iya handling d’inshi mu kad’ai ba.”
Cikin firgici Umma tace
“Ki rufamin asiri Zainab!
Tun a jiyan ya fara sintirin nemanta..
Babban abunda yafi d’aga min hankali shine
‘Nace mishi yau zara dawo daga gidan Hansai!
Dan ce mishi nayi nan taje sai kuma aka yi rashin sa a Hansai d’in ba lafiya shine nace ta d’an zauna tunda Yaranta ita duk maza ne ba zasu iya jinya ba!’
Wallahi Zainab In kinga yadda mutumin nan yayi min fata fata d’azu da safe za ki sha mamaki
Kin sanshi a kan Jalila da Ja’afar..
To yanzu kafin ya fita kasuwa sai da yayimin gargad’in ‘In tafi gidan Hansai da kaina In d’auko mishi y’arsa idan ba hakaba na bari ya dawo babu Jalila a gidannan duk abunda yayi mini in kuka da kaina!’
Har kud’in mota ya bani
Yanzu gashi yamma tayi na san duk inda isha tayi ya dawo gidannan
Ta Ina zan fara?
Ya zan yi?
Ina zan ga Jalila ni Halimatu!!”.
Ta k’arashe maganar tana fashewa da kuka.
Da kyar Anty Zainab ta samu ta lallasheta.
Sun jima suna tattaunawa daga k’arshe suka yanke shawarar fad’awa kowa ba a san inda take ba!
Tasan su Kaka zasu san abun yi kuma in sha Allah za a ganta ba tare da asirinsu ya tonu ba!
Amman muddin suka tunkari su Ummu da Huda da zancen aka tambayi Arshaad to sai gaskiya ta fito
Sukuma ba zasu so a san asalin dalilin b’atan nata ba.
Umma tana kuka wiwi da majina suka nufi k’ofar fita daga d’akin dan zuwa wajen su Kaka.
Anty Zainab ce a gaba Umma a baya
Kicib’is!! Haka taja ta tsaya tana kallon Jalila wadda ta shigo yanzun nan..
Da sauri Umma ta ture Anty Zainab d’in tayi kan Jalilan ta hau duddubata kafin ta jawota jikinta ta rungume ta sa kuka
Ga mamakinsu sai sukaga Jalilan itama ta fashe da kuka!!
Shiruuu, Umman tayi ta hau lallashinta tana tambayarta amman tak’i kulata!
Nan suka jata suka kaita bakin gado suka zaunar da ita suka hau tambayarta suna lallashinta…
Bata ce dasu k’ala ba
in banda kukan da take yi kamar ranta zai fita!
Da kyar da sid’in goshi bayan kamar awa d’aya aka samu tayi shiru..
Bata ko kalli inda suke ba ta ja pillow ta kwanta ta juya musu baya
Tanaji Umma tana yi mata magana tayi banza da ita!
Ko minti biyar bata yi da kwanciyaba baccin wahala yayi gaba da ita…
Bata san lokacin da Anty Zainab ta tafi ba
Ta dai ji lokacin da Baba ya haska ta da tochila yana cewa
“Ya naga fuskarta duk a kumbure?”
Tanajin Umma tana yi mishi magana bata gama fahimtar zancen nata ba wani baccin ya sake kwasheta…..
Ba ita ta tashi ba sai washegari wajajen 10:00pm
Da Umma ta fara yin tozali dan haka tayi saurin kawar da fuskarta ta mik’e ta zauna.
Bata kalletaba ta sauk’o daga kan gadon ta duba wardrobe d’inta ta d’auka brush da makilin tayi hanyar waje
“Jalila zo nan!”
Taji muryar Umman.
Sai da ta juyo ta kalleta tukunnan ta d’auke kai ta fice daga d’akin, ta bar Umman nan zaune da baki a sake.
Umman ji take kamar ta bita har wajen sai kuma ta tuna ba su kad’ai bane a gidan dan haka ta hak’ura ta zauna tana zaman jiranta a d’akin!
Bata dawo d’akin ba sai da tayi wanka!
Tana shigowa, ko gama ajjiye kayan jikinta data fita da su waenda yanzun ta cire ta ruk’o a hannunta bata yi ba
Umma ta hau ta da fad’a!
kamar zata had’iyi harshenta
ta inda take shiga bata nan take fita ba..
Ko kallon inda take Jalilan bata yi ba…shirinta kawai take yi cikin nutsuwa..
Hakan kuwa ba k’aramin sake fusata Umman yayi ba
Dan haka ta fincikota cikin b’acin rai tace
“Wai aljanun rainin wayo kika je Auwal d’in ya saka miki?
Wacce sabuwar d’abi’a kika d’ebo ne?
Ya Ina yi miki magana tun jiya kin banzatar dani kamar ba uwar da ta tsugunna ta haifeki ba??”
Ta k’arashe maganar cikin d’aga murya.
Wasu zafafan hawayene suka zubo a kan kumatun Jalila!
Cikin tsananin d’acin zuciya tace
“Umma abunda nima nake ta so in tambayeki kenan
‘Anya kuwa kece uwar da kika haife ne?’
Kece uwar da kika reneni a jikinki?”
Bata damu da yadda kalamanta suka sake b’ata ran Umman ba taci gaba da magana “Umma da na nuna miki bana son alak’a ta da Auwal ya kamata ace kin fahimceni a matsayin ki na Mahaifiyata!
Ban tashi sanin na tafka babban kuskuren biyewa son zuciyarki da nayi ba sai shekaran jiya da kika kasa kwata ta kika kasa cetona!
Sai a lokacin na lura da yadda ni da ke muka taru muka jefe rayuwata a cikin tsanannin tashin hankali!”
Kuka mai k’arfi ne ya kwace mata, cikin kukan tace
“Umma yanzu wa kike tunanin zai aureni a haka?
Me kikaso In cewa Mijin da zan aura?
Bari kiji in gaya miki, Auwal har fyade sai da yayimin da na k’i in bashi had’in kai a farko!
Sannan yau ya ce mini ‘ko kiransa Idan nayi raina sai ya b’aci!’
A kan kawai ya tambayeni in fad’a mishi alak’a ta da Arshaad nace mishi ‘ba komai’
Kuma ya tabbatar mini da ba aurena zai yi ba!
Yace kawai ya fad’amin haka ne saboda In saki jiki da shi
sannan maganar auren da yace Arshaad zai yi
Wannan itama k’arya ce!.
Umma har ‘Akuya’ ya ce mini!
Yace bai tab’a ganin macen da aka yi winning d’inta a cikin sati daya tak ba
Sai ni.
A cikin sati d’aya kika tunzura ni na bi wanda ban sani ba kika jefa rayuwata cikin tashin hankali da rud’ani!
Duk ata dalilin
burin ki wanda na tabbatar yanzu bazai tab’a cika ba!.
Umma ni kinga rayuwata ta riga ta lalace ko?
To ki zuba ido ki gani!
Muna nan zaune a cikin gidan nan Arshaad zai zo a d’aura mishi aure da Huda ya d’auketa ya kaita gidanshi taji dad’i ta huta tayi rayuwarta cikin kwanciyar hankali!
Saboda ita Mama ta bata tarbiyyar data kamata, ta kama kanta ta kama mutuncin ta...........”
Mahaukacin marin da Umman ta d’auketa da shi ne ya sanyata had’iye ragowar maganganun ta!
A take ta durk’ushe a wajen ta fashe da wani matsanancin kuka…
Umma kanta bata san lokacin da hawayen tashin hankali suka zubo mata ba!
Kasa magana tayi kawai ta suri mayafinta tayi gida wajen Baaba Laraba.
Ita kanta Baaba Laraban ba k’aramin tashin hankali ta shiga ba daga jin labarin da Umman ta zo mata dashi..
Tabbas Yaron nan shak’iyi ne!
Amman ko d’an shed’an ne shi
wallahi sai ya dawo ya auri Jalila
Ko da kuwa ace za suyi yawo tsirarane!
Sanann sai sun raba Huda da Arshaad rabuwa ta har abada!!
Kamar mahaukata haka suka zama….a iya ranar kad’ai sai da suka je wajen mutane uku!!
Sannan suka hak’ura suka koma gida
Shima dan sunga dare yayi.
Haka nan duk a gajiye suka nufi gidajensu da niyyar fitar sassafe washegari idan Allah ya kaimu............
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
35
Washegari Kamar yadda Mom ta yi niyya…
Haka nan ta d’auki video d’in da ta shiryawa!
Ta saman balcony d’in d’akin Mammy ta d’auki video d’in Aslam da Arshaad lokacin suna shirin fita..
Ko ta kan Mammy wadda take ta faman tambayarta “me za tayi?” Bata bi ba, ta fice abunta tana cewa “In na dawo zan yi miki bayani”…
Sai dai kuma
tana zuwa gidansu Aslam d’in ta tarar su Gwaggo Asabe sun yowa Mommyn rakiya
Flight d’inta nan da awa d’aya (9:00pm) zai tashi!!
Lokacin appointment d’inta da Neurologist d’in da Granpa yayi mata booking yayi…
Kamar Mom ta had’iye zuciya haka taji, ba yadda ta iya haka nan ta hau yi musu fatan alkhairi suka wuce ita da Aaima. Flight d’in Abuja za su bi, idan sun sauk’a a Abujan Aaima zata wuce makaranta ita kuma Mommy su wuce tare da Dad…
BAYAN WATA D’AYA!
(After a month!!).
Da gudu Jalila ta fito daga d’akin Umma..
Bata kai ga k’arasawa band’akin da ta fito na niyyar zuwa ba! Ta hau kwarara aman da ya taho mata babu shiri
a nan bakin rijiyarsu wajen wanke wanke!.
Da sauri Mama ta fito daga d’aki jin mutum yana amai
Dai dai nan itama Umma ta fito da waya kare a kunnenta tana cewa
“Haba Zainab! tafiyar taku ba sai gobe ba?
Kiyi sauri kizo muje mu kaita asibitin mu dawo a san abunyi.
Kinga yanzun ma fa tana sa ruwa a bakinta kinganta ta fito ta hau amai!
Gara a yita a gama dan ni wallahi jikina ya na bani c.....”
Ganin Mama ne ya sanya ta had’iye ragowar maganar tata.
Ita kam Mama ta Jalila ma takeyi, dan haka tayi saurin k’arasawa inda take ta hau shafa mata baya tana yi mata sannu….
Dama fa ita kwana biyu ta d’an ga wasu changes a tattare da Jalilan
Kuma tana lura da yadda Umman ta hanata zaman tsakar gida kwata kwata! Maybe ko dan ta lura da kallon kurillar da take yiwa Jalilan ne? Oho!
Da kyar Jalila ta samu ta amayar da d’an ragowar ruwan da yake a cikin ta sannnan ta d’ago tana mayar da numfashi
Dai dai nan Umma ta k’araso wajen nasu tana hararar Mama..
Da mamaki Maman take k’arewa Jalilan kallo!..Tayi wani haske na ban mamaki
Bakinta sun yi pink sosai!
Sannan k’irjinta yayi mugun cika!
A hankali Mama da taji k’irjinta ya buga da k’arfi ta lumshe idanuwanta tace
“Innalillahi wa innailaihirrajiun”
Kafin ta bud’e su ta zubasu a kan Jalilan wadda itama ta kafeta da nata idanun…
A hankali Maman tace mata
“Sannu, me yake damunki?”
Jalila ancikin wata d’ayan nan ba k’aramin sanyi tayi ba,
yanayinta ma gaba d’aya ya sauya kamar ba Jalila ba..
Ta bud’e baki za tayi magana kenan Umma tace
“Ina ruwan ki!?
Sannan da kike wani salati
shin aljana kika gani ko me?
Kinga! Maryam!! wallahi ki fita a harkaata ni da y’ay’ana..
Ina jin ku jiya ke da Bilkisu kuna munafurcin Ja’afar
Bayan ke Huda ta fi sati bata a gidannan Allah kad’ai ya san inda ta tafi wannan karon!!
Ki fita a idona tun muna sheda juna wallahi….”
Tana ga fad’in haka ta jaa hannun Jalilan fuuuu suka shige d’aki.
Mama kam kasa motsi tayi a wajen…duk kalar tarin rashin d’aa’ar da Jalila ke zuba mata hakan bai hanata jin tsananin tausayinta ba!
Tabbas idan idanuwanta sun gane mata daidai to d’anyen ciki ta hango a jikin Jalila!
Bayan yadda ilahirin jikinta ya nuna
Aman da ta gama yi yanzu mai mugun k’arni ya sake tabbatar mata….
Salati kawai take yi tana sake nanatawa a cikin zuciyarta…
Ta ma kasa d’aga k’afafuwanta ta bar wajen!
Da kyar ta samu ta d’an motsa ta jawo ruwa a rijiya ta d’auraye wajen
daga nan ta sake luluwa duniyar tunani…..
A haka su Ummu suka shigo suka sameta.
Sai da su Sakina suka yi hugging d’inta tukunna tayi firgigit ta dawo daga duniyar tunanin data lulu.
Ummun ce ta d’an k’ura mata ido sanann tace
“Tunanin me kike yi haka?”
Wata nannauyar Ajiyar zuciya ta sauk’e kafin tace
“Ba komai”
Daga nan suka d’unguma suka yi d’aki.
Ba kalar tambayar da Ummu bata yi mata ba amman tace mata “ba komai” kawai!
Saboda hasashen alkhairi ake so a yayata, na sharri kuwa ba a fad’i!
Harshe na da kaifi!.
Ganin tak’i fad’a ya sanya Ummu kawai ta kyaleta
dan ta san da tanaso ta sani to da tuni ta fad’a matan..
Shiyasa bata sake yi mata maganar ba ta sako wani zancen ta hanyar cewa
“Mama anata shiri..
Gobe da sassafe duk zamu wuce.
Dan Allah ki zo kema mu tafi mana
Kin san In babu ke ba zan ji dad’in bikin ba.”
Murmushi Maman tayi kafin tace
“Bilkisu ke kad’ai fa kike ta gayyatata!
Jiya ina ji Zainab da Sadiya suna yada min magana bayan kin wuce..
A haka kikeso In kwashi k’afa in tafi bikin y’arta har Kaduna?
Besides kin san ba ishashshiyar lafiya gare ni ba those days
kar inje su yi mini wani abun itama Hajiya ta d’aura da nata inje jinina ya hau!.
Dan Allah na rok’eki da girman Allah ku barmu a nan Ai naji Baaba Talatu ma tace
‘In an d’aukota daga Kaduna a nan gidan Kaka za a fara sauk’a saboda y’an tsofaffin da basu je su Kadunan ba!
Bayan an d’auke su sai a wuce gidanta’.
Nayi miki alk’awarin k’arfe takwas zan shirya ga anko na nan ma na wunin kai amarya an d’inko…duk inda takwas da rabi tayi ina gidan Kaka kuna zuwa sai mu wuce tare gaba d’aya.
Banda abinki ma, In dai ke da Sakina kunje ai kamar munje ne ko?”
Ta k’arashe maganar da d’an murmushi a kan fuskarta.
Murmushi Ummun itama tayi.
Ba dan ransu ya so ba
haka suka hak’ura akabi tsarin yadda Maman tace…
Sakina itama daa cewa tayi ba zata je ba
Sai da Mama ta lallab’a ta tukunna ta yarda zata je d’in.
Kamar minti talatin da yin wayar Umma da Anty Zainab sai gata nan!
Tana shiga d’akin Umma tace
“Yauwa Zainab!
Na gode da kika bani lokacinki,
mu je ko?”
Tayi maganar tana k’ok’arin tashin Jalila wadda tayi bacci.
Dakatar da ita
Anty Zainab d’in tayi ta hanyar cewa
“Tsaya tukunna
Yanzun nan Baban Khadija ya kira yanata faman masifa
wai danginshi suna chan sun fara mitar ya uwar amarya har yanzu bata k’arasoba!
Yanzu haka da nake yi miki maganar nan drivern da akayi shata zai kaini Kaduna yana bakin k’ofar gidan Kaka yana jira!.
Yace ba zai you ince sai gobe zan je ba!
Dole in tafi a yau…
So kiyi hak’uri ba zan iya rakaki asibiti ba gaskiya
Amman ga wannan”
Tayi maganar tana zaro pt a jakaar ta, sannan ta ci gaba
“Yanzun nan na tsaya na siya na taho dashi..
Scanning ne kawai ba zai nuna ba!
Amman ciki in dai akwai shi ko na kwana biyar ne to zamu gani.
Tashe ta yanzun nan ta gwada mu gani.”
A hankali Umma ta sauk’e ajiyar zuciya sanann ta k’araso ta tada Jalila.
Dalla dalla Anty Zainab ta yiwa Jalila bayanin yadda zata yi amfani da abun
sannan ta d’aura da cewa
“In babu za muga layi d’aya
In kuma akwai za muga layi biyu”
Karb’a tayi ta fita zuwa band’aki!
Kamar minti biyar haka sai gata ta dawo..
Anty Zainab ta mik’awa, cikin rawar jiki Umma ma ta taso tazo ta hau lek’awa…
A tare suka saka salati kafin Umma ta zauna dab’ass!!! A k’asa ta d’aura hannu a ka ta fashe da kuka!.
Da sauri Anty Zainab ta tsugunna ta shiga lallashinta…
Ita kam Jalila tunda ta shigo ta mik’a musu suka karb’a ta wuce kan gado ta zauna ta rafka uban tagumi!
So take tayi kuka amman ta kasa…
Wani irin tuk’uk’i ne yake taso mata daga k’asan zuciyarta!
Inda ace zata ga Auwal yanzu wallahi da sai ta kasheshi!
Ba abunda yake b’ata mata rai irin yadda ya dinga muamala da ita a wulakance! Kamar ma irin kyamarta d’innan yake yi sai kace an yi mishi dole!.
Da kuma yadda ya fito k’iri k’iri ya zazzage ta ya gurza mata rashin mutunci!!!
Taya zata haifi cikin nan??
Ta san ko sama da k’asa zasu hadu Auwal ba zai tab’a accepting cikin ba!
Ace ma ya karb’a yayi accepting….shikenan ta zama bazawarar k’arfi da yaji kenan??
Dan ita dai ba zata zubar da ciki ba!
‘Tana tuna wani lokaci…akwai wata a ajinsu…
Ta tab’a yin ciki!
Malamin da yayi mata ya kwasheta zuwa wani asibiti
dan basaso makarantar ta sani da kuma iyayen ita Yarinyar. Haka nan aka zo garin cire ciki Yarinyar ta mutu!.
Sannan Akwai wata ma a bayan layin su
Itama b’arin ciki kawai tayi ta mutu…..’
Wata zuciyarce tace mata “ba gara to kema ki mutun ba!
A haka ma tun baki haihu ba kina tunanin ta yaya Arshaad zai soki
Ballantana yanzu idan kika haihu ko kallon ki ba zai yi ba.“
Tunda Jalila take a rayuwarta bata tab’a jin tashin hankali irin na wanann rana ba!
Ji take inama ace ba a haliccetaba
Banda wani irin huci da ajiyar zuciya ba abunda take yi…
Chan!!!
Kamar an tsikareta, da mugun gudu suka ga ta mik’e tayi waje
dan haka suma suka tashi
suka rufa mata baya.
Da kyar bayan sun fita suka jiyo motsinta a kitchen dan kafin su fito har ta b’ace musu kamar wata aljana.
Da gudu kamar mahaukata haka suka nufi
kitchen d’in!
Tun kafin su k’arasa warin d’an kalanzir d’in da suke kunna icce da shi ya bakwanci hancinansu…
Suna shiga suka ganta tana k’ok’arin kunna ashana tana wani irin kuka zata had’iye zuciyarta!
Ga jikinta sharkaf!! Ta kwarara kalanzir ta koina.
Umma kasa k’arasawa wajen tayi…
Ba abunda take jin tsoro sai ‘Kar taje tana matsawa Jalilan kuma ta kunna ashanar taje
wutar ta tashi da ita!’.
Anty Zainab ce tayi k’ok’arin k’arasawa ta gudu ta kwace ashanar ta jefar sanann ta d’auketa da mari!!!
A take ta durk’ushe a wajen tana wani irin kuka abun tausayi.
Sai a lokacin Umma ta samu ta iya matsawa kusa dasu.
Tana zuwa tasa hannu ta d’ago ta ta rungumeta a jikinta tana shafa bayanta tana lallashinta.
Da kyar suka samu tayi shiru.
A hankali Umma ta d’ago fuskarta tana shafawa, tace
“Ki kwantar da hankalinki ki nutsu ki daina kuka ki bani hankalinki mu nemo mafita!
Sannan dan Allah kar ki sake yunk’urin kashe kanki Jalila
Ni Sadiya na yi miki alk’awarin ba zaki wulak’antata sanann zan bi miki hakkinki za kiyi dariya za kiyi farin ciki in shaa Allah
Amman fa sai kin nutsu, sannan sai kina raye tukunna za kici ribar bak’in cikin nan da kike ciki a yanzu!
Kin ji ko?”.
A hankali ta d’aga mata kai tana sauk’e wasu tagwayen ajiyar zuciya.
Nisawa Umma tayi kafin tace mata “Jalila ko da wasa bai tab’a gaya miki sunan unguwarsu ba?”
Shiruuu, ta d’anyi kamar tana tunani…fuskarta tayi mugun kumbura idanunwanta sun k’ank’ance sun yi jazir!
A hankali tace
“A jikin duk motocin da yake amfani da su Ina ganin ‘MT’ a sak’ale a jikin glass d’in gaban motar tashi
Amman turarene irin wanda ake sawa a d’aki ko band’aki ko office dan k’amshi yake fitarwa na tab’a tab’ata ma hannunna ya kwana yana k’amshi.
Sannan na tab’a ganin wasu takardu a motar tashi shima an yi rubutun ‘MT’
Babba sosai!
Sai kuma wasu bayanai a k’asa a cikin envelope mai kyau irin mai shara sharan nan.
Inaga ko yana da alak’a da company d’in ne…watak’ilan in mukaje ‘MT’ d’in mu sameshi a chan.”
Ajiyar zuciya Umma ta sauk’e kafin ta juya wajen Anty Zainab tace
“Kiyi tafiyarki kawai Zainab
Kar yayi ta jiran ki!
Zan dinga gaya miki halin da ake ciki ta waya..
Bara mu tafi MT ni da Jalilan.”
Ajiyar zuciya Anty Zainab ta sauk’e kafin tace
“Kar ki bari ya raina muku hankali!
Ku bud’e mishi wuta sosai!!
Jalila kar ki bari ya ga lagonki
ki daina wannan kukan.
Sannan kar ki k’ara attempting abunda kika so kiyi yanzu
Komai yayi safi maganinshi Allah kin ji ko?”
A hankali Jalilan ta d’aga mata kai.
Shafa kanta tayi tana d’an murmushi tukunna ta yi ma Umma sallama ta wuce.
Tana fita Umma ta kamo hannun Jalila suka fito a kitchen d’in.
Sai da ta dallawa k’ofar d’akin Mama harara a ranta tace
“Munafukai na san sarai kuna jin mu.”
Tukunna suka shige d’aki….
Babu abunda yafi bawa Jalila mamaki irin yadda taga Umma ta had’e mata kayanta kakaff!! Hatta inne wears!
Gashi Umman tace mata
“Kar ta kuskura tace komai
Kawo yanzu har zuwa suje wajen Auwal a gama magana kar tace komai!
Ta bar mata komai a hannunta.”
Sai da ta had’a Ghana most go uku manya!!
Tukunna ta fice taje tayi wanka ta dawo d’akin.
Tana gama shiryawa ana kiran azahar, dan haka ta cewa Jalila “ta taso su tafi!
Kar su makara ya tashi a office d’in.”
Umman ce tayi jigilar kayan ta fitar ta tsare musu adaidaita sahu suka kama hanyar Mai Turare & co.
A bakin tangamemen had’add’en company d’in mai adaidaitan ya sauk’e su.
“Hmm…yana aiki a nan ai dole yayi ta wasa da kud’i yana yiwa mutane rashin mutunci.”
Umma ta fad’i hakan a ranta
bayan ta gana k’arewa k’ererren ginin kallo.
Kayan su suka kwasa
sannan suka sallami mai adedeta sahun suka nufi bakin gate d’in shiga…
Suna zuwa wani soja a cikin masu gadin ya fito ya tsaresu
yana yi musu kallon tara saura kwata kafin yace
“Where to? Maam!”.
Sai da ya sake maimaita tambayar tukunna tace
“Muna son ganin Auwal.”
Da mamaki yake sake k’are musu kallo dasu da kayansu kafin yace
“Sir Auwal?
Mai Turare?”.
Da mamaki Umma ta d’an juya ya kalli Jalila da sauri sai kuma ta juyo gareshi tace
“Yes yes shi.”
Dariya sojan yayi
kafin cikin gurb’atacciyar Hausar shi yace
“Bar nan wajen!
Bana son raina.”
Yana gama fad’in haka ya juya
Sai a lokacin Jalila tace “sir”
Yana juyowa ta mik’a mishi wayarta.
Kallonta yayi kafin yasa hannu ya karb’i wayar
Da mamaki yake kallonta yake kallon hoton da suka d’auka ita da Auwal a cikin mota!
Yafi minti d’aya a tsaye yana kallonta da hoton
Daga k’arshe ya sauk’e ajiyar zuciya yace “ok”
ya mik’a mata wayarta ya juya yayi ciiki…
Kallon hoton take yi a hankali tana shafa fuskar wayar
tana tuna lokacin da ta d’auki hoton…
Lokacin zuwan sa na biyu ne,
tanata y’an hotunanta Ita d’aya shi kuma yana driving,
ba tare da ya sani ba ta d’an karkato ta d’auke su.
Gashi nan ya fito tarr! Amman iya gefen fuskarshi sai dai duk wanda ya sanshi yana gani zai san shin d’in ne….
“Jalila kar fa ki fara son Yaron nan!
Dan in dai kina sonshi to ba zaki iya abunda na shirya ba.
Ki daina kallonshi ki goge hotonnan tunda yanzu na san ya gama aiki.”
Muryar Umma ta katse mata tunani.
Murmushi kawai tayi ta maida wayar lock ta rik’e a hannunta.
A chan office kuwa!
Ana gayawa Auwal wata na nemanshi a waje yace “Ace musu aiki yake yi!”
Shi bai ma kawo Jalila bace ba yayi tunanin a cikin tarin y’an matanshine wata ta boyisa har office, dan sun saba,
sai dai kuma yayi mamakin yadda bata shigo har office d’in nashi ba
Instead
Ta tsaya a gate!….
Kamar bayan minti goma sai ga mai gadin ya sake dawowa.
Yana zuwa yace matar da take tare da Yarinyar tace ace mishi “Dangin Mamansa ne suka zo daga k’auye!”
“Dangin Adama?”
Suka ji muryar Granpa wanda ya shigo zagaye yanzu a bayansu!!!!
Sai da Auwal yaga wani duhu na y’an sakanni…
Tukunna
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 30 Chapter of 32