Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ta wahalar da Masoyiyata ba. Bare ta shafama Auntynmu FAWAS Yace lokaci yayi ya kamata muje ko KHAMIS Yace ina😳 Ai yau ba xuwa xance bare club dan wannan daran na Aunty XEE ne xanje gida ina buqatar kwantawa in tsara mata kalamai. Na barku lafiya (ya fita) cikin nisha'di FAWAS Yace naso naga Aymana Wlhi RAMADAN yayi Murmushi Yace kanajin wani filing kenan dan baka xuwan axxiqi Yace hmm watoh RAMADAN ina San Aymana Amma banajin xan Aureta Gaskiya. Kuma abin mamaki ta tsaya min arai kamar maiya RAMADAN yayi Murmushi Yace har yanxu dai kana tana tare da wannan burin naka Yace sosai ma kuwa Damuwata 'daya a ina xan sami 'Yar Qauyan Yace hmm yanxu dai muje in rakaka gun Aymanan Amma dan Allah karka matse musu 'ya dan abinda kayi shi xa'ama 'ya'yanka Yace kada'de kana fa'da mana wannan Kalmar inda karatune nasan ni xanxo na 'daya pls muje dan Allah karkace komai RAMADAN ya ta6e baki Yace toh Allah ya ganar daku...... Qawata nashigo babbar harka fah😀 Gaskiya arxiqi da'dine dashi. Na samu wani Alhajin Abujah Wanda ya rikitani yan xunnan da tsabar ku'di har nera million 'daya......... XEEE wacce take kwance tana jinyar xuciyarta da tatafi da tunanin KHAMIS Wanda ya hanata nutsuwa Sam..... Aiko tanajin furucin SAILUBAH tadiro daga gado Tace what one million naira 😳 SAILUBAH tayi Murmushi Tace kema abin yabaki mamaki ko. Karya tsoratar dake dan yanxu aka fara wasan Inaso gobe kixo gida ki gani ganin idanki idan kuma kintashi xuwa kixo da Wannan qaramar jakar taki dan ki sami rabanki XEEE Tace abin mamaki dama nasan burinki xai cika. Xaki ganni qarfe tara gobe yanxu ma dan dare yayine SAILUBAH ta kwashe da dariya Tace shegiya XEEE taji maganar nera aiko goban xaki wanke idanki dasu Tace na sani aminiyata idan ina tare dake ban wanke idona da naira ba ai babu ranar daxan wanke idan dasu SAILUBAH tajah numfashi Tace ya kikayi da qaramin yaran naki Tace hmm ina sane ai naqi kiranki dan ya burkitani SAILUBAH Wlhi Wlhi Wlhi ina MASEEFAR SON KHAMIS Ya Xanyi Nan takwashe Komai tagaya ma SAILUBAH. SAILUBAH tayi mata dariyar rainin hankali Tace karkiyi yunqurin ki ransa. ki bari har sai shi yane meki akan ki bashi shawarar imba haka bah Wlhi ina tabbatar miki saiya baki wahala yadinga garaki Tace Kinga ko kiran shi ya shigo a qaramar wayata kamar yasan hirarshi muke SAILUBAH Tace yauwa. Na sanki da rikicewa kinutsu karya rainaki da yawa pls Tace hmm SAILUBAH kenan bakiji yanda jikina yake rawa ba. SAILUBAH tajah tsaki Tace Gaskiya kinada matsala XEEE da Takaici XEEE tayi dariya Tace hmm Allah ya jarrabeki dasan qaramin yaro kiji fiye da yanda nakeji.......... Cikin maseefa Tace ba AmEEn ba 'yar is....... XEEE ta katseta da cewa saida safe ta tsinke hirar tasu SAILUBAH Tace tajah tsaki Tace Allah ya rabani da soyayyar qaramin yaro........ XEEE ko bajewa tayi agado tatattara nutsuwarta cikin bugun xuciya ta'dauki wayan KHAMIS Wanda saura ka'dan tayanke a karo na biyu Tace hello Yace inata kira Aunty. Allah yasa jin da'dine da lafiya da kwanciyar hankali ya hanaki 'dauka Tayi murmushi Tace toh bansan me xance maka ba KHAMIS Amma ina cikin lafiya da kwanciyar hankali musamman mah yanxu Yace toh madallah dama nakiraki ne akan......... Sai kuma yayi shuru Cikin sanyi XEEE Tace akan nabaka shawara kan budurwarka ko Tace eh Aunty Allah yasa baxan takura miki ba. Wlhi xuciyata CE take san xuwa gareta yanxu gashi kuma idan naje bansan me zance mata ba Shuru XEEE tayi kishi nacin xuciyarta. Dama ace ina tare dake tana shafi gefan fuskarki na dawo dake daga tunanin da kika fa'da KHAMIS ya fa'da Cikin sanyin murya.... [7:24PM, 19/11/2016] Rahamat Nalele 👯: XEE tajah numfashi Tace hmm ba tunani na fa'da ba kawai...... Yayi saurin katseta da cewa kar kiyi min musu Aunty inaso kawai naji me yajefaki cikin tunani Taja numfashi Tace tunani nakeyi yanxu idan Nace kar kaje gunta baxa kabi umarnina ba kuma ni haka kawai Naji bana san kaje gunta wlhi kaje sai nayi kuka. shiyasa kaga nayi shuru Kuma baxan iya gaya maka dalilin hakan bah KHAMIS ya lumshe ido tare da gyara kwanciya kallo 'daya xaka mishi Kasan yana cikin wani hali na tafiya a cikin SO da qauna Yace yanso ki gyara kwanciyarki Tace nagyara Yace haba Aunty. Me xaisa baxan bi umarnin ki bah. Ki shareta kawai Wlhi ba xanje gareta ba na hakura. Dan da kiyi kuka gwara in hakura da ita gabaki 'daya dan nasan kukanki xaifi damun xuciyata fiye da soyayyar da nake mata XEEE taqara qan qame wayan akunnan ta cikin muryar sanyi Tace ina sanka Qanina da xaka ha'kura da ita gabaki 'daya da sai nafi kowa jin da'di. Yayi Murmushi yana raina wayo irin nata. Ga wata xaxxafar soyayyarta da take cafkar xuciyarsa Yace LA Idan hakan xai saki jin da'di Wlhi xan iya hakura da ita har abada Amma sai dai in xaki..... Sai ya kasa qara sawa Cikin murna Tace Amma sai dai me Yace ina jin tsoran qara sawa ne Aunty. Tace kafa'da man. Karka damu. Tafa'da da San jin furucin nashi Yace ki bani minti biyu kacal Xanyi addu'a kafin in fa'da miki. Xakiji shigowar sako yanxu Tace toh ina jira dan Allah karka wucce 2 minutes 'din Yace angama Aunty.... Shuru XEEE tayi tana addu'ar Allah yasa ta mallaki KHAMIS a matsayin mijinta ita ka'dai. Dan yayi mata tako ta'ina. Sai juyi take KHAMIS ko dariya yayi Yace yes my Luv Allah yasa Ki xama mata agareni Sannan yayi rubutu kamar haka...... _xan ha'kura da ita gabaki 'daya idan har xaki mayemin gwurbinta. Xanso Ki xama mata agareni Ki haifamin yara kyawawa kamarki_ Saiya tura mata XEEE najin shigowar sakwan tayi saurin dubawa.... Wani qara tasake cikin farin ciki ta kwashe da dariya...... Mamah tashigo hankalinta tashe Tace meya faru ne Zainab XEEE Ta rungume maman tana Tace yau Xanyi kwanan farin mamah nasamu wanda yafimin Surajo Din gure mata kai mamah tayi tajah tsaki Tace Nina 'dauka wani abunne Wlhi Da dariya XEEE Tace aa ba Komai koma gun BABAH kawai Fitta mamah tayi tana fa'din Allah ya shirya XEEE ta koma gado tana da'da karanta sakwan nasa. Kafin ta kashe wayan nata gabaki 'daya Qarfe 11:30pm na dare SAILUBAH ta kwanta danyin bacci. Sai kuma tatuna bata tambayi Qanin nata ko yaci abinci ba Nan tafara Ne mansa a waya. Sai kuma tatuna sunyi fa'da tajah tsaki da dai kiran nasa dan tasaba da hakan in bata kirasa ba hankalinta baxai kwanta bah Lokacin sun dawo kenan daga wajan 'yan matansu FAWAS yayi gida shi kuma ya kwanta kenan yaga kiranta Yayi Murmushi dan yasan abinda xata tambayesa Sai yaqi 'daukar wayan yana ji har takira sau uku Daga qarshema ya kashe wayan gabaki 'daya yabi lafiyar gado SAILUBAH tayi kwafah Tace Wlhi in dai akan Alhaji Aminu ne sai dai kata fishinka tajah tsaki takwanta Can takasa bacci sai juyi takeyi Ta da'de da sanin idan RAMADAN yayi fushi da ita qaurace mata yakeyi na Wasu kwana Wanda hakan ba qaramin axaba bane agareta Dan har ciwo takeyi na rashinsa Salloli tadinga yi tunda baccin yaqi 'daukarta kamar yanda shima ya kwana Yana lafular Washe gari Suna breakfast da Abbanta take bashi labarin Alhaji Aminu da kuma bashi qarin bayanai akansa kamar yanda yabata jiya Da murna Abban nata ya kar6i takaddun gannun nata yana dubawa Can ya kalleta Yace ai wannan yaran Malam Saluhu ne Kiga ikwan Allah ban sanshi da wannan 'dan ba Kuma yaushe yayi ku'di haka Hmm Allah me iko SAILUBAH Tace Abba Waye mahaifin nasa Yace baxaki sanshi ba Amma acan baya da nake da ku'di yayi aiki a qarqashina mutumin kirkine Tace ayya. Yace Naji da'di Sosai da kika bi umarnina kika kawo min Wanda kikeso. Karki damu xan nemi mahaifin nasa muxanta Tace toh Abban nata na barin gidan tatashi dan xuwa lalla6o qanin nata Sai matar Abban nata Tace xan samu dubu 'daya dan Allah agunki fita nake san nayi Amma ba ishash shan ku'di a hannuna SAILUBAH Tace eh xaki samu na manta in gaya miki jiya nasamu ku'di ahannun shi Alhaji Aminun da yawa xan baki dubu 'dari biyu Amma Karki gayama Abba Da wata irin murna ta rungumi SAILUBAH Tace Allah ya miki albarka kinji ai Wlhi ba Wanda xaiji SAILUBAH Tace toh Allah yasa Nan taje ta ibo mata mata tabata Kana taje gun Kakah Tace Kakah na kawo miki Wasu ku'dine da wani Alhaji Aminu yabani Tace aa ki barsu suyi miki amfani kinga ni ba abinda xasuyi min tunda na tsufah SAILUBAH ta dafata Tace Karki damu dubu ashirin yaban shine nace bara na baki dan ba'abinda Xanyi dasu yanxu kuma kinga inna ba Abba baxai kar6aba xaice in mayar masa da ku'dinsa kuma kinga bakyau maida hannun kyauta baya shiyasa nakesan kikar6a dan Allah Kakah ta waro ido Tace har dubu ashirin gaskiya ku'din yay yawa Karki sake kar6ar ku'dinsa haka Tace toh. Da miqa mata XEE na tashi da safe ko breakfast batayi tabu'de wayanta tana san qara karanta sakwan masoyin nata...... Sai kuma ga kiransa ya shigo mata... Ita kanta batasan ya akayi tayi saurin 'dauka ba da cewa hello..... Kin hanani bacci jiya Aunty gashi yanxu yana damuna dan ma yau bani da lectures da abin ya ha'du min biyu. dan Wlhi baxan iya xuwa ba. Xuciyar tacika da tunaninki da fargaba. KHAMIS Yafa'da kamar xaisa ma XEEE kuka..... Tace toh minene Yace ina sanki ina qaunarki xaki Aureni Tayi Murmushi Tace har na haifa maka yara masu kama dani kyawawa Ina sanka KHAMIS Yajah numfashi cikin farin ciki Yace na samu nutsuwa Aunty xan 'danyi bacci kafin naxo ganinki Tace ina fatan xakayi mafarkina Yace kwakwalwar tawa babu komai acikinta sai tunaninki. Mafarkin ki shi yadace da ita Cikin murna Tace me xan ce ne dan Allah Yayi Murmushi Yace da'dine yayi miki yawa my Luv. kawai ki kwanta kema xanxo miki cikin baccinki na tayaki hira. Kuma xanso Ki canja min Suna daga Qanina xuwa......... Tayi saurin katse shi da cewa xuwa my sweetheart.... Yace yayi Sosai saikin ganni mun ha'du (Toh ha'duwar XEEE da FAWAS kenan. Rahamat na gaisheku👯) Shuru SAILUBAH tayi cikin mamakin ganin kofar RAMADAN akulle da'alamar xai hukuntata ne kamar yanda yasa ban Tayi kwafa xuciyarta nayi mata xafi tana kuma tsoranma kanta ciwo kamar yanda lamarin ya saba xuwan mata. Da kuka tayi part 'din momynsa tana tambayarta ina jaye..... Momy Tayi Murmushi Tace lefin me kikamai haka. Tace Wlhi Momy bawani abun xafi bane Amma yake san hukuntani kamar yanda ya saba. danya samin ciwo😰 Khairat tayi dariya Tace Aunty LUUVAH wai yaushe xaku dena yin fa'dane ke da Ya RAMADAN ya dena miki haka yana saki kuka Ta harareta tare da kallan Momy Tace dan Allah Momy ina yake..... Yace Wlhi Auntyna ban Sani ba Kawai dai ni bana san kixama mata agareshi ne Tajah tsaki da sakin fuskarsa Tace nidai ina san shi dan ku'dinsa Amma ban shirya Auransa yanxu ba Yace pls my Aunty Ki temaken Karki Aure shi. Takalle shi ka'dan Tace har naji kuma bana san shi tunda baka san shi Sai kasan yanxu maganar ba a hannuna take bah tana gun Abbana. Shuru RAMADAN yayi duk ya burkice tunaninsa 'daya shine Abbanta Sam Baya magana biyu yanada xafi Sosai. Ba abinda yafi dacewa kamar yata addu'a dan itace mafuta. Ya kalli Auntyn tashi cikin damuwa Yace kiyi min alqawarin baxaki Soshi aranki ba Ni kuma xanta jifansu da addu'a har Allah yasa xancan ya wargaje SAILUBAH ta harareshi Tace wai in tambayeka man Yace ina jinki Auntyna Wai meyasa Sam baka san ka ganni da wani 'da namiji Yayi murmushi Yace nima ban sani ba. Amma xanyi qoqarin in sani nan gaba Ta qara harararsa Tace hmm kafin kasani nixan fara sani dan nasan tabbas akwai manufarka akan hakan Yace Auntyna kenan xanso Ki rigani sani. Amma kiyimin alqawari idan har kika sani baxaki qini ba Tace duk duniya bawanda nake jinshi araina kamar ka.. Ba ranar da xataxo min wacce xatasa in qika. _Yayi Murmushi da fa'di aranse tana kan layi Amma takasa ganewa_ Afiliko cewa yayi hmm xanso in dauwama dake har qarshen rayuwata Tayi Murmushi Tace wai wane irin SO kakemin ne Qanina Yace irin son da masoya Su......... Sai kuma yayi shuru Tace qarasa mana Tashi yayi ya 'dau wayarsa tare da kama hannunta Yace idan na qarasa mummunan mari xansha agunki Ta kulle 'kofar tasa suka nufi waje Tace kome yasa Ya kalleta ka'dan da Murmushi Yace bansan me xance miki ba Ta kallesa........ Wani kallo ya sakar mata wanda yake da tabbacin ya kulle maganarta kenan Aiko tuni jikinta ya mutu mu'dus Cikin wata wahalalliyar murya Tace bacci yaxo min yanxu Cikin sanyi murya Yace nasani Auntyna. Ya fa'da da kai hannunshi gefan fuskarta ya qara da cewa xaki iya kaiwa 'dakin ki koni in kaiki Tace hmm Ba 'daukata xakayi ba bare inji damama Inna ganni a'dakina dole qafatace takaini. Karka damu Qanina xanje da sayyadata Yayi Murmushi da janye hannunsa Yace in har baxaki iya takawar ba. Ki fa'damin. Dan Wlhi 'daukarki baxai ban wahala ba. Kodako xanta yawo dakene ahaka Tadaki girjinsa ka'dan cikin mutuwar jiki Tace saboda ka rainani danni macece. Inxa'a duba na tabbata saina fika nauyi Yace hmm toh naji muje in kaiki karki xube min ajiki dan naga baccin ya fara cin qarfinki...... Haka suka jera ya Kaita har 'dakinta takwanta Ta kallesa Tace karfa kaje club Yace toh Tace imma kaje xanjika ai Ya rufe mata qafafunta Yace dan Allah kiyi bacci karki dashi yau tsakar daje Tace dan kar na jiki ko Yace ko 'daya inaso yaudai Ki mori baccin ne Tace kaima Kasan na saba Yace saida safe Tace mu tashi lafiya Yace Allah yasa da fucewa FAWAS ya harareshi Yace ka shanyani kamar wani kayan wanki Yace am sorry kasan....... Bai qarasaba wayanshi tayi qara. Yana dubawa yaga wacce sukaci karo ce a Jifatu Ya 'dauka da hello Tace kana magana shahuda Yace ayya sunanki kenan Tace eh RAMADAN naji 'dakin kar6ar number naka Dan xan kiraka lokacin da nake so da kuma buqatar kalaman ka Yace ayya da fatan kinkai gida lafiya Tace lpy lau Yace toh Alhamdulillah naji da'din sunanki Sosai Tace haka mutane da yawa suke cewa. Nayima tunanin ko qarya suke Yace bane Su da yima babbar yarinya qarya sun da'di iya gaskiyarsu ne kawai Tayi murmushi Tace kamar yanda kaji nace maka sunana shahuda. Ni 'yace ga Alhaji iroro me harkar siyar da mai Ni ka'daice 'yarsa muna xama a garin abuja unguwar maitama Mahaifina cikakken me ku'dine bana wasa ba yana sanmu ni da mahaifiyata Sosai. Bikin 'Yar qanwar momyna ce ya kawomu kano Yanxu haka gobe mukesan kumawa abuja RAMADAN Yace daga kalamanki nagene ke me gaskiyace. Kuma baki so. ki yaudari mutum a har karki dashi. naji ina sanki dan inasan mutum mai wannan halin Tayi dariya Tace Nagode sai mun sake waya ka gayamin kai ko waye gudnyt Yace ok gudnyt FAWAS ya kalleshi Yace wacece Yace yarinyar da nake baka labari ce Yace shegiya taga 'dan saurayi😆. RAMADAN yayi dariya Yace kuma yafi karfinta ba 👯: Haka rayuwar tasu tacigaba da tafiya yau da da'di gobe sa6anin haka Soyayya me qarfice tashiga tsakanin KHAMIS da XEE Ba Wanda bai sani ba har acikin makarantarsu Mutum biyu ne basu sani bah. Sune iyayan XEE dana KHAMIS Sam bata canja xali ba tsakanin SAILUBAH da XEE wajan qin karatu SAILUBAH da RAMADAN sun shiga tashin hankali ba'dan ka'dan bah Dan yau saura kwana uku bikin SAILUBAH da Alhaji Aminu Xa gwan qasa ya dinga mata tawajan Abbanta ya nuna mishi yana bala'in Santa ayi Komai da wuri Yana xuwa duk sati ya ganta ya kuma bata ku'di me tarin yawa Ana saura sati biyu bikinne ya bata kyautar wata lafiyayyiyar mota Amma ta biyo ta hannun Abbanta ne wanda daqer ya kar6e a cewarshi ai Auranta xaiyi yabari ayi Auran ya bata Ya nace dai saida Abbanta ya kar6a Eh motar tatafi da hankalinta SAILUBAH Sosai Amma ganin RAMADAN duk ya rikice mata shiyasata qin nuna farin Cikin nata Dan yanxu ya canja mata gabaki 'daya... Ita gani takeyi kamar haushinta yakeji Yanxu haka xaune take ita da qawayanta wata tana mata gyaran jiki dan ginsu Su dilke jiya sukayi walima. XEE Tace ikwan Allah kenan SAILUBAH. Ashe xaki rigani Aure. Tace hmm Wlhi XEEE xuciyata xafi takemun kwata kwata na tsani Auran nan Wata khamsa'u Tace meyasa Tace hmm tunda RAMADAN ya nunamin baya so naji nima bana so XEEE Tace na lura har ramewa kukayi ke dashi Wata ummi takalli XEE Tace keko sabon da sukayi da juna na wasa ne SAILUBAH Tace ni yanxu damuwa ta ya qaurace min kwata kwata Na ne meshi awaya na rasa Rabona dashi yau kwana hu'du kenan Wlhi xaxxa6in nan da nakeji duk na rashinsa ne Nasan ina ganinsa Komai xaixo min da Sauqi Wata humaira Tace hmm ki kwantar da hankalinki inda RAMADAN ne qila anjima kigansa dan nasan duk inda yake yafiki shiga tashin hankali SAILUBAH tayi tagumi Anisa Tace nidai kuna burgeni yanda kuke San junanan nankun nan XEE Tace 'dan iska KHAMIS yaqi gayamin inda yake SAILUBAH Tace hmm xan ha'du da shine shima Washe gari aka kawo kayan Sa Lalle da akwatuna goma Sha biyu reras 'Yan unguwa sai xuwa gani suke dan kayane nagani na fa'da Anan ne fah tsoro ya kama SAILUBAH dan Alhaji Aminu ba qaramin ku'di ya kashe ba Qarfe goma sha 'daya na safe SAILUBAH Tatashi hankalin XEE harda kuka ita dai suje sunemo RAMADAN Cikin marairai cewa XEE takira KHAMIS Tace my sweetheart Yace na'am my Luv Tace kayima Allah da Annabi ka gayamin inda kuke Wlhi SAILUBAH kuka take damuwarta taga RAMADAN. Hankalina ya tashi KHAMIS ya waro ido Yace pls my Luv kar hankalinki ya tashi dan Allah ayanxu kam gaskiya baxaku ganmu bah Dan muna can yanhar xuwa qauyan Takai Kinsan Aliyu na makarantarmu Wanda ya rasu a qauyan yake. Shine 'daxo muka shirya xuwa gaisuwa am sorry my Luv saidai in mun dawo kuganmu Tace toh ka kulamin da kanka Yace insha Allah Tace Sannan kasa ya kunna wayansa Ko tasamu nutsuwa Yace angama my Luv Tace i Luv u Yace me 2 my baby XEE ta kalli SAILUBAH Tace toh kinji Tace Naji har hankalina ya kwanta. Allah yasa ya bu'de wayansa Tace AmEEn Kamar yanda KHAMIS ya fa'dama XEE Suna kan hanyarsu ta xuwa takai. Toh haka abin yake da gaske FAWAS dake tuqasu ya kalli KHAMIS Yace Gaskiya soyayyarka da Aunty XEE tana tafiya dani Yace hmm ina Santa da yawa FAWAS FAWAS yayi dariya Yace naji tana maganar Aunty LUUVAH Yace eh. Yana me kallan RAMADAN dake karanta wata jarida KHAMIS ya 'dora da. Toh 'dan iska hankalinka ya kwanta tunda ka sakatah kuka akanka Katemaketa ka bu'de wayanka dan Allah danni ta Masoyiyata nakeyi Dan nabata tabbacin xan saka ka bu'de wayanka RAMADAN yajah tsaki Yace karka dameni dan Allah. Yace Wlhi saika bu'de wayanka ko'dan Aunty XEE ya fa'da da 'dauko wayar tasa.......... Kan RAMADAN yayi magana FAWAS yajah wani furgitaccan burki Wanda ya basu tsoro Yana sauke numfashi sama sama idanshi na kan mudubi yana kallan bayansa Cikin maseefa KHAMIS Yace wai kai wane irin 'dan iska ne xakaje ka kashemu dan iskanci Ni ban gaji da rayuwa ba dan ban ajiye 'ya'yana ba ehee RAMADAN yayi Murmushin dole dan rabansa da Murmushi yafi sati uku Yace ka lura man KHAMIS yagano wata xa6in shi ce FAWAS ko fa'di yake Ya Allah innalillahi wayyo kaina Kunga wata xanka'da xiya KHAMIS ya juya yana san ganin wacce ta gigita FAWAS haka Kut😳kut😳kut Yace Saka makwan ganin wata xanka'daxiiyar budurwa wacce take sheqa gudu tamkar xata tashi sama Ba gyale ajikinta Wata fanka ceciyar rigace tasa sai xaninta da kallabi Sai wani siririn gyale dataci 'dam mara dashi Kallo 'daya xaka mata kagano Abu biyu Tana da kyau na bam mamaki. tare da kuma matsanancin damuwa. Yanda take gudun Komai na jikinta na rawa shi yasa FAWAS rufe idansa🙈 da hannu biyu KHAMIS yajah numfashi Yace eh Lalle yau Allah ya kawo maka xa6inka Ganin takusa xuwa garesu yasa RAMADAN fitta daga motar yasha gabanta Ta kallesa da wata muguwar harara Tace da Allah matsamin sauri nake Yace tayaya ma xa'ayi im matsa miki bayan kina sheqa gudu haka Tace toh ina ruwanka hakan na saba kuma ba Wanda ya ta6a tareni Yace ko Tace gaskiya man Yace eh ba shakka dama haka kuke rayuwarku Ku 'yan qauye HAMEEDA ta qare mishi kallo tun daga sama har qasa tabi motarsu da kallo Kana ta dawo da kallanta kansa tatabbatar ba 'yan qauyansu bane Allah yayota dasan 'yan burni Da gaske RAMADAN yayi mata MASEEFAR kyau Ita duk a iya gane gananta bata ta6a ganin namiji Wanda Komai ya masa dai dai kamar RAMADAN ba Atake tayi tunanin shi balarabe ne taji tana san shi Amma baxatace ga irin son dataji ba Ya 'daga mata gira. Nan tadawo daga tunanin Tace gaka qaramin yaro Amma sai qarfin halin tare wacce ta girmeka RAMADAN yaji kamar ya tsinka mata mari dan duk duniya ba wacce xatace mishi qaramin yaro ya share sai Auntynsa Yayi murmushin yake Cikin 'daga murya yace FAWAS kafito Wlhi. tunkan na tsinka mata mata mari. KHAMIS yayi dariya Yace aisai ka fitta Kasan ka'dan da aikinsa ya falleta da marin... FAWAS ya fito daga motar Yace sannu ko Ta kallesa ka'dan. Gabanta yafa'di dan ganin wani kyakkyawan kuma Tace yauwa Ta maida kallanta ga RAMADAN Tace waxa ka mara Yiyi mata wani mugun kallo Yace ban dake akwai wata ne anan Xatayi magana Yace Kinsan Allah kika qara bina da qaramin yaro Wlhi saina miki mari biyu ajere. Haba da Allah Daga ganina xaki kirani da qaramin yaro ke ba qaramar yarinyar bace Tace kut😳 shekarata ashirin da hu'du ko kaffara baxanyi ba na girmeku karka qara kirana da qaramar yarinya RAMADAN yayi Murmushi dan ganin yarinyar 'Yar ayice Yace oho Ashe ba da'di Tajah tsaki xata wucce..... Yace 'dan jini ka'dan mana Tace lafiya Yace atunaninki lafiyace xatasa na tsaidake Yanuna FAWAS Yace sanki yakeyi da Aure dafatan xaki soshi Tayi dariya da kallan FAWAS Tace gaskiyane kuna da kyau Sosai KHAMIS ya fitto Yace har dani Ta qura mishi ido canTace eh harda kai Amma kunyi min yara sosai Wai mema kuka sani a Aure da xaka kalleni kace abokinka xai aureni. Kun san mah me ake kira da Aure Suka kalli jununsu atare FAWAS yayi Murmushin yaqe Yace ki bani dama in aureki sai in nuna miki me ake nufi dashi Tayi dariya Tace toh xan baka dama Amma sai nayi shawara da xuciyata Tafa'da dasan barin gun RAMADAN Yace da kata malama Tace muryarka tana d....... Kanta qarasa ya wurga mata wani mugun kallon da ya hanata qarasawa Yace Ki fa'da mana gidanku Itama harararshi tayi ta wucce shi FAWAS Yace dan Allah Karki tafi da gudu. Tace naji Qanina tabar gun da sauri Kuma daidai nan wayar RAMADAN ta fara ringing RAMADAN ya kalli KHAMIS Yace wayace ka kunna min waya dan Allah KHAMIS Yace Aunty LUUVAH CE dai Ahankali ya kar6i wayan da 'dauka Da kuka SAILUBAH Tace meyasa kakemin haka RAMADAN Da sanyin murya Yace menayi Auntyna Tace so kake ka kasheni Yace idan na kasheki inyi rayuwa dawa...... Tace hmm ina San ganinka yanxu. Yace muna qauyan takai fah😳 Tace ko qauyan inane ina San ganinka yanxu nace. Tana fa'din haka ta kashe wayan KHAMIS Yace yadai Yace mukoma gida yanxu pls....... FAWAS Yace kut. Kama isa Gaskiya kai 'dan rainin hankaline Toh bari kaji. Wlhi baxa mubar qauyan nan ba harsai na sace xuciyar yarinyar can RAMADAN ya 6ata fuska Yace hankalina ya tashi. Auntyna tana can tana kuka akaina Bana san kukanta kai kasani. Kabari mah qara xuwa Yace Wlhi Wlhi ba'inda xamu saina sace xuciyar yarincan Ta rikitani over baxan iya bacci ba wlhi. Gwara Ku tunda kun saba. Dan wannan ba bakwan abu bane awajanku Shuru RAMADAN yayi dan yasan tunda FAWAS ya gigice saiya 'dorata akan hanya xaibar qaunyan KHAMIS na jinsu yayi shuru yace aransa Allah ya tsallakar dani saura ku Ahaka sukaje gidan me gari sukayi gaisuwa dake yaran jikan gidanne Duk da yake agidan mutuwa suke. Hakan bai hana mutanan qauyan xuwa ganinsu ba Bayan sallar axahar kowa ya Washe suma suka shige mota dan xuwa gidansu HAMEEDA Wani yaro suka samu me surutun tsiya. KHAMIS Yace Kasan gidansu wata budurwa kyakkyawa haka Tana da 'dan shekaru Yaran ya 'daga

Chapter 5 of 33