Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
'Yar uwartace gidansu kusan 'dayane dan iyayansu sunyi xaman gaskiya da amana hakanne yasa suka kasance tamkar 'yan Uwa YUSUF inasan yarinyar nan dan haka kawai tunda namata kallo 'day Naji qaunarta tashigeni ina Santa YUSUF ya sauke sanyayyiyar ajiyar xuciya danjin LABEEBAH dai ba MATAR Yayan nasa KAMAL bace yakalli momy ahankali yace xanje in kwanta Tace toh atashi lpy katuromin Salim Yace Toh Yana fitowa daga 'dakin Momy shashin KAMAL yayi da sallama Amma ina samun Yayan nasa yayi rungume da XARAH Yana leman bakinta Da sauri ya komah baya Yace umm hmm hello KAMAL yasaki XARAH ahankali Yace yes come....... Bai qarasa furucin nashi bah YUSUF yashiga Yace gun Auntyna naxo KAMAL yayi Murmushi da kallan XARAH Yace gatanan YUSUF ya'dan sosa qeya yana qumbiya qumbiya Yaba KAMAL dariya dan haka Yace ko sirrine abun YUSUF aa Cikin bet room KAMAL yayi Yana cewa bari inje in shiryΓ  kayanmu kafinnan kungama Sirrin komadai miye indai TEEMAH nace xata gayamin XARAH tayi dariya tace hakane My luv Murmushi YUSUF yayi da zama kan hannun kujera ya fuskanci XARAH xaiyi magana tarigashi da cewa. tunda mukaxo banga Sadeeq bah sai Aliyu ya haka Yace hmm yana can saudi iyayan maman nasune suka roqi alfarmar abar musu shi kinsan dama maman nasu ita ka'daice dasu kuma gashi ta tafi shiyasa momy tace abarmusu shi kawai XARAH tace ayya Allah yaji qanta Yace AmEEn Nagode. Am dama labarin LABEEBAH nakesan kiban Tace saika biya Yace fa'di konawane Xan biya Tace toh gyara xama kasha labari Yace nagyara Tsaf XARAH taba YUSUF labarin LABEEBAH har San datakema KAMAL Shuru YUSUF yayi can Yace a xan canki idan nafahimta ranar da kuka ha'du da Ya KAMAL aranar itama LABEEBAH taha'du da KAMAL 'dinta Ko shakka babu XARAH tabashi Murmushi yayi tare da gya'da kai dan yagane sarai nawani bane KAMAL 'dinda LABEEBAH takeso fa ce Yayansa. Nan take kishin yayan nasa ya dirtsu aransa ......... KAMAL ne ya katse mishi tunanin nasa tawajan fitowa daga bet room Yana cewa imma ka kamu da santa ne toh kasani Jameel ya rigaka da ita Tashi YUSUF yayi Yana Murmushi sanda ya kusan fita Yace haba Yayana ai ban gama warwarewa ba tukunna koxan yi soyayyah sainan gabah yana gama fa'din haka baijira cewarsa bah. Ya fitta abinsa...... KAMAL ya kalli XARAH Yace kinga mutafi gidanmu tunkam Momy takoremu Tace ina😳 aini anan xanyi xamana Yawota jikinsa yayi Yace kokin xauna bashi xaisa naqi kar6ar hakkina bah Tace kai My luv agidan Momy fah muke Xura hanunsa yayi Cikin rigarta Yana cewa bara na tabbatar miki da agidan Momyn muke................... YUSUF ko Yana fitowa suka da'da cin karo Atare ko suka dafe goshinsu Ya galla mata hararah tare da cewa biyoni LABEEBAH tabishi tana tunanin KAMAL ne ko YUSUF Han cintane ya bata amsa. Wajan bambamce mata shamshinsu A Falansa ya tsaya itama tsayawa tayi tana kallansa Yajuyo karab suka ha'da ido Wani MASEEFAR SOONTA ne yataso mishi Yace dan Allah meyasa kikama xuciyata mummunan illah haka Tawaro ido Tace me namaka Yace da alama ke muguwace LABEEBAH tayi larai-larai da ido Tace muguwa kuma Yace eh mana dan 'daxu kinci xalina yanxuma kinkuma ci Bama wannan bah meyasa kike qoqarin cin amanar 'Yar uwarki XARAH A furgice Tace ban gane bah Ya galla mata harara Yace meyasa xaki SOO mata Miji Kin tsaya kina raina mata hankali wajan San mijinta. Tunaninta da gaske kina da KAMAL 'dinki. batasan mijinta kikeso bah Dama har yanxu akwai irinku maciya amana Akan me xakiso mijinta kije kinemi nakiman Kalleki dan Allah ko kunya baki jibah kinasan mijin 'Yar uwarki............ Kuka LABEEBAH ta6arke mai dashi baqin cikinta yanda ya gaya mata baqaqen kalamai Tace waya gama Ya KAMAL nakeso. Duk wandΓ  ya gayama qarya yake min. taqarashe maganar da qara rushemai da kuka Da'di Yakama YUSUF Yace kinga malama denamin kukan gulmah Ni 'dinnan na hangode son ya KAMAL a idanki xaki qaryata nine. Yanxu inje in gayama XARAH komai Da sauri takalleshi tare da qarasawa gabanshi ta durqusa tana kallan nasa tace dan Allah karka fa'da mata Dan Allah Wlhi nadena sanshi Ya cije baki dajin da'din yanda xai sarrafata yanda yakeso Yace tashi. ba musu Tatashi Yace daga yau naqara ganin soyayyar Ya KAMAL a idanki Wlhi Wlhi Wlhi saina miki dukan tsiya Taqa kafeshe da ido tare da gya'da mishi kai Yace gobe da safe Xan dingaya miki dokoki akan Ya KAMAL kina jinah Tace eh Yace toh jeki...... Har takai 'kofa Yace tsaya Nan tajuyo da tsayawa cak Yaqaraso da xaro hankicif a ajjihunsa bawani shayi Yakama fuskarta ya goge mata hawayanta tsaf Sannan yasaki fuskar tata. Aiko tafice da sauri Wani tsalle YUSUF ya daka ya dire a kujera dare da cewa gudβœ… Allah karabani da MASEEFAR SOO Sam LABEEBAH bata koma gun XARAH bah. Dan direct 'dikin da momy taware musu ita da Sumayya tayi Nan tasamu Sumayya dasu Safna Batayi gigin kallansu bah ta wacce can qarshen gado takwanta abinta dan tasan Suna ha'da ido xasu tambayi meyasami idanta Sagna Tace Aunty LABEEBAH bacci xakiyi tun yanxu Tace eh kainane yakemin ciwo. Atare dukkan Su ukun sukace ayya Allah yabaki lpy Tace AmEEn Bara inkawo miki magani cewar Safna Tace toh Taje takawo mata ta qar6a tasha Sannan tayi toilet tayi Alwala tagabatar da magriba da isha'ii da shafa'i da wuturi Sannan takwanta tana tunanin gamuwarta da YUSUF Da gaske kannata ciwo yake mata dan tabbas YUSUF ya rikitata Bata ankaraba taji hawaye na xubar mata. Ashe duk yanda take 6oye soyayyar KAMAL aranta wani xai iya gane hakan Jitayi tana San ganin Ya Usman 'dinta da Rukayya da Innah Tasan da bata xoba ba. da YUSUF bai hango soyayyar da takema KAMAL 'dinba. Sagna CE takatse mata tuninta tawajan cemata aunty LABEEBAH kitashi muyi hira dan Allah karkiyi bacci. Lumshe idanta tayi dan nuna alamun tayi bacci adole Ganin tayi shuru Sumayya Tace tayi bacci ai Aikowa cewar Sagna KAMAL ne yashigo Yana cewa ina suke. Safna tace Aunty LABEEBAH da Sumayya. Yace eh Sagna Tace Aunty LABEEBAH tayi bacci Sumayya ko tashiga toilet Yace OK in tatashi kuce musu mumun tafi gobe kwa rakusu Safna Tace toh yayah saida safe Yace Allah tashemu lpy ya ficce LABEEBAH taqara gimshe ido tana shaqar qamshin KAMAL Ahaka bacci yayi awan Gaba da ita Cikin caccin natane taji wayanta tana qara taduba taga ba Suna Tsarin number yasata xubama wayar ido..... Ya YUSUF ne Yace inbashi number-ki. Sagna ta katse mata tunaninta da fa'din hakan Waro ido LABEEBAH tayi ta kalleta. Tako gya'da mata kai alamun tabbatarwa. Tace ok ya naganki ke 'daya. Tace Safna sunyi gun Momy itada Sumayya.. Tace OK Kara wayan tayi akunnanta da sallama gabanta na fa'duwa dan ba qaramin tsoran shi YUSUF 'din tajiba Dai-dai nan Sagna tafita Kamilalliyar muryarshi CE ta isar da sakwanta akunnan nata Yace meya saki kuka bayan nagoge na'daxo Tace nifa banyi kuka bah. YUSUF ya lumshe ido tare da gyara kunciyarsa kallo 'daya xakamai kagano farincin da yake ciki awannan lokacin Idan kuma kaqarema fuskarsa kallo kagano kishi da rikici kala kala a kwayar idansa Yace 'daxo mexai kaiki gun Ya KAMAL. LABEEBAH ta 6ata fuska kamar Yana gabanta Cikin shagwa6a Tace nifah gun XARAH xanje ba gunshi bah Shuru yayi mata kamar ya sauka akan wayar Har ta dubah koya kashene sai taga sa6anin haka Shurun itama tayi tana jiran cewarshi Ke da waye a 'dakin. Ya jefu mata tambayar Taqarema 'dakin kallo tace ni 'dayace Kashe wayan yayi yayinda tabi wayan da kallo tana tunanin shikuma wannan wane irin mutum ne....... Bata ankareba takai kallantw 'kofah aiko saita ganshi a kofar 'dakin Gabanta yafa'di Yace naxone na miki saida safe tunda ke baki iyabah Taturo baki Tace toh saida safam Ya harareta Yace mutashi lpy Yana fa'din haka ya 6acema ganinta Zuciyarsa cike dajin da'di dama yaxone kawai dan yaqara ganinta dan xuciyar tashice ta buqaci hakan Ita ko Sam bata samu bacci yanda ya kamata ba dan xuciyar tata da fargaban YUSUF takwana Washe gari bayan gari yayi haske Su Sagna sukayi skull Dadynsu ya fitta Yarage daga Momy sai Su LABEEBAH da YUSUF Momy takalli LABEEBAH Cikin so da qauna Tace kuje kuyi breakfast mana ranah nayi Tace toh Nan sukayi dining ita da Sumayya suka cika cikinsu. Bayan sun dawo falanne YUSUF ya fitoh idanshi ya sauka akan LABEEBAH da take kusa da Momy Gabanta yafa'di Yace gudMrning my mom Tace Mrning my son da fatan katashi lafiya Yace lafiya lau Sumayya CE tafara gaisheshi kana LABEEBAH Ya amsa Cikin kulawa kan yajah bakinsa yayi shuru Ga mamakinsu sai ganin Momy sukayi taje dining ta ha'da mishi breakfast takawo mishi Sanda ya bafara ci Yace tnx my mom Allah yabarni dake Tace AmEEn my son Bayan taxaunane takira darebansu Safna a waya Tace inasan xuwa anjima kakaimin wasu yarana gidan KAMAL. Yace toh ranki yada'de. Takashe wayan idanta akan YUSUF Yace mexai hana insun gama in kaisu dan Xanyi tagun Tace Yauwa mah Sha biyu saura suka gama shirinsu tsaf tare da yima Momy sallama Tace kwana biyu xaku mata fah. kodawo Ku qarashemin kwanakin naku LABEEBAH tayi Murmushi Tace toh Momy Sumayya Tace Su Sagna xasu xoko Momy Tace eh kai xaku gansu YUSUF Yace toh muje Nan suka shiga motartashi duk kansu agidan baya suka xauna Haka yajasu Sumayya nata xubah YUSUF na'dan biye mata LABEEBAH dai binta take da eh ko aa Yana yin fakin suka fara ciki kicin bu'de kofar Amma taqi bu'duwa Fitowa yayi ya bu'dema Sumayya tafitoh Yace Auntyn naki xata rakani anguwa. Sumayya tayi Murmushi Tace toh sai kundawo Yace Yauwa qanwata Aunty XARAH Tace toh LABEEBAH najin haka tafitoh da sauri Tace niba inda xan rakaka. Tafa'di hakan da niyar bin Sumayya Cikin gidan Ganin haka yasa yayi saurin riqo hannunta da sauri Sannan ya 'dagama Sumayya hannu alamun saisun dawo ta gya'da mishi kai. 🌡🌡🌹🌹🌡🌡 *MASEEFAR SOO* 🌡🌡🌹🌹🌡🌡 Sanda ya tabbatar da shigan Sumayya gidan Sannan ya kalli LABEEBAH da wani mugun kallo tare da sake mata hannunta ya bu'de mata gidan gaba cikin 'daure fuska Yace shiga mu tafi Cikin tsoro tashiga kamar tarushe da kuka. Sannan shima ya shiga yajah motar Awani gun shaqatawa yayi parking Asan nanne ya kalleta Yace saboda kina xumu'din San ganin Ya KAMAL shine yasaki qin San binah Ta kalleshi ka'dan Tace ni bashi nakesan gani ba Yace maqaryacciya abin nan naban mamaki. Akanme xaki SOO Ya KAMAL Yana mijin 'Yar uwarki Nima ban sani ba. Tabashi amsa cikin jin haushi Yace dokokin daxan dinga miki shine Wlhi naga ko da wasa kin kalli Ya KAMAL saina mugun 6ata miki Wlhi Ke barima kiji namiki gwari-gwari daga yau banaso naqara ganinki da shi. Ko hanya ce taha'daku toh kicanja hanya. Sam karna kuskura naga kinyi sanadin daxaku ha'du da juna Inba hakaba saina gayama XARAH cin amanar da kika mata nasan mijinta Kuka LABEEBAH tafashe dashi mecin rai tayi da nasanin xuwa Abuja Imin shuru kafin in maqureki anan Shuru tayi Yaci gaba da cewa dafatan kinji me nace miki Cikin shagwa6a Tace naji Yace gud my baby toh share hawayan ko banasan kukan. Jitayi kamar ta sheqa mishi mari dan takaicinsa Ya sata kuka kuma ya lallasheta Saka bayan hannunta tayi tana goge hawayan Ganin haka yasashi janyota jikinsa ya ha'data da qerjinsa Yana goge mata da hankicif 'dinsa ahankali Itako lumshe ido tayi danjin da'din turaransa Yace am sorry babyna xaki sha ice-cream Ta'daga mai kai tayi ahankali Yace. Toh bari na kar6o miki ko. Yafa'da yana me xareta daga jikinsa Sannan ya fitta daga motar Shuru LABEEBAH tayi tana tunanin shi Tana kallo ya siyi biyu nashi da nata. Ya shigo motar ahankali ya rufe tare da kallanta. Ya gyara xamansa sosai yana fuskantarta. Tare da bu'de ice-cream 'din Yace toh bu'de bakinki Ta kalleshi qasa qasa Tace xansha da kaina Yace no nusuwata bu'de in baki. Taturo baki Tace nifah da Kaina xansha Wani kallo yajefeta dashi. Bashiri ta bu'de bakinta yabata Haka ya dinga bata tana Sha ha'de da lumshe ido dan da'di Gareshi ko hakan ya fara jefashi cikin wani hali Dan haka ya fara bata da sauri Sanda takusa shanyewa tace ta'koshi Bai matsa mataba yabu'de nashi yasaka mata kan cinyarta yace na baki dan haka nima saiki ban Tawaro ido Tace banta6a bah atututan mutum abu bah Yayi Murmushi Yace habah nutsuwata nine qatu. Yafa'da shima da waro idon Tagya'da mishi kai alamun tabbaci Yace bani dan Allah Ta kalleshi ka'dan xatayi magana ya 'dan harareta Murmushi tayi tafara bashi ahankali ahankali. Duk lokacin da xata bashi saiya wurga mata kallan SOO. Saitaji wani iri Sam bata gane bah dan damuwarta shine yakaita gun XARAH. Ahaka dai yasha da'dan dama. Kana kallansu kaga masoya a xahiri Amma a ba'dili LABEEBAH batasan hakaba hasalima dagaske 'daxu xumu'din San ganin KAMAL 'dinne yaso hanata binsa kamar ya fa'di Yauwa nutsuwata yanxu muje innuna miki garin abujah kafin mukoma ko Tace toh dan Wlhi tsoran shine yake shigarta. Dan batajin xata iya mishi musu akan Komai Haka YUSUF ya dinga yawo da ita yana jin da'di Tabbas garin abujah ta ha'du iyakar ha'duwa hakan ne yasa LABEEBAH sakewa dan tanasan rayuwar yawo. Musamman tawannan tabu'de ido Sun biya ta supermarket yasiya mata kayan xaqi da sauransu Ahan yar Su tada wowane tana shan sweet Yana kallanta cikin SOO da kauna. Yace nutsuwata Takalleshi Tace meyasa kake kirana da hakan. Yace haka kawai dan kindace da sunanne. Shuru tayi Shima shurun yayi........ Ta dubah wayanta ga mamakinta taganta akashe Tace la wayata tamutu bayan acike take da chaji. Tafa'da tana me kunna wayan. Sai taga ta kawo Yace nina kasheta Tace meyasa Kai tsaye Yace saboda banasan XARAH da Ya KAMAL Su damemu Tace Amma hakan yadace dan hankalinsu sai tashi kuma Wlhi inasan ganin........ Ya KAMAL Ya katseta da fa'din hakan Kobashi kikesan gani bah Cikin wani yanayi Tace XARAH nakesan cewa fah Yace gud niba qaramin yaro bane Tace Wlhi XARAH xance...... Tsayawa yayi da motar agefan titin ya fuskanceta sosai Yace baxa kiga XARAH da Ya KAMAL bah. Dan yanxu haka gidan Momy xan maidake Afurgice takalle shi tare dayin larai-larai da ido. Hawaye nasan xubowa Ya gallah mata harara Yace Wlhi kika sake hawayannan ya xubu saina tsinkeki da mari. Aituni tamai dashi tana 'kifta ido Yajah qarimin tsaki dajan motar. Haka motar ta'dau shuru har suka iso gidan Momy xata fitta ne Yace kinga malama ban sallameki bah Bata kalle shibah Amma tafasa ficewar Yace idan Momy tatambayeki yasu XARAH kinuna mata kamar acan kika ini Sannan idan XARAH takiraki kikawomin wayar ninasan abinda xan gaya mata. kinji nutsuwata. Yaqarashe da lallashi Tattaro jarumta LABEEBAH tayi tagallah masa harara Tace idan naqifah. Yayi Murmushi Yace xaneki xanyi Tace sai kace wata 'dalibarka Yace lah😳 Aike yanxu kinxama 'yar rainona kinga bana saki asahun la'dibai naba Dan kinsan shi 'dalibi malami yakan 'dan rangwanta masa. Amma 'yar raino bata buqatar rangunci Ta kawar da kallanta daga kansa Tace kai xaka gane wannan karatun naka koko ince xauranci Ya 'dan janyota jikinsa da muryar lallashi Yace kwarai da gaske Amma dan Allah kiyi abinda Nace miki plx kitemaken Qara langwa6emai tayi tare da 'dago fuskarta xuwa kallansa Tace nima katemaken naga XARAH Yace namiki alqawarin gobe xaki ganta da yardar Allah Tace ko Cikin marairaice mata Yace Allah da gaske Yafa'da daniyar kai mata kiss πŸ’‹A mma ya fasa........ Xatayi magana kenan kiran wayan KAMAL ya shigo. takalli YUSUF ka'dan a'dan tsorace... Da shagwa6a Tace Ya KAMAL ne in 'dauka Cije le6e YUSUF yayi tare da qara maqaleta. ya kai bakinsa kunnanta Yace banaso ki'dauka Amma tunda kinaso 'dauka Aiko da sauri ta'dauka tare dasan raba jikinta da nashi Amma yaqi yarda da hakan Yaqara maqaleta Tace hello Ya KAMAL................ Wani burkitaccen kiss YUSUF yakai mata awiya me shiga cikin jikin mutum batare da ya ankareba Ai LABEEBAH batasan lokacin da tasaki wayan Tafa'di a gefanta bai. batir 'din ya fita Mai makwan tabi wayan saita kwantar da kanta a qirjin YUSUF tabi wayan da kallo shiko YUSUF abinda yake so kenan dan haka ya 'dago ha6arta Yace yadai taturo baki kallo 'daya xaka mata kasan jikinta ya mutu. Da shagwa6a Tace wayan tafa'di Cikin kwai kwayan Muryarta Yace toh me kikeso namiki Tace nidai kakira min shi naji mexaice Yace wlhi baxan iyaba nutsuwata Saita fashemai da kuka tana cewa nidai gaskiya kakira shi Shuru YUSUF yayi Can Yace kinasan na kira miki shi ko Ta'dagamai kai Yace toh kibari anjima saina kira miki shi Tace nidai....... Ya katse da cewa xakiyi biyu babu in Kika matsamin Shuru tayi Shima shuru yayi 🌡🌡🌹🌹🌡🌡 *MASEEFAR SOO*🌹 🌡🌡🌹🌹🌡🌡 Sun 'dauki minti biyar 5 ahaka shuru mabai magana. Saima da'da langwa6emai da tayi Ganin haka yafara shiga wani yanayi yasashi xareta daga jikinsa xaiyi magana kenan suka hango Safna da Sagna sun fitoh Da kalleshi Tace dan Allah bu'demin Ya YUSUF plx Saurin goge mata hawaye yayi da hankicif 'dinsa Yace plx kisan me xakice Murmushi tayi tace kanasan koya min qarya. Yace kare kanki xakiyi dan sunsan bana duka bare suyi tunanin ko na dakekine kanta tayi magana sun iso Ya xuge gilashin motar suka leqo da kansu Sagna Tace lah Aunty LABEEBAH yanxu fah muke shirin xuwa Ta qaqalo Murmushi Tace eh gashi Ya YUSUF ya dawo dani Tayi dariya Tace Yauwa gwanda dama kinga saimuyi kitsammu ko Safna Tace hakane gobe maje Ya yadanna gefan motar saiga kofar tabu'de da sauri LABEEBAH tafita tana cewa muje inyi Sallah saimu fara ko Aiko Sagna da Safna suka bi bayanta Suna cewa bakiyi bah Tace eh Wlhi YUSUF yashafah kansa tare da sauke ajiyar xuciya dan ganin tamanta da wayarta ya 'dauka yajefa ajjihunsa Yace godiya gareka Allah Na roqeka karkasa Yayana ya ankare da wannan baiwa taka Idan Santa alkairine agareni kamallaka min ita Yana fa'din haka yajuya kan motarsa daniyar yin masallaci. Momy Tace yana ganki 'Yata Ta'dan rufe ido cikin kunya Tace hmm inasan xama kusa dake ne Momy Cikin jin da'di Momy ta rungumeta Tace ayya Nagode sosai 'yata ina tare dake. LABEEBAH jin sanyi tayi aranta koba Komai tanada Masoya Innah Ya Usman XARAH Sumayya ga Momy mah. Kuma tana hangen tausayinta a idan KAMAL Tagode ma Allah daya barta dasu Haka tayi Sallah tayarfema Sagna da Safna Kansu da kitso Wanda kallo 'daya xakama kannasu kayi tunanin injinne ya xane kan dan tsabar kyau dakan da yayi 7:00pm nayi sai ganin Sumayya da YUSUF LABEEBAH tayi Sanda suka ke6e Tace ya haka Tace hmm Aunty LABEEBAH kedai bare Ya YUSUF akwai tsari bansan me yagama Aunty XARAH bah kawai sai cewa yayi inxo mu tafi tace ingaishe mata dake Tace hmm namanta wayata a motarsa Sumayya Tace nako ganta agunsa 8:30pm na dare ne Suna hirarsu me da'di a'dakin Momy. Momynma tana 'dakin Dady YUSUF yashigo Yana cewa nutsuwata Duk suka sura mishi ido Sagna CE Tatashi tace Ya YUSUF kayi budurwane Yace me kika gani Tace Naji ka'ambaci nutsuwata ne Ya saci kallan LABEEBAH tare da ta6e baki Yace share kawai xokiji Tace toh tabishi Safna takalli LABEEBAH qasaqasa batadai ce Komai Sumayya ko taji meyace Amma tunaninta ko waya yagamayi shine yashigo da qarashen Kalmar a bakinsa. LABEEBAH ko dama tasan da ita yake....... Sagna CE tashigo da murnarta Tace Aunty LABEEBAH Momy nakira Da sauri LABEEBAH Tace toh tana ina Tace tanacan falan mu Toh Tace tafitta 🌡🌹🌡🌹🌡 *MASEEFAR SOO* 🌹🌡🌹🌡🌹 Waige wage tahauyi dan bata hango kowa bah Ruffffff Taji an rufe mata ido ta baya Tajah numfashi dan tagane waye Tace Ya YUSUF....... Yace na'am nutsuwata. Yafa'di hakan da xagayowa gabanta Tace Kaine Momyn Yace eh Tace toh miye Yace kafin muxogun ya akayi kika gane nine Kawar da kanta tayi daga kallan fuskarsa tace qamshinka ne ya ganar dani kai Yace watoh kenan kinma qamshin turaran Ya KAMAL farin sani Takalleshi ka'dan. Nan tahango rikici da futuna acikin idan nashi _ai har duniya tana'de nayima turaran Ya KAMAL farin sani. Eh qamshinsa Yana sani nutsuwa. Tafa'di hakan aranta_ Afiliko cewa tayi aa banta6a riqe qamshin waniba sai naka Yace gud Dama kwalliyarki CE tamin kyau shine nakisan 'daukan ki photo Taqare mishi kallo Tace kayi kyau kaima sosai Yayi Murmushi Yace aisaimu mu'dauka tare in ba damuwa Tace mexai kawota Yace Mene Tace damuwar Matsowa yayi kusa da ita suka jera tare da seta wayanshi ya haskesu da hotuna Haka yadinga 'daukarta Sannan Yace yunwa nakeji nutsuwata Tace toh kaci abinci man Ya kalleta da wurga mata mata wani shegen kallo. Wanda yasata sunkuyar da kanta da sauri dan taga irin abinda yake fitowa daga cikin KAMAL Wanda yake shiga idan ta shinetoh yake qoqarin shiga idan nata yanxu Ya 'dago ha6arta Suna kallan juna Yace plx ki fanshi Momy dan Allah kiciyar dani yanxu Da'da ware ido tayi Tace meyasa saini Yaqara kusanta kanshi gareta kamar xai rungumeta Yace saboda natsinci kaina cikin farin ciki 'daxo da kikaban ice-cream plx gobema xaki qaraban. Yaqarashe da shagwa6e mata. Ba qaramin rikicewa LABEEBAH tayi bah cikin sauri Tace eh Allah ya kaimu Murmushi ya sakar mata kana ya'dan nesanta kanshi da ita Yace muje ko Cikin sanyi Tace xuwa inah Yace Wlhi indai yanxu mah baki ciyar danibah baxan iya bacci bah kuma baxanci bah Jan numfashi tayi Tace gaskiya kana da futuna Ya YUSUF yayi Murmushi tare da kama hannunta sukayi dining Yana cewa Hakka abinxai kasance in raineki kema Ki rainan

Chapter 8 of 22