Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
bawanda take gani sai hotan fuskar KAMAL Yarikita mata ganinta tarasa yanda xatayi me kenan Tafaru taqare Dallacan kindameni da motsi tun 'daxo kin hanani bacci sai kijuyanan kijuyacan saikace me tattare da damuwa... Zarah CE maima Labibah wannan furucin Tace yi hakuri nakasa baccinne Tace toh kitashi kiyi sallah man Ni bacci bakeji Sam Labibah bataqi ta Zarah ba Tatashi tayi dayo Alwala tafara nafula...... Washe gari ta'dan jita garau Zarah taxubah mata ido Tace lafiyanki ko naganki haka Labibah takalli kanta amirro taga idanta ya'dan fa'da Tace mekika gani Tace jikinki yayi sanyi da yawa Tace nima haka kawai najini yau da nayi tunanin baxan iya komaiba Amma naga harna'iya aikin gida Tace damuwata dai ina lafiyanki lau. Labibah tayi Murmushi ha'de da riqe hannun Zarah Tace lpy nake 'Yar uwata Tace toh madallah Kyakkyawan saurayine ajin farko fari tas. Kallo xakamai kasan ya ha'du tawajan ku'di ilimi nutsuwa hankali wayayye kuma karufe kallan naka daga gareshi da miskili ne me sanyin hali. KAMAL kenan Misalin qarfe 5 da mintuna dareban daya 'dauko KAMAL daga airport ya saka hancin motarsa agidansu KAMAL 'din Cikin nutsuwa ya fitoh yana qarema gidan kallo kamar yau yafara ganin gidan. Yalla6ai shikenan ba wani abu ko. Direba ya fa'di hakanga KAMAL Cikin girnamawa Yace no ba Komai yayi Cikin falon Yayinda direba yayi gunyin parking dan ajiye motar Hajjiya Anisa wacce suke kira da Momy mahaiyarsu tana zaune kan kujera tana danna waye. Mace kyakkawa taqarshe 'Yar duma duma Da sauri KAMAL yaje Yakama hannunta ya sunbata Yace i miss u Momy Cikin farin ciki Tace nima nayi missing 'dinka KAMAL. Ya kabaro min kakah Tana lafiya tacema agaisheki. Toh ina amsawa Yace yanaji gidan shuru bakowa Momy tayi Murmushi Tace sunajinka suka shige aiki Yace da kina famah dasuko Eh wallahi bakaga yanda nadinga cewa sutashi suyiba Amma sukamin kunnan Uwar shegu Yace hmm Salim fah. Tace Yana gun dadynku office 'dinsu wai suna lissafi akan fudda zakka Yace oho hakane fah danni kannaje kano nafitar da tawa Tace madallah Allah ya qara bu'di. Kaje kayi wanka ga abincinka nan anjera maka Komai Yatashi yana cewa AmEEn da shigewa shashinsa. Yasami komai tsaf kamar yanda taxata. Nan yayi wanka ya canja kaya yana niyar fita saiga qannansa biyu Safna da Sagna Suka durkusa suna gaidashi da mai sannu da xuwa Cikin kulawa Yace Yauwa nasameku lafiya Sukace qalau yayah ya kakah Tana gaidaku Muna amsawa Suka fitoh atare. Direct kan dining yayi. Momy taxubamai abincin yafaci yana cewa yau nasamo miki sirika momy...... Saura ka'dan tasake cup 'din dake hannunta Tace KAMAL mekace Yace dagaske Momy nasamo miki sirika Fatima-zarah Zama tayi Cikin farin ciki da annushuwa ta'daga hannu sama tana kwarara addu yau tasamu labarin da takesanji Tace a ina take kuma 'yar waye Yace ba 'yar kowa bace dan iyayanta talakawane lis. Tananan unguwarsu Auwal Tace toh Allah ya tabbatar da alkairi Yace AmEEn Momyna..... Dadyn shine yashigo shida Salim Yace my soon kadawo Yace nadawo dady dafatan nasameku lafiya Yace qalau my soon dama inasan magana dakai inkagama kasaman Yace angama dadyna Murmushi yayi yayi Cikin 'dakinsa ko ince shashinsa Salim Yace sannu brother kadawo lafiya Yace lau lau ina maryam Yasosa qeya Yace aitafi qarfina yayah shiyasa kawai narabu da ita. Yace ko Yace da gaske Momy tayi Murmushi Tace hmmm yaudai yayanka yaxomin da xance me da'di yayomin sirika Da sauri Salim yakalleshi Yace kako kyauta yayah Allah yasa ayi damu Yace AmEEn Shin suwaye Bayin Allan nan Alhaji Sale da Alhaji Nasir uwarsu 'daya ubansu 'daya Mahaifinsu yarasu tunsuna yara Tun tasowarsu sun bu'di ido da ku'di dan haka su'din tun asulinsu masu dashine mahaifiyarsu hajiya Saude nanan da ranta Itace suke kira da Hajjiya Baqaramin so suke mataba. Itama tana sansu Alhaji Sale da Alhaji Nasir suna San junansu Sana'ar iri 'dayace watoh Su 'yan canjin ku'dine Sannan basu tsaya ananba suna ta6a kasuwanci sosai Shiyasa sukeda ku'di bana wasaba Sunada mataye 'dad'dai Alhaji Sale yana zama garin Abuja shida matarsa Hajjiya Anisa balarabiyace 'yar usuli dan acan Saudi Alhaji Sale ya Aurota Mace mekyan hali dasan mutane Sam abin hannunta bai rufe mata ido bah. Dan kan tasamu sheda tagari Sunada yara 4 KAMAL Yusuf Safna & Sagna KAMAL shine Babba sai Yusuf Wanda ayanxu yake qasar Saudi da xama shida Matarsa 'yarcan dan iyayanta sunqi yarjemai yaxo musu da ita Nigeria Kasan cewarta ita ka'dai garesu Toh dama shi Yusuf 'danba ruwansa ne. Dan yasaba da Saudi shiyasa baiwani damuba saboda yana ganin 'yan uwan momynshi Dan haka aka musu Aure da Matarsa Mufeedat. Sunada 'yayansu biyu Sadeeq da Aliyu Yusuf dai sana'ar saida gwala gawalai yake anan Saudiyan Sai KAMAL wanda yake cikakken doctor nasalin ciwuka daban daban KAMAL yasan kan aikinsa Duk wani matashin doctor dayakejin kansa agarin abuja saidai yakoma Bayan KAMAL Dan manyan qasarnan nasansa saboda kwarewarsa akan aikinsa Suna girmamashi KAMAL yataka matsayi babba danshi'din na musammanne Doctor KAMAL waraka shine sunan da manyan doctors 'din kasarnan suke kiransa dashi A England yayi karatunsa cibiyar bokan duniya Gashi qaramin yaro Amma sai aiki Dan Allah yabashi Shekarun KAMAL ishirin da tara cif 29 Amma sai baiwar ilimi da sanin aikinshi Wasu doctors suna mamakin aikinsa idan suka duba shekarunsa KAMAL yayi ku'di bana wasaba Saidai yanada zuciyar sadaka da kyauta shiyasa yakeda tarin Masoya KAMAL yanada wani hali shidai bayasan hayaniya shiyasa baicika magana bah Amma yanayi da wa'yanda yasani SAIDAI FAH 😳 'DAN LUV NE 👈🏻 Yanasan soyayya Amma baisamu wacce tadace dashiba sai Fatima-zarah Tunda Yusuf yayi Aure Momy da Dady suka sakashi agaba wai sai shima yayi Shiyasa daya kawo musu xancan Fatima-zarah zuciyoyinsu suka cika da farin ciki Tunda KAMAL yadawo daga karatu yakasance a Kano naniqe da Hajjiya kakah. Tsowuwar da take sanshi kamar ranta. bataso KAMAL yayi nisa da ita koka'dan Shiyasa daya fara aikinsa Abuja yake xuwa duk qarshen. Wata yana dubata Yakanyi kwana biyu haka. saiya komah Bashakka Hajjiya kakana najin da'di Yanxu ko jin da'dinta xaifi nada tunda yaxo mata da xancan Fatima-zarah Ta'udurce aranta xata saka KAMAL yaqarasa gininsa nanan kusa da inda take yasaka Fatima-zarah aciki Safna da Sagna ko sune 'yan autar Momyn KAMAL 'Yan biyune. Masu bambancin ra'ayi Itadai Safna yarinyace mehankali da nutsuwa Sam magana bata dameta bah Shiyasa KAMAL yake shiri da ita Yayinda Sagna takasance maraji da San shige shigen yawo da surutu Ga 'dan rashin kunya dasan raini idan kasake mata Amma tasan wa'yanda takema rashin kunyar tata. Dan aduniya bawanda take jin tsoro kamar KAMAL dan baya mata da wasa Sam Shine yake gyara mata xama Ayanxu dai ita da Safna suna aji shidda na secondary Bayan dama sun kusa sauke alqur'ani da sanin wasu takaddun addini Alhaji Nasir ko yanada Kano da xama inda Hajjiya kakah Mahaifiyarsu Tace baxasu watse Su barta ba. Ba Alhaji Sale bashi baxai yuhuba Dan haka yaxauna a Kano shida Matarsa Hajjiya Zainab Yanada yara goma cif Kuma "dayane dansa namiji watoh Salim Ya aurar da mata hu'du4 saura biyar5 wayanda suke karatu uku kansu 'daya dasu Safna biyu kuma qannansu ne Salim Yana harkar kasuwancinsa da Dadyn KAMAL. Wannan sune asalinsu KAMAL 〰〰〰〰〰〰〰 Hira sosai KAMAL yakeyi da Momy Yana bata labarin Su Fatima-zarah Yace kinsan wani abu. Tace aa Yace dana ha'da ido da 'yar uwarta Aisha-Labibah sainaji gabana yafa'di Momy tagyara xama Tace toh ita FATEEMA bakaji fa'duwar gaban agareta bah Yayi Murmushi Yace banji komai ba illa sanda da qaunarta dayama xuciyata shigar baxata tanada kyau sosai ina Santa Tace ita AISHA ba kyakkyawa bace Yawaro ido Yace wow tanada kyau Momy sosai gatada da'din murya Wallahi Momy inasan jin muryarta dan gaskiya tafi FATEEMA da'din murya Murmushi kawai Momy tayi. Washe gari KAMAL ya tashi ya kintsa kansa da shiga irin tasu ta likitoci doctor sai Qamshin turaransa yake Yafitoh kenan daga part 'dinsa kamar ance yakalli window. Aiko yaga Sagna ta falle Ado meba fulayoyi ruwa da mari KAMAL ya bu'de window da mamaki yaji tana xaxxagama Ado masifah wai dan tsabar iskanci Yana galinta xata wucce yawani watsa mata ruwan da yakeba fulayoyi Yace Wlhi saginiyatu banganki bah Ran Sagna yaqara 6aci dan tatsani yacemata saginiyatu dan haka taqara falleshi da mari Tace wai waye saginiyatu. Kullun saika kirani da sunannan wai Sagna ne baxaka iya fa'daba dan qauyanci Ado yayi shuru yana ganin rashin mutunci irinnan Sagna. Sam bata ganin girman manya aqallah ya bata Kusan shekara shidda Amma hakan baisa ta raga mishi bah Yace toh kiyi hakuri....... Takaici ne yasa KAMAL wuccewa xuwa dining yana kuma mamakin Sagna Ashe rashin kunyar tata tawucce inda yake tsammani Dady da Momy da Salim Safna suka kalleshi da mamakin 6acin randa yake fuskarsa Safna da Salim suka gaisheshi ya amsa. Sannan yagaida Su Momy Dady Yace yanaga kamar ranka a6ace lafiyadai ko Yace no is ok Yafara break 'dinsa kenan Sagna tashigo falan fuskarta a 'daure......... Ganin mugun kallan da KAMAL yawatsama yasa jikinta yafara rawa Momy takalleta tata6e baki dan tasan babanxaba KAMAL yabita da mugun kallannan Aiko Yace watoh kega 'Yar iska mara kunya ko Shi Adon qanin ubankine daxaki falleshi da mari da haka Tuni Sagna tarikice Tace dan Allah yayah kayi hakuri Yace ko. Tayi shuru. Tashi yayi yabata mugayan marika biyu wa'yanda suka gigitata Sannan yayi boll da ita Yace duk ranar danaqara ganin kin 'daga hannu kin mari Wanda ya girmeki Wlhi ranar saina miki dukan mutuwa Cikin kuka Tace Wlhi baxan qaraba Cikin tsawa Yace jekibashi hakuri yanxu Da sauri tatashi xataje yabi da qafah Aiko takwasa a guje tana kuka Yajah tsaki da 'daukar jakar laptop da wayoyinsa Yace Momy Dady natafi Xasuka mishi fatan alkairi yafito yashige motarsa sai hospital.... Cikin kukako Sagna takebama Ado hakuri Baiyi mamakiba dan yaga futan KAMAL yana jifanta da harara Yace karki damu saginiya....... Baiqarasa ba tagallamai harara Yace yi hakuri Sagna Kwafah tayi tayi falo Momy mah harararta tayi Tace mutuniyar banxa aigwara yadinga gyara miki zama kokya kintsu Dady Yace shashasha ba. kedai bakiyi hali mekyau ba dan albasa batayi halin ruwa Yana fa'din haka yafita shida Salim Momy mah tashi tayi tabar falan Aiko Sagna taqara fashewa da kuka gani take kowa ya tsaneta bamai Santa sai yayanta Yusuf dake Saudi Tausayinta Yakama Safna Tace kidena kuka kinji Kikuma tashi mutafi lokaci natafiya Tsaki tajah tasa6i yakar skull 'dinta tafita batare da tacema Safna komai bah Itama Safna nan 'daukar jakarta tayi tabi bayanta Direban Su yajasu xuwa skull KAMAL ko yana xuwa asibitin nasu yadinga kar6ar gaisuwa agun doctors da ma'aikatan gun Dan dai KAMAL shina mutanene Sakina 'daya daga Cikin ma'akatan itada Nafisat wa'yanda suke bala'in San KAMAL kuma qawaye ne Amma kowacce taqi yarda da manufar 'yar uwarta haka suke tafiya acewarsu kowacce tata tafish sheta Suka gaida KAMAL Cikin girmamawa ha'de mai kwarkwasa Yaxuba musu ido dan yada'de da harbu jirginsu. Nan take yatuno da Fatima-zarah yayi Murmushi yashige office 'din Murna tacika su atunanin kowacce acikinsu ko yafara santa ne KAMAL kam yau aiki kawai yake yana tumanin FATEEMA Yayinda yake hasashen acikin satinnan xai koma Kano 〰〰〰〰〰〰 Suna tafiya Cikin nutsuwa dan xuwa gidan matan Bashir yayan Fatima-zarah dan kaimata 'dinkinta datasa FATEEMA takar6arnata LABEEBAH Tace nidai naqagu mutumin nan yaqara dawowa FATEEMA Tace wai meyasa kika damune Tace haka kawai dan naga ya cafki zuciyarki. Tayi Murmushi Tace ban 6oyemiki ba. Dan nafa'da miki tun shekaran jiya inamaji ajikina shi'din Mijina ne Tace Allah yasa dan kundace da juna nidai fatana yadawo Wlhi hakan zaisani farin ciki Tace naga alamar kinaso kifini 'dukin dawowarsa Cikin tabbatarwa LABEEBAH takalli FATEEMA Tace kwarai Wlhi nafiki 'doki dan banaso wani yayi masa kwacanki Cikin farin ciki Tace isiyaka yaruga shi fah Dariya LABEEBAH tayi Tace harkin qara tunumin ranar da muka fara ha'duwa. Dan tsabar qarya kika wanice wai isiyaka ya rigashi Wai wayema isiyakan Cikin dariya FATEEMA Tace inafah nasanshi. Kawai bakina yafa'di hakanne Tace Nasani ai Dai-dai nan suka shiga gidan Bashir Sunko taki sa'a Jamila nanan matarshi biyu dan aikwaita da yawo Suka gaisar da Lami Uwar gida da take tsakar gida tana daka Tace saiyau naga idanko LABEEBAH Tace hmm makaranta ne yake 6oyemu Tace bawaninan islamiya kawai kuke xuwa..... Kan taqarasa Jamila tafitoh tsakar gidan tana cema FATEEMA ina saqon nawa Cikin rashin kulawa FATEEMA tabata dan taga tana wani yatsina. Aiko tafusga takoma 'dinta Lami tata6e Cikin 'daga murya Tace bagani Xanyi dakika wani shige afusace Jamila talequ dakanta Tace Ai? Harkin xargi kanki. Mumafuka me shegen saka ido Wai wai wai😳 Cikin 6acin Lami Tatashi xatayi 'dakin Jamila nan LABEEBAH taruqota uwarkice munafuka mesa ido 'Yar gidan matsiyata Lami tafa'da cike da 6acinrai. Aiko Jamila tafitoh itama tafitoh tarama xaginda tamata. Nan fa'da yakaure daqer Su FATEEMA suka raba fa'dan Bayan sunjama Jamila kofarta Xama sukayi a tsalar gidan suna kuma tausar Lami ABEEBAH takalleta Tace Aunty Lami meyasa ko yaushe kuke Cikin fa'dene Tace hmmm barni da ita Wlhi saina koya mata hankali 'yar iska ta Auremin Miji kuma tafini kishi akansa LABEEBAH taqara gyara xama Tace wai miyene kishi Lami takalleta gala gala Tace kishi. Bakisan kishi ba Tagya'da mata kai Cikin tabbatarwa Tace bansanshi Amma koma ya yake nasan yana xuwane agun wa'yanda suka 'dau keshi da xafi Dan Allah Aunty Lami kudena fa'dace fa'dacannan Sam Bashi da fa'ina. Kucire Komai aranku kuxauna lpy ko ya Bashir yasami kwanciyar hankali Murmushi Lami tayi tana niyar magana FATEEMA tajah tsaki Tace hmm Ni tashi mutafi inkuma ba yanxu xaki tafiba kinga tafiyata. Tana gama furucin taficce agidan Cikin sauri LABEEBAH tabita tana yima Lami sallama Da gudu tacin mata Tace wai meyasa bakyaba Su Aunty Lami damarki. Na lura duk lokacin dasukayi fa'da bakya bada hakuri kodai kice wani Abu Tace hmm haushi sukeban saisu dinga abu kamar wasu marasa hankali Toh wai miye abun fa'dan dan Allah. Taqarashe kamar dajan tsaki Shuru LABEEBAH tayi har sukaje gida Mamah Tace kundawo. Cikin rashin walwala FATEEMA Tace eh. Mamah takalli FATEEMAN tace kunsa mesu suna abinda suka saba ko LABEEBAH Tace me kika gani mamah Tace hmm naga fuskar FATEEMA ne a murtuqe Murmushi LABEEBAH Tace Tace eh ai baxasu denaba Yauwa mamah fa'damin menene kishi Mamah tamaida kallanta kan LABEEBAH Tace kishi wani abune Wanda yake jikin kowane halitta kuma yarabu kashi biyu ne dana hankali dana rashin hankali Na hankali shine Wanda kanajinshi Amma kake Danneshi dan karya fito bare gangar jikinka yanuna Na rashin hankaliko shine wanda Yana taso maka kake saurin baiyanashi har yasaka ka aikata abinda bai daceba Ya mutun xaiji daxaran yataso masa. FATEEMA CE tafa'di hakan Mamah taqara gyara xama da kallanta Tace mutum yakanji ya tsani wanda abun kishin ya ha'dasu Yakanji ranshi Yana 6aci idan yaga abin sansa yanasan wani Hankalinsa natashi idan yagansu Cikin farin ciki Saiya dinga rayawa aransa dama nine Idanko ya kasance dama wanda yakeso zuciyarshi abin sannanshi biyune wato kubiyu Toh idan yaga abin San nashi yakula 'dayan har yabashi wani dama suna Cikin farinci. Toh sai xuciyarshi ta tinxira tafara ganin kamar sunci mar fuskane ko yacimar fuska. LABEEBAH tajah numfashi Tace toh Allah ya rabamu da ciwan kishi Ananne FATEEMA tayi dariya Tace wato kishinne ciwo Mamah takar6e da cewa kwarai kishi ciwone XARAH Bayan kwana biyu ne. Xuciyar Aisha-Labibah. Tagama nisa Cikin soyayya da qaunar KAMAL Wanda sanda kowa ya tambayeta miyene matsalarta me yake damunta Shuru takeyi musu dan itakanta tarasa dalilin dayasa daga ganin mutum so 'daya Amma xuciyarta tacika da qaunarsa Yanxu hakama xaune take Cikin dakinta kan 'Yar loluwar katifarta tana tunaninsa tana addu'ar Allah yasa taqara ganinsa ko xuciyarta tarage mata ra'dadin da take mata FATEEMA tashigo da murnarta tana cewa ketashi Ashe har angama maganar Rukayya da ya Usman....... Sam LABEEBAH batasan FATEEMA rashigoba sanda FATEEMAN ta ta6ata taqara da cewa wai wane irin tunani kikeyine LABEEBAH Wanda yake gusar miki da tunaninki Me yake faruwane. Cikin sanyin yanayi LABEEBAH Tace nima bansan me yake shirin faruwa daniba Jinake idan bashi baxan iya rayuwa bah. Gashi ya 6oyema ganina yaxanyi FATEEMA plx kitemaken saiga hawaye. Cikin rikicewa FATEEMA Tace mekenan LABEEBAH Waye shi A ina yake Kalamanki sun nuna kinfa'da soyayya Yaushe hakan tafaru bansani bah Share hawayanta LABEEBAH tayi Tace wani saurayine yatafi da imanina. Kallo 'daya namishi naji gabana yafa'di Nagane sanshi nakeyi ne sako makwan kasa bacci da nakeyi Ya rukitamin tunanina FATEEMA Ya burkitamin kwakwalwata Ya gur 6atamin tunanina da sanshi da qaunarsa. Idan mukaje islamiya me makwan inyi karatu saikiga nafa'da tubaninsa So 'daya nagansa. Amma yatafi ya barni da tunaninsa Wlhi FATEEMA ba wani Abu wanda xai faran tamin rai ayanxu face ganinsa. Taqarashe ta rushewa da kuke. Jan ajiyar xuciya FATEEMA tayi tare da tausayinta ta guge mata hawayan nata Kana Tace yaushe hakan tafaru kuma a ina Tace ranar Jumma'a da yamma Bayan mundawo daga islamiya Mamah ta aikeni shine nagansa yaxo huccewa FATEEMA Tace rana 'daya kenan da muka ha'du da wannan mutumin dayace yana sona kin tuna Da sauri LABEEBAH Tace eh ranar Amma meyasa tun aranar baki gayamin bah Tace hmm lokacin abin bai daman hakaba Tace har yau kuma baki qara ganinsa bah Tace eh ban qara ba Meyasa xuciyarki takamu tasan wanda bata sanshi. Meyasa tamiki wannan rashin adalcin LABEEBAH tajah numfashi Tace duk iya tunanina narasa gano dalili FATEEMA takalleta cike da tausayi Tace toh Allah ya bayyana miki shi Tace AmEEn FATEEMA tafitoh kenan daga gidansu LABEEBAH taga wata shegiyar mota ta faka a kofar gidansu. takalli me mallakin motar........ Waxata gani saurayin daya caki xuciyarta takejin xai xamo miji agareta KAMAL yafitoh Cikin qasaita ya jingina da jikin motar. Saiya bala'in yin kyau Takawar da kallanta daga gareshi xata shiga gidansu Yace Haba XARAH me nayi daxa'a nunamin rashin kulawa haka kamar ba'a sanniba Takalleshi Tace dama ansanka ne Yace eh mana. Nasan ba'a manta da niba kawai xa'amin alayene Tayi murmushi Tace kaga Malam idan tambaya xakayi kayi dan an hanani magana da maxah tunda akamin Miji........ Sam FATEEMA batasan ya akayiba sai ganinsa tayi agabanta Yace Mene kina nufin an miki Miji Tace eh wani abune Yace eh Kitemaken kije kice bakisan wanda xa'a bakin plx Yaqarashe da muryar shagwa6a kamar xaimata kuka. Abinka dame tausayi. saitaga yabata tausayin. Dan tunaninta kuka zaisa mata Tace wasa ne Da sauri yasauke ajiyar xuciya Yace nagodema Allah Ina sanki XARAH kisoni plx Tace hmmm matsamin nashige gida Yawaro ido waje Yace haba my TEEMAH. Kiyi baqo Amma kidinga qoqarin raba kanki dashi Ta kalleshi Tace me kakeso yanxu Nuna mata kan dakalin qofar gidansu LABEEBAH yayi da hannu alamar suxauna Ba musu taxauna shima yaxauna qamshin turaransa na bugarta Yace sunana KAMAL nidai doctor ne banda Aure Momy na da Dady na suna raye Ina da qanne uku Yusuf shine yake bina yanada mata sai mata masu binshi 'yan biyu Safna da Sagnah Da fatan kin gamsu dani kuma xaki soni kamar yanda nake sanki. Tayimai fari da ido Tace Xan soka Amma sai 'yar uwata tayarda da hakan Yace wacece kenan Tace Aisha-Labibah Yace OK nasan xata soni. Tace ko Yace gaske Aisha-Labibah ko tana nan yanda FATEEMA tabarta Amma kuma saita tsinci kanta da dajin fa'duwar gaba. Yayinda tadingajin qamshin turaran KAMAL yana bugarta. Hankalinta sai yatashi. Dan haka taxaro hijab dinta danufin fitowa. Danta tabbatar da xargin da xuciyarta takeyi Ina xaki da sauri haka. Kamar me tashi sama Mamah tafurta hakan idanta akan LABEEBAH Tace bako ina xandai kar6i abu gun XARAH ne Shuru mamah tayi tana qura mata ido Candai Tace meyake damunki ne AISHA Tace bafa Komai mamah kawai kainane yakemin ciwo kuma nasha magani Shine yasaki kuka Tace eh Mamah cigaba tayi da aikinta Tace aishikenan Da xafin nama LABEEBAH tayi hanyar waje. Amma kuma sai taci karo da XARAH Tace Yauwa LABEEBAH Wannan mutumin yaxo. Cikin farin ciki Tace kai haba. Tace Wlhi da gaske Tace yayi dai dai muje in ganshi. Tace dama kenaxo kira. Aiko LABEEBAH takama hannun XARAH suka fitta Subhanallah. Aisha-Labibah Tace aranta. Sabuda wani kyau da KAMAL yaqara mata akaro na biyu na ganinta dashi Cikin fara'a Yace lale marhaban da qanwata Cikin sanyin murya da daidaita nutsuwa Tace barka da rana datafan kaxo lafiya Yace lafiya qakau qanwata XARAH Tace yaxo da Babban al Amari wai sai xuciyata tasoshi. shine nace saikin amince hakan tafaru Tace daga ganinsa baxaiyi cutaba. Dan yayi kama da masu rike alqawari Na hango sanki kwance mala mala kwayar idansa Kisoshi plx dan Allah ina tayashi roqo dan tani na amince Gud my qanwa kinyi kinha'du Gaskiya da ana samun irinku Masu gyara so. Toh dako Masoya baxasu dinga shan wahala ba Naji da'di axuciyata daga yau nabaki wani matsayi acikinta. Nagode sosai Cikin farin Cikin furucinsa Aisha-Labibah ta rufe fuskarta Cikin shagwa6a Tace ba godiya tsakanina dakai yayana. Dan abinda yadace kenan nayi XARAH Tace hmm Lalle kaxo da qafar dama LABEEBAH Tace ba mamaki kam. Toh ina muku fatan alkairi Tana fa'din haka tashige gidansu XARAN KAMAL yabita da kallo kana ya maida da kallan nasa kan XARAH. Yajefa mata wani shu'amin kallo Cikin kwayar idanta. Wanda yasata sunkwai da kanta batare data shirya bah. Zuciyarta na mata da'di sanshi na shigarta Xo gareni my luv plx yafa'di hakan da wata murya me da'di Fa'dawa gadan Innah Aisha-Labibah tayi Cikin farin ciki ta rungumi fitoh Wani da'dine yake xiyartar xuciyarta. Sai taji duk duniya ba abinda xaidinga sata farin ciki kamar tadinga kallan KAMAL ako yaushe kuma tadinga jin muryarsa. Me kashe mata jiki Innah Tace meya miki da'di ne LABEEBAH yau naganki garau haka In ban mantaba kinkai kwana biyar ban ganki cinkin sukuni da farin ciki haka ba. Sumayya tace kwarai da gaske Innah yau farin cikin Aunty LABEEBAH na musam manne Da murmushi Aisha-Labibah Tace hmm yau naga abinda yafimin Komai da'di a duniya Innah. Kuma har Cikin jinina da xuciyata 💗. jina nake nafi kowa farin ciki yau Innah Tace ikwan Allah wannan wane abune. Cikin sanyi kuma Tace wani abune wanda da alama xai wahalar dani kuma ba samun shi Xanyi bah Innah tata6e baki Tace bidai ahankali dan in kika fa'da soyayya nice wacce Xan fara kwace miki mijin naki inga ya xakiyi Simayya tayi dariya Tace wayaga idan Aunty LABEEBAH ranar Duk sukasa dariya. LABEEBAH Tace banso naxo asunan kakarki bah innah dan nasanki da riqe Miji kar6a Ki kwacemin shi da gaske Tace aiko saidai in ban ganshi bah Cikin dariya Tace baxan bari kiganshi bah... Ahaka FATEEMA tadawo tagansu Cikin farin ciki taxauna jagab tana niyar magana Saiga wani yaro Yana shigowa da kaya. Sanda yagama tsaf. Innah Tace kai kayan waye haka Yace wanine Yace in kawomah Fatima-zarah wai ince KAMAL ne Cikin wani yanayi LABEEBAH tamaimaita sunan abayyane Tace KAMAL XARAH takalleta Tace ai sunanshi kenan Tace abin mamaki Tace namefah LABEEBAH tagyara xama Tace sunansu 'daya Da sauri XARAH Tace da Wanda yasace xuciyarki Tace eh Wlhi Tajah numfashi Tace mun xama 'daya kenan Innah Tace kuncikani da surutun dana kasa gane kansa Shin waye KAMAL Nan LABEEBAH Tace wani ne Yace yanasan XARAH tun ranar Shine sai yau yadawo Innah tabi kayan da yaran yashigo dasu da kallo Tace shine yaturo da kayannan LABEEBAH Tace eh Innah tamiqe ta'dauki gyalanta taleqa waje. Aiko bataga kowa bah tadawo Tace yatafi Dana maida mai da kayansa Sumayya Tatashi tajanyo kayan tana dubawa Dogayan rigunane da takalma da hijabai acikin ledar farko Da'yar nedar kuma kayan tie ne danginsu madara vombita da Milo suga bota dadai sauransu Sai kudi bandir 'daya 'yan Dari bibbiyu Kunsan Sumayya da kwa'dayi tuni tafara ha'diye yawo dan ganin madara da milo Baban sune yashigo da sallama da ledar cefane a hannunsa Innah talar6a tana amsa sallamar tasa Yace kayan wayene haka Innah takoromai Bayani. Yace Ayya KAMAL ne Ayya gabatarmin da kansa kanaki. Amma ke

Chapter 2 of 22