Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Tuni Jiddah tabar kuka masu hawaye sai dai kukan zuci, a haka aka fiddota wajen motocin d'aukar amarya da akalla sunkai 25, dan haka kowa yasamu waje aka shilla da amarya. Y'an anguwa wasu Na sambarka wasu Na tausayin Jiddah. ('('('('('('('('('('(' *Gidan Alhaji Garba mai tabarma* babban gidane sosai Wanda kallo d'aya zakai masa ka tabbatar da maishi ya tara. Bayan an wangale musu k'aton gate d'in gidan kusan motoci goma suka sami wajen shigewa ciki harda ta amarya. Tarba suka samu mai k'yau daga dangin Alhaji Garba, wad'anda suketa fatan ALLAH yasa wannan karon an dace Jiddah tazo kenan. 6angaren Jiddah aka kaita, Wanda ya k'awatu da kayan alatu tamkar suyi magana, komai yaji zam, duk had'uwar gidan Alhaji Garba da dukiyar cikinta hakan baisa dangin Jiddah jin zasu tayata murnaba. Basu wani jimaba suka juya, akabar Jiddah ita kad'ai kudundune cikin hijjabi daboda zazza6i Mai tsanani daya sake rufeta. Kusan mintuna ashirin da tafiyar y'an kawo amarya Jiddah tafara jin hayaniya sama-sama, abinda ya dameta shine matsalarta, dan haka bata damu kanta dasonjin mike faruwaba. Zuwa wani lokacima sai taji gidan tsitt tamkar babu kowa a cikinsa. Tun tana sauraren k'arar AC har barci 6arawo ya saceta a haka, dama Allurar bata gama sakintaba. *Ango* Kusan k'arfe sha biyu da rabi ango yashigo gidan, lokacin gidan yay tsit kowa yakama gabansa, Daga y'ay'ansa sai matarsa hajiya deluwa. Fakin motar yay yafito hannunsa d'auke da k'atuwar leda, Kai tsaye sashen Uwargida ya nufa Wanda yafi kowanne sashe girma a gidan. Tsit babu motsin kowa sai AC da TV daketa faman aiki, ko ina tsaf tamkar ba taron biki akayiba, koda yake yasan babu wani Wanda ya Isa taka mata sashe da sunan zuwa biki. Ledar hannunsa ya ajiye yanufi corridor d'in dazai sadashi da d'akunan barcinta. Na farko yafara lek'awa babu kowa, Na biyu ma haka, sai a Na uku ya hangota zaune a saman gado, hamshak'iyar macece wadda ta amsa sunanta Hajia, daka ganta kasan tagama jik'uwa cikin nera, ta girma sosai sanan tanada k'iba dai-dai gwargwado, dan bawata k'atuwa baceba can, Ammafa babu k'arya Y'ar gayuce, dan ko shirin barcin Nata kad'ai ya Isa tabbaatar maka hakan, gata Fara tas masha ALLAH. Manyan idanunta ta sauke akansa, kafin tasaki wani murmushi cikin kissa tafara fad'in ?Kaga ango Mijin Amarya Hauwa'u?. 'Dan Murmushin yak'e Alhaji garba yayi, ya zauna kusa da ita k'asan zuciyarsa Na mamakin canjawarta akan wannan auren nasa, Ada inhar zaiyi aure zata d'aga hankalinta, randama aka kawo amarya bata Barin kowa yayi barci Mai dad'i a gidan, amma tunda yafara maganar auren Jiddah ko kad'an bata ta6a nuna damuwartaba, hasalima lefen Jiddah itace ta had'oshi matsayin gudun mawarta. Fuskarsa d'auke da murmushi yad'an shafa kumatunta. ?Uwargida ran gida!?. Fari tayi masa da fararen idanunta, kafin ta furta ?Fad'I kanka tsaye alhajina?. Yad'an dara, ?Kinyi k'yau gimbiya ta, sai nakejima tamkar ked'in aka kawomin a yau?. Wani shegen murmushi ta Saki, ?Alhajina rufamin asiri, kaga tashi katafi wajen matarka, kar zumud'in son ganinta yasaka juyemin kalaman daka tanada dominta anan wajen?. ?Haba gimbiyata, aike kin wuce aimiki jirwaye da zancen wani, duk abinda yafito zuciyar Abubakar a kanki to lallai nakine, babu Mai kamanceceniya dake balle kamoki?. Murmushi takuma Saki tana kamo hannunsa ta sumbaci tsakkiya, kafin yagama dai-daita da shiga sak'on Nata ta haye saman gadon sosai taja bargo da fad'in ?Ango mukwana lafiya, kadai bimusu yarinya a hankali karkai mata irinna hajarah, nasanka yanzu haka kaje ka d'irko magunguna?. Wata Y'ar dariyar mugunta yasaki yana mik'ewa, ?Hajjaju akwaiki da tsokana wlhy, ni sharri kikemin babu wani magani danake sha, Na barki lafiya?. Cikin watsama bayansa harara da murmushin mugunta tace ?A gaida amarya?. Fita yay yana fad'in ?zataji?. Daga nan sashensa ya nufa Wanda shima ya had'u, sai dai baikai girman Na hajiya deluwa ba ko kad'an, had'uwa kawai zai iya nuna masa. Sai faman zabga murmushi yake yana cire kaya. Wanka ya shiga kusan mintuna talatin sannan ya fito, ya saka jallabiya bayan ya goge jikinsa, yakawo turare ya fesa. Ledar daya shigo da ita ya bud'e yaciro wata karamar leda aciki, saida ya bud'e firij ya Ciro gorar ruwa sanan yakoma bakin gado ya zauna yana zazzage abinda ke ledar saman gadon, magungunane masu d'an yawa, ya 6alli kusan kala shida ya shanye yana zabga murmushi, sai shafar gemunsa dayasha aski yakeyi, tashi ya kumayi ya d'auki wata gorar da aka had'a tsumin magungunan gargajiya a ciki nanma yasha sosai sanan ya d'auki babbar ledar ya fito zuwa sashen amarya Jiddah. Lokacin daya shigo sashen Jiddah tsit nanma, dan ita koma TV babu a kashe komai yake, sai k'amshi irin wanda akasan d'akin amarya dashi. Bakinsa har k'arshen kunne ya Isa bedroom d'in Jiddah, sai wani lasar la66a yake tamkar tsohon maye=??=?#?............ '?? Yau dai nasan Naga idi=??>?z??& @& *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*=?-?=?O???

Chapter 9 of 31