Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
a binciko muku dukiyarku ta Dubai da Kuwait da America Muji ya suke Junior ya tashi yana cewa toh ni bara naje 'daki nayi wanka kafin wani abokina yaxo Momy Tace toh RAMADAN senior ko saka SAILUBAH yayi agaba yanata mata shagwa6a da kashe mata jiki Ya kama hannunta Yace my Aunty kinji wai Dady Aure xaiyi min a this year ko SAILUBAH tayi dariya Tace toh miye 'dan Qanina ai gwara ayi maka dan kadena xuwa yawon club Kasan har kuka nakeyi idan nasan katafi can Ya sakar mata wani kallo da cewa Allah Ta lumshe ido tabu'de ahankali Tace Allah Yace toh kidena dan nadena xuwa Tace da gaske Yace eh. Tace toh gayamin Yace miye Auntyna Tace Kasan fah Abbana yasani agaba Yace eh Tace toh yaxanyi Ya shafah gefan fuskarta Yace bayanda xakiyi Auntyna kibar Komai agun Allah Saiya dubeki ya fitoh miki da miji cikin sauri batare da kinsha wahala ko kintada hankalinki ba Tace ina jin tsoran ya badani ga Wanda bai dace bah........ Janye hannunsa yayi daga fuskar tata Ya tsaida kwayar idanshi Cikin nata Kusancin yayi kusanci Dan Suna shaqar numfashin juna Awannan lokacin RAMADAN yayi imani duk abinda yaso yima Auntyn tashi xata bada kai Dan yagama kashe mata jiki Kallan da suke yima junansu yayi yawa. Hakan yasa xuciyar SAILUBAH tafara bugawa Tamkar yasan xuciyar tata bugawan take... Yace Aunty I luv u...... Gaban SAILUBAH ya bala'il tsinkewa ya fa'di Kanta tattaro nutsuwarta ya shigar da hannunsa cikin nata yana 'dan Murmushi Yace ina sanki Auntyna baxan bari Abba ya aura miki Wanda baxai dece dake ba. Saboda xanta jifanshi da addu'a har Allah yasa yabarki kikawo Wanda kikeso....... Wata sanyayyiyar ajiyar xuciya SAILUBAH ta sauke da Murmushi akan fuskarta takai bakinta kumatunsa ta sakar mai kiss Abinda yasaba ji shidai yaji Taqara bashi a kumatu. Yana kallanta Tace nagode Qanina Tashi yayi yana Murmushi Yace toh ni nayi skull xan duba miki Komai gobe sai mutafi tare ko Tace nifah nagama skull Yace yi hakuri mana mu'danje gobe Taturo baki ka'dan Tace kanasan takura min ko Yace aa my Aunty Tace toh Allah ya kaimu Ina wannan mara kunyan Yace 'dan uwana Tace koma Waye Yace yana 'daki yace ma yana gaidake Tace kafiya kare mutum Yayi Murmushi da bata kiss ahannu yafita tabishi da kallo. Xuciyarta cike da San qanin nata Yana fitta yakira KHAMIS da FAWAS Yace musu gays akwai matsala fah FAWAS Yace nafi kowa shiga cikinta xa'a rabani da HAMEEDA KHAMIS Yace hmm muha'du a skull pls xan rasa Aunty XEE..... SAILUBAH ko RAMADAN na fitta da minti goma ta'dauki gyalanta sai 'dakinsa dan tatashi da abinda junior yayi mata jiya Xuciyarta na gaya mata gwara tacimishi mutunci ko tasami nutsuwa Aiko tana turo 'dakin tagansa yana Reding wani novel Suka kalli juna Nan take xuciyoyinsu suka bada dam fa'duwar gaba tabayyana a fuskokinsu Taqare mishi kallo tsaf kana Tace naxo inja maka kunne👂🏻kaji da kyau ni ba sa'arka bace. Naga iskanci da rashin kunya Suna maka yawo akah. Toh ni 'dinnan xan sauke makasu Mara mutunci kawai har xaka kalleni kace baxaka bani kowane irin matsayi na SOO bah Ni sa'arkace daxaka bari baxan tunaninka ya saka furtamin wannan Kalmar. Ko ajikina Kaga anrubuta ina buqatar soyayyar qaramin Yaro 'dan iska mara kunya kamarka ne iye tambayarka nakeyi Tashi junior yayi yana murmushi Cikin halin ko in kula ya xuba drink yasha yana binda da wani shegen kallo of 2 down. Tun safe yatashi da muradin San ganinta Da San jin muryarta ko yasami nutsuwa Ganinta yanxu yasa hankalinsa ya kwanta xuciyarsa tacika da farin ciki Kalamanta basu 6atamai raiba danya shirya gyara mata su Ya sauke kallansa akan bakinta ya cije harshe cikin sanyi Yace kingama Tabishi da mugun kallo Yace toh mu dawo baya mana ka'din👌🏻 Tace me kenan Yace kina maganar ko naga an rubuta kina buqatar soyayyar qaramin Yaro ajikinki Toh na yaushe Bayan banxar xuciyarki da wawan tunaninki ya kasa wayar miki da kai ki fahimci kinda'de da fa'dawa soyayyar qaramin Yaran Wawiya kawai. Kowa kika samu saiki kai hannunki jikinsa Toh bara kiji daga yau kika qara kirana da 'dan iska saina nuna miki halin 'yan iskan danni tantiri ne acikinsu Kinxo ki jamin kunne akan ke ba sa'ata bace. Toh angaya miki ni sa'anki ne Nafa'da baxan baki kowane irin matsayi bah. na SOO Dan baki kai in baki bah Nidai na rainaki Sosai Wlhi Amma kina da wasu abubuwa daki mallaka Wanda nakeso agame da mace wayayyiya me aji........ Ki dinga killa cema mutumi na kanki dan yana maseefar sonki. Idan kikayi wani kuskuran da wani yaganki yafara sanki Wlhi saina hukuntaki. Dan inasan farin cikinsa Ya qarashe maganar tashi da miqa drink 'din hannunsa yana Murmushi........ 'Daga hannu SAILUBAH tayi xata sheqa masa marii Yayi saurin gare kansa tawajan riqe hannunta Ya waro fararan idonsa kamar na senior Yace kut😳 Tunda nayi wayo ba'a ta6a marina bah Kikayi kuskuran hakan Wlhi saina miki dukan tsiya Yafa'da da sake hannunta tare da quqarin 'daukar wayarsa da take ringing. Yaga Abbas abokin nasa......... SAILUBAH ta'dora hannu aka🙆🏼 taxabba'da ihu da fashewa da kuka Kuka take Sosai dan tunda uwarta ta haifeta ba'a ta6a cimata mutunci irin wannan ba Kuka take hawaye na xuba mata. xan cikan sa nayi mata yawo acikin kwanyarta Ganin haka yasa junior in 'daukar wayar Abbas Ya xuba mata ido yanajin kukan nata har cikin ransa Saiyayi yunqurin barin 'dakin dan yasan Abbas xuwa yayi 'daukar nasa Ai tamkar ta ankare tasama kofar key Tare da goge hawayanta takallesa cikin kallan tsana Tace kai ka'isa Ka'isa kafita daga 'dakinnan batare dana hukuntaka bah Wlhi saina xaneka kafin kabar 'dakin nan Junior yaxuba mata ido. Tausayinta ya kamashi. Sam bayasan ganin mace cikin damuwa bare yaga tana kuka Sai dai indole ba yanda xaiyi Nan yaji yanasan lallashinta. Amma bata xahiri ba taba'dili 😬 Yafara tunanin ta inda xai lallasheta Aiko dabara tafa'do masa Yacire bell 'din jikinsa ya miqa mata Yace gashi Ki xanenin dan sauri nake amma ahannnu xakimin SAILUBAH ta kar6a dan xuciyarta xafi take mata Amma me😳 Kunsan ance kowane bawa da qaddararsa arayuwarshi Wani Kaga Allah yasa mishi tsoran abinda bai taka kara ya karya ba. Toh hakance tafaru da junior Tun yana qarami Allah ya jarabce shi da tsoran kyenkyaso..... Idan ya ganshi har sumewa yakeyi Shiyasa idan kaje 'dakinsa na waje ko na abuja xaka rantse da Allah ba'a rayuwa acikin 'dakin Dan koyaushe ma'aikata acikin aikinsu suke Toh Yanxu mah kamar ance ya kalli gefansa Aiko yaga kyenkyaso Wani tsalle yayi sai gashi abayan SAILUBAH Cikin bala'in tsoro Yace kyenkyaso kyenkyaso Yafa'da afurgice SAILUBAH ta kallesa da mamaki furgicewar da yayi Yana mammannewa abango cikin tsoro yake nuna mata shi da hannu SAILUBAH tabi kyenkyason da kallo kana ta kallesa tana rayawa aranta gaskiya bata ta6a ganin 'dan iska 'dan rainin wayo kamar junior ba 😳😳😳 Abin mamaki hawaye tagani yana xubamai pls dan Allah Ki kukoreshi xan mutu Nan taga idanshi yafara juyawa yana kakkafewa jikinsa na rawa Yana kallan kyenkyason cike da tsoro SAILUBAH tasaki baki tana kallansa Bata ankareba sai ganinsa tayi luuuuu..... Ya xube aqasa Tana kai hannuta gareshi taga Ashe sumewa yayi Aiko nan take tayi cilli da bell 'din hannunta ta bu'de furiji ta 'dauki ruwa ta watsa masa Ina Junior bai farfa'do ba Tayi sauri tabu 'kofar hankalinta tashe xata futta Sai kuma taji mutsi Nan tajuyo da sauri Aiko sai taga kyenkyason ne ya hau kan wata leda yake motsi Taje takashe shi da takalmi tayi waje dashi Kana tasake yayyafama junior ruwa. Nan yajah numfashi ya bu'de idansa ahankali aiko yana ganinta Ya qanqameta fa'di yake dan Allah kifitar dashi Tace sakeni Yayi saurin saketa ka'dan Tausayinshi ya kamata Tace na kasheshi na futar dashi tanunamai 'kofa. Kaganshi can mah. Junior ya koma bayanta Yana cewa xanbar 'dakin nan yau Baxan iya da kyenkyaso ba Ya fa'da da tsoro atattare dashi Kunsan SAILUBAH da tausayi Nan tafa'da tunani tana rayawa aranta Ikwan Allah Wato kowa da abinda yake tsoro Kalli yanda kyenkyaso ya rikita junior harda sumewa Tayi nisa atunaninta ya durqusa a ganta Yace dan Allah ki'daukeshi nasamu na hucce Ta kallesa yayi sanyi qalau abin tausayi Tace meyasa kakejin tsoransa Yace nima bansani ba Inaga dai tunda aka haifeni idan naga kyenkyaso nake sumewa Bana sanshi Xai iya kashe ni wata rana Pls 'daukeshi na wucce baxan qara kwana a'dakin nan bah SAILUBAH tayi Murmushi nan kuma tatuno da rashin kunyar da yayi mata Tace baxan 'dauke ba Ya waro ido😳 cikin tsoro Yace sabo dame Tace saboda baka da kunya baka da mutunci Sam bakasan darajar na gaba dakai ba Junior ya kalli 'kofa sai yaga kamar kyenkyason bai mutuba Hakan yasa ya matso kusa da ita yana kallan kwayar idanta Ya fashe mata da kuka Yace dan Allah dan Annabi kitemaken Wlhi ina maseefar tsoran abunnan Kuma baxan qara yimiki rashin kunya ba har abada indai Xaki temaken ki'dauke shi Hankalin SAILUBAH ya tashi. ta hango tashin hankalin da tsoran da yake tare dashi. cikin sauri Tatashi Tace toh kayi shuru manah. Hankicif ya 'dauka ya goge fuskarshi dashi. Yana kallanta ta'dauki kyenkyason ta'daureshi a baqar leda tasa a abin xuba sharan senior tarufe shi Sannan Tace kaga nasashi Cikin nan kuma yana leda mah shikenan 🙅🏼 ko Yayi saurin 'daga mata kai tare da xuwa gefanta ya sakar mata kiss a kumatu Yace nagode Auntyn brother yafa'da da Murmushi akan fuskarshi Tace kaifah 'dan iska ne Wayace kamin kiss Yace namiki ne dan nuna godiyata gareki bawai dan kinkai ba Ai kinsan baki kai wannan matsayin da xankai tsaftataccan bakina kumatunki ba Tace ko Yace gaske Tace hmm xakaci gaba daga inda katsaya min arashin kunyar ko Yayi mata kallan raini Yace eh Tayi Murmushi ganin ya ficce daga part 'din. Tace aranta xaka gamu danine tunda nagane abunda yake hargitsaka ni dakai ne shegen Yaro kawai Haka tabar gidan xuwa nasu tana jinjina lamarin tana mamaki Ashe akwai mejin tsoran kyenkyaso Tana xama takira XEE Mamah CE ta'dau wayan take gaya mata tana skull Tace toh intadawo takirata. Maman Tace toh Daga jiya xuwa yau har 'yan unguwar sunsan Auran SAILUBAH mutuwa yayi Dan ita kanta in katambayeta cewa take mijin bame halin kirki bane shiyasa barinma Auransa Can wajan qarfe uku RAMADAN senior ne da FAWAS da KHAMIS agidansu FAWAS RAMADAN Yace wai Dady Aure xaiyimin a shekarar nan FAWAS yagyara xama ya gaya musu yanda sukayi da dadynsa KHAMIS mah yafa'di yanda sukayi. Duk hankalinsu tashi yayi KHAMIS Yace yanxu haka Dady ya kori babah me gadin gidanmu FAWAS Yace nima haka RAMADAN Yace Ku gwaraku tunda kunbu'de hanya Auntyna batasan kanta bah haryanxu FAWAS Yace baka dai nemi tasani ba Ni yanxu damuwata HAMEEDA. Pls kurakani gareta yau KHAMIS yajah tsaki Yace idan narasa Aunty XEE toh Wlhi mom Dad sun rasani kenan..... RAMADAN yayi murmushi Yace ga shawara Yace ina jinka Yace tunda baka nuna mata komai bah a skull toh anjima idan kaje gidansu kagaya mata Sai kaji me xatace Yace ko RAMADAN Yace kwarai Yace toh Allah ya kaimu dare RAMADAN ya dafah FAWAS Yace toh kai kuma sharri mu wucce kawai Da sauri FAWAS yashige toilet Minti biyu ya 'dauka yafitoh Ya shirya kansa suka nufu qauyan takai Suna xuwa ko suka sami Yaron aike FAWAS ya kirashi Yace yakira mishi HAMEEDA aiko da gudu yaran yashige gidan. Tana gaban mulhu kamar Kullun. Yaran Yace ana sallama dake HAMEEDA Tace Waye Yace wasu 'yan gayune a mota Da sauri ta 'dauki hijabinta dake rataye a igiya Tashige 'dakinta tafeshe shi da turare tasaka Kana tayi niyar ficcewa...... Inna tace toh akuya me San Maza sunyi kira jiki na 6ari anfeso hijabi da turare ko Tace aa fah Innah Tace nayi qarya kenan Shuru HAMEEDA tayi Innah tajah tsaki Cikin baqin ciki Tace saiki gaya masa sakwan kawun naki Wlhi idan bai turo iyayansa acikin sati biyu bah toh kitabbata Auran Alo ya hau kanki. Tace toh xangaya mai jah tsaki innan tayi HAMEEDA ko tayi futowarta Allah Sarki takwana biyu bataga masoyin nata bah Dan haka tana ganinsa tawage haqura FAWAS yayi Murmushi Yace aminci ya tabbata agareki ya masoyiyata kuma YAYATA Tace kaima ya tabbata agareka kaxo lafiya Yace qalau matata da fatan yau kin shirya min kalamai Tace eh kuma masu da'di Yace toh Madallah gayamin Tace kawuna da inna sunsani agaba wai dole saina gaya maka katuro magabatanka nan da sati biyu inba hakkaba Su Aurar dani ga Alo.... Gaban FAWAS ya fa'di cikin 'daure fuska Yace waye kuma Alo Tace wanine adanginmu Yace kina sanshi Ta kallesa da harararsa Tace Amma ai Kasan ba wanda nakeso sama dakai Shine xakamin wannan tambayar Yace toh kunta6a hira dashi Tace aa Yace Ki gayamin gaskiya cikin fusata Tace wai xanma qarya ne Yace nasa ni tunda 'dan uwanki ne ai xaki iya muna funtata kuna tare kicemin bakya tare Ran HAMEEDA ya 6aci ta 'dago ta kallesa. Nanta hango kishi mala mala kwance a fuskarsa Ganin haka yasa tamayar da 6acin ranta Tace hmm qaxami ne fa Kuma bashi da ilimin arabi bare na boko Bakinsa wari yakeyi idan yaxo gaida inna Na tsaneshi Sam bana sanshi Shiyasa da maganar tashi tafitoh na sona da yake yin nace bana sanshi Shine fah kawuna yace toh in gayama ka turo magaba tanka Sanyayyar ajiyar xuciya FAWAS yasake dan yanxu hankalinsa ya kwanta dayaji gar Yace yauwa YAYATA dan Allah Karki bari kalma 'daya tashiga tsakaninki dashi Tace toh Yace batun iyayena ko xan gaya musu Tace toh Yace toh gayamin Tace wani abu Yace dabaki ganni kwana biyu bah me kikaji aranki Tace baqin ciki da tashin hankali mana Ya gya'da kai Yace dama kina sona har haka Tace Kaine farin cikin ruhina Kaine farin Cikin xuciyata Kaine farin cikin idanuna Ina sanka FAWAS Kana hanani bacci Idan na rufe idona ganinka nakeyi cikin mafarkaina Idan nabu'de hotan fuskarka nake gani ga kowane halitta idan nayi ido hu'du da ita Idan ina aiki tunaninka yafiyin aikin nawa yawa Sai inta kwa6a innah tata xagina Ina sanka ina sanka ina sanka Bansan yaushene xuciyata takamu da sanka har haka ba. Farin ciki yacika xuciyar FAWAS Yace Allah kanunamin ranar daxan mallakeki amatsayin matata Tace AmEEn In kawo maka 'dan wake Yayi saurin girgixa kai alamar aa Tace meyasa Yace haka dai Tace haka kawai Yace naci abinci ne Tace toh meyasa kaci Bayan nace kidenaci in xakaxo gareni Yace mantawa nakeyi Tace meyasa dukkan wani abu baka mantashi sai wannan FAWAS yajah numfashi Yace kibarni haka dan Allah Kwakwalwata ta tushe damuwata yanxu in San yanda Xanyi iyayena suxo Su mallaka ma iyayanki sadakinki Kona samu in mallakeki cikin watanni biyu Tawaro ido Tace wata biyu fa kace 😳 Yace eh Tace yayi ka'dan Ina lefin wata biyar Kaga lokacin dangi sunsan da tafiyata gidanka Sai suyimin kayan 'daki anutse Amma wata biyu yayi ka'dan Ko tsintsiya banga innah da kawu sun siya min ba Bare aje kan kujeru gado randa ledar 'daki tukunya......... Xuwa yanxu FAWAS ya saba da surutu da shirmen HAMEEDA Ganin da yayi dare nayi shiyasa shi katseta da cewa YAYATA Tace na'am Yace xamu tafi Tace tun yanxu Yace eh Kinga dare yayi Tace toni ban gaji da hirar dakai ba. Yayi Murmushi Yace so kike na kwana anan Taturo baki da cewa eh Murmushi yayi ya hau lallashinta dayi mata da'din baki har yasami Kansa tabarshi Ya miqa mata ku'di taqi kar6a. Sanda ya ha'da da rokwanta Allah Sannan takar6a a shagwa6e Suna hanyar dawowa gida ne. RAMADAN Yace ko tawajan surutu HAMEEDA xata nisha'dantar dakai FAWAS yayi Murmushi Yace kunji dai itama ansakota agaba ko KHAMIS yayi dariya Yace Allah na roqeka kasa asako itama Aunty XEE agabah RAMADAN yayi dariya Yace AmEEn Bayan sallar isha'I ko KHAMIS Yana tare da XEE Yake gaya mata halin dayake ciki Yace pls my luv Karki bari arabamu Komai wiya xan nace miki Pls karkiyi yunqurin barina Sanki yagama yin tasiri ako'ina na jikinsa Cikin sanyi XEE Tace Musa addu'a agaba. Basan ya akayi nafa'da soyayyarka ba KHAMIS in bakai baxan iya rayuwa bah Shuru yayi mata danshi yafi jin tausayin kansa akanta Haka suka rabu xuciya cike da damuwa Itama hakan abin yaxo mata Dan tana shiga gidan nasu iyayanta suka sata agaba Akan tagaya musu Wanda takeso Tace KHAMIS..... Babanta Yace KHAMIS Wanne 😳 Tace KHAMIS dai BABAH Mamah tadoka salati Tace KHAMIS qaninki😳 Tace eh Ni shi nake so Baban nata yaxuba mata ido Yace Zainab baki da hankali KHAMIS ba sa'an Auranki bane Yayi yaro Kin girmeshi da shekara kusan shidda. Kiyi tunani mana Tayi shuru Yace kirabu dashi kinji Hawaye ya xubo mata. Tace Wlhi BABAH baxan iya rayuwa ba KHAMIS ba...... Gauuu mamah tafalleta da mari Tace sai yau nasan baki da hankali. Ko kinsha giyar wake iyayansa ba yarda xasuyi ya aureki ba BABAH Yace koni baxan yarda ta aureshi ba. XEE tafashe da kuka da barin falan Mamakinta yacika iyayan nata Tana fa'dawa gado takira SAILUBAH wacce take kwance har lokacin tana tuna junior dana dariya wani lokacin taji tausayinshi Gashi tana so senior yaxo tabashi labari...... Ta'dauki wayan tana fa'din qawata yane XEE tafashe mata da kuka wiwi Tace SAILUBAH xan rasa KHAMIS Tace bangane bah....... Nan ta Kwashe Komai tagaya mata SAILUBAH tayi dariya Tace dalla Ki kwantar da hankalinki Kinsan fah ba qaramin so iyayan KHAMIS suke masa ba Idan sukaga ya kamu da ciwo aidole su aura mishi kee 6angaransa kenan Naki ko duk yanda akayi dake kika kafe kikace shi kikeso aidole suma su hakura su barki dashi XEE tajah numfashi Tace wato duk Wanda Allah ya jarrabeshi da SOO toh yagode masa SAILUBAH ba ciwan dayafi so xafi da ra'da'di SAILUBAH Tace hmm Allah ya futar da kowa daga matsalar da yake ciki Tace AmEEn Suka ajiye waya SAILUBAH tayi dariya Sosai Tana cikin yine senior ya shigo Yaqare mata kallo Yace Auntyna wannan dariya haka Tace kadai bari so maseefa ne RAMADAN yayi Murmushi Yace Sosai Kin fa'da San wani ne Tace ni😳 Yace eh Tace aa Yace hmm dama naxone kibani labarin yanda akayi 'daxo junior yace baxai kwana a room 'dina ba Na tambayeshi Yace in tambayeki SAILUBAH tagyara xama tabashi labari tiryan tiryan Abin yaba RAMADAN tsoro tausayin 'dan uwan nashi ya kamashi Yace toh kidena dariya dan Allah Tace tunda nasan me yake sashi tsoro ya shiga uku aguna Wlhi Yace kai Auntyna Tace sai da safe Yace Aunty Tace miye Yace kiyafe mishi pls Tace hmmm kabarni dashi dan saina koya mishi yanda ake bin naga Ta6e baki RAMADAN yayi yatashi yaje yayi mata kiss ahannu Yace bye bye gud night Tace Yah night Tabishi da kallo har ya ficce Daqar Dady da Senior RAMADAN suka lallashi junior ya hakura ya kuma room 'din senior bayan an caje 'dakin tas an tabbatar ba wani kyenkyaso?? Washe gari XEE tana tare da SAILUBAH Suna tattauna matsalolinsu Senior ya shigo Yace Auntyna baki shirya bah Tace eh jeka kawai nafasa Murmushi yayi Yace Aunty Tace RAMADAN Yace Kusan darajar karatu fah Tace toh Yajuya ya fitta XEE Tace wa yaketa wani karatu anata luv SAILUBAH tayi dariya Tace ba wance ta fa'domin sai Saudat XEE tajah tsaki tace Allah ya ha'data da shegiyar kishiya makira...... SAILUBAH tagyara xama tabata labarin junior tsaf Mamaki da al'ajabi yacikata Tace yanxu RAMADAN 'yan biyu ne Tace eh mana In kintashi tafiya kilesa zakiga 'dayan kisha mamaki Sam bashi da kunya Kuma Wlhi baki isa Ki tantance kowa acikinsu bah Jiyanma dan nasan nawan yayi skull ne shiyasani tabbatar da wancan 'dan iskan XEE Tace aiko xanje in gansa. Yanxu tashi ki shirya kinga lokaci na tafiya SAILUBAH tajah tsaki Tace toh me xaku siya mata nema..... Kan XEE tayi magana Kakah tasaka tata maganar Tace ina xakune SAILUBAH Tace gidansu Maimunan da Nace miki yaune kamunta. Amma kafinnan saimun 'danyi siyayya a kasuwa. Tace oho yarinyar kirki inkunje Ku gaishe min da mamanta XEE Tace toh Matar baban SAILUBAH CE tafitoh cikin shiri Tace Kakah nima natafi gidan Umma (qanwar ta) Kakah Tace toh saikin dawo Har takai 'kofa tadawo Tace da ku'di awayarki ne SAILUBAH Tace eh Tace 'dan sammin nakira abbanki da Allah SAILUBAH tamiqa mata wayan Takar6a da danna number tasa Kana tafito harabar gidan Bayan tagama wayanne tamanta tawo waje da ita Lokacin yayi daidai da fitowan junior yauma Abbas yaxo 'daukarshi ya xaga dashi gari Sai suka ha'da ido haka kawai ya tsinci kansa da gaisheta Tace lafiya lau RAMADAN kaga namanta nafitoma da Auntyn taka wayarta ungo kaimata Junior ya kar6a yana cewa toh adawo lafiya Tace AmEEn Ya 'dauki minti biyu yana kallan gidan shin Ya shiga ne ko ya tura Yaro yakai mata....... Abbas ya dafashi Yace abokina lokaci na tafiya fah Yayi Murmushi Yace 'dan jirani ka'dan???? Yana fa'din hakan ya shiga gidan A falan yasamesu lokacin Kakah tabar falan XEE Tace ha'a kadawo ne kuma Kallo 'daya yayi mata yasan itace Aunty XEE Yayi mata kallan mutunci Yace eh SAILUBAH ta harareshi Tace kaji maqaryaci harda wani cewa eh kamar shine Toh qamshin Ku yasa naganeka Meyakawo Yayi Murmushi dayi mata kallan raini yana qarema falan kallo Yace mexai kawoni kuwa Yafa'da da cillah mata wayarta Yaci gaba da fa'din akwalar wayarki mamanki tasani kawo miki banda haka mexai kawoni Tace wai kai meyasa kayi cos a rashin kunya ne Ya harareta da jan tsaki xai bar falan Takalli XEE wacce tasake baki tana kallan Junior Tace mata kingan shi ko Sam bashi da kunya gashi 'dan iska me tsoran kyenkyaso?? Ya juyo ya kalleta cikin nuna rashin damuwa da furucin nata yanuna XEE da hannunsa Yace kinci darajarta dana nuna miki iskanci a falan gidanku kamar yanda nayi miki kashedi Duk da haka kinci bashi. Shawara 'daya xan baki. kar kiyi kuskuran da xamu sake ha'du da juna ni da ke Dan ba abinda xai hanani nuna miki ni tantirin 'dan iskane.... Ya qarashe maganar Cikin nuna rashin kunya da raini?? Kana ya futta XEE Tace heeeee?? Naga mara abun al'ajabi SAILUBAH tajah numfashi Tace tunda uwata ta haifeni banta6a cin karo da Wanda ya bala'in rainani da cimin mutunci irin wannan shegen yaran ba. Sam kuma yau banji Komai ba akan kalamansa dama jiyane bakiga yanda yasani kuka bah XEE Tace ni tsoro fah yabani Gashi ba abinda yaraba shi da RAMADAN namu Wlhi in ahanya ne naganshi 'dauka Xanyi RAMADAN ne Harfa tsayinsu 'daya qaurin jikinsu 'daya???? SAILUBAH Tace ina ganesu dan qamshinsu Na saba da RAMADAN kinga ko qamshinsa baxai bar hancina bah XEE tajah numfashi Tace sai kiyi taka tsantsam dashi dan na hango abu 'daya atare dashi Tace miye shi XEE tata6e baki Tace baki lura idan shi a bala'in bu'de yake ba Yafi RAMADAN bu'dewar ido Sosai Tace hmm barni dashi na da'de da hango hakan tuni. Kinga tashi muje siyayyar nan kinmaqi fa'dar abinda xamu siya mata Tace musiya mata kayan kitchen kawai..... Junior ko yau rijiyar xaki suka nufah Abbas Yace pls abokina ka'daure yau dai kayi budurwa wacce xata xama mata agareka. Dan naga Shakira dai ba Auranta xakayi bah Yayi Murmushi Yace hmm nakamu dasan wata Amma baxan sameta bah Abbas Yace me yasa Yace haka dai Yace toh basai kasamu wata ba ka......... Abbas bai idda xancansa ba sakamakwan wata budurwa data Sha gaban motarsu...... Yayi saurin taka burki cikin 6acin rai ya fitto xai sauke mata maseefa..... Saidai ganin hankalinta tashe shiyasa shi harararta Yace da Allah malama matsa min ahanya Wawiya da yanxu na ka'deki fah Cikin raunanniyar murya Tace dan Allah Ku tamakeni wasune suke bina xasu 6atamin rayuwa dan Allah kutemakeni........ Kan Abbas yabata amsa wata mota daxo tayi wani wawan parking a kusa dasu Maxa hu'du suka fitto daga cikinta Da sauri taje bayan Abbas tana fa'din kagansu ko 'Dayansu ne Yace kina 6ata mana lokaci fah Dalla xoki shige cikin Junior ya fitto Yace idan taxo ta shige uwarku xaku mata..... Duk suka kalleshi ya Kawar da idan nashi daga Kansu yana jan tsaki Wani cikinsu Yace kai 'dan gidan uban Waye Kasan Waye ni Duk yarinyar danaji sha'awarta dolene inyi amfani da ita Tayimin dan haka kai baka isa ka hanani cinma abinda nakeso bah. 1 ni 'dan gidan ubanka ne 2 Allah yasa kaine 'dan shugaban qasar Nigeria 3 toh daga yau kadena kusantar kowace 'ya mace. Idanko kayi nasarar cigaba da kusantar mace. Toh katabbatar nama gurin bugun wasa ne 4 Wlhi na'isa har nayi yawa. Indai kaso cinma burinka akan yarinyar nan Toh namaka alqawarin hakan baxata faruba....... Junior ya qarasa maganar

Chapter 12 of 33