Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
bayan d'aurin aure aka gudanar da gagarumar walima wadda malamai suka zazzaga wa'azi akan aure da rayuwar ma'aurata, tareda jan doguwar Addu'a ga wad'annan ma'aurata. Amarya Maimunatu tana cikin farin cikin mallakar cikar burinta, yayinda ango baka gane nasa yanayin. Bayan kammala walima aka mik'a amarya d'akinta tareda fatan alkairin ALLAH yasa bad'i adawo suna............... '???#?>?#?, ALLAH ya taimakeni ba a had'a daniba nima=???& @&._* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*=?-?=?O????-??& @&. ('('('('('('('('('('(' A gidan Umma kam bayan biki da kwanaki uku kowa ya Kama gabansa, aka barsu su kad'ai, daga ita harsu Walida babu Mai isashshiyar lafiya, kowa damuwa da tausayin Jiddah da kewarsa ta isheshi. Washe Gari dole Uncle yahaya yanemo likita yazo har gida ya sakama Umma k'arin ruwa saboda batajin dadi sosai. Bayan la'asar Zarah ta cire Mata saboda ya k'are, ruwa Mai d'umi suka had'a Mata tai wanka, suna tsaka da gyaran gidan saiga Abba. Kowacce kai a k'asa ta gaidashi. Bakinsa ya ta6e ya wuce d'akin Umma, dan ya lura yau su Zarah awani yanayin jin haushi suka gaidashi. Umma na zaune tana cin faten waken da Maman Sadiq ta aiko Mata Abba ya shigo, kallo d'aya taimasa ta d'auke kanta. Zama yay shima yana wani kumbura. Umma tace, ?Ina yini?. Bai amsaba, sai tambaya daya jefoma Umma. ?Yagana waike aurar da y'arne yasaki maida kanki haka? Lallai aiki ya sameki ashe?. Wani murmushin takaici Umma tayi kafin ta d'ago ta kalleshi ido cikin ido, ?Koma minene ya maidani haka wannan ba matsalarka baceba, saidai inason maka tambaya d'aya. Shin nawa Alhaji Garba yabaka kabashi Jiddah??. Gaban Abba ne ya fad'i, bakinsa Na rawa yace, ?Yagana ban gane wannna maganar banzar takiba? Dan Zan bada auren y'ay'ana sai an biyani kud'i??. ?Humm Alhaji kenan, bar ganin ka fini shekaru wlhy kar nake kallonka, a ina kasamu kud'in biyan banki bashin da kaci musu??. Harara ya watsa mata yana huci, ?Shak'eni Na fad'a miki mana yagana??. ?Aiba saina shak'eka bama, zaka fad'ane cikin kwanciyar hankali. Wlhy Alhaji ka farka daga nannauyan barcin daya d'aukeka, wato ka ciwo bashin kud'i a banki lokacin da suka baka Na kar6a yayi bakadashi ko? Saboda kakashe kud'in akan matarka da y'ay'an Sonka yanzu anema kabada kud'in ko kaddarorinka hankalinka ya tashi ko? Karasa ina zaka nufa matarka tabaka shawarar Neman bashi wajen Alhaji Garba. Shikuma dayake tsohon banzane kaje da buk'atar kud'i yabuk'aci musanyarsu da yarinyata saboda ta tsole idonsa, wlhy danasan auren manufa kayi da Jiddah ko sama da k'asa zata had'e baza'ayi aurennanba. Amma ko yan.............? Wata razananniyar tsawa ya daka Mata yana mik'ewa a zabure, ?Daga bakin wane mak'aryaci wannan zancen ya fito? Ko rantsuwa nayi babu kaffara nasan yahaya ne........? ?Kwarai kuwa nine??. ?Cewar Uncle yahya dayake shigowa yanzu?. Daga Umma har Abba juyawa sukai suna kallonsa, fuskar Uncle yahya a matuk'ar d'aure yacigaba da fad'in ?Wlhy ko'a mafarkina ban ta6a zaton rashin son gaskiyarka yakai hakaba Yaya, yanzu dan ALLAH har nawa Jiddah take da zakayi wannan kulla-kullar akanta? Ashe har mutane masu mutunci sukazo Neman aurenta amma ka shirya musu k'arya? Namaka magana ka gaggayamin son ranka, Anya Yaya kana tsoron gamuwarka da ubangiji kuwa??. ?A'a bana tsoro dan Ubanka, shin komadai kaine Ubansu Jiddah ban saniba??. Daga Uncle yahya har Umma a tsorace suke kallon Abba. Muryar Umma Na rawa alamar tahowar kuka tace, ?Alhaji kana cikin hankalinka kuwa? Mu kake jifa da wad'annan munanan kalamin??. Shiru yay yakasa bata amsa saboda ya fahimci 6acin rai ya sakashi yin kato6ara..... Uncle yahya yay murmushin takaici yana fad'in ?Karki wani damu kanji da kalamansa Yagana, idan yamana sharri wannan yarage tsakaninsa da Ubangijinsa, dan shine zaimana hisabi, wannan kuma ni bazaisa naji komaiba saboda ban ta6a kwatanta aikatawaba koda a zuciya balle zahiri, ka saka a ranka kuma alhakin wad'annan bayin ALLAH kawai ya isheka ishara inhar baka rok'i gafararsu ba ka gyara mu'amularka dasu. Maman Nafisa ga magungunanki nan, ni nawuce gida?. Uncle yahya nagama fad'a ya fice abinsa. Umma ma tashi tai ta shige uwar d'aka abinta. Da sauri Abba ya bita. Da sauri tace, ?kaga fitarmin a d'aki zakari, idan kuma ni kake buk'atar nafita to lallai yanzu Zan barmaka gidanka tafiyarda har abada bazan dawoba koda hakan yana nufin Zan mutu da igiyar aurenka a kaina?. Baki ya bud'e zaiyi magana tai saurin janyo hijjab d'inta ?ALLAH ya baki hak'uri nizan fita?. Bai jira amsartaba ya fice. Duk abinda ke faruwa su walida naji, dan haka suka had'e kai a tsakar gida suna dirzar kuka. Itama Umma yana fita tafad'a kan gado ta fashe da kuka maiban tausayi. ('('('('('('('('('('(' Tunda Jiddah ta koma sashenta taketa juya maganar hajia deluwa a zuciyarta, da mamakin kalamun saurayi da hajia ta Kira da Ashir Wanda take kyautata zaton d'ansune kenan. Lallai ita taga takanta, mutanan gidan kowanne da nashi matsalar.... Motsin dataji a bayantane ya sakata saurin juyowa, gabanta yay mummunar fad'uwa saboda ganin Ashir. Murmushi ya sakar mata yana matsowa gab da ita, ?Auntyn mu gaisuwar bangirma nazo kawowa?. Yay maganar yana d'aga Mata gira d'aya. Baya Jiddah ta matsa sosai jikinta harya Fara tsumar tsoro, Ashir ya kuma kwantar da murya tamkar yana gaban matarsa ko budurwa yace, ?Wani ya ta6a fad'a miki kinada k'yau kuwa babie? Da sabon jini kika dace babie ba dad ragowar basirba, kizo nabaki dukkan farin ciki dan nine dai-daike nasan dad babu abinda zai iya miki wlhy, shegen aure-aurensane kawai da basa k'arewa......?. Duk maganarnan da Ashir yake jikin Jiddah 6ari kawai yake, dan tsaf tagama fahim manufar Ashir a kanta, babu abinda takeyi sai Addu'ar Neman tsarin ALLAH daga shed'ancinsa, yayinda tuni hawaye sun cika Mata idanu. Ganin Ashir yamatso zai kamata yasata afkawa d'aki a guje Ashir ya take Mata baya.............. '?#?>?#?>?-? *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*=?-?=?O???

Chapter 10 of 31