Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da Alhaji garba ya kawo Mata na sayen baki, a kullum kuma Alhaji garba Na tambayarta Ana kawo mata abinci? Itakuma saitace eh kawai. Bai ta6a sanin ba'a kawowaba shidai, dan itama hajia deluwa daya tambayeta haka takecewa ankai Mata. da wannan ya d'auke hankalinsa bai saka idoba. Yau kuma gashi a lissafi sashenta zai kwana, duk fargaba ta isheta Sallamar Alhaji garba tajiyo cikin nishad'i, dan muryarsa a matuk'ar sake, tasan farin cikin nasa baya rasa nasaba da rutsata tana sallar walha d'azun, dan sai kusan 9 ya fita daga gida yau, yashigo mata sallama ne ya isketa tana sallah, tun sannan yaringa farinciki da tambayarta Ashe tasamu tsarki? Itadai kasama bashi amsa tayi a d'azun...... Tunanintane ya katse jin yace, ?hummmmmm!? Yana toshe hanci. Da mamaki ta kallesa, ganin zai juya da sauri tace, ?Alhaji sannu da dawowa?. Hannu kawai ya d'aga Mata ya fice da sassarfa. Yana fita ya sauke numfashi da fad'in ?Kai wannan wane irin warine a sashen yarinyarnan??. Babu Mai bashi amsa dan haka yay gaba zuwa sashen hajia deluwa. &&&&& Wasa-wasa dai sashen Jiddah ya gagari Alhaji garba harma da Ashir dake fakon Jiddah yay ramuwar gayya. Ita kuma Jiddah haka kawai takejin wani masifar tsoron maza, ko maganar namiji taji a TV saita rikice, cikin kwana uku kuma saiya koma ma tana tsorata da ganinsu koda a TV ne, dan dama ananne kawai take ganin nasu, tunda ba fita take konan da canba. Tashin hankali Na biyu abinda take samu taci komai ya k'are, yauma duk a jigace ta wuni saboda yunwa, sallama ta magrib sai a zaune tayita saboda rashin karfin jiki, babu abinda take d'urama kanta sai ruwa. Zuwa washe gari ko ruwa tasha sai amai, saboda babu komai a cikinta, ga wani Uban jiri dake d'ibarta. Cikin ikon ALLAH saiga bilki mai aikin hajia tazo kawo Mata waya inji Alhaji, dan yakai kararta wajen Abba shine abban yace ya had'asu, shikuma bazai iya zuwa sashenba shiyyasa ya aiko bilki. Ganin halin da jiddah take ciki sai hankalinta ya tashi, dan jiddah da k'yar ta iya fad'a mata yunwa takeji, da hanzari ta ajiye wayar takoma sashen hajia deluwa a sace ta had'o tea da abinci takawo sashen Jiddah. Itace ta taimaka Mata tad'ansha tea d'in cikinta ya warware, sannan tabata abincin shima kad'an taci saboda cikinta ya cinkushe, tanama gamaci sai amai. Sosai bilki taji tausayinta, itace ta taimaka Mata ta gyara jikinta sannan ta gyara wajen, koda Abba ya Kira sai bilki ta d'aga a matsayin Jiddah, yagama bambaminsa harya yanke wayar bilki dake mamaki da al'ajabi bata tankaba, aiko ko fad'a ma Jiddah yanda akayi batayiba. Tadai koma sashen Alhaji tace masa Jiddah batada lafiya. ?ALLAH yabata lafiya?. Yafad'a a k'ufule yana amsar wayarsa. Tundaga ranar sai bilki takoma kaiwa jiddah abinci a sace, dukda Jiddah nasamun abinci sai ciwo ya zame Mata jinya, kullum tana a kwance babu lafiya, ciwon baya da k'irji ga wani tsoron maza dake kuma shigarta babu gaira babu sabar. A haka tacika sati uku a gidan, ranardai Alhaji garba yakasa hak'uri, dan haka ya aika bilki da yamma dayake yadawo da wuri saboda juma'ace ta kirawo masa Jiddah. Tunda Jiddah taji Mai kiranta saita birkice tahau kuka da rokon bilki taje tace tayi barci. Bilki tace, ?Hajia karama dan ALLAH kizo muje Karna rasa aikina?. Jin wannan furici Na bilki ya saka jiddah Binta, dan bata fatan bilki ta rasa aikinta ta sanadinta. Sai dai kumafa suna yin ido biyu da Alhaji garba jikinta ya Kama rawa tafara kuka da Neman kofar fita, da sauri yazo ya rufe kofar yana matsota cikin toshe hanci, yayi alkawarin yau ba wariba kominene saiya more dubu d'ari biyunsa Na sadaki. Yana kai hannu zai ta6a jiddah ta kwala Kara da lalumar filawa dake kusa dashi ta kwala masa akai. Take anan ya zube a sume, jiddah kuma tayi waje da gudu tana kuka. A k'ofa sukaci Karo da hajia deluwa zata shigo, ram ta rike jiddah tana tambayarta miya faru? Ina jiddah takasa magana, jikinta sai kuma 6ari yakeyi saboda hango Ashir da Bala dake nufosu saboda jin kururuwar jiddah. Da k'arfi ta hankad'a hajiya ta nufi fita da gudu, Ashir da bala sukai tara-tarana kamata, Bala Na rik'e hannunta shima ta hankad'eshi da karfin tsiya yafad'i kasa da fasashshen kai ta fice a guje saboda Mai gadi da Ashir da direba da suma ke tara-taran kamata. Haka jiddah taita gudu, mahaukaciya zam a titi, babu inda take dosa sai hanyar gida kuma, saikace wadda ake control da remote. Mutane da yawa sunyi yinkurin kamata abu ya gagara saboda mazane. A gidan Alhaji garba kam tashin hankali biyu, Alhaji da bala duk sun sume, hakanne yasa Ashir kiran y'an sanda ya sanar musu su Kama jiddah, yayinda mai gadi da driver ke kokarin saka su Alhaji mota za'a kaisu asibiti. Hajia deluwa kuwa sai shar6ar majina take tana kuka da tsinema jiddah, ita bazata yardaba inhar mijinta da d'anta suka rasa ransu wlhy saita kashe jiddah itama, shi bala daga dawowarsa kwana biyu kenan Jiddah ta kashe matashi. Haka taita sambatu har sukaje asibiti dasu. ('('('('('('('('('('('. Su Zarah na zaune a tsakar gida kowa nad'an wiki cikin rashin kuzari, dan tunda Jiddah tabar gidan dukkan farin cikin gidan ya gushe, Ga Umma kuma ta hanasu zuwa gidan Jiddah su ganta kwata-kwata, sai Maman Sadiq ce da aunty Nafisa suka shirya zuwa gobe su dubota, shiyyasa Umma tace Subari idan sunje sunga hankalinta kwance suma saisuje. Da gudu Jiddah ta shigo musu, dan haka suma duk sai suka kwasa da gudu zuwa cikin d'aki, amma k'arar da jiddah ta kwala tana zubewa a k'asa yasakasu lekowa a rikice, ganin jiddarsu ce duksai suka yo waje hankali a tashe, gaba d'aya kanta sukai suna kiran sunanta, amma ina fisge-fisge kawai take tana kwalla gigitattar k'ara...... A haka Uncle yahya yashigo a rikice shima, dan tuni sama'ila Mai shago dasukaga shigowar jiddah anguwar Ana shirin sallar magriba sukaje suka kirashi. Yana kai hannu zai ta6a Jiddah takuma sakin wata k'arar datafi ta farko. Kowa saiya kuma birkicewa, ga kofar gida yacika da y'an anguwa, kowa yana tambayar miya sami Jiddah?. Isowar motar y'an sandane yasa kallo komawa Kansu, kutsawa sukai zuwa cikin gida babu ko tsayawa Neman iso. Babbar magana, y'an sanda dai sunga abinfa yawuce tunaninsu, dan shigowarsma saita kuma kid'ima Jiddah tacigaba da sakin wani ihu Mai fita da gurnani maiban tsoro, sai wata irin fisga takeyi nason guduwa daga rikon da sukai Mata........ Tashin hankali ba'a saka maka rana=???, wayyo jiddah.=?#? ('('('('('('('('('('(' A 6angaren Aliyu kam Maimunatu na samun tsarki a ranar yay shirin gwajin lafiyarsa cike da fargaba. Da farkoma shareta yay kusan kwana goma da samun tsakinta, saida yau yaji yakasa jurewa saboda sha'awar kasancewa da mace yakeji ainun. Dan haka yaymata shiri Na musamman irinna masu ililin da sukasan sirrin yanda ya kamata a tunkari mace, musamman ma budurwa. Cike da tsoro yayta driving Nata akan abinda yakamata tayi kafin akai ga kwanciya, sunyi salla da tambayoyi dayay Mata akan addini Wanda baisamu Matsala da itaba sai kad'an-kad'an. Daganan kuma sukai shirin barci. A farkon Fari da fargaba yake sarrafata, da lamura sukai nisa kuma sai komai ya tafi dai-dai fiyema da yanda yay zato. A ranar yasamu nasarar Fara bin hanyar cikar burinsa, dan baiyarda yazo Mata kaitsayeba. Haka yayta Binta a hankali har tsawon kwanaki hud'u kafin yayi Mai gaba d'aya. Maimuna dai kam tazama Aliyu, Aliyu kuma yazama maimuna. Saidai muce ALLAH yabada zaman lafiya Na har Abadan. A kwanakin da suka biyo baya sosai yake Nuna Mata kulawa Mai cike da martaba ta, dukda tasan baya sonta b?i ta6a Nuna mataba koda a fukane kuwa. Saima mamaki da yake bata yanda ya iya sarrafa mace a zaman takewa Na yau da kullum da shinfid'arsu. Abin ba'a cewa komai sai sambarka. Tuni kaunarsa takuma mamaye jini da ruhinta, suk hanyar dazata k'yautata masa ita takebi. A haka sheikh Aliyu yafara gudanar da al'amuran addini a anguwar, masallacinsa da makarantarsa suka Fara aiki, da dare maza magidanta ke d'aukar karatu, wataran kuma ya gudanar da tafseer. Da safe kuma matan aure, da yamma yara da y'ammata. Kafin kacemi makaranta tafara cikewa, dan kowa yaji babban malami sheikh Aliyu maina ne, to baya sanya saiya kawo iyalansa dashi kansa. Angwanci yayi matuk'ar kar6ar Aliyu, danya murje yayi wani 6ul-6ul dashi, sai wani k'yalli da cikar kamala yake k'arawa. Kullum yaje gaida malam kuwa saiya tsokanesa akan mirjewar da yayi, hakama malam mustafa. A yanzukam bashida wata Matsala, komai yana tafiya masa dai-dai saidai abinda ba'a rasaba Na kalubalen rayuwa Wanda ba'a taba raba Bawa dashi musamman ma irinsu dake d'auke da nauyin al'umma............. '?-??& @&?& @&?& @&?& @&?& @&>?p?>?p?>?p?=??_* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu=?-?=?O???

Chapter 11 of 31