Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sanyi kozatasha tirelar maganin gyaran Kanta to wlhy tamkar a banzane, dan bazai Mata amfanin komaiba, dan haka idanma zaki maida hankalinki ki maida, yanzu hakama hajiya ladidi mai adashe tace zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zata kawo miki wani?. Kan Jiddah a k'asa tace, ?To Umma nagode . ('('('('('('('('('('(' Aliyu kam ya ajiye wayar yay yana maida hankalinsa ga Maimuna, dan kimarta tawuce ya amsa wayar wata mace a gabanta, a ganinsa hakan tamkarma cin fuskane da had'a k'iyayya a tsakanin matan nasa.  Hiya-huwa kinyi k'yau ainun Masha ALLAH?. Wani dad'ine ya ratsata jin sunan daya kirata dashi, ta kama hannunsa ta sumbaci tsakkiya, cikin narke masa tace, ?Hilmy yanzu kaima zakayi fiyema dani?. ?haba-haba, ai idan ana dara fidda uwa ake gimbiyata, samun k'yak'yk'yawa irinki acikin Mata sai an tona, kina kallon kaniki a madubi kuwa??. ?Kai yayana kadaina fasamin Kai hakanan fa, kaidai zauna Na shiryaka muje ka karya, dan sak'onin daka sakani Na amsa wad'anda Zan iya jiya naci Karo dawani mai muhimmanci?. Kallonta yayi sosai, ?Mi sak'on yace??. ?A'a kabari saika karya?. ?Karki damu fad'amin kinji?. Mai tafara shafa masa, _?Cayay ka taimakeshi da shawara akan lafiyarsa, yanada Mata harda yara a tsakaninsu, iya gwargwadon iko suna gamsar da juna a shimfid'a, dukda dai ya fuskanci shi mutumne mai rauni dan baya iya jan lokaci wajen tarayya da ita amma sai bata ta6a nuna damuwartaba akan hakan, Sai kuma dukda wannan matsalar daya sani saiya k'ara aure, to a yanzu halin dayake ciki shine baya iya gamsar dasu su biyun, amaryar tashi kuma tafara nuna itafa bazata iyaba, itama Uwargidan haka, hakan kuma yafara kawo musu matsalar yawan hayaniya da matan nasa musamman Amaryar, shikuma yarasa yanda zaiyi, ya gwada magunguna da ake saidawa Na gargajiya sai dai tasirinsu kuma bawani mai tsayi baneba agaresa ake komawa Y'ar gidan jiya, shikuma duk yanason matansa yanason cigaba da rayuwa dasu.?_ Ajiyar Zuciya Aliyu ya sauke, ya taimakama Maimuna dake k'ok'arin saka masa kaya, saida suka kammala tasa masa turare sannan suka fito yana fad'in ?Wannan matsalar abar dubawace, kuma insha ALLAH zanyi magana akanta yau a masallaci, dan munada majalisi, matsalace babba wannan Maimoon data dabaibaye Mazajenmu Na arewaci, ammafa tamafi illa a kudancinmu, kawai sudai sun fimu himmar gyara kansune, matsalarmu mu mazan arewa shine mun d'auka mace ita kad'ai yadace ta gyara mana kanta, mukuma abinda muka iya kawai munemo kud'i muyita aure Ana kiranmu jarumai a waje, a cikin gida kuwa bama iya hasalama iyalinmu komai, Mata da yawa suna cutuwa ta wannan sigar, saidai basa iya magana saboda kunya, soyayyar mutumin arewa a iya wajene kawai saikuma amarcin watanni uku, ita kuma mace kota tsufa tana buk'atar tattali da soyayya ga mijinta, koda bakada wadatar dukiya soyayyar dazaka nuna Mata kad'ai wlhy zakiga ta gamsar da ita da jagorantar zamanku har k'arshen rayuwa?. ?Wlhy Yaya maganarka gaskiyace kuma?. Maimuna dake zuba masa a bincin tafad'a cikin damuwa. Ajiyar zuciya shima ya sauke, dan abi yana Sosa masa rai, amma insha ALLAH a wannan Karon zai amayar dashi ya huta, dan ba Neman ilimi da tafseer kawai al'umma suke buk'ataba, akwai wasu manyan abubuwa Na rayuwa da muhimmancinsu yakai adinga tunatar da mutane shi kodan samun sauk'in da duniyar aurarrakinmu ke fuskanta a halin yanzu. ('('('('('('('('('('(' Jiddah da Umma na a tsakar gida suna shirin girkin rana da hira wadda rabinta duk ilimin zaman aure Umma ke k'arama Jiddah haske akai cikin hikima. Tamkar an jefo Abba ya banko k'ofa jikake garam!!!, duk zabura sukayi suna kallonsa, Kai tsaye kan Jiddah dake tsaye a bakin rijiya yayi tamkar wani bajimin zaki........... '?-?). wata tace ba sunansu hakaba, Barbarawa kamar bunsuru wai=??, bani Na fad'aba Y'ar uwarkuce tace, karku dafani yau su tawan (miss Xoxo)?& @&?& @&?& @&._ *_Albishirinku fa, CIKI DA GASKIYA mafa ya sauka a gareku adai YouTube channel tv na Abban Dausayi, saiku garzaya kar ayi babuku gayis_*.?& @&?& @&?& @& *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*=?O?????

Chapter 19 of 31