Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ta cece kuce. Masu bada hakuri nayi, masu neman ba'asi nayi, haka masu zuga nayi. Uwani kuwa sai mayar da zancen take yi. In da Allah Ya taimake ni duk sanda nazo wucewa ta ofishin 'yan sandar unguwarmu sai na duka na gaishe su kullum, suna ganina suka gane ni nima na gane su. Kalmar da suka fara ambato itace ah kece daman? Ke kuwa yarinyar nan mai hankali meya jawo kika shiga rigima irin wannan? Na fashe da kuka nace ku taimake ni dan Allah ina neman wata alfarma guda daya. Sai mai kivar cike yace yarinya ai babu wata alfarma da zamu iya yi miki anan, duk wata alfarma sai dai ayi ta a ofishinmu. Tunda an riga an kira mu dole mu tafi dake. Nace daman zanbi ku, bana so ku saka ni a gaba da ankwa ku wuce dani ta gaban mutanen unguwa yara suna bina suna kallo kamar wacce tayi sata. Zan hau babur ya kain ni sai mu hadu a can. Wallahi ba zan gudu ba. Sai suka yi dariya suka ce idan kin gudu ma ai zaki dawo, ba gamu a kofar gidanku ba. Ko zaki shiga duniya ki bar iyayenki saboda bashin da bai kai dubu ashirin ba? Suka yi min izini na tari acaba na hau, duk da babu nisa daga gidanmu. Na dan dade ina jiransu sannan suka karaso, aka shiga da mu uku ofishin mataimakin DPO, 'yan kallo aka barsu a farfajiyar suka ci gaba da gulmace gulmacensu. Saii a lokacin na gane makiyana wadanda ada na dauka masu kaunata ne, wadanda ada bana kulawa ashe sune masu kaunata, sune masu jimamin abinda ya same ni, sune masu nemar min afuwa a wajen wadanda na yiwa laifi, sune masu fada har da tayar da jijiyoyin wuya idan aka zage ni. Uwani ta mayar da zance, haj rabi ma haka sai aka tambayeni shin abinda suka fada gaskiya ne kuwa? Na amsa nace haka ne, sannan na basu hakuri gami da yin alkawari zan biya nan da kwana biyu. Uwani ta zabura tace karya nakeyi bani da ko kobo, don haka yace a kulle ni babu ruwansa. Mataimakin DPO ya sake tambayata haka aka yi? Na amsa masa da haka ne. Don haka yace aje a kulle ni har sai yayana yazo yayi belina kuma yayi alkawarin zai biya sannan a fito dani, idan kuwa yaki zuwa sai a kaini kotu alkali ya yanke min hukuncin dauri daidai laifina. DUK KYAN TAKALMI 2* 1 BABI NA BIYAR Washegari misalin karfe bakwai saura kwata na safe aisha farida ta shirya tsaf tana sauraron 'yan gidan su tashi. Ta hada kudaden nan ta kidaya naira dubu goma sha biyu ne cif cif tasan dai uwani zata daga mata kafa tunda sauran naira dubu biyar ne kacal har zuwa wani lokaci. Abida ce ta fito kofar daki tayi hamma tayi mika yayin data murtsike luhu luhun idanuwanta wadanda suka kumbura a sanadiyyar kukan da ta sha yi a cikin dare, ga rashin bacci. Ta tura kofar dakin aisha farida don ta duba yaranta, tayi matukar firgita a lokacin da ta ga fararen kayan jikin aisha farida a tsaye a tsakiyar daki har sai data daka tsalle tayi kara. Nan da nan aisha farida tayi magana tace anty abida lafiya kika firgita? Nice fa. Abida ta dafe kirji tayi ajiyar zuciya tace aisha yaushe kika dawo? Tayi murmushi tace ai anan na kwana. Abida ta tambaya cike da mamaki yaya akayi kika fito daga wajen 'yan sanda? Aisha farida ta sake yin murmushi tayi ajiyar zuciya sannan ta fito da himilin kudin nan daga aljihun wandonta. Tace kinga na hado naira dubu goma sha biyu saura naira dubu biyar. Ai zasuyi min hakuri har in samu ko? Abida tayi shiru kamar mai tunani yayin da hankalinta yayi mummunan tashi ta dubi aisha farida cike da fargaba. Ina kika sami wadannan makudan kudin a dare daya? Anya kuwa aisha kin kwana a gidan nan? Kada ki boye min komai, ni mai baki shawara ce a gaba daya matsalolinki. Matsalarki matsalata ce, damuwarki damuwata ce, haka duk abinda kika yi aka zage ki a gari bake kadai aka zaga ba, ni sai na fiki jin zafin zagin. Yadda hankalin abida ya tashi na aisha fariida sai ya fi nata tashi, nan da nan ta dago ta kafawa abida ido tana kallonta yayin da kalma daya rak ta gagare ta furtawa don tashin hankali. Kan kace kwabo hawaye ya fara zazzagowa daga idanuwan ta. Abida ta lura da tashin hankalin da farida ta shiga sai itama ta fara hawaye ta fara magana cikin sanyayyiyar murya. Aisha farida ba wai ina zarginki bane sai dai ina gudar miki fadawa mummunan rayuwa a sandiyar dan karamin bashin nan. Kije ki cuci rayuwarki a banza. Dole in tuhume ki don nima nasan dole yayanki zai tuhume ni haka kuma ya kamata a shariance. Aisha farida ta matse hawaye ta langabar da kai tace tabbas na kwana da shirin zaki tambayeni haka amma ban taba zaton zance a gida na kwana ba ki karyata ni ba shine abinda ya bata min rai amma inda zan yiwa Allah godiya shine na hadu da yaya dazu da tsakar dare ina fitowa daga bandaki shi kuma zai shiga har ya ambaci sunana na amsa da alama shima yayi mamakin gani na. Abida ta gyara tsayuwar ta da alama taji dan sanyi a ranta ta dubi aisha farida ta tambaya cike da zumudi. Yaya akayi kika fito daga ofishin 'yan sanda? Kuma a ina kika samo wadannan makudin kudi? Aisha farida tayi murmushi ta jawo hannun abida suka zauna akan tabarmarta tayi ajiyar zucia sannan ta gyara zama ta zayyanowa abida labarin duka abinda ya faru da ita jiya tun daga sanda ta fita qofar gida wajen 'yan sanda da yadda sukayi acan ofishinsu da zamanta dakin da aka kulleta zuwa lokacin da akayi belinta da kuma zuwanta fish park harta hadu dasu barrister mu'azzam da hirar da sukayi Har zuwa yadda ya bata kudi da kuma sanda ya kawota gida abida ta gamsu da labarin Aisha humaira kuma taji dadi har saida ta daga hannun sama tayi wa Allah godia ya taimakesu ya basu yadda zasuyi su biya bashin da basu dashi.kibani kudin nan sannan ki tashi ki tafi makaranta salin. Alin basai yan gidan sun tashi sun ganki ba kuma babu ke babu bawa wasu labarin abinda ya faru ko labarin inda kika samo kudi gudun kada yayanki wata rana yaji yazo ya titsiyeni da tambaya sannan kibarshi akan kin yi mata tiyata kada ma ki sake kiyi zancen malam kika kaiwa kudi koda wasa kibarni dasu ni nasan Ni nasan yadda zanyi inyi musu bayani kada kice komai jikin A.farida na karkarwa da dauki jakarta ta rataya tana gaggawa ta nufi qofa zata fice abida ta kira sunanta a sanyaye ta juyo ta kalli abida da cike da tausayiabida tace kina da kudin acaba ne? A.farida ta gyada kai tace inada naira 150 ragowar wanda canjin 200 dinda kika banina hau acaba jiya zuwa ofishin yan sanda.abida tayi ajiyar zucia tace kiyi haquriki gyara duk abubuwanda aka wuce ki ki mayar da hankalinkisosai harsai kin kamo 'yan ajinku domin anbarki baya.A.farida ta gyada kai tace insha'allah zan mayar da hankali akan karatuna na tafi saina. Dawo ta juya a gigice cikin sauri ta kuwa ci sa'a bata ci karo da kowa ba a tsakar gida haka qofar gidansu harta fito unguwarsu sannan ta samu acaba ya fisgeta sai asibitin malam aminu kano tana shiga cikin asibiti sai ta nufi bangaren da pfishin gogan nata yake ba har sauri ta qara gami da kawar da kai gefe don kada ma ta kalli bangaren.bata marmarin taci karo dashi ma balle ta tuna dinbin bacin ran da ya kimtsa mata a baya ta qudiri niyya a ranta ita dashi har abada koda kuwa shine kadai da namiji da yayi saura a fadin doron qasa.tana shiga aji sai yan aji suka mata caaa!suna tambayarta ina ta shiga ne ta bace kwata-kwata ba'a ganinta koba da lafia ne? kasancewar ramar datayi kuma duk tayi baqi don wahala.ai kuwa kun san amsar da zata basu balle ma sun saka ta akan hanya cewar ko bata da lafia ne? tuni ta amsa musu da eh bani da lafia ta qara da cewa harda kwancia a asibiti'',haka tayi ta bin metron da nurses tayi musu irin wadannan gunduma-gunduban karairayi su kuwa suka bita da sannu Allah ya sauwaqe dole su yarda mana saboda tsananin ramar da tayi gata daman ba jiki ba.bata yi qarya ba tabbas data sha jinyar zuci jinya a zucia kuwa wani lokacin har tafi jinyar jiki ta rame qurqet saboda tashin hankali. Daga nan ta duqufa tambayar abubuwan da kayi bata nan ta dinga kwafar jotin dinda frnds sukayi akan cuttutuka da yawa ta tabbatar an wuce ta sosai a cikin satitikan da take qin zuwa.tambaya take tun qarfi abun daba ta gane ba daga dalibai ,metrons da doctrs abun da ya shafa sannan ta bazama ta koma makarantarsu wajen malamin da yake alhakin duba ta wato (supervisor )dinta yazo har sau 2 baya samunta don haka tana cikin matsananciyar matsala idan batayi da gaske ba.saita maimaita attachment din nan next year hankalin A.farida yayi matuqar tashi a lokacin da yan ajinsu suka zagayeta ta suna neman mata mafita kowa yana bata shawarar abun daya kamata tayi ta shiga matsancin kokonto ana tantama anya kuwa har akwai wani bayanin da zata yiwa malam basiru ya saurare ta yadda ransa ya baci yana ta fada akan yazo 2X duba ta bai same ta.hawaye mai radadi ne ya surnano daga idanunwanta yayin data tuno wanda yayi mata silar abun daya same ta taji haushin 5r shuraim ya rafe ta .ta cije lebe ta girgiza kai tace a ranta shuraim na biyewa sharrin zucia a karo na farko na wahalar da kaina insha'allah ba za'a sake ba a. Karo 2 zucia nafi qarfinki yanzu duk inda kika kai ga hango haduwar dr shuraim bazan saurare kiba kece kika yi qayatamin shi a rai kika dinga zuga ni gashi a kusa-kusa zan same shi kikayi ta zurmuqani a rami har sai dana yi zurfin da na kasa fita saida aka agaza min na fito to ba za'a sake ba zanyi yaki dake har inda qarfina ya qare babu ke babu hasko min dr shuraim shi daban ni daban kowa ya tsaya a matsayinsa.ta sharce hawaye ta miqe ta suri jakarta ba tare da tayi wa kowa sallama ba ta fice daga asibitin kai tsaye ta nufi makarantarsu ofishin malam basiru ta nufa sai dai kash ta daki gurbi ya fitaa ita kuma tazo abokan aikinsa suna ce mata yanzu zai dawo-yanzu zai dawo taki qarewa abun qarfe 12 na rana sai ga Aisha farida a zaune ofishinsa har qarfe 5pm dole ta tafi gida tinda bai dawo ba. Ranta bace hankalinta a tashe ga qishin ruwa da yunwa yini guda bataci abinci ba dadinta ma dai tana zuwa tayi salla sannan ta dawo tavi gaba da jira domin A.farida bata wasa da sallarta.ta iso gidansu da misalin 5:45saida ta hadu da jama'ar unguwarsu da dama qofar gidansu zauren gidansu da tsakar gidansu sai suke jin kunyarta wasu ma basu iya hada da ita.tana gaishe su suna qasqantar da ido a qasa tamkar sunga surukarsu sai mamaki ya rufe ta tana shiga dakin aunty abida ta tura kai ta shiga kasancwar yay husaini bai dawo ba kafin abida tace mata wani abu Aisha.farida ta jero mata tambayoyi zokat suka mata zucia tace anyi abida lafia yan gidan nan kuwa?me yake faruwa ne?me kika fada musu suke kasa hada ido da ni?ko suna zargina da aikata wani abun kunya ne? abida tayi murmushi ta girgiza kanta tace ko daya kada kiyi zargin duk wannan jeki ki cire kayan makarntarki ki dauki abincinki kici yana gefen kayan ki kici naga alamar kina jin yunwa ki saurareni ina zuwa dakin naki yayanki ne yasani aiki yanzu zan gama kada ya dawo ya iske ban gama ba ransa ya baci.A.farida ta fice a sanyaye a zuciayarta cike da fargabar abun da abida zata fada mata ta cire kayan makarantarta ta saka wata yar yaloluwar t-shirt fara da baqin skirt kan ba kwali ta shinfida yar tabarnarta ta jawo kwanon abincinta ta bude wake da shinkafa ne da mai da yaji ga tashin hankali ga abincin ya sanqare sannan ga matsananciyar yunwa turawa take da kyar take hadiyewa maqogwaronta ya tsuke yayin da hanjin cikinta duk sun kanannade. Ta miqe da sauri ta bude wani farin bokiti mai murfi da moda akai shine ruwan da suka tadana na musamman don shansu ta debo a kofi ta dao ta zauna tana tura garau- garau tana korawa da ruwa ta kusa gama ci sai ga abida ta shigo fuskarta cike da murmushi tazo gefen Aisha ta zauna yayin da Aisha tayi qasaqe tana sauraronta abida tace Aisha. Yay makaranta?yaya kuma gogan naki likita?nan da nan Aisha ta hade fuska murtuk daga gani zuciayrta ce ta dugunzuma da jin kalmar sunan likita abida bata sami wannan amsar ba don haka saita sauya hira nan da nan.tace Aisha tayi ajiayr zucia tace na shigo unguwar nan sai na ga jama'a musamman mata suna ta kawar da kai basa iya kallona idan na gaishe su sai naga sun sunkuye-sunkuye haka dana shigo gidan nan ma duk basa iya hada ido dani me yake faruwa ne?abida ta tuntsire da daria tace ai daman haka rayuwa take maganinsu nayi''maganinsu kamar yaya? Aisha farida ta tambaya yayin data ajiye cokalin da yake hannunta gaba daya ta tattara hankalinta gaba daya wajen abida abida ta langwabar da kai gefe tayi shiru zuwa wani dan lokaci tace bayan fitarki dazu da safe nayi fiye da mintina 30 ina zaune ina tunanin qaryar da zan shiryawa su uwani da husaini yadda zan wanke ki daga zargi na tshi na shiga daki na iske husaini sai na fito da kudaden nan ina qidayawa yayi min tsawa yace ina na samu kudi da sassafe? Nace masa ai kudin nan a hannuna ya kwana tun bayan magrib aka kawo min sai yace waye ya kawo min?na gyara zama nace mace mai jegon da Aisha ta taimaka mata itace ta taso da ita da mijinta suka kawo kudin da yake Aisha tayi musu waya ta fada musu halin data shiga a sanidiyyar bashin data ci don ceto rayuwarta.dole suma hankalinsu ya tashi a lokacin suka bazamo suka hado kudin nan 12k suka kawomin sannan suka je office din yan sanda suka fito da Aisha ai a gidan nan ma ta kwana a daki ta labe taqi fitowa sai da safen nan ta shirya ta fice makaranta husaini yayi shiru can yace dani ashe da gaske ne kudin asibiti ta biyawa qawarta,ba qarya take ba?nace da gaske ne mana me Aisha zata yi da zunzurutun kudi kudin nan yarinyar da abin dunia bai dame taba,bata da buri ko kadan duk abun da ta samo komai kanqantarsa sai ta godewa Allah.yace yanzu saura nawa ne cikon kudin nace saura saura cikon 5k shima sunce zasu je su nemo su cika a cikin satin nan ma zasu kawo sai ya miqe ya je ya bude aljihun rigarsa ya zaro wasu kudade yan dubu_duba sai ya qirgo 5k ya bani yace gashi idan wadancan sun kawo sai a bani nima ba kudina bane kudin qungiya muke hadawa a office don tallafawa duk wanda ya shiga damuwa a cikinmu rashin lafia ko aka yimasa haihuwa ko kuma idan zaiyi aure a bashi tallafi''na karba cike da murna gami da durqusawa nayi masa godia bayan na shirya shi na shirya yara sun tafi nima nayi wanka na kammala dan aikin gida.hantsi yayi kowacce ta fito da tabarmarta tsakar gida ta zauna majalisar gulma ta hadu ta cika tayi damqam da munafukan mata har maqota kowacce ta zaro gyale ta shigo taji inda aka kwana da maganar kudin wajen Aisha.a wanne hali kike a can ofishin yan sanda? shaci fadi iri-irihaka mugaye kalamai ne ke fitowa daga bakunan masu dadin zance sai sun ga nazo giftawa ma sannan ake sake daga murya ana ambato sunanki,harda mai cewa lallai Aisha ta dauko ruwan dafa kanta a shekara 1 ma bazasu iya wadannan kudade ba sai dai tayi zaman gidan yari kawai. Na dauko kujerata na nufo inuwar da dandali yake fuskata cike ta da murmushi na gaishe su wasu ne suka amsa a sheleqe wasu kuwa sai suka kawar da kai gefe suka yatsune fuska suka ci gaba da ambaton Aisha tayi ganganci gobe ma ta qara na dade a zaune na buga tagumi ina dubansu ba kunya ba tsoron Allah a gabana basu daina mugayen furucinsu ba akanki.talaka ya shiga 3 a duniayar nan maganin abun kada ka taba kayan wani saika zauna lafia amma muddin ka shiga gonar wani tofa ka hadu da wulaqanci Allah yabamu yadda zamu yi don alfarmar Annabi Muhammad (S.A.W)''Aisha farida ta karbi salatin suka qarasa a tare suka shafa ta dafe qirji saboda tsabagen fargaba ta qagu taji abun da ya far tace me kika ce musu ke kuma? abida ta gyara zama tace biyi kisha labari daman sai irin haka ta same ka zaka su waye jama'ar da kake zaune dasu su yan gidan nan ashe haushin abin da kika yi ba ma suke ji ba suna yi mana baqin cikin ashe daman can akan irin rufin asirin Allah yayi mana ne suke adawa.ummulkhairi ta tabe baki tace ato qarshen alewa qasa qarshen tika-tiki tik! qarshen qarya dai yazo da anayi mana yatsuna ana wanka ana qalqale qafa ana siyowa yara gwanjo suna tsukewa ana yi mana gani-gani mu ba mu iya kula da miji ba sai iya bini-bini ana kusa da miji ana yimasa fari da ido.uwani tace kin manta a dafa abinci haka kawai sai an zuba kori yayi qamshi an yayyanka salat da tomatoes da albasa''Mairo maqoriyarmu tace au irin wannan iyayin ake yi muku ashe a gidan lallai kuna shan kallo. Ummulkhairi tace idan kince kallo ma ai daya ke nan sai idan miji zai shiga bandaki zoki ga yadda za'ayi ta kuza ruwa ana sharewa ana yayyafa abin qamshi kamar fin mazanmu yayi su da suke shiga da zarnin''uwani tace kun manta yar gayun gidan nan wai ita 'yar boko Aisha magana daya sai an sako turanci goma kullun ana qalqale kayan makaranta ana goge kaushi anayi wa manu yan matan gani-gani saboda suna soya awara a qofar gida su basu zuwa boko''Aisha ta zubo da hawayen daya cika mata ido ta girgiza kai anti abida me ya kawo duk wannan? daman haushinmu suke ji? abida ta zubo da hawaye tasa gefen zaninta ta matse tace ke kya fada farida daman sun dade suna so suci min mutunci to basu ga fuska ba don bana shiga harkarsu zunde da yafice kala-kala kullun suna yimin basu isheni. Kallo ba sai in nuna ban san suna yiba saboda iya zama da jama'a.zan gaishe su ko baza su ansa ba. Zan bawa ya'yansu duk abun dana dafa ko su basu amsa ba zan bawa 'ya'yansu duk abunda dana dafa ko su ban basu ba.bana bari suga hudar da zasu shigo jikina balle ayi gulmar wata dani haka ban damu da sai naji gulmata da akeyi ba.bani da lokacinsa sai lokacin mijina da ya'yana kema bakida lokacin kanki ma balle na wasu mu ba yan gari bane amma munfi sy yan garin sanin jama'ar arziki da samun Alkhairi shine haushinsu sai yanzu suka sami damar amayarwa da abun da yake zuciyarsu.yadda kika ga na zuciyarsu.yadda kika ga na zubo da hawayen nan sau 1 na sharce da gefen zanina haka nayi bance komai ba sai na saka hannuna a gefen zanina na zaro wadannan kudi na miqawa uwani ta zazzare ido sai hannunta ya dauki karkarwa ta karba a sanyaye.tana qirgawa a yayin da idanuwan masu leqe suka fi nata firfitowa masu kama baki sunayi haka masu susar tsohuwar kwarkwata suka fara yi ba tare da sun san ma abun da suke yi sunyi matuqar mamakisun razana haka sun ji kunya uwani da yan tayinta suka kidaya kudi naira 17k ta cika cif-cif. Uwani bata iya dago da ido ta dube ni ta iya ce min komai ba sai nice tambaye ta nace sun cika ko da saura kudin da farida ta ranta?ta gyada kai tace sun cika haka suke nace to ki kaiwa haj rabi kice tayi haquri ba za'a sake ba yanzu ma qaddara ce Allah ya aikowa Aisha tayi jihadi ne don ta ceto ran qawarta data qoqarin mutuwa akan gadon asibiti zata haihu saboda bata da jini kuma ba zata iya haihuwa da kanta ba sai tiyata shine tazo ranci kudin ta kai kafin mijin ya aiko daga lagos anan aka sami matsala da bai aiko da wuri har ta kai aka kai ta wajen yan sanda aka daure.Allah yana bayan mai gaskia. Allah yana taimakon wanda ya nemi. Taimakonsa Allah yana duban zuciyar na gari da mugu kuma yayi hukunci a kansu tun daga nan dunia da qawar Aisha mai jego taji labarin halin da Aisha ta shiga a dalilinta tuni ta taso daga kan gadon asibiti taje ta fito da farida ta kawo ta gida ta hado kudin nan da aka ranta Allah ya dubi zuciyar Aisha yaga kyakyawar niyyarta ya taimaketa ya fitar da ita daga tozarci da abin kunya. A gida aisha farida ta kwana, ta tashi da safen nan ta tafi makaranta taci gaba da karatunta. Yanzun abinda ya rage shine idan ta dawo da yamma kuje wajen 'yan sanda ku tabbatar musu da ta biya kun janye kara, sai a soke shikenan a zauna lafiya. Uwani mun gode da taimakon da kikayi mana, akasi aka samu har ya zama rigima. Kiyi hakuri, itama ba haka taso ba. Su dukka suka yi shiru kamar wadanda ruwa ya cinye su. Nayi murmushi na dube su daya bayan daya nace ku gafarce ni, daman ina da matsala daku bansani ba, kuma babu wacce ta tare ni ta sanar dani? Ai da tuntuni kun sanar dani halin da ake ciki don ban san inayi muku laifi ba ma a tsawon zamana daku, kusan shekaru goma. A bangarena bani da matsala daku ko kadan, ina taka tsantsan kada in batawa wani, ina iyakacin kokari inga na fitar da hakkin makotaka da Allah Ya wajabta a kaina shine inyi muku sallama, in gaishe ku duk sanda muka hadu a tsakar gida, in duba ki idan baku da lafiya, inyi muku jaje ko gaisuwa idan kun rasa wani dan uwa ko wani abu. In taya ku murna idan aure ko haihuwa sun same ku. Menene yayi saura kuma baya ga duk wadannan? Ku gafarce, laifi daya ne da nake muku, kuma ba zan daina ba shine ina kula da mijina yadda ya kamata, ku kuma ba kwa so. Nayi alkwari bazan daina tsafta ba, haka ba zan daina ciwa 'ya'yana ado ba da gwanjo, haka ba zan daina wankewa mijina bandaki ba duk sanda zai shiga, haka ba zan daina sanya curry ba ina dafa masa dadadan abinci, koda kuwa ace mijinmu daya ne daku, balle babu hadina daku. DUK KYAN TAKALMI 2* 2 A gida aisha farida ta kwana, ta tashi da safen nan ta tafi makaranta taci gaba da karatunta. Yanzun abinda ya rage shine idan ta dawo da yamma kuje wajen 'yan sanda ku tabbatar musu da ta biya kun janye kara, sai a soke shikenan a zauna lafiya. Uwani mun gode da taimakon da kikayi mana, akasi aka samu har ya zama rigima. Kiyi hakuri, itama ba haka taso ba. Su dukka suka yi shiru kamar wadanda ruwa ya cinye su. Nayi murmushi na dube su daya bayan daya nace ku gafarce ni, daman ina da matsala daku bansani ba, kuma babu wacce ta tare ni ta sanar dani? Ai da tuntuni kun sanar dani halin da ake ciki don ban san inayi muku laifi ba ma a tsawon zamana daku, kusan shekaru goma. A bangarena bani da matsala daku ko kadan, ina taka tsantsan kada in batawa wani, ina iyakacin kokari inga na fitar da hakkin makotaka da Allah Ya wajabta a kaina shine inyi muku sallama, in gaishe ku duk sanda muka hadu a tsakar gida, in duba ki idan baku da lafiya, inyi muku jaje ko gaisuwa idan kun rasa wani dan uwa ko wani abu. In taya ku murna idan aure ko haihuwa sun same ku. Menene yayi saura kuma baya ga duk wadannan? Ku gafarce, laifi daya ne da nake muku, kuma ba zan daina ba shine ina kula da mijina yadda ya kamata, ku kuma ba kwa so. Nayi alkwari bazan daina tsafta ba, haka ba zan daina ciwa 'ya'yana ado ba da gwanjo, haka ba zan daina wankewa mijina bandaki ba duk sanda zai shiga, haka ba zan daina sanya curry ba ina dafa masa dadadan abinci, koda kuwa ace mijinmu daya ne daku, balle babu hadina daku. Menene laifin aisha farida kuma a cikin gidan na, ko kuma ince a cikin unguwar nan? Hana idanuwanta baccin da take yi ne take zuwa karbar haihuwarku komai dare? Ko kuwa allurar da takeyi muku idan likita ya rubuto muka ta hutar daku zuwa chemist? Kitson da take yi muku kyauta ko kuwa ko yawa 'ya'yanki karatun da takeyi, duk sati ba tare da ko sisinku ba? Taya ku girki da takeyi, ko kuma rainon 'ya'yanku da take yi muku koda yaushe shi ya zama laifi? Gaishe ku da takeyi koda yaushe, ko hirar da take zama kunayi da ita shine laifinta? Allah sarki rayuwa, ai kuwa Aisha farida mutum ce babu wacce bata morarta a cikin gidan na, koma nace a layin nan gaba daya. Ummulkhairi na dade da sanin cewar ke kike wanke kafa kike zuwa ki sami mahaifiyar musbahi ki caccaka mata karya da gaskiya don ta tsani aisha farida a matsayin surukarta, burinki ya cika har sai da kika haddasa wannan gaba a zuciyar uwar musbahu, ta tsinewa aurensa da aisha farida, tace idan dai tana raye ba zai aure ta ba. Na sani aisha farida ta sani, musbahu ne ya fada mata shima ya sani. Sai ummulkhairi ta mike tsaye ta hau bambamin fada mai tafe da borin kunya tsagwaronsa. Tana jan Allah Ya isa ba zata yafe sharrin da nayi mata ba. Na mike tsaye nima na nuna mata ruwa ba sa'an kwando bane, haka shiru shiru ba tsoro bane gudun magana ne. Kalmar da na fada mata ta karshe daga ita na gaggauta barin wajen itace kinji dadi, kin raba auren musbahu da farida, amma baki isa ki hana Allah Ya bata wani mijin ba, daga wani bangaren, bangaren da baki sani ba. Kuma wanda baki da matsayin da zaki taka kiyi gulma. Ummulkhairi ke da sauran makiya, ku bude idonku sosai zaku sha mamaki, zaku sha kallo, zaku ga irin mijin da aisha farida zata aura idan har muna raye. Insha'allah sai Aisha farida tayi auren da babu wacce ta taba yin irinsa a gaba daya unguwar nan bana a layin nan ba ko gidan nan Allah yana tare da mu kuma da shi muka dogara yan gulma suka hau gasgata maganata suka hau nadama suna fadar alkhairin Aisha farida data taba yimusu a rayuwa nan da nan na bar wajen na kyale su suna ta kame- kame kanka ce kwabo dandali ya rore ya qare daya bayan daya suna ta sulalewa suna guduwa saboda kunya Aisha farida ta riqe baki don mamaki gami da farin ciki abunda abida tayi.tayi mata dai-dai ta burgeta tayi murmushi tace anty abida dama ke iya fada?amma bantaba ganin kinyi ba?abida

Chapter 9 of 23