Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kiranta yana shigewa bedroom yabar Umma a falo. Sai dai kuma har wayar ta tsinke bata d'agaba. Kuma kiranta yayi.
Hajia Hindu dake kallon wayar taja guntun tsaki sannan ta d'aga. Ko sallama babu tace, “Alhaji kana inane?”.
Dukda tambayar tabashi haushi saiya danne, saikace wani yaronta. Amma a fili sai yace, “Haba Maman kalifa ko gaisuwa ma babu?”.
Dogon tsaki taja, a harzuk'e tace, “Kaga malam nifa ba wannan ya sakani kiranka ba, yara suncemin tun jiya baka gida, gashi yau sun tashi motarsu ta zuwa makaranta babu mai........”
Cikin nuna damuwa da 6acin rai yace, “Amma driver d'innan d'an iskane, shine bazai kirani a waya ya sanarminba?, to lallai bazan yarda da wannan iya shegenba......”
Hajia Hindu ta katse masa magana da fad'in, “Aiba laifinsa bane shi kad'ai, inda jarabarka bata motsaba katafi wani waje ka kwana hakan zai faru? Kamayi duk yanda zakayi kakaimin yara makaranta kafin su makara”.
Kafin yayi magana ta yanke wayar. Ya dafe kansa saboda takaicin yanda Hindu ke datsa masa magana tamkar boyi-boyinta. Da hanzari yahau shiryawa, dukda ba zaman gidan yakeba yanada kaya a gidan.

Lokacin daya fito Umma na k'ok'arin had'a masa shayi da kayan tea d'in da Nafisa ta kawo musu.
Ganin zai fice tayi saurin fad'in “Abban Nafisa ina kuma zakaje ga Karin kumallo ina had'a maka?”.
“Kinga barshi Yagana, su kalifa zanje nakai makaranta karsu makara, motar da ake kaisu makaranta babu mai”.
“To”.
Kawai Umma tace masa taja bakinta tayi shiru. Shikuma ya ajiye dubu uku a hannun kujera yay ficewarsa batareda yayi bayaniba.
Ko motsi Umma kasawa tayi a wajen balle tasamu damar d'aukar kud'in. (Nace,  Humm =ØAÞ).

('('('('('('('('('('('


Lokaci da Aliyu ya fito daga cikin gida malam ya shige falonsa da k'ofar ke a zaure Na biyu.
Sallama yayi ya amsa masa tare da bashi izinin shiga.
Malam dake kishingid'e bisa lallausar dardumar dake wani sashe Na falon ya d'ago ido yana kallon Aliyu bayan ya rufe littafin dake hannunsa. Zama Aliyu yayi a gefen dardumar, malam yaymasa alama daya matso kusa dashi. Matsawa yay yana guntun murmushi.
Saida suka nutsu malam yace, “Aliyu!”.
Cikin sanyinsa yace, “Na'am baba”.
“Aliyu ina muka kwana akan batun aure? Nazata a shekara d'aya da dawowarka yaci ace kazomin da zancen samun Matar aure, amma sainaji tsit, mike faruwane?”.
Kansa a k'asa ya kasa kallon malam, cike da kunya yace, “Baba ai har yanzu......”. Saikuma yay shiru.
“Har yanzun mi?”. Cewar malam yana kuma tsareshi da idanu.
Aliyu yakuma k'asa da kansa. “Baba har yanzun banida tabbas akan samun......”. Nanma ya kasa k'arasawa.
Murmushi malam yay, dan ya fahimci inda Aliyun ya dosa.
“Ali kenan, to ai a ganina auren shine zai banbance mana hakan ko? Zamanka haka babu aure a matsayinka Na babban mutum mai koyar da ilimi da yad'ashi ko kusa bai daceba, aure shine cikar kamala Na kowanne d'an Adam, duk girmanka da mulkinka da addininka saika saka rigar aure kake kuma daraja a idon jama'a. Yakamata ka nemo Matar aure hakanan, idan kuma ni Na nemo maka to shikenan. Ni dai nabaka watanni uku idan ALLAH ya kaimu, daka dawo daga tafiyar nan da zakayi kafara shirin aure, inason kafin azuminnan mai zuwa ka ajiye iyali, kaje kayi shawara, zaka nemo kona nema maka kafin ka dawo?, idan kuma kanada wadda kakeso saika sanarmin, dan nikam nagaji da ganinka haka kana yawo babu aure”.
“Amin afuwa baba, insha ALLAH Zan duba, abinda Na yanke zakaji zuwa Safiya idan ALLAH ya kaimu, ALLAH ya huci zuciyarka”.
“To Alhmdllh, ALLAH ya kaimu lafiya, kenan kanada wadda kakeso?”.
”A'a baba”.
“To shikenan, kaje ina saurarenka zuwa safiyar. Akwai wasu littatafai da Malam Salis keso, nace masa Zan tambaya masa ko kana dasu”.
“To Baba wannene?”.
“Yafa bani a rubuce dama dan karna manta, duba littafincan ko ciki Na saka takardan”.
Mik'ewa Aliyu yayi zuwa inda kantar buks d'in malam take, ya bud'e littafin dake a jiye a k'asa da malam ya nuna masa. A shafin farko yaga k'aramar takarda dan haka ya d'akko yana nuna masa.
Kai malam ya jinjina alamar eh itace.
Aliyu yay masa sallama sannan yazo ya fice domin zuwa makwancinsa..

K'aramun gida dake jikin masallacin malam nanne gidan da yaran malam maza duk suka zauna kafin aurensu, ayanzu haka Aliyu ne kawai a ciki sai idan malam yayi bak'i ai musu masauki anan.
'Dakinsa dake can k'arshe ya bud'e da key ya kunna fitilar wayarsa sannan ya shiga da sallama, d'akine babba dake malale da kafet ruwan makuba (oxblood) sai k'atuwar katifarsa irin wadda ba'a sakawa a gado, sai firij da kantar litatafai da k'aramar wardrobe ta kayansa, d'akin babu wani tarkace dan mazaunin cikinsa ma'abocin tsaftane a koyaushe. Fitilar wayarsa ya kashe ya kunna wadda yake amfani da ita idan babu wuta, dandanan d'akin ya gauraye da haske.
Wata k'ofa danake k'yautata zaton bayice a d'akin naga ya shiga. Kusan mintuna 30 saigashi ya fito da alama wanka yayi.

Bayan malam Aliyu ya kammala dukkan uzurorinsa yazo ya zauna a gefen katifarsa yana jawo lap-top d'insa, yanar gizo ya Shiga domin duba sak'wannin jama'a Na neman fatawa da masu gaisuwa.
Ahankali yake binsu d'ai-d'ai yana dubawa, wata fatawar ta tausayi wata ta mamaki, wanima takaici ne tsantsa a ciki. Wasu yakan basu amsa, wasu kam wucewa kawai yakeyi. Wani sak'o dayaja hankalinsa matuk'a ya nutsu yana kuma dubawa.

*_Assalamu alaikum. Malam barka da warhaka, malam wlhy inada damuwa ne, kuma Na rasa Wanda Zan tunkara da ita. Mu hud'u iyayenmu suka Haifa, mata biyu maza biyu, nice nake bima babban wanmu sai k'anwarmu sai kuma autanmu, to malam yanayin rayuwar da muka tashi ta ak'idar boko saiya zamto ta6a jikin juna irinsu runguma da zama kusa da juna hakan ba komai bane nida y'an uwana, wannan kusancin mai tsanani saiya kaimu ga fara wuce iyaka har yayana yafara kwanciya dani, iyayenmu basu ta6a saniba konace ak'idar data lullu6e zukatanmu bata ta6a kai tunaninsu da zarginmu ba, malam yanzu haka maganar da nake maka inada ciki wata hud'u kuma bansan da shiba sai kwanaki 6 da suka shige, hankalina yatashi na nufi d'akin yayana danna sanar masa saina taddashi yana irin abinda yakeyi da ni da k'anwarmu dake bimin. Malam narasa yazan fassara wannan halin dabbancin namu, sakacin iyayenmu ne? kokuwa d'aukar ak'idar da bata dace da addininmu ba?, wlhy jinake tamkar Na kashe kaina malam, nayi nadamar rayuwata data y'an uwana, malam ka taimakeni da shawara dan ALLAH=Ø-Þ=ØOÞ<Øûß_*

Tagumi kawai malam Aliyu yayi ko yatsansa yakasa motsawa, sai had'iyar yawu yake mai d'aci da k'yar, idonsa ya kad'a yayi jazur, yama rasa yanda zai fassara wannan kwamacalar, anya wannan duniyar kuwa mutane na tunanin barinta?.
Kansa dayaji yana Sara masa ya dafe tare da ture lap-top d'in gefe ya zame ya kwanta a katifar.
Gaba d'aya zuciyarsa ta k'untata, wasu hawaye masu d'umine suka silalo masa a kumatu.
Yaja tsawon lokaci yana jujjuya abin a ransa, har agogo ya nuna k'arfe 1am bai iya runtsawa ba, mik'ewa yay yashiga toilet ya d'auro alwala ya dawo yafara jero nafilfili, a cikin sujudansa yana kuka da jaddada neman gafarar ubangiji. Sai kusan 3am ya idar, jin idonsa ya cika da barci yakoma saman katifar ya kwanta.
Amma maimakon barcin yazo saiya fad'a duniyar tunani akan maganar baba kuma, dukda wancan maganar yarinyar nata cin zuciyarsa a gefe. Harga ALLAH a yanzukam baisan kuma ina zai nemo mataba, dan tun tabon da Asma'u tabar masa har yanzu baigama gogewaba, gashima bashida tabbaci akan ingancin lafiyarsa har yanzu.
Kwanciyarsa yakuma juyawa yana ayyana kodai yabama baba damane kawai, k'ila shi yanada wadda ya hango ta dace dashi, tunda yasan baba bazai ta6a masa za6en tumun dare ba.
Da wannan tunanin barci ya saceshi bai fargaba............
'<Øûß








*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*=Ø-Þ=ØOÞ
?[11/20/2019, 4:16 PM] =ØžÜNoorunnisa=ØžÜ: *_Typing=ØòÜ_*



*_=Ø¡ÜHASKE WRITER'S ASSO...._*



*_=اÜMUTUM DA DUNIYARSA....!!=اÜ_*
_(ya dace ya gyara kansa)_



*_Bilyn Abdull ce>ØÝ<Øûß_*

*_[6......]_*


..............Da k'yar ya iya tashi da asubar farko, dan kansa ciwo yake masa, bayi yashiga ya d'aura alwala kafin ya fito ya canja kayan barcinsa zuwa jallabiya ruwan madara, yad'an fesa turare sannan ya fice.
Tunda ya dawo shike kiran sallar farko a masallacin, yauma kamar kullum zazzak'ar muryarsa mai cikeda sanyi ta karad'e anguwar. Koda ya kammala kiran salla ba zama yayiba, saida ya gabatar da nafila raka'a biyu kafin yay zaman karanta littafi mai tsarki. Ahankali mutane d'ai-d'ai suka fara fitowa, ciki harda malam.

Bayan an idar da sallar Asubahi Aliyu bai fitaba, zaman yin azkar na safe yay, saida ya kammala sannan yafito a massalacin. Shiga yay suka gaisa da Malam.
Kallo d'aya malam yayi masa ya karanci damuwa mai tsanani a fuskar d'an nasa, har zai mik'e ya tsaidashi ta hanyar kiran sunansa,
“Aliyu!”.
“Na'am baba” ya amsa yana waiwayowa ga malam.
“Dawo ka zauna”.
Bai musaba ya dawo ya sake zama kansa a k'asa.
“Mike faruwane? ko bakada lafiya?”. Malam ya tambayeshi cikeda kulawa.
Ajiyar zuciya M. Aliyu ya sauke, cikin sark'ewar murya yace, “Lafiyata k'yalau baba, kawai dai wani abune da ban ya girgiza dukkan kuzarina”. Shiru yad'anyi yana sauke numfashi da ajiyar zuciya, yayinda malam ya kafeshi da Ido amma baice komaiba. M. Aliyu yaci gaba da fad'in “Wani sak'one ya birkita dukkan hankalina wlhy baba...............” tiryan-tiryan ya shiga karantoma baba sak'on yarinyar jiya. Shi kansa baba maganar ta girgizashi, har gumi yad'an tsatstsafo masa a goshi, yanayinsa dukya sauya. Wata ajiyar zuciya ya sauke k'arfi yafara fad'in “Dolene ka girgiza Aliyu, duniyarnan cike take da curkud'ad'd'un abubuwa masu hargitsa tunani, babu abinda ke kusanto duniya sai alamomin tashinta, inaga kamata yay kanemi gidansu ita yarinyar, dan mahaifinta yakamata mu fara gani”.
“To shikenan baba insha ALLAHU zanyi k'ok'arin hakan”.
“ALLAH ya bada nasara, ya maganarmu ka yanke shawaran”.
“Baba kawai nabar maka za6i”.
“To Alhmdllh ALLAH yasa mu dace”.
“Amin” m. Aliyu ya fad'a hannunsa dafe da kansa.

A k'ofar fita daga Falon malam yaci Karo da yayansa Abubakar, hannu ya bashi sukai musabaha cikin girmama juna, Aliyu ya tambayi iyalansa da aiki kafin suyi sallama, Abubakar ya shige shikuma Aliyu ya fice.
Cikin gida ya koma ya sake kwanciya, dan kansa ya matsa masa da ciwo ainun.



('('('('('('('('('('('

Umma ta dad'e zaune zuciyarta Na suya, ta tsurama tea d'in data had'ama Abba ido, wai ko kunya baijiba a gabanta yake fad'in zaije yakai yaransa makaranta saboda motar da ake kaisu babu mai, bayan a gaban idonsa su Walida suka fita amma ko ALLAH ya kiyaye baice musuba? Sai yaushene Alhaji zai fahimci kuskuren da yake tafkawa a rayuwarsa? Kosai guri ya k'ure masane?. Wani lokaci takanji kamar bazata iya jure wannan zamanba, musamman idan ta kalli halin k'unci da yaranta suke a ciki. Sai dai kuma wani 6angaren tana duba wani Abu, yaranta sunkai girman da gidan mahaifinsu shine adonsu, dan burin kowacce y'a a nema aurenta tana gidan mahaifinta gaban iyayenta biyu. Wasu hawayen takaicine suka ziraro mata, tayi murmushin da iyakarsa hak'oranta tareda mik'ewa tahau tattare kayan shayin da Wanda ta had'ama Abban.
Sallamar Dauda ta jiyo a tsakar gida, ta amsa masa tana fad'in, “Ina zuwa Dauda”.
Daga tsakar gida ya amsa da “to”.
Tea d'in data had'ama Abba ta d'auka ta fito, Dauda ya rissina yana gaisheta, cikin sakin fuska ta amsa masa kamar yanda ta Saba. “Yau naga ka makara, ko Baku tashi a makaranta da wuri bane?”.
Dauda yace, “A'a muntashi, Na tsaya yin rubutune a allona”.
“To ALLAH ya taimaka, bara Na kawo maka abincinka ka karya saikai maza ka kaimin 6arzan masarannan dan ALLAH, yau sonake nayi dambu, kowa yagaji da shinkafarnan”.
“To hajia” dauda ya fad'a cikin girmamawa.
Kunu da fanke Umma ta kawo masa, ta had'o da shayin data had'ama Abba duk tabama Dauda.
Wasu y'an aikace-aikacen tafara ragewa kafin Dauda daya fita soro cin abinci yagama yakai mata 6arjin masaran.
Babu dad'ewa ko saigashi, dama ta had'a masa a wani k'aramin boket, dan haka kud'in 6arjin ta bashi dana abinda zai sayo Mata Na cefane. Sannan ta nuna masa masaran.
Bayan tafiyarsa bata zauna ba, ta kunna redio tana saurare da rage wasu ayyukan gudun zama tunani ya addabeta.



&&&&&&&&&&&&


Koda Jiddah ta fita bata zame ko inaba sai gidan Uncle yahaya, ta iske su Sadiq sun tafi makaranta, sai mamansu kawai da Uncle yahaya daya dawo jiya. Sosai ta nuna farincikinta da ganinsa, shima cike da tsokana da k'aunar yaran d'an uwan nasa yake fad'in “Sayyadata mafarkin dawowata kikayine?”.
Dariya Jiddah da Maman Sadiq sukayi, Jiddah tace, “kamar kasani kuwa Uncle, dukda dai banyi mafarkinba amma tunda asuba dana tashi zuciyata keta kwad'aitamin Abbana ya dawo, ashe da gaskene”.
Uncle yahaya yace, “ALLAH ya albarkaci wannan zuciya da tarin alkairi yarinyata”.
“Amin Uncle, kadawo lafiya? Wlhy munyi matuk'ar missing naka, kusanfa watanka biyu kenan?”.
“Nima ina cike da kewarku, dan banda yanda zanyine, inasu Zarah da Maman Nafisa?”..
“Duk kowa lafiya”.
“To Alhmdllh, nima yanzu nake shirin karyawa naje Na gaida Maman Nafisan ai”.
“To shikenan Uncle, Abba ma yana gidan, inba dai kafin kaje ya fitaba”.
“Yau kuma ya tuna da anguwar tamu kenan?”. Uncle yahaya ya fad'a cikin takaici.
Jiddah ma saida yanayinta ya canja. Maman Sadiq ce tai saurin canja yanayin nasu da fad'in “To Y'ar Uncle tashi ki had'a tea ga doya nan a kula”.
“Wai, wlhy mama cikina a cike yake, makaranta Zan tafima lokaci yayi”.
“Haba dai jiddodo ai d'anyar fata bata fashewa, ki k'ara lodawa kawai”.
Dariya Jiddah tayi tana mik'ewa da fad'in “Lallai Uncle ka tanaji kud'in kaini a d'inke nawa, dan nasan dai zai iya fashewa inhar na k'ara masa wani abu”.
Nanma dariya Uncle da Maman Sadiq sukayi. Jiddah ta nufi hanyar tafiya tana musu sallama.
Kiranta uncle yayi yabata d'ari biyu.
“A'a Uncle basai kabani ko nairaba, naci Na k'oshi mizanyi da kud'i?”.
“Hawa Napep mana, ko har yanzu dai bakiji fad'ana Na hanaki wannan tafiyar k'asanba?”.
Shiru kawai tayi tana murmushin yak'e, dan tasan tafiyar k'asa zuwa makaranta yazame mata tamkar dolene, tunda ba kullum Umma ke tashi da kud'iba, bazai yuwu ace kullum kuma zatazo wajensa ta amsaba, inama laifin wahalar da yakeyi dasu akan karatun da buk'atun yau da kullum alhalin mahaifinsu nada ransa bai mutuba................
Uncle ya katse mata tunani da fad'in “Ina kuma kika tafi Hauwa'u!?”.
Ajiyar zuciya ta sauke ta risina ta kar6a tana masa godiya, sannan tayi musu sallama ta fita.

Uncle yahaya ya jinjina Kai kawai yanamai jin takaicin halin d'an uwansa, wai ALLAH yay maka k'yau ka butulce masa saboda shaid'ancin zuciya, ga wasu can suna nema da miliyoyin kud'i basu samuba. Yaja guntun tsaki yana faracin abincin da Maman sadiq ta ajiye masa.
Batace masa komaiba, dan tasan inda tsakin nasa ya dosa.

Yau da wuri Jiddah ta Isa makaranta kasancewar ta hau napep da kud'in da Uncle yahaya ya bata.
Makarantace babba mai d'auke da d'alibai Mata zallah, amma yara da k'anana harma da matan aure.
Wata musabak'a dasu Jiddah sukaje tazo Na d'aya shine ta burge wani bawan ALLAH, a take a wajen yaymata albishir d'in d'aukar nauyinta zuwa wannan makaranta harta gama, dan da iyakarta islamiyyar anguwarsu, a yanzu haka kuma sune ke a aji shida fanin y'an Mata. Tunda Jiddah ta shigo makarantar take samun nasarori, kwakwalwarta takuma bud'ewa, dan ayanzu haka babu wani Kalmar larabci dazata layance mata, a littatafai kuwa Na fannin Addini tuni tayi babbar zarrah, 6an garan Qur'an tadad'e dayin sauka tana akan hadda. Kai bama itaba dukkan Wanda kagani a ajin su Jiddah to kwarone a makarantar, makarantace daduk Wanda yake cikinta lallai ya kwankwad'i ilimi ya k'oshi, dan ana tatosune daga wasu k'ananun makarantu Ana kawosu nan, babu ruwan wannan makaranta dakai d'an wanene?, duk Wanda kagani kaifin kwakwalwace ta kawoshi.
Kamar yanda dokar makarantar take duk Wanda ka iske a aji dolene kayi sallama, Na ciki su amsa maka, sannan kabisu d'ai-d'ai kabasu hannu kuyi musabaha>ØÝ<Øûß.
Yanzuma hakace ta kasance ga Jiddah, bayan tayi sallama duk suka amsa, ta yaye nik'ab d'inta tanabinsu d'ai-d'ai suna gaisawa cikin musabaha da murmushi shinfid'e akan fuskarta, saida takai har k'arshe sannan tadawo mazauninta Na gaba ta zauna kusa da Madeena Isma'il da kusan itace k'awarta da suke mutunci sosai a makarantar.
Murmushi sukaima juna bayan sun kuma kama hannun juna suna gaisawa.
“Ukti yau naga kin iso da wuri?”.
Jiddah tace, “ki Bari kawai ukti, yau dai naji fad'anki banyo tafiyar k'asaba”.
“To Alhamdllh da farajin maganata”.
Y'ar dariya sukayi a tare, wadda shigowar malam Mustafa ta katsesu. Duk suka mik'e suna gaisheshi kafin yabasu izinin zama.
Jawabin daya kawoshi ya fara musu, danshi ba koyar dasu yakeba, shine Vice principal na makaranta.
”Umm Assalamu alikum, nasan zakuyi mamakin ganina a wannan lokacin, wani uzirine ya tasomana Na gaggawa, an gayyaci wannan makarantar cikin jerin taron k'arama juna sani Na k'asashe goma da aka shiryama d'alibai, taron kuma zai gudana ne a sati mai zuwa, insha ALLAH zamu za6i d'alibai biyarne kacal, wannan ajin shine Na manya idan aka cire ajin matan aure, dan haka mun yanke shawarar d'aukar d'alibai biyu a cikinku, insha ALLAH malam Usman zaizo anjima ya za6i wad'anda zasu jagoranci tafiyar amma ta hanyar rubuta jarabawa, daganan zuwa awa d'aya kunada damar yin nazari, zamu dakatar da malamai yau gaba d'aya daga kowanne darasi”.
Atare ajin ya d'auki kabbarar *ALLAHU AKBAR!!!*.
Malam mustafa yay musu sallama ya fita.
Nanfa kowacce tashiga duba littatafanta da fatan dacewa.


('('('('('('('('('('('

Abba kam yana isa katafaren gidansa ya iske su kalifa tsaitsaye a harabar gidan suna jiransa. Babu Wanda ya gaidashi, saima tunzura masa baki da suka shigayi wai sunyi fushi.
Fuskarsa cike da fara'a ya hau fad'in  O shalelen Abba amin afuwa kunji, maza kushiga mota Na kaiku karku makara, Abba yayi laifi ayi hak'uri”.
Cikin tura baki Hassan yace, “Amma Abba tunfa d'azu muke jiranka, kabarmu dukmun bushe a tsaye”.
”Ai nace ayi hak'uri ko Hassan, Muneer taho kaji”. Yak'are maganar yana Kama hannun autansu Muneer.
Kalifa kuwa da Hussain uffan basuceba, shi kalifa ma iyafis ya saka a kunne, Hussain kam yayi cid'in-cid'in da fuska yana wani shan k'amshi.
Ko'a mota Muneer ne kawai ke fira da Abba, amma Hussain da kalifa da Hassan tamkarma babusu a motar.
Ya diresu a makarantarsu mai tsananin k'yau ta y'ay'an manya y'an gata, ya zaro dubu d'aya yabama Kalifa, babu ko godiya yay wucewarsa aji, Hussain da Hassan kuma d'ari biyar², suma dai babu godiyar, amma sun d'aga masa hannu alamar bye.
Munner ne aka bama d'ari biyu dukda an shiryo masa abinci a lunch box nashi kuwa.
Kalifa ajinsa uku 6angaren sakandire, Hussain da Hassan su kuma aji biyu, Munner kuwa yana firamare 5 ne.
Saida Abba ya raka Munner har sashen y'an firamare sannan yashiga motarsa ya fito daga makarantar................
'<Øûß



Kuyi manage please=ØÞ=ØLÜ<Øûß


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu=Ø-Þ=ØOÞ<Øûß_*
[11/21/2019, 2:43 PM] =ØžÜNoorunnisa=ØžÜ: *_Typing=ØòÜ_*



*_=Ø¡ÜHASKE WRITER'S ASSO...._*



*_=اÜMUTUM DA DUNIYARSA....!!=اÜ_*
_(ya dace ya gyara kansa)_



*_Bilyn Abdull ce>ØÝ<Øûß_*

*_[7.....]_*


..............Kamar yanda malam Mustafa ya fad'a bayan awa d'aya malamin da zaima su jiddah jarabawa ya shigo, sallama yay suka amsa masa tare da gaisheshi.
Ajin yayi shiru kowa yana kallon malam Sulaiman, yad'an tura hularsa baya yana shafa gaban goshinsa da nazarinsu, saikuma yay murmushi ganin duk sunyi tsuru-tsuru sun zuba masa idanu. Zama yay inda aka tanada domin zaman malamai kafin ya kuma maida hankalinsa Kansu.
“Inaga nama canja shawara kawai, zanyi jarabawar da baki”.
Kallon kallo aka komayi tsakanin su Jiddah, kowanne a sanyaye ya amsa

1 Comments On MUTUM DA DUNIYARSA
avatar
rukayya-yahuza

1 year ago

Reply

Kai book dinnan ya hadu iya haduwa

Please Login or Register in order to submit comment