Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya gudu karta kamashi aiko tabishi yana gudu tana binshi abin gwanin sha'awa. Can ta ritsashi Tace wana kama Yace yi hakuri Momyna baxan qara bah Tace toh ina kaje Yace gun Dadyna.... Waro ido LABEEBAH tayi Tace oho a ina ka ganshi Yace acan gashima Yace inbaki Da sauri LABEEBAH kar6i ledar tabu'dewa. wata fulawa CE mekyau sai handkerchief da turare da 'dan wani not a paper ka'dan Tayi saurin bu'dewa. _nadawo gareki my baby_ Gaban LABEEBAH yayi wani bala'in bugawa ba shakka wannan qamshin KAMAL ne a handkerchief 'dinnan me hakan yake nufi Nan ta waroma SAUBAN ido Tace a ina yabaka Yace acan. Yafa'da yana me nuna mata bayanta Nan tajah hannunsa suyican suyi nan Ko ina SAUBAN nuna mata yake Yace anan yaga Dadyn nashi Can dai da tagaji taje ta 'dauki abinda takeso na kayan make-up da kayan xaqinsu tayi gaba Awajan biyan ku'di mah cemata sukayi taje anbiya mata Tace Waye sukace MALUDDEEN LABEEBAH tacika da mamaki ahaka suka dawo gida take bama XARAH labari Dariya XARAH tayi Tace qila na saudiya ne ya biyoki. LABEEBAH tayi tsaki Tace koma Waye plx yayi saurin bayyana agareni naxa'ku in gansa Wlhi Rukayya Tace kiyidai ahankali kar yana 'kofah yajiki yajah miki aji Tace ni ina mace banjah masa ajibah saishi XARAH Tace ai indai agarekine qamshinsa wannan ka'dai baxai barki kija mai ajibah LABEEBAH tajuya idanta Tace xan baku mamaki ne Washe gari da misalin qarfe goma Bayan LABEEBAH takai SAUBAN skull Tana xaune agidansu XARAH tana karanta wani littafi wai shi *K@ULAT D@ ALHAXAWAN ABUJAH* Daga ita sai XARAH ne agidan dan innah taje kantin kwari siyayya Wani yaro ya shigo Yace ana sallama da LABEEBAH Tace kaje kace waye yaran Yace wai inji MALUDDEEN Cikin sauri LABEEBAH Tatashi Tace kace ina xuwa. Yace toh Dake XARAH na bayi Sai kawai taxari gyalanta ta tafitoh wajen dan dama a kin tsanta take . [12:09PM, 18/10/2016] Rahamat Nalele💋: Wani baqin mutum tagani jingine a jikin mota Yana binta da Murmushi Yace sannu Ko Tace Yauwa Yace dama yaran da kika kai skull 'daxone matsala ta meshi plx xaki iya binmu kiga halin da yake ciki Da sauri LABEEBAH Tace eh dan Allah meya sameshi tafa'da kamar xatasa kuka Shiga motar yayi da Bu'de mata yana cewa muje ki gani Aiko LABEEBAH tashige harda saurin rufe 'kofar shiko ya figgi motar da sauri Juyo wannan da LABEEBAH xatayi idanta ya sauka akan MALUDDEEN. Habawa aiko tasaki wani ihu yayi saurin rufe mata baki da hannunsa. Ta waro mishi ido abala'in tsorace Yace Ki nutsu my baby Aiko sai LABEEBAH tayi luuu taxube sumammiya. MALUDDEEN ya janyota jikinsa Marwan dake gidan gabah Yace tab😳 'dan Uwa ta sume fah Yace nasan xa'ayi hakan Wani kata faran gida NIGO yayi parking a cikinsa. MALUDDEEN ya 'dauke bai direta ako inaba sai a falan gidan kan kujera Ya xauna kusa da ita da yayyafa mata ruwa Nan LABEEBAH ta farfa'do Ai tana qara ha'da ido dashi taqara sumewa Ya dafe kai da qata yayyafa mata ruwa Nan taqara farfa'dowa Wannan karan fashewa tayi da kuka tana dan Allah dan Annabi aljani karabu dani Ya kai hannunsa gefan fuskarta nan taji wani shock tayi saurin lumshe idanta gabanta na fa'duwa Yace plx my baby Ki nutsu kuma kiyimin shuru da kukannan Tsit LABEEBAH tayi dan itadai har ga Allah tasa aranta MALUDDEEN aljanine Yace Yauwa toh tashi Tatashi da jingina ajikin kujerar tana addu'ar neman tsari da aljanu Sannan idanta aqasa ya xubah mata ido can yayi Murmushi Yace niba aljani bane da kike neman tsari dani Tabi qafarshi da kallo nan taga irin ta mutanece Takalleshi Cikin shagwa6a Tace toh kai Waye kuma meyasaka kawoni nan Ya kalleta ka'dan Wato har yanxu ga shi dai baxata dena yimai shagwa6a ba Yace ni sunana MALUDDEEN...... Tayi saurin katse shi da cewa toh kasaka KA afarkwan sunan naka mana kaga saiya bakah KAMALUDDEEN Yace dakyau my baby haka sunan yake LABEEBAH taqara furgita Tace qamshinka 'daya dashi fuskarku 'daya jikinku 'daya muryarku 'daya Komai naku 'daya meyasa haka xata faru bayan ba'a mutuwa adawo. Kawai dai kai aljanine Yace naji ni aljanine kuma Auran Ki nakeso nayi Tawaro ido Tace aiba'a Aure tsakanin bil'adama da Aljani Yace xa'a fara daga kaina Yafa'da dakai bakinsa goshinta yayi mata kiss Yaci gaba da cewa natsanci kaina acikin farin ciki yau ina tare da baby na Kuka LABEEBAH tasa mai Yace shuru Shurun tayi Yace xan dingaya miki shara'do'di biyu Na Farko xan dinga kiranki awaya munayin hira Na biyu Xan dinga xuwa gareki kuma kifitoh Ta bala'in marairaicewa Tace dan Allah karabu dani Yace Wlhi baxan rabu dake bah. Kuma idan kika bah qawarki XARAH labarin nan saina hukuntaki LABEEBAH taxuba mai Tace toh mai dani gida dan Allah Xan mai dake Amma sakin bani breakfast dan banyi bah. Yafa'da yana nuna mata kan table inda kayan break 'din suke Tace meyasa saini xan baka. Yace saboda ke kike da alhakin 'daukar hakan LABEEBAH tagya'da kai Haka tanaji tana gani tadinga bah aljanin nata abinci yanaci yana qare mata kallo Ita kuma tana kukan xuci Can Yace oya tashi namaida ke gida ko Babyna Bayan KAMAL babyn MALUDDEEN babyn aljani babyn YUSU....... Sai suka ha'da ido ya sakarmata Murmushi Da sauri tatashi ko gyalanta ba 'dauka bah tafara yin hanyar waje Yace kinga Tatsaya cak Ya qaraso gareta da yafah mata gyalan nata. Ya'dago ha6arta tarumtse idonta. Saiya kai bakinsa kan nata yayi mata qaramin kiss tabu'de idan nata ka'dan saiya janyota jikinsa ya rungumeta Na tsawan minti 'daya ya sauke ajiyar xuciya kana Ya kama hannun suka fitoh Wannan motar dai dasuka sato ta acewarta ita suka shiga. Ya jasu LABEEBAH dai tunda ta sunkuyar da kanta qasa bata 'dago bah dan itadai addu'arta "daya taganta agida Shiko MALUDDEEN kallanta yake jifah jifah xuciyarsa cike da santa da qaunarta Itadai taji sun tsaya dan haka ta'dago ahankali takalli inda suke nan taga qofar gidansu ne murna tacika tayi yingurin fitta nan taji 'kofar akulle Tajuyo ahankali takallesa Tace aljani budemin tohhhhh Yace kalleni Ahankali.tatsaida idanta akansa. Nan xuciyarta tafara bugawa dan Wlhi gani take wannan KAMAL ne Yasa hannunsa ahankali ya janyota jikinsa tare dasa handkerchief 'dinsa yana goge mata fuskarta LABEEBAH tayi lub a qirjinsa yayi Murmushi Yace kar kiyimin bacci Da sauri tajanye kanta daga gareki Yafita daga motar yaje ya bu'de mata Nan tafitoh tayi hanyar gidan nasu. Sanda takai 'kofar gida tajuyo tana kallansa Suit CE ajikinsa sky blue tayi mishi kyau Sosai Ta shagala da qare mishi kallo ya 'daga mata gira dayi mata nuna da ido alamun lafiya Har tana bige goshi wanjan yin saurin shigewa gidan nasu MALUDDEEN yayi saurin runtse idanshi da bu'dewa yanajin tamkar shine ya bige Haka yajah motarsa yana tuna babyn tasa LABEEBAH ko tana shiga gidannan nasu taxauna akan turmi ta xubah uban tagumi Tunani takeyi yanxu XARAH tarabu da 'yan shan jini gashi ita kuma ta ha'du da aljanu Har yamma LABEEBAH rasa nutsuwarta tayi. Har kowa ya lura da sauyin nata Suka tambaye ko lafiya Tace Bakomai XARAH Tace da Komai LABEEBAH tunda kikace 'daxo naje na 'dauko SAUBAN a skull nasan akwai abinda yake damunki Dan ko ciwo kike saikin je 'daukosa LABEEBAH Tace bafah Komai. XARAH tata6e baki Tace Allah yasa Kusan qarfe tara wayan LABEEBAH tafara ringing Data 'dauka saitaji muryar KAMAL Yace my baby Aida sauri tagyara xama da cewa innalillahi Yace wa'inna'ilalhirraji'un Cikin sarewa da shagwa6a Tace toh Me nene kuma Yace fa'damin Tace mene Yace me kike cema YUSUF idan kika kasance dashi LABEEBAH tawaro ido eh Lalle lamarin aljanu sai Su har yasan YUSUF Tace na manta Yayi Murmushi Yace Ki tuno Tace Wlhi na manta Yace kosai na tunomiki Tace aa me toh Kake san ji Yace so nake Naji me yafara birgeki dashi har kikaji kina sanshi LABEEBAH tayi shuru tana tunani can Tace kaga yana da kirki kuma yana sonah..... Sai tayi shuru Shima shurun yayi can Yace shikenan Tayi saurin 'daga mai kai kamar yana gabanta da cewa eh Cikin sanyin murya Yace bansan wane irin so nake miki ba my baby kowa yanada wacce yakeso ni dai ke naso kuma xanci gabah da sanki har qarshen rayuwata LABEEBAH tajah numfashi cikin sanyin kuka tace nima ina sanka Yace kar kiyimin kuka Rufe bakinta tayi da hannu hawaye ya xubu mata. Yace plx kiss me Wataro ido 😳 Yayi murmushi yace in baxa kiyi min bah nixan na6ullo ta bango inyi miki Da sauri LABEEBAH tayima wayar kiss hannunta na rawa Yace toh kiyi bacci da mafarkaina kinji Toh Tace mai da kashe wayar XARAH tata6ata nanta tsorata Tace Waye ya furgitaki haka Hawaye ya xubuma LABEEBAH Tace wani ne Wlhi yajefah soyayyarsa axuciyata daga xuwa dare ya hargitsa min nutsuwata XARAH Tace tab salan soyayyarsa ya bani sha'awa kalli yanda yasaki kuka lokaci 'daya LABEEBAH takwanta da jawo SAUBAN jikinta batace mata Komai bah Washe gari kusan qarfe hu'du XARAH da LABEEBAH ne suke tawowa gida dan sunje gidan Ya Bashir Innah CE ta aikesu fa'da masu aihuwar wata makwaf ciyarsu Xasu shugo layin nasune XARAH taga Alhaji Nura wannan me ku'din unguwar tasu takalleshi ya kalleta Tace A'uxubillahi Sai yayi saurin wuccesu LABEEBAH Tace yadai Tace hmm masu ku'dinnan 'dai-'dai kune ku'din nasu na Allah da Annabi LABEEBAH Tace meyasaki fa'din haka Tace hmm share kawai......... Kan LABEEBAH tayi magana wata shegiyar mota me xafi da 'daukar hankali tayi parking agabansu MALUDDEEN ya leqo da kansa Yace jimana 'yan mata dan Allah ku'dan jini ka'dan tambayarku Xanyi _jimana 'yan mata dan Allah karku shareni ina tambaya ne_ XARAH LABEEBAH suka tuno da wanda yayi musu wannan furucin ashekarun baya Gabaki 'dayansu xubah mishi ido sukayi XARAH tagigice ta furgice Tafara nunashi da yatsa Tace KAMAL....... MALUDDEEN ya ta6e baki yace MALUDDEEN saikin Sannan ya maida kallansa ga LABEEBAH Yace dama sunanki xan tambaya my luv _dama sunanki xan tambaya my luv_ LABEEBAH tatuno da Kalmar da KAMAL ya gayama XARAH tun farkwan ha'duwarsu dashi. Sai tayi murmushin yaqe ta'dan kalli XARAH ka'dan tare da qarema gun kallo tatabbatar tarihine xai maimaita kansa me makwan akan XARAH sai taga akanta lamarin yakesan juyewa ita da ALJANIN nata saita qarayin murmushin yaqe wai kafi kuka ciwo Tatsaida idanta akanshi da kyau Tace ayya banda sunah. Yace yayi murmushin jin da'di dan ganin xata biyema wasan nashi Yace kice ke 'Yar baiwace. Tace ba mamaki kam yayana Sauri muke kaga baifi taku hamsin xamuyi ba mushiga gidanmu. Dan haka kasamu damar daxaka iya tambayar cikakken gaskiyar xancanka nabaka minti 'daya. Yace gaskiyar xancan shine tunda na'dora ido akanki xuciyata takamu da soyayyarki ina sanka my luv Lamarin fah yafaraba LABEEBAH tsoro Amma ta dake tasa aranta saitaga abinda ya turema buxu na'di Dan haka tagyara tsayuwa da kyau Tace tab kamakara dan isiyaku ya rigaka shiga Birnin soyayyata dan haka sai anjima.......... Luuuuuuuu XARAH taxube aqasa sumammiya LABEEBAH ta kalleta Sannan takalli MALUDDEEN tata6e baki xata rushemai da kuka yayi saurin katseta da cewa idan kika min kuka Wlhi saikin sani Shuru tayi saita kalleshi ta kalli XARAH data sume... Shima maida kallansa yayi ga XARAH yana murmushin mugunta Sannan Yace temaka mata mana kin barta axube LABEEBAH ta xubamai ido Tare da kalar tausayi Tace ai baxan iyaba ni 'daya bah Yace OK inje in kira miki Sumayya ne. Yafa'da da kwaikwayan ta. Ta kallesa da kyau Tace me yasa saika kirata bayan gaka kawai ka temaka min Yace wa ni😳 Saiya girgixa kai da 'dauko wani ruwa daya ke gefansa ya miqa mata Yace yayyafah mata idan tatashi kice mata takwantar da hankalinta kar tayi sanadin daxaki rasata Yana fa'din haka yajah motarsa LABEEBAH tabishi da kallo lallema aljaninnan bashi da mutunci da tausayi. ta dai xubama XARAH ruwan amma shuru XARAH bata farfa'do bah Gashi har yara sunfara taruwa Can saiga Ya Usman kamar anjefushi Yace Subhanallah meya same ta LABEEBAH tayi shuru Baijira cewar taba ya kinkimi XARAH yayi gidan nasu da ita Akan taburma ya direta cikin tashin hankali yake tambayar LABEEBAH waime ya sameta ne Tace wani tagani me kama da KAMAL Yace ikwan Allah nan ya dinga yayyafah mata ruwa Can ta farfa'do Aiko ta qamqame hannun LABEEBAH Tace Wlhi ko kaffara baxanyi bah LABEEBAH KAMAL ne wannan mutumin . LABEEBAH ta girgixa mata kai Tace bashi bane aljani ne XARAH ta gallah mata harara Tace Wlhi ba aljani bane mutum ne kuma KAMAL ne Ya akayi haka. dama bai mutu bah LABEEBAH Tace nagaya miki aljanine XARAH tajah tsaki da fashewa da kuka Tace Allah ya isa Turai Allah ya isa Kin cutar dani kin ha'in ceni..... Usman ya katseta da cewa kinga dakata Yan xuma tana shirin maida ke cikinsu ne XARAH Tace aa Ya Usman kawai dai ta cutar dani ne Bata ban shawara ta gari ba Nayi nadamar saninta Ba wacce na tsana a duniya kamar ta.. Usman yajah numfashi Yace toh Madallah tunda abinda nayi xato bashi bane Yana fa'din haka ya bargun XARAH ko taciga da sambatunta tayi tana kuka Fa'di take aranta indai wannan bawan Allan KAMAL ne itakam ta mutu ta lalace. Idan kuma aljanine tabakin LABEEBAH tabbas tayi gamo da MASEEFAR SON SA😳 LABEEBAH ta xuba mata ido kawai sai kayi tunanin XARAN take kallo nanko tunanin aljanin saurayin nata take Ita dai kam ta kashe wayanta dan bataso ya kirata ya hargitsa mata kwanya Har Washe gari XARAH fah😳 tashiga tashin hankali ba'dan ka'dan ba. Idan ta rumtse idanta fuskar MALUDDEEN take gani Ko kaffara tace baxa tayi ba KAMAL ne Gashi yanxu ba ita bah Hajjiya Turai bare takirata ta tambayeta ya abin yake Can tayi tunanin takira Su Musa jage mana Aiko takirasu tana tambayarsu dama KAMAL bai mutu bane Musa jage Yace me kika gani Tace wani ne ya bayyana agaremu Komai nasa na KAMAL ne Yace toh Gaskiya yanda kika kashe shi haka muka ya dashi a ruwa yanda kika umarcemu Kashe wayan tayi tana tunanin ya abin yake A abujah ko abinda ya faru shine motoci sunkai biyar wa'yanda sukayi parking a cikin gidansu Momy MALUDDEEN ne fitto daga 'daya daga cikin wa'yannan motocin ya'dan tsaya ka'dan yana shaqar shamshin gidan. Kana yayi Murmushi ya 'dagama Marwan hannu Yace xomu shiga tare ko Nan Marwan mah ya fitto suka shiga cikin falan gidan......... Dake Dady yana gidan Kasan cewar lahadi Safna da Sagna basa nan Suna gidan wata qawarsu Gidan yarage daga ma'aikatan gidan sai Momy da Dady Dady yana dining da jarida ahannunsa shi bacin abinci yake ba Amma daka gansa xakasan yayi shirin cine Gaban dady ya fa'di dan jin muryar da har ya mutu baxai manta da ita ba. ya juyo ahankali idanshi ya sauka akan MALUDDEEN Kasan cewar shi na Miji kusan Allah ya horema wasunsu nutsuwa Yayi tasbihi ga Allah xuciyarsa tana bugawa Yayi qarfen halin nuna MALUDDEEN da hannunsa Yace KAMAL MALUDDEEN yayi mai shuru Saiga hawaye ya xubuma Dady Yace nasan gixan da idanona yasaba munne Hawayan ne ya xubuma MALUDDEEN KAMAL Yace Dady ba gixo idanka yayi maka bah. Nine KAMAL 'dinka Da sauri dady yayi cilli da jaridar hannunsa ya tashi ya iso ga KAMAL tare da ta6ashi KAMAL ya rungumesa cikin kuka Yace nine KAMAL Dady KAMAL ne Dady qamqameshi yayi Sosai yana cewa Kaine Kaine KAMAL dama baka mutu bah Momy tafitoh idan akan dining tana cewa ayya Dady na barka shuru Tun a kitchen nakejin qamshin turaran KAMAL. Ganin datayi Dady baya dining tajuyo da kallanta inda taji motsi ai cak Momy tatsaya ta qurama KAMAL 'dinta ido tana cewa KAMAL Yace na'am Momyna Aiko sai ganinta sukayi a qasa tasume Bayan da kamar 10 minutes Momy ta farfa'do KAMAL ya fara dacewa Wanine yaxo min akan anturo shi ya 'dauke Banyi wani tunani ba na shiga motar tasu aiko wani daga cikinsu ya fesamin abu Abin mamaki Momy Dady ban tashi tsintar kaina ba sai agun Sarki Yayan maman saurayinnan Ya qarashe xancan nasa da nuna musu Marwan Nan take Momy da Dady suka shafa kansa cikin farin ciki suke godema Sarki.... KAMAL ya qara da fa'da musu yanda Sarkin ya tsincesa Momy da dady sunyi mamakin yanda KAMAL ya lulaqa qasar Armiyaniya (Toh ai ba'a mamaki da lamarin ubangiji ) Da kanta Momy Tatashi ta gyarama KAMAL part 'dinsa na gidan Murna tacika xukatansu Sai waya da waya Momy da dady suke Suna gayama Mutane bayyanar KAMAL Kan kace kabo KAMAL ya fara amsa xan cikan mutane na murna da bayyanarsa KAMAL ya sallami mutanan nasa daya manta dasu a farfajiyar gidan nasu Yace sai sun ha'du kawai Sagna da Safna sundawo daga gidan qawar tasu Suna saka qafarsu afalan nasu suka ha'da ido da KAMAL kwalla qara sukayi dan ganin Yayan nasu Momy taje taqaraso dasu cikin falan nan tagaya musu abinda yace musu . [6:00PM, 19/10/2016] Rahamat Nalele💋: Aiko suka rungume Yayan nasu murna cike a ransu Sagna Tace bara na kira Aunty XARAH da Aunty LABEEBAH KAMAL ya lumshe idansa dan jin takira LABEEBAH Momy CE tayi saurin cewa Karki kirasu ki bari jibi xan ka'da mai walimar murnar bayyanarsa kinga gobe sai in sa a kawo minsu nan in musu baxata. Saidai kawai sugansa Safna Tace kuma gwara ayi haka KAMAL yayi Murmushi yana cewa aransa sun rugaku ganina momy. Musamman my baby Kusan qarfe tara KAMAL ne a shashinsa shida Marwan suna hira Marwan Yace abinda ka fa'dama Sarki da ban abinda kacema Su Momy da ban Ni kuma ka fa'damin Komai KAMAL Yace banta6a qaryaba Amma sanda XARAH tasani yi Na fa'dama Sarki hakane dan kar yayi yunkurin sadani da iyayena awannan lokacin Saboda banga amfanin bayyanata agaresu awannan lokacin ba Sannan na gayama Su Momy hakane dan banasan hankalinsu ya tashi da XARAH Su tsaneta kamar yanda na tsaneta kaga in haka tafaru baxan sami ha'din kansu yanda nakeso akan mallakar LABEEBAH da nakesan yi ba Dan xasuyi tunanin ai XARAH da LABEEBAH haka suke dan haka dole LABEEBAH ta'ibi wasu halaiyar XARAH Kaga idan sukayi wannan tunanin na rasa LABEEBAH kenan har abada Kai kuma na gayama gaskiyane dan kawai ra'ayin kaina Marwan Yace tunaninka Yayanah yana jaaaa Allah ya karemin kai Yace AmEEn Nan MALUDDEEN wanda ya koma KAMAL ya dinga kiran wayan LABEEBAH shuru Marwan Yace da mutananka har yanxu Suna aikinsu da kaga dalilin rashin samunta da bakayi bah Yayi Murmushi Yace watoh Marwan inama LABEEBAH wani SOO wanda yafi qarfin ~*MASEEFAR SOO*~ Fatana taxama jarumata dan nalura xatayi ragwanta Marwan Yace ba daga nan take ba Yayanah Amma ina maka fatan samunta yanda kakeso KAMAL yatashi yana cewa Nagode Saidai nayi maka shish shigi Marwan Yace namefah. Yace nayi maka mata Marwan ya waro ido cikin dariya Yace ayya Yayanah kamin afuwa dan naga wata xanka'da xeeeya😳💃🏼 KAMAL yayi Murmushi Yace Safna ko Sagna Tace itoh medai rawar kannan haka. Yafa'da da ta6e baki KAMAL Yace nasoka da Sumayya Amma ba damuwa tunda Sagna tatafi da xuciyar taka ba wani abu Yafa'da yana me ficcewa daga 'dakin Direct gun Momy ya nufah Yace Momy tasakar mai Murmushi Yace nayi Babban rashi Tace hmm har mu mah Yayi Murmushi Yace Allah kaji qan YUSUF Tace AmEEn Ya gyara xama Yace Wlhi momy nadawo da ~MASEEFAR SON~ 'yarki LABEEBAH Ta kalleshi ka'dan dayi masa Murmushi Tace ainayi mata Miji Da sauri KAMAL ya kama hannun Momy Yace haba Momy kituna mana Tunfarkwan soyayyata da XARAH nace miki banajin wani filing akan sai akan LABEEBAH Kin tuna😄 har nace miki idan na ha'da ido da ita tsintar Kaina nake a fa'duwar gaba Kin tambayeni banajin hakan ga XARAH nace miki eh Pls my Momy idan ban auri LABEEBAH bah mutuwa xanyi Wlhi Tace KAMAL ka nutsu katsaya ka maida matarka XARAH Yayi saurin waro ido😳 Yace wa ni😳 inaaa Na gama Auran XARAH har abada Momy Tace meyasa Yace Wlhi Momy baxan qara rayuwar Aure da XARAH bah. Dan tayimin lefin da inhar nabari taqara xama mata agareni toko baxan ta6a yima kaina adalci ba Kuma baxan yafe ma kaina bah Sannan baxan ta6a yimata adalci bah A taqaice dai na tsaneta baxan qara yarda taxama mata agareni ba Momy taja numfashi Tace ka gayamin dalilinka Yace ba dalili momy Tace ka gayamin Gaskiya toh Ya qara kama hannunta Yace kishare kawai Momy kibar batunta ki Auramin LABEEBAH kawai idan kina san farin cikina Momy ta jinjina kai Tace OK Allah ya shige mana gabah Yace Yauwa Momy kin bani 'Yar taki Tace nabaka idan ita 'din tayi na'am da kai Ya tashi yana Murmushi Yace ai duk duniya ba wa'yanda suka dace da juna sai ni da LABEEBAH tayi na'am dani Momy Nagode miki goodnyt.... Momy tabishi da kallo cikin Murmushi ta sani YUSUF yaso LABEEBAH Amma tayi mamakin yanda har ya mutu bai kusanceta bah Abin ya bata mamaki Sosai A *kano* ko LABEEBAH CE xaune da wayarta ahannunta sai juyata takeyi tana wasi wasin kunnata saboda fargabarta da aljanin nata XARAH na gefanta ta xabga uban tagumi tana tunanin wannan bawan Allan da taji LABEEBAH ta ambata da aljani. MASEEFAR😳 SON shi takeji har cikin ruhinta😳 Sumayya na xaune da SAUBAN tana buga game yana cewa taba shi ya buga dan tabuga game over da yawa tadena mishi wayo Tayi dariya Tace Lalle yaran nan kanada kwakwalwa Rukayya na xaune kan turmi jiki asanyaye dan yanxu tagama amai dan ciki ya kusantuta😄 Innah tashigo da waya ahannu kallo 'daya duk suka mata sukasan tana cikin farin ciki da murna Tace toh yaran Momy gobe da safe direba xaixo ya kwasheku ya kaiku garin na Abuja dan tana ha'da wani walima bayyanar abinda basuyi xatoba dan haka tanasan ganinku agun LABEEBAH da XARAH sukace toh Duk da Innah talura yaran nata na cikin damuwa Amma batayi gigin tambayarsu bah Dan tasan ko tace miye cewa xasuyi ba Komai Mu samman ma XARAH da jiya tana kallanta cikin dare tana riskar kuka dan a 'dakinta suka kwana BABAH yaje qauyan garin babba nanan kano wajan wani amininsa acan ya kwana Tajuya ta fitta Sumayya takwashe da dariya Tace ai xuwa Abuja danine Rukayya Tace hmm bakiga mutanan naki duk Suna cikin damuwa bane Sumayya Tace eh nagani ai nadena damuwa da damuwarsu tunda sun xa6i subarta acikinsu ai shikenan LABEEBAH taja numfashi tayi shaha'da ta kunna wayar tata Aiko ko 2 minutes batayi bah saiga wayan KAMAL aljanin nata ya shigo Aiko saita rushe da kuka kowa ya xuba mata ido tayi saurin shanye kukan ta'dauka da cewa hello Yace waya ta6amin babyna Taturo baki kamar tana gabansa Tace kaine mana Dan Allah a ina kata6a jin anyi Aure tsakanin aljani da mutum Murmushi KAMAL yayi Yana kwance akan gadan shi Marwan na kujera yana kallan wani film na mutuniyar tawa Rahama Sadau👯 waishi JININ JIKINA😄. Yace toh ya xanyi Babyna Allah ya jarab ceni da MASEEFAR SONKI. Akaina xa'afara wannan Auran LABEEBAH tagyara muryar xatayi kuka Yace Kinsan Allah kika yimin kuka alokacinnan da nake buqatar farin ciki Saina 6ullo miki yanxu na maqureki da tsotsan wannan munafukin bakin nan naki daya ke cewa wayyo aljanina kaxo gareni naxaqu inganka axuci Amma baki yana cewa dan Allah karabu dani Hakane ko ba haka bah. Yafa'da tasan tabashi amsa LABEEBAH takalli Su XARAH da suka xuba mata na mujiya (ido) ta marairaice Tace ba haka bane fah😳 _ba haka bane fah_ Ya maimaita mata furucin nata da cewa xaki fa'damin gaskiya ko saina 6ullo yanxu....... Tayi saurin cewa hakane da fashemai da kuka Yace ya salam Cikin shashsheqa Tace dan Allah karka 6ullo nayi shuru Yace ai ina kallanki goge hawayan ko na goge miki Da sauri tagoge hawayan Tace toh nagoge Yace nayi missing 'dinki babyna xanji da'din ganinki gobe Tace a ina xaka ganni Yace ba naja xakuxo abuja bah LABEEBAH tawaro ido Tace harcan xaka Bini Yace mexai hanani binki Bayan mu iska kawai muke Bi. Kanki qifta ido munje bangwan duniya fah😝 LABEEBAH tajah numfashi. Tace hmm ina sanka Yace nasani Babyna kici gaba da suna kinji Ta 'dagamai kai kamar yana gabanta Tace toh Kiss💋 ya sakar mata tare da kashe wayan Marwan Yace naga alamar kanajin da'din jin kukan Auntyna KAMAL Yace haka take Sam in batayi bah. hankalinta baya kwantawa Amma kukan yana tafarfasa xuciyata Marwan Yace toh kadena sata mana Yace ko ban sata

Chapter 18 of 22