Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
inda Su junior RAMADAN suke Innalillahi'wa'inna'ilaihirraji'un Shine abinda junior RAMADAN yafurta hannunsa dafe da qirjinsa Nishi yake sama sama can jadawo normal 'dinsa cikin wani hali Yace bala'i...... Isma'il Yace karo na farko kenan da wata yarinya taburkitaka arayuwarka Yace tayi tayi tayi... Ta ha'du. Kuma tayimin Kamar yanda kifiya take xuwa da gudu take cakar mutum wlhi haka naji maseefar sonta ya caki xuciyata. Isma'il Yace ai kashiga kawai. Naga kamar bata da matsala..... Cikin tsawa junior ya katseshi da fa'din akwai matsala Yace wacce iri oga Yace na hango soyayyarta da qaunarta acikin idan 'dan uwana Da alama itama tana ciki Allah na roqeka dan San da kakema shugaban halitta tsaftatacce kayayemin abin da naji araina yanxu. Karka barni nafa'da *MASEEFAR SOO* kamar yanda XARAH tafa'da ta aiwatar da qurorinta AmEEn Amiien my RAMADAN😭 Isma'il Yace Amiien. Kana sukaja motarsu junior bai dena ganin fuskar SAILUBAH a idanshi bah Direct gida sukayi. Anan falan junior yaga Dad 'dinsa Batare da Yace mishi Komai ba yayi yunqurin barin falan xuwa ga shashinsa RAMADAN...... Yaji Dad 'din nasa ya kirasa Cikin 'daure fuska Yace na'am Yace kayimin afuwa duk abinda xakayimin karka nisanta kanka dani Hakan xaisa nashiga cikin wani hali Cikin nuna halin ko in kula Yace inasan xuwa ga Dady Naziru Da sauri Alhaji Aminu ya waro ido Yace a ina Kasan shi Kai tsaye Yace a diaryn daka hanani karantawa Ina San 'dan uwana ya ganni inaso kuma inji Wasu bayanai Cikin tashin hankali ya miqe Yana fa'din. Daka bar xuwan kawai Sabo dame..... Ya tambaya cikin San sanin amsa cikin sauri Yace saboda na isa dakai Yace daba. Amma banda yanxu Yana fa'din haka yabar falan yayi part 'dinsa Tunanin dukiyar daya samu gurin Dadyn nasa yakeyi Yasan yanada maqudai ku'da'de a banki banker Cikin sauri yanemi yaran nasa awaya Ko cikakken minti biyu basuyi ba saigasu RAMADAN ya miqa musu ATM dinsa Yace inaso kuje Ku fitomin duk ku'din da yake ciki Da mamaki sukace toh. Dan dai sunsan ba qaramin ku'dine a ciki ba Bayan sun tafi ne ya fa'da tunanin SAILUBAH da Yayan nasa Sintiri yake tayi dan xuciyarsa cakarsa take tana qara cusa mishi soyayyarta Shi kuma yana quqarin yakiceta Saidai so baisan haka bah Bai San adadin lokacin daya 'dauka yana tunanin ba. Saida yaji xuciyarsa nayi masa xafi Sannan yayima kansa gata wajan yin Alwala ya gabatar da sallar axahar Alokacin ne yaransa suka shigo garesa Suka miqa masa maqudan ku'da'dan dashi kansa sanda yayi mamaki dan dama baisan yawansu bah Yace no ku kasashi kashi hu'du Sukayi yanda Yace Yatashi yana ha'da kayansa cikin lokaci qanqani yagama ha'dawa Yace 'daya daga Cikinsu yakai masa motarsa...... Bayan yaran ya dawo ne Yace Ku hu'du ne cif.... Ina so kowannanku ya 'dauki kaso 'daya Cikin tsananin mamaki kowa ya 'dauka Yaciga gaba da fa'din Na dena daga yau Nadena fashi Kuma inaso ne kudena Shiyasa nabaku wannan ku'din dan nasan xai tamaka muku kwarai da gaske wajan riqe kanku Kuyimin alqawarin kundena dan Allah Wlhi xuciyata tafasa takeyi idan natuna abin da mukayi arayuwa Duk da banta6ayin kisa ba Amma mutane bila adadin sunsha harbi a danginsu qafa. Hannu. Kafa'da Nayi nadama inaso kubari pls Cikin sanyin yanayi sukace Wlhi oga mundena Dama kaine uban tafiyan. Tunda bakayi ai ba harkar. ko munyi yunqurin yi abin baxai mana dakyau ba Yayi Murmushi Yace kuje karku qara tunawa dani arayuwarku Kusa aranku kun barni kenan har abada. Kun rabu dani kamar baku ta6a sanina ba.... Da sanyi suka fitta Suna waiwayansa. Yayinda Isma'il yaqi tafiya ya tsaya da kasan sa ahannu Da mamakinsa junior RAMADAN Yace me katsaya yi kai Cikin xubar hawaye Yace Wlhi oga nafisan kasancewata dakai akan in kar6i ku'dinnan na barka Junior yayi Murmushi ya da'de da sanin Isma'il masoyinsa ne na Gaskiya yana hango soyayyarsa acikin kwayar idansa Yace karka damu kana da number na. Xaka iya jina akowane lokaci kakeso Yace yanxu bakamin katanka da kanka ba Ya 'daga mai kai da fa'din eh Isma'il yayi Murmushi da 'daga mai hannu Yace bye Allah ya dubeka ya baka nasara akan duk abinda kakesan aiwatarwa Da farin ciki Sosai Yace AmEEn nafah goge Yace karka damu Kana ya ficce. Junior ya bishi da kallan qauna Senior RAMADAN ko Tafiyarsu suke ahankali. Sam basu damu da sukai da wurri ba Hira suke cikin jin da'di dan kallo 'daya xaka musu subaka sha'awa. Basu suka iso igadaba sai bayan isha'di Da gajiya lis suka rabu da juna Sai dai 'yan unguwar sunyi mamakin ganin SAILUBAH... Acewarsu bai kamata taxo ganin gida yanxu ba. (Kunji saka ido irin na Mutane) Ba qaramin mamaki Abban da Kakah sukayi ba. Wajan ganin SAILUBAH tsulum a falan nasu. Ta xube jikin khakah Tace wash nagaji munsha hanya Cikin sarqewar murya Abban nata Yace ya haka meya kawoki gida yanxu Tace Abba 'dan shan jini kuka auramin Wanda yake kashe qananun yara yake yin ma'digo. Bayan da ya fahimci nagano shi shine yayimin saki uku....... Da fusata Abban Yace qarya kike mutuniyar banxa kawai Ai dama basan Auran kike ba. Nasan sai kinyi duk yanda xakiyi dan kirabu dashi Cikin sanyi Tace Wlhi Abba da gaske nakeyi Ya daka mata tsawa da fa'din xaki rufimin bakine ko saina mammakeki anan SAILUBAH tayi shuru tana turo baki Ya 'daga wayansa Cikin 6acin rai yakira Alhaji Aminu Lokacin yana cikin aikata masha'arsa a hotel Cikin isa da gadara ya 'dan tsaida sha'anin nashi ya 'dauki wayan Ganin sirikin nasa. Ya 'dauka da fa'din hello.... Abban SAILUBAH Yace ganinta nayi yanxu tana gayamin abinda hankali baxai iya 'dauka ba Nasani xata iyayima Komai dan tarabu dakai. Tunda daga baya tanuna bataso. Inaso naji daga gareka ya abin yake Alhaji Aminu yayi Murmushi ganin Abban nata bai yarda da abinda taceba tunda har yana neman jin ta bakinsa Yace Wlhi Abba kamar kasani. Haka kawai tasani agaba wai saina saketa harda nunamin wuqa. Ni kuma na tsorata da yanayinta har ban san lokacin dana mata saki uku bah. Sannan naji tana fa'din wai saita kwullamin sharri agunka bansan me tace maka ba. Cikin 6acin rai Abban Yace hmmm toh shi kenan tunda Komai ya abku Yace kayi hakuri Abba dan Allah Yace aa karka damu Allah yabaka wacce tafita Yace AmEEn sukayi sallama Da 6acin rai Abban nata ya kalli kakah Yace hmm aidama nasani kin dai ji abinda yace da kunnanki Kantayi magana SAILUBAH ta cafke cikin sauri da fa'din Wlhi qarya ya gaya maka Abba na rantse maka Ya kalleta da Takaici yanaji aransa kamar yatashi ya na'da mata dukan tsiya Amma ya 'daure Yace tunda ban isa dake ba ai shikenan kije xan nemeki Amma kisani nabaki watanni takwas kifitoh min da Wanda kikeso. Na rantse da Allah kika xarce haka da Almajiri xan ha'daki dashi Kuma kika qara kasowa Saidai kinemi wani uban ba niba. Tashi kiban waje Oho dai SAILUBAH Tace aranta dan ta'dauka wani mummunar hukunci xai 'dauka akanta sai taga sa6anin haka. Dan wannan mesauqine xata tsaida wani Nan tatashi sumi sumi tayi 'dakinta...... Kanta shiga kakah Tace ya 'dora miki idda ne Da sauri SAILUBAH Tace aa Da saurin fa'dawa 'dakin nata Tanajin Kakah na fa'din aigwara haka danni Sam dama bai kwantamin arai bah Abba yatashi yayi 'dakin matarsa batare dayace mata Komai dan Takaici SAILUBAH tajah numfashi dan ganin 'dakin nata Yana nan yanda yake harda kayanta dan ba'a kyautar ba kamar yanda tace Tayi Murmushi da fara tsaftace 'dakin cikin rera waqar *M shariff* Senior RAMADAN ko Bayan ya leqa ga mahaifan nasa na xahiri sungansa da mamakin rashin sanar dasu dabaiyi ba. Sai kawun nasa Sai yayi part 'dinsa yayi wanka Momy ta kawo mishi abinci Da qar yaci Yayi salla kana ya kwanta cikin farin ciki Anan ne yakira FAWAS Yace 'dan iska👯 na HAMEEDA dawo fah😀 Yana fa'din hakan ya kashe ya kira KHAMIS Yace na Aunty XEE na dawo toh😀 KHAMIS Yace da gaske Yace Sa wasa. Am inajij bacci sai gobe Ya kashe wayan. SAILUBAH mah da tayi wanka kiran XEE tayi Tace shegiya ta KHAMIS kina cikin kwanciyar hankali kin cafke yaro kin hanashi saqat😀 XEE da take kwance kanta na mata ciwo dan sun sami sa6ani KHAMIS jiya shine har yau abin yake damun xuciyarta. Ai tuni Tatashi xuciyarta cike da San jin qawartata Tace haba Qawa me yayi xafi xaki tadamin hankali haka Kinsan Allah gobe nake cewa Xan biyo RAMADAN SAILUBAH tayi dariya Tace basai kin biyo shi ba. Dan yanxu haka ina gida XEE tawaro ido😳 kana kuma tayi dariya😀 Tace anyi 'Yar iska anan. wannan ai story ne Cikin San tabbatar mata SAILUBAH tagyara kwanciya Tace Wlhi da gaske XEE Tace kin rantse fah😳 Kar kisa inxo yanxu dan tabbatarwa Tace Allah ya kaimu gobe kixo kisha mamaki Amma yanxu ko kinxu a gajiye nake XEE Tace ai ba'a qarya kusa da gida. Bani labari pls SAILUBAH tayi dariya Tace Allah sai mun ha'du gobe Kinga bacci nake ji...... Ta katse wayan da dariya Tagyara kwanciyarta Sai kuma tafara kiran RAMADAN Yace yane my Aunty Tace lau kaci abinci Yace eh Tace tsakani da Allah Yayi Murmushi Yace Abba yayi fa'da ko Tace hmmm kadai bari Ashe maxa ma sun'iya yanko qarya Yace Sosai mah Ban labari plx Tace bacci fah nakeji Yace nasani pls bani ka'dan👌🏻 mana my Aunty Tayi Murmushi da kwashe yanda sukayi ta gayamai Yace tab yanxu waxaki fidda Tace ina xan sani. Amma ai Kasan baxan rasa bah Yayi Murmushi Yace Hakka ne. Musamman idan na tayaki xa6e Tace hmm pls karka dawomin da halin ka fah Yace Auntyna kenan. Karki damu da wannan kinji Tace yauwa 'dan Qanina kaci abinci pls Yace Allah naci Tace toh gudnyt Tace Yah nyt my Aunty...... Haka sukayi baccinsu cikin kwaciyar hankali Xuciyoyinsu cike da farin ciki Washe gariko a Abujah junior ne ya fitoh cikin shiri Yace toh Dad ni natafi Kano..... Alhaji Aminu Yace katenaken karkaje Yace Wlhi Dad ba abinda xai hanani tafiyar nan sai mutuwa. Alhaji Aminu yayi shuru cikin wani hali Ganin haka junior yayi Murmushi Yace Nagode da ilimin da kabani sasai kuma yanxu na canja shawara xanci gaba da kiranka Dad 'dina dan soyayyata da nake hangowa a kwayar idanka..... Yanxu sauramin sati uku hutuna ya qare. Xan qarasa shi acan. daga nan xan wucce skull akwai Wasu ku'dade a hannuna. Na barka lafiya my Dad Yana fa'din haka ya ficce daga falan Wani mashin 'dinsa yagani roba-roba wanda yake matuqar yimasa kyau idan ya haushi Shegen mashinne dan ya ha'du Arayuqar junior Sam bai damu dasan hawa mota bah yafisan 'dalewa mashin 'dinsa. Amma yanxu ya xaiyi dole ya hau mota dan tarkacan kayansa Hakan ya tada motarsa tagani tafa'da ya bar harabar gidan yana yimata kallan qarshe dan yasa aransa baxai qara dawowa qaxamin gida irin wannan ba Xan nemi nashi na kansa ( RAMADAN junior kenan. Idanshi ya rigada ya bu'de da lera shiyasa Sam bai maida Komai komai ba. ) Haka Yana motar nan wutta yana san isa cikin sauri Qarfe 1:30pm na rana SAILUBAH ce me cin abinci cikin nutsuwa saiga XEE Tace 'Yar Uwa ya haka SAILUBAH Tace xauna kisha labari Aiko XEE tabaje tana fuskantarta SAILUBAH takwashe Komai ta gayama XEEE Taqara dacewa naga maseefa ganin idona. Kan yarinya nagani ancire mata fah😳 XEE ta doka salati Tace Allah ne ya temakeki daya cinye mana ke😟 Tace kedai bari. Aini yanxu ni da alhazawan garin Abujah sai ido XEE tayi dariya 😀 Tace naso ganin idanki lokacin da kika gano Gaskiyar shi Waye Tace ai kika ganni alokacin tausayina xakiji Tace hmm naji SAILUBAH dan Allah ya ku6utar dake hankali ya kwanta ta 6angaranki Kishi ne yake damuna SAILUBAH yaxanyi da KHAMIS Quruciya na damin shi 😂😂😂😂 Me SAILUBAH xatayi imba dariya Tace ke tsinannan kishinki baxai barki kixauna lafiya ba KHAMIS ko idansu ya da'de da bu'dewa akan mata Kigafah yanda matan suke binsu suke sharesu Sannan kice baxai ta6aki ba baxai kuma ta6a wata ba. XEE tajah numfashi Tace Kinsan abinda yafaru ne jiya SAILUBAH Tace saikin fa'da Tace ganinsa nayi da wata budurwarshi alayinsu Saudat Ban lura ba da Farko sanda naga motarshi Na qurama matar ido ina naxarinta Ashe Xanyi mummunan gani Dan kamashi nayi yana kissing 'din buduwar tashi a motar. Kinsan ni da kishi nan take ko hankalina ya tashi. Narasa ma me xan musu Sai kawai na wuccesu nashige gidan Saudat Ashe yaga wuccewar tawa Dan haka bansan yanda akayi ba Ina xama sai gashi ya shigo Hankalinsa a 'dan tashe yana wani Sosa qeya Yace am so sorry my..... Nayi saurin katseshi da fa'din. Karma ka yaudari kanka dan Wlhi ba saurararka Xanyi ba.... Kamar xaiyi kuka yafara cewa na rantse da Allah sharrin she'dan ban ta6a kissing 'dinta ba Nayi banxa dashi dan gani nayi yana san raina min hankali Ya kalli Saudat dake tafitoh daga betroom ya durqusa a gabanta yace dan Allah dan Annabi Aunty ki temaken kibata hakuri wlhi sharrin she'dan kuma wlhi banxan qara ba Saudat tace ni basan kan xancan ba faroshi daga Farko Kamar xai gaya mata sai kuma Yace hmm ina San im mayar da ita gidane kuma taqi Tace toh kabarta man Bayan yanxu taxo Xaiyi magana.... Ta ta katseshi da fa'din kamin rai KHAMIS kabarta ina cikin wani hali Wlhi. Shawara nake nema kaga ba SAILUBAH Ya kallan na gallamai harara Cikin tsoro Yace in jiraki Na bishi da mugun kallo da cewa Wlhi baxan bika bah. Katafi kawai idan nadawo xan nemeka Daqar ya tashi ya tafi Wlhi tun jiya haryau naqi saura ransa Da xaran nagansa sai inji raina ya qara min xafi dashi Sam narasa nutsuwa kwatakwata Dan daurewa kawai nakeyi idan yakira nake qin 'dauka Plx ya xanyi dan Allah Wlhi ji nake kamar in sami yarinyar inja mata kunne akansa. Ke koma inci ubanta inhuta SAILUBAH tayi dariya har sanda XEE ta qulu Tace Kinsan me xakiyi yanxu kisami nutsuwa. Cikin 6acin rai Tace dana sani koji xakiyi ne Sarai SAILUBAH tasan ta qulu dan haka Tace toh kiyi hakuri naga ranki ya 6aci Abu 'daya xakiyi kisaman muku nutsuwa da tabbatacciyar rayuwa Shine Karki saurareshi yanxu. Dan natabbata damuwar da yake ciki tafi taki KHAMIS yana maseefar sonki Kece xaki juyashi yanda kikeso idan kinso Naji da'din yanda kika nunamai fushinki gaba baxai qaraba Inko xai qara baxaiyi kusa da inda kike ba. Ki shareshi na tsawan sati 'daya na tabbata lokacin yagama gasuwa Kin nemamma kanki mafuta mutunci dan xaiji shakkar qara aikatawa ko abayan idan nakine. Dan gani xaiyi kamar xaki gansa XEE tajah numfashi Tace gaskiya baxan iya shareshi na tsawan sati 'daya ba. Gaskiya yayi yawa SAILUBAH tajah tsaki Tace toh ai shikenan kije kiyi abinda yadace miki Dan gaskiya shawarar daxan iya baki kenan...... Kan XEE tayi magana wayarta ta'dau ruri Tana dubawa taga KHAMIS 'din ne Tayi shuru tana naxari SAILUBAH Tace ki'dauka kawai horan da kika masa jiyama ya isa... Cikin sanyi ko ta'dauka. SAILUBAH taji kamar tashaqeta dan gatse tamata Amma sai ta'dauka. Cikin sauri Yace Wlhi da baki 'dauka ba dasai dai kijini a gadan asibiti Tace naji da Allah miye Yace kiyi hakuri Wlhi baxan qara ba Tace toh naji Yace inxo in ganki yanxu Tace aa Yace dan Allah Tace aa Yace xan miki kuka fah Tace toh ina gidansu SAILUBAH Yace toh ganinan Tace ka nutsu kayi breakfast da wanka fah Yace kamar Kinsan banyi ko 'daya daga ciki ba Tace toh kayi pls Yace angama my Luv I Luv u Tace me 2 Suka ajiye waya..... XEE tabi wayan da kallo tana raya Gaskiya so maseefa ne SAILUBAH Tace kin samu nutsuwa ko Tace Sosai mah. Agidansu RAMADAN ko Dad 'dinsa ne ya sami momy cikin farin ciki yake CE mata Yayah Jibiril ne yakirani yanxu wai 'dan namu xai kawo mana xiyara yau yana kan hanya Momy ta waro ido Tace da gaske Yace sharrin ku kenan wasu matan ba dama megida ya fa'di xance sai kunsashi rantsewa Tayi Murmushi Tace ayya kayi hakuri abinne yaban mamaki yau RAMADAN xaiga 'dan uwansa Yace aikuwa dai Dan haka a shiryamai abubuwa masu da'di dan ya tabbatarmin baya wasa da cikinsa Tace toh angama dadynsu Yayi dariya Yace harnatashi daga Dadyn RAMADAN nakoma Dadynsu Tace eh mana. Dan ga 'dayan yana San bayyana Yace yama bayya Kinsan farin cikin da nake ciki kuwa Tace aibasai kace bah. Dan Komai naka ya bayyana hakan Yace bari nakira Auwal na gaya mai Tace ya dace kam RAMADAN ko Tambayar wani 'dan department 'dinsu yayi qarfe nawa yau suke da lectures Yace biyu Yace Owkie. Hakan ne ya bashi damar sakankan cewa yaci gaba da baccinsa Yana cikin baccinne FAWAS ya shigo 'dakin nasa ya tasheshi da cewa 'dan is ya Abujah RAMADAN ya tashi yana fa'din Kasan da Auntyna nadawo FAWAS ya waro ido Yace ban gajine bah Yace mijinne ya saketa FAWAS yace bani labari pls naji xuciyata na bugawa RAMADAN yayi dariya Yace tadena toh dan Allah Nan dai ya gayamai abinda yaga xai iya fa'damai FAWAS yacika da mamaki Yace hankalinka ya kwanta Yace Sosai mah FAWAS ya gyara xama yace mungano San Aunty LUUVAH ne yake damunka Yace wai sai yanxu kuka Ankare da hakan Yace eh mana Yace hmmmm FAWAS ina maseefar sonta Wlhi FAWAS Yace bama saika rantse ba.... KHAMIS ne ya shigo cikin gayu yana wani murmurxa hannu alamun sanyi na damunsa duk dako yasaka suwaita RAMADAN Yace baka xagi sanyin da yawa bane. Shi yasa yake damunka Yace kadai bari Ya kadawo lafiya lau yace eh na sameku lafiya kuma Yace aini bana lafiya sai yanxu da safennan na samu nutsuwa FAWAS Yace ta hucce kenan KHAMIS yayi dariya Yace ba dole ba. Dabata hucceba narantse da Allah kuka xansa mata RAMADAN Yace bani haske pls kun barni a duhu Yace FAWAS ya baka bara na ganta cikin gidansu Auntynmu. Yama ka barota FAWAS Yace xama ka ganta Yace ban gane ba Cikin lokaci qanqani FAWAS ya bashi haske Yaja da baya cikin tsoro Yace wayyo Auntynmu Amma wannan akwai 'dan iska tsinanne me fuska biyu FAWAS Yace jeka dawo KHAMIS ya fitto yana mamaki Amma me😳 Yana futuwa sai ganin junior RAMADAN yayi ya tsaya da mota yafitoh yana qarema unguwar kallo KHAMIS ya kallesa dakyau Cikin bala'in tsoro Yace RAMADAN yaushe kafitoh Junior ya kallesa Cikin San basar da xancan nasa Yace dan Allah ina tambayar gidan Alhaji Naziru ne Cikin qara ru'dewa KHAMIS yajah da baya ya shige cikin gidansu SAILUBAH da gudu yana fa'din innalillahi..... Junior ya ta6e baki idanshi ya sauka kan wata budurwa. Yace 'dan jini ka'dan 'yan mata Jamila wacce yakira da 'yan mata tamai fari da ido Tace hmmm RAMADAN kenan yau kayi ra'ayin kulanine Yayi Murmushi Yace kiyi hakuri ba nakin bane wannan Pls xaki iya nunamin gidansu Tace Gaskiya kana da rainin hankali gidan nakunne ka manta gaka gashi Junior yabi gidan da tanuna mai da kallo cikin takaicinsa Bai qara kulata ba ya shige motarsa da juya kanta xuwa cikin gidan Yana danna alama..... Megadi naji ya bu'demai Jamila tabishi da kallan mamaki da kuma sawa arai ya gama rainata Aiko yanayin parking saiga Dad yafito kamar ance ya fitoh Junior yafito Cikin San qarema gidan kallo. Amma sai idanshi ya sauka akan Dady Kallo 'daya Alhaji Naziru yayi masa ya ganeshi duk dako ba abinda ya rabashi da senior RAMADAN Da sauri yaje ya rungumeshi yana fa'din Allah nagode mah daka dawo min da 'dayan 'dana Junior qara rungumeshi yayi cikin farin ciki da jin da'di. Dan kallo 'daya yayi masa yaji qaunar tsowan aransa..... Momy CE ta katsesu daga xancan xucinsu wajan fa'din Toh Dadynsu ka qanqameshi ka hanani ganinsa Jin haka yasasu raba jikinsu da juna Suna Murmushi Kama hannunshi tayi sukayi falo Sanda tatabbatar ya xauna tace nayi farin ciki Sosai da ganinka 'dana Yace nagode Momy nine nake farin Cikin kasan cewata daku Gaskiya Naji da'din hakan Dadyna Ya qare xancan da kallan Dady Sai Dady yayi Murmushi ya xauna kusa dashi Yace Allah yaci gaba da albarkar rayuwarku Yace AmEEn....... Khairat ce tashigo falan tana fa'din Dady kaga ankwan bikin Qawata Amina Ya kama hannunta Yace ga 'dayan yayanki ya dawo Ta kalli junior tace Ya RAMADAN ne fah Dady Dadyn yayi Murmushi Yace aa wannan 'dayan ne Ta qurama mishi ido sai tayi Murmushi Tace Wlhi Ya RAMADAN ne😀 Momy Tace shegen musu yayi miki yawa jeki kira RAMADAN 'din a 'dakinsa Da mamaki Khairat tanufu shashin RAMADAN tana shiga sai taga RAMADAN da FAWAS....... Tace 😳 lah lah lah FAWAS Yace lpy qanwata Tace Ya RAMADAN yaxama biyu FAWAS Yace kamar ya fah Tace gawani anan gawani acan falansu Dady RAMADAN yaji gabansa ya fa'di Yace ke me kike nuqunuqun cewa Tace toh Momy na kiranka Da sauri ya tashi yabi bayanta har xuwa falan.......... Yana ido biyu da junior gabansa ya fa'da cikin wani yanayi na mamaki da Al'ajabi ya nuna junior da hannu Yace innalillahi Dady yatashi yaxo gareshi ya kama hannunshi ya xaunar dashi Yace ga 'dan uwanka RAMADAN Senior ya kasa 'dauke idanshi akansa Yace ko bakace bah Dady kallan dana masa naji gabana ya fa'da tabbas wannan 'dan uwana ne Dady Yace haka abin yake Ku 'yan biyune Ahankali RAMADAN yakai hannunsa jikin junior ya ta6a kafa'darsa..... Momy da Dady suka fashe da dariya. Junior yayi Murmushi Yace kanutsu brother nine dai 'dan uwanka Momy Tace kai shi yayi wanka anshirya mishi abinci Senior RAMADAN Yace toh Amma..... sai kuma yayi shuru Suka tashi atare senior sai kallanshi yakeyi. Candai ya kasa jurewa sai kawai ya ware hannunshi alamar ya rungumeshi Aiko nan take junior ya rungumeshi Yace I miss u my brother Senior Yace miss 2 den I Luv u Me 2 junior Yace Momy da Dady da suke bakin 'kofah suke kallansu sai xuciyoyinsu suka cika da tausayinsu musamman ma Dady FAWAS sai ganinsu kawai yayi Abinda yasa yagane senior RAMADAN abu 'daya ne Shine kayansa Yace FAWAS ga 'dan uwana yaxo garemu FAWAS Yace kut😳 wannan naganshi ahanya aisai dai inta mishi xubah. Dan 'dauka xanyi Kaine RAMADAN Yace mu 'yan biyu ne FAWAS Yace Waye babba acikinku Senior ya kalli junior Yace koka sani Yace Sosai mah in gaya mai ne Yace ya kamata Yace toh Kaine Babban nine qaramin Senior yayi dariya Yace aha Naji da'din hakan Sosai. Kaga idan kamin lefi xan hukuntaka da tushe Yace bama xanyi ba bare ka hukuntani Yace ga toilet shige kayi wanka dan dama ban da'de da tara ruwa ba Yace Nagode brother Senior RAMADAN Yace karka sake Junior yayi Murmushi Yace wai godiyar Yace eh Yace toh brother Yana fa'din hakan ya shige toilet 'din FAWAS ya dafah RAMADAN Yace abin sha'awa dama nine nake da qani haka Yace xaka samu Yace kai haba Saidai 'dana Momy ai ta tsufah kaifah 'dan iska ne RAMADAN Yace Naji qaunarshi Sosai Cikin raina FAWAS Yace aidole ne Amma meyasa tunta muke dakai baka ta6a bamu labarinsa bah RAMADAN yayi Murmushi Yace toh Amin afuwa pls. dan naga gaya muku bashi da amfanine tunda baya tare damu...... KHAMIS ko yana shiga gidansu SAILUBAH jingina yayi da bango yanata nanata inna'lillahi Ya 'dauki lokaci kafin ya leqo..... Baiga kowa bah. Dan lokacin har junior ya shige gidansu Yayansa RAMADAN Ganin hakan KHAMIS yayi tunanin kodai idanshine ya nuna mai haka Ko kuma aljani ya gani ne Haka dai ya dinga tsaqar xuci har ya kai falansu SAILUBAH Anan yaga tauraruwarsa XEE Yace Barka da ranah Aunty LUUVAH Tace barka KHAMIS nasa meku lafiya Yace lafiya lau Tace sai kawai kaganni..... Yace eh Wlhi ya abin yake SAILUBAH takama baki Tace ni dana Aure 'dan shan jini me kisa kuma 'dan luwa'du Yace dama fah ni ban wani yarda dashi bah Tace hmm kaidai bari kawai Yace nabari tunda bai ta6a mana lafiyarki ba. Dan da yayi gangancin yin haka da sai yayi tuntu6e da Babban maseefar da baxata barshi ba har qarshen rayuwarsa SAILUBAH Tatashi tana Murmushi Tace hmm kunaji dani qannena Yace Sosai my Aunty. Ta qarayin Murmushi tanufi 'dakin Kakah tana fa'din kuji da'dinku masoya Duk Murmushi sukayi KHAMIS na ganin tashige 'dakin Kakah yayi saurin durqusawa agaban XEE idan shi cikin nata Yace kiqara yafemin my Luv dan Allah Tace nace ya wucce ko. Yajah numfashi Yace Nagode my wife insha Allah baxan qara bah Tace kama qara bani ba kai Yace toh ya xakiyi da Sonah Tace saidai san nakan ya kasheni. Tafa'da da wurga mishi harara Yayi Murmushi

Chapter 10 of 33