Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ALLAH yay mana arzik'in sauro kam tamkar d'angwate da kud'i?. Dariya sukayi su duka har Jiddah, ta rufe tukunyar tuwon data gama tuk'awa tana d'an yarfama rutsin wutar ruwa danya rage zafi kar tuwon ya k'one. ?Y'ammatan Umma ya kuka baro Aunty tamu dasu Affan??. ?Lafiya lumi wlhy Yaya Jiddah, tamace ace miki ta gode da cika alk'awari?. Murmushi kawai Jiddah tayi, dan tasan laifinta. ?Wai ina Umma??. ?Cewar Zarah dake k'ok'arin shiga bayi?. Jiddah tace, ?Taje gidan Uncle yahaya, Maman Sadiq ce k'irjinta ke ciwo, shine taje dubata?. Walida da Zarah suka had'a baki wajen fad'in ?Ayya ALLAH ya k'ara lafiya to?. ?Amin?, Jiddah ta amsa. Ledojin walida ta d'auka takai cikin d'aki tana fad'in ?Yaya Jiddah mi zamu tayaki dashine? Naga yau aikin yamuku dare?. ?Wlhy kuwa auta, amma nama gama, dan miya na farayi sannan, sai dai idan tsakar gidannan zaki share a kunna maganin sauro musami wajen zaman hira?. Walida ta amsa da to tana nufar inda tsintsiyarsu take. Zarah ma koda tafito sai tace bara ta kwashe tuwon ita kuma. Haka suka k'arasa dukkan ayyukan suna hirarsu a nutse, dolene su burgeka, dankuwa akwai shak'uwa da k'aunar juna mai yawa tattare dasu, hirar tasuma duk akan Auntynsu ce Nafisa. Ana kiraye-kirayen Sallar magriba Umma ta shigo, a lokacin su Jiddah sun gama komai, sai k'ok'arin d'aura alwala da sukeyi, amma banda Zarah dake fashin salla. Atare suka amsa sallamar Ummansu, yayinda suke mata sannu da zuwa da tambayarta mai jiki. ?Da sauk'i Alhmdllh, y'an yini sai yanzu muke ganinku??. ?Wlhy kuwa Umma, aunty dasu Affan Na gaisheki, yanata kukama saiya biyomu gashi gobe akwai makaranta?. Y'ar dariya Umma tayi tana cewa, ?Ja'iri yau kuma? Amma ranar dayake yaga babansa ai babu yanda banyi ya zaunaba yak'i. Yaya kuka baromin yarinya ta??. ?Lafiya lau take Umma, ammafa ni sai naga aunty Nafisa kamar laulayin ciki take??. Harara Jiddah ta zubama Zarah mai maganar, ?O ke Zarah, wlhy bakida kunya, yaushe kikai girman gane mai ciki??. ?Tab lallai, kaji Yaya Jiddah da wani batu dan ALLAH, cikin saikace wani abu........? Hijjab Umma ta cillam? Zarah tana fad'in ?Zarah k'aniyanki kinji, Anya kuwa ba aure zansa ayi mikiba??. ?Wlhy dama yafi Umma, dan Idonta kullum k'ara fetsarewa yakeyi yarinyar nan?. Waleeda dake alwala ta kwashe da dariya, yayinda Zarah ta kwad'a Mata harara. ?A'a nikam Yaya Zarah karki huce kaina, bani nakar zomanba?. Haka kullum suke cikin tsokanar juna da wasa da dariya, hakan kuma baisa raini yashiga tsakaninsu ba, Ummansu ta maidasu tamk'ar k'awayenta, sune abokan hirarta sune shawararta, shiyyasa suma basuda wasu aminai a waje sai ita, saikuma a tsakaninsu su biyar. Sune abokan juna, sune aminan juna, sune y'an uwan juna. *_Dare_* Da daddare suna zaune a tsakar gida sunacin tuwo, yayinda Zarah kema Umma bayani akan kayan da sukazo dasu. ?Umma tsarabar Dadyn Affan ce Aunty tace mu kawo, takuma bamu kud'in makaranta tace gobe muje mu biya mukoma makaranta?. Umma tace, ?ALLAH sarki Nafisa baiwar ALLAH, ALLAH ya saka Mata da alkairi, yamata albarka itada zuri'ar ta daku baki d'aya, ALLAH ya cigaba da had'amin kanku kunji?. ?Amin Umman mu?.suka had'a baki wajen amsawa. Kayan aka shiga bud'ewa, sabulan wanka da wanki, sai man shafawa da omo, kayan shayi da maltina rabin katon, da biredi manya guda uku da kud'in makarantar su Zarah sai kaji biyu gasassu. Addu'a sukaita zubama yayar tasu, Umma ta kirata tai mata godiya da addu'a, tace aima dadyn Affan godiya shima. Sund'an ta6a hira zuwa tara na dare suka mik'e domin kwanciya, saboda sauro daya damesu gashi kuma su Zarah zasu makaranta gobe. ('('('('('('('(' Da wuri su Walida sukai shirin makaranta, sannan sukai Karin kumallo da d'umamen tuwon jiya da Jiddah ta tashi da wuri ta d'umama musu. Bayan wucewarsu makaranta tagyara gidan duka da taimakon Umma, dukdama gidan bawani babba baneba. Saida tagama komai itama zuwa tara da rabi tai shirin tafiya Islamiyya. Tsaf tai shirinta cikin Uniform d'inta kalar ruwan toka, (ash color) yad'au guga sai d'aukar ido yake, turarenta da Aunty Nafisa ke k'ok'arin saya musu ta fesa kad'an, sannan ta d'aura Nikab, saidai bata sakeshiba tafito rataye da jakarta mai d'an tsawo kamar suwaga. 'Dakin Umma tashiga da sallama, tana zaune da alama sallar walha ta idar. ?Umma naga bakiyi Addu'a ba, gashi nakusa makara, nawuce saina dawo?. Kai Umma ta d'aga Mata batare da tayi magana ba, dan batason katse addu'arta. Jiddah Na fitowa soro ta Saki nik'ab d'inta tare da gyara hijjab d'inta tai addu'ar fita daga gida sannan tafito. Tafiya take a nutse kuma a sanyaye, kanta a k'asa dukda ta sakaye fuskar tata da nik'af. Kullum haka take cikin suturta jikinta, dayawan y'an anguwar a haka suka Santa, saika Tara mutum goma basu iya siffanta maka kamannin fuskartaba, saidai a tafiya kokuma kwatancen ta da suna mai saka hijjab har k'asa da nik'ab, amma mafi yawancinsu sun manta da kamanninta, dan tunda tafara mallakar hankalinta takoma suturta fuskarta.............. '?????p?>?p?>?p?=?L??#??& @&?& @&._ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*=?-?=?O???

Chapter 2 of 31