Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Dan XARAH tanunamin ka'dan daga halin kishiyoyi LABEEBAH ce take wannan furucin kamar ta6ab6iya Tayi taku 'daya xuwa biyu tadawo gaban madubi Tace Wlhi haka xanje Aiko taqara feshe jikinta da turare tafito falo tatsaya cak tana tunani Can dai ta kwalla wata furgitacciyar qara........ KAMAL daya tare da laptop 'dinsa ai sai yayi saurin tureta gefe yafitoh da gudu ba na wasa ba........ Burki yajah a falan yana 'dan numfashi ganinta haka hannunta na dama yana cikin bakinta tasaka 'danya tsanta 'daya cikin bakin nata 'dayan kuma ta riqe qugunta dashi. Tana wani kallansa a'dan tsorace kuma a irin shagwa6annan tana kuma qifta ido Ya qare mata kallo tundaga sama har qasa ya ha'diye yawo tare da dafe kansa cikin muryar sanyi Yace mene ne Cikin shagwa6a Tace wani abune naga ya wulla yayi part 'dinka shine yaban tsoro Yace wane abune haka Tace kamar kyenkyaso Da mamaki yace kyenkyaso Ta 'dagamai kai Harararta yayi Sannan yayi yun qurin barin falan...... Aiko taqara sakin wata qarar Ya juyo cikin wani yanayi ya tsaya kawai yana kallanta Tace kaxo ka 'daukeni dan Allah kar inna biyoka yabi takan qafata. Tafa'da da 'dagamai hannunta alamar ya 'dauke kawai Yayi Murmushi watoh shagwa6ar babyn tashi tana burgeshi kuma tana tsamashi akanta. Saiya dinga jin xuciyarsa tana da'da har binshi wajan qara jin ~*maseefar SOONTA*~ Xuwa yayi ya 'dauketa batare da yace Komai bah Kan kadansa ya direta ya kalleta cikin wani yanayi Yace baby kinyi kyau sosai cikin wannan shigar. Tayi Murmushi Tace kanaso indinga mah Yace aa Tace meyasa Yace saboda jefani xakiyi kawai cikin damuwa da maseefa Matsowa tayi kusa dashi takama fuskarsa Tace ina sha'awar kiss Yayana Rungumota yayi dakyau suka xube tare dayin dariya lokaci 'daya Yace ina sanki matata kitemaken dan Allah Tace nima ina sonka YaYaNa dame xan temake ka. Yashafah qugunta Yace da wannan Ta cikin kunnansa Tafa'da masa ai nakane kayi yanda kakeso YaYaNa nimafah tun 'daxu nakejin abun..... Ya waro ido😳 Tayi sauri rufe fuskarta alamun kunya tana kuma dariya Yayi murmushi. Da cewa Allah da gaske. Tashemai ido 'daya Sosai mah Wayyo Allah nah LABEEBAH ta 'dannani ko'darta dan acewarta ba abinda ya sauya mata na tashin ciwan KAMAL ya xuba mata ido kawai Shidai yasan LABEEBAH tafitta daban agunsa akan Komai Dama xata jure buqatarsa baqaramin kwanciyar hankali xai samu bah Tana da da'di tana da xaqi Sannan ta mallaki duk abinda yake buqata agun matar Auran Sa Abin daya basa mamaki 'daya ne yanda tanunamai jarumtaka jiya Yanxu haka Kusan qarfe takwas ne Yagama shirinsa dan leqa asibitin nasa Yana dining tana kan cinyarsa yana breakfast yana bata Da gaske yana jin huccin xaxxa6in da yake damunta Amma taqi yarda ta nunamai Yace my baby ina tsintar Kaina a farin ciki idan ina tare dake sumamman idan kinbani abinnan Ta kalleta ka'dan da rufe fuskarta Yace toh gayamin me yake damunki inajin xafin jikinki Da sauri Tace Bakomai Murmushi yayi kawai danya gama gane nufinta xata jurema buqatar sane dan karyayi mata kishiya Ya ta6e baki da rayawa aransa dake ka'dai nakesan rayuwa Laveevah. Xan takura miku harki saba da futunata hakan xaisa in canja ra'ayina. Wayarsa ya 'dauka ya kira Marwan Yace pls ka wucce Dubai kawai inaso na 'dau wata 'daya dan inaso in gyaro rayuwata Marwan Yace ba damuwa Tashi LABEEBAH tayi tana cewa lokaci yayi YaYaNa karna saka makara kamar jiya. Ya tashi yana Murmushi ya rungumeta Yace ina buqatarki Gaban LABEEBAH Yafa'da. Shiko yayi fuska tamkar bai lura da canjin yanayin nata ba. Ita ko Tunaninta jiya ai yayi kuma daurewa kawai takeyi yanxu dan Wlhi so take ya fitta tayi jinyar kanta. Amma da tatuna da batun kishiya saita kallesa Tace toh yanxu kake buqatar. Ya 'daga mata gira alamar eh Gaskiya KAMAL yanada futuna inji LABEEBAH. Dama haka Auran yake ataba mutum wahala ana kwatsarsa kamar rijiya Tana kuka yanayi sanda yasamu nutsuwarsa yace Kinsan Allah baby bana gajiya dake. Tayi qarfin halin juya mishi ido da murmushin yaqe Tace nima haka Yace Amma meyasa kike kuka Tace bana sanin inayine saboda jin da 'dinka da jarumtakarka Yawaro ido Yace au Hakkane Tace hakane mana Yace toh Kullun kenan xan dinga shagalina Kamar LABEEBAH xata fashe da kuka tace daya fii Ya rungumeta abayyane ya furta. Baki ba kishiya MATAR KAMAL..... LABEEBAH tafara ramewa Kullun cikin ciwo take KAMAL yasata agaba Sosai fiye da tunanin me tunani LABEEBAH bata da saqat Sam Saidai xuwa yanxu tarigada tasaba da futunar tasa Ita dai yanxu ciwan da yake cafkarta da xaran ya gama biyan butarsa shine kawai matsalarta Ya yinda ta lura har wani qara qibah yakeyi. kuma ko yaushe cikin farin ciki yake. Musamman da talura idan ya kalleta farin cikinsa yafi bayyana Tanemi ciwan mararta tarasa Dan tunda akayi Auran nata bata sake al'ada bah Yau watanta 'daya kenan da sati uku Kuma yau takesan yakaita gidan Momy ta'dauko SAUBAN 'dinta Yace aa Tace dan Allah Yace Ko cin amarcina banyi ba xaki 'dauko shi ya hanani yanda nakeso Tawaro ido tace bakaci amarci bafa kace Ya ta'daga mata gira dayin murmushi dan ganin yanda ta waro ido Yace konaci ne Ta sunkuyar da kanta Tace toh kaini in gaida Momy shikenan Yace shikenan my baby. Amma ban bakin ka'dan Tayi murmushi wato dan Ya KAMAL 'dinta cikakken 'dan Luv ne. Ta matsa gare shi yayi mata make✔ kiss me tsayawa aran Masoya Sannan tayi bet room tafara kicikicin 'daukar gyale ya shigo Yace badai gyale xakisa bah Tace da wai shi Yace aa kisa hijab Ta kallesa xatayi masa musu. ya wani 'daure fuska Ba shiri tasaka hijabin akan wata doguwar rigar atamfa datayi mata maseefar kyau Yace Yauwa ko kefah Haka ja hannunta sukaje mota Yanda yake tuqin ya isa ya tabbatar maka yana cikin nisha'di ya kalleta ka'dan ganin tabama game hakalinta yayi Murmushi Yace my baby....... Taji wani xirrr [9:22PM, 29/10/2016] Rahamat Nalele💋: Na'am Kiji dani kibar batun game 'din nan Kashe wayan tayi gabaki 'daya Tace toh YaYaNa me kakeso imma Wato baby da'ace xanga me kamarki da Komai naki toko ba shakka xan qara da ita. Dan Kinfi mata dubu aguna. Kece tauraruwar me haskaka taurari. Kece abin San kowane 'da namiji Tayi Murmushi Tace Kaine Likitan xuciyata dake dubata Me jinyarta asa'inin da takamu da cuta Ayanxu tawarke dan ba abinda yake damunta. ka canja mata yanayinta ka sabuntata Na kuma 'dauki alqawarin xan farinta xuciyarka har qarshen rayuwata Dan abinda kama xuciyar tawa Sam ba abinda xai iya biyanta. Kabarta da xallar kishinka da qaunarka katemaken Mijina karkamin kishiya Wlhi inkayi mutuwa xanyi Ina sanka Mijina Murmushi yayi. lokacin yayi daidai da kammala parking 'din motar tashi a harabar gidan Momy Ya janyota jikinsa ya Yace dake ka'dai nakesan rayuwa baby Kitemaken kira qaimi a kan buqatata. Hakan xai temaka min sosai wajan 'dauke hankalina akan wata 'ya mace sa. Cikin shagwa6a Tace Ya KAMAL Cikin wani yanayi Yace kin mallake shi har abada kece da KAMAL Ta 'dan daki qarjinsa Tace Komai nawa anyi shine dan kai Shiyasa idanuna suka qi kar6ar kowane 'da namiji a cikin xuciyata Komai namallaka nakane YaYaNa Plx kayi duk yanda xakayi dani ni takace. Ya kai mata wani lafiyayyan kiss Yace ina sanki Tace nima haka Ina buqatarki Nima haka Ya 'dagata yana Murmushi Yace toh ya xa'ayi kenan Tace kawai mukoma gidanmu kasan nan akwai masu...... Ya katseta da fa'din Wlhi da gaske xan juya kan motar mukoma gidan A shagwa6e Tace toh waya hanaka da gaske mu koma 'din Yace kina kwa'dayin san ganin momy kuma muna cikin gidan nata fa. Tace toh miye nasan xataso in faranta maka fiye da in ganta. Ya lakuce mata hanci Yace Allah yabarni dake my baby Tace AmEEn Yafitoh ya bu'de mata kofar motar tafitoh Sannan ya rufe ha'de da kama hannunta sukayi falan gidan Momy na xaune tana karanta jarida ta'dago da kallanta garesu LABEEBAH tayi saurin kwacar hannunta tayi gunta tana cewa momyna tare da gaisheta Momy tasaki baki tana kallan LABEEBAH da kyau LABEEBAH ko kwantar da kanta tayi kan cinyarta Momy tamaida kallanta ga KAMAL Wanda ya xauna kan kujerar da take kallan tata Tace KAMAL..... Yace na'am Momy Tace me kakema LABEEBAH haka tarame kamar ba wacce aka kaima ba. Ya kalli LABEEBAH wacce itama shi tabi da kallo Yace Wlhi Momy bana mata Komai ina ganin xaman guri 'dayane kawai Momy tayi Murmushi Da dafah kan LABEEBAH Tace fa'damin gaskiya me yake miki kikayi wannan uwar ramar shiko sai qiba daya qara Tace Wlhi ba abinda yake min Momy tayi 'da jim can Tace toh kinada cikine LABEEBAH tawaro ido da kallan KAMAL Ya 'daga mata kai alamar tace eh tare da kashe mata ido 'daya LABEEBAH ta sunkuyar da kai qasa tafara wasa da xuban hannunta Momy taqara maimaita tambayarta LABEEBAH taqara qasa dakai Momy tayi Murmushi ta kalli KAMAL Tace kasa nine Yace aa Amma ina tunanin dai haka nima LABEEBAH takalleshi da sauri tana rayawa aranta lalle namiji bashi da kunya Momy Tace toh ina ganin shine dan wannan uwar ramar ba xaman guri 'daya bane KAMAL yayi Murmushi Yace Momy kenan Wlhi baxan ta6a cutar miki da 'yaba Tace hmmm halinku na maxa ai sai Ku Tashi yayi yana bin LABEEBAH da kallo Yace kuma data ramen sai tayi haske ko momy. Momy tata6e baki cikin gatse tace har kyau taqara. Yayi Murmushi dan yaga tafara hawa Yace my baby Kikula da kanki kuma kigayama Momy mijinki ba abinda yake miki Ta 'dagamai kai da cewa toh Sanda yakai kofah kana yayi mata bye bye Momy tabishi da kallo LABEEBAH Tace Allah Momy Ya KAMAL baya yimin Komai. Amma shine kikayi wannan ramar haka Tace aidama haka nake Momy ta jinjina kai Tace oho in kinki fa'damin wata ranah inkika jiki aqasa an kwashi xuwa asibity kya gayamin. LABEEBAH tayi shuru tana tunanin itadai futunar mijin natane yake ramar da ita da kuma ciwan nata Ta kalli Momyn Tace ina SAUBAN Momy tagyara mata kwanciya ajikinta Tace ban fa'da mukuba ai nasashi skull da islamiya anan tunda kumdawo kenan LABEEBAH Tace inasan na 'daukeshi Momy Tace bayanxu ba. Sai nan da wani 'dan lokaci [1:15PM, 30/10/2016] Rahamat Nalele💋: . Can wajan ranah duk suka dawo. SAUBAN na ganin LABEEBAH ya maqaleta yana fa'din Momy Kullun sainayi kuka akaini gunki sai wannan Momyn tadinga cewa xata kaini kuma taqi kaini Yafa'da yana mai nuna Momy LABEEBAH tayi Murmushi Tace ai xata kawoka toma bagashi naxo ba Yace dani xaki tafi Tace eh Nan ya hau murna Momy na dariya tana mai tsiya LABEEBAH CE ta saka Su Sagna a gaba xuwa kitchen Tace yau ni xanma Momy da Dady girki kutayani Sagna Tace kai Aunty nifah nagaji baga 'yan aiki ba Safna Tace Wlhi nima haka LABEEBAH Tace duk abinku yaudai sai kun tayani girkin nan Wlhi. Haka suka tayata suna mita Sai dai da suka gaba sunfi kowa ibewa Bayan sallar isha KAMAL ya shigo gidan LABEEBAH ta ha'damai abinci yana ci Suna hira da Momy inda yake ce mata yana tunanin acikin satinnan xaije Armiyaniya daga can ya wucce Dubai Momy Tace Amma nan xaka kawomin LABEEBAH ko Yace wa. LABEEBAH tabashi amsa Yace tab ai Momy qafata qafarta Momy tayi Murmushi Tace naji da'din hakan Allah yayi muku albarka Yace AmEEn LABEEBAH najinsu daga 'dakin Momy Taja numfashi Da Farko har tafara murna bada ita xaije ba Ashe dai baxata hutaba Can basu jima ba Momy taxo gareta Tace taje sutafi Tace Momy harnaji ba da'di. Momy tayi Murmushi Tace Karki damu xaku da'da xuwa kafin kutafi can Armiyaniya Tace dani xaije Momy Tace abin daya dace kenan ai 'Yata LABEEBAH ta sunkuyar da kai. Haka Su Sagna suka rakakota har mota KAMAL yaja Su AmEEncin Allah ya tabbata agareki tauraruwar raina me haskaka gani na Cikin sanyin murya Tace tare dakai YaYaNa masoyina abin farin cikin ruhina Nayi missing 'dinka Sosai Yace Nagode Amma xanso nagani abaiyane. Tayi Murmushi tare da matsawa kusa dashi tayi mishi kiss a kumatu Tace yayi Yace ai baya isata Taqara yimasa nan ya lumshe ido Tagyara xamanta Tace kar kaje kayar damu. Hmm muje gida kakar6i saban karatun dana 6ata lokaci ina San karantar dakai Yace kafin kibani naki xan fara baki nawa Tace harna xaqu inganni kana karantar danin Yayi murmushin jin da'di. Gaskiya daban sameki matsayin matata ba danayi babban asara Tace nice xanyi asarar hakan dan irin ka 'dayane acikin maxaje ban ha'da ka da kowa ba bare ayi tunanin samun irinka Daidai nan yayi parking motarsa agindan nasu Afalan ya baxa mata kayan xaqi dayayo mata shopping 'dinsu ita da SAUBAN dasu Sagna Aiko tabaje tadinga cin danginsu chocolate. Ya sata ta kawo mai fitsarinta. Nan takawo mai Anan ne ya fara gwadata yana cewa dama nasan da Babyna acikin nan Ta lumshe ido danjin yanda yake shafa mararta Tace banajin akwai fah Ya harareta tare da cigaba da dubata Aiko yagano tana 'dauke da cikin wata 'daya da sati biyu Ya kalleta da murna Yace Wato sati 'daya kika tsallake ko Tace hmm ance aihuwa da xafi ko Yayi Murmushi Yace aa ni xan ' dauke miki xafin Tace Saidai kawai in aihu ba ciwo Yace eh allura kawai xan miki Tayi Murmushi dan a tunaninta ta'dauka da gaske ne Ya rungumeta Yace ina sanki matata kiyi quqarin bani yara doxin Ta waro ido Tace 12 kenan fah Yace eh sunyi ka'danne Ta girgixa mai kai alamar sunyi yawa Ya harareta da cewa toh Wlhi kishirya bani Su dan ina sansu Sosai Lumshe ido tayi dan taga yafara aika mata da karatun nashi Kwana Uku nayi KAMAL yashirya musu tafiyar inda sukaje sukayi sallama da Momy Dady sukayi musu fatan alkairi yake gaya musu LABEEBAH nada ciki Ba qaramin murna sukayi bah Dady Yace wata nawa xakuyi KAMAL Yace xamukai wata takwas haka Yace toh Allah ya kiyaye Washe gari suka cale Armiyaniya Satinsu 'daya sukayi Dubai inda LABEEBAH taga tangameman gidan KAMAL Tace tab Amma gidannan yayi kyau YaYaNa Yace danke aka yishi Kowane lungu da sa'ko hotunanta ne. Hakan yasa taqarajin San mijinta *banyan wata shidda* *🙆🏼ya xarah ta takene jama'a🙆🏼* A Kano ko abinda ya faru shine XARAH ta lalace ta ko'de duk tafitta daga haryacinta saboda MASEEFAR SON tsowan mijinta KAMAL Abin na damun Usman Innah BABAH Rukayya Sumayya Duk sun rasa me yake damunta dan sun mata tambayar duniya agareta takasa basu gamshash shiyar amsa Sai dai Tace ba abinda yake damunta Yanxu haka yaune take kan taburma tana hawaye tunaninta 'dayane taga KAMAL ido da ido ko xata samu nutsuwarta da Sauqi aranta Saidai me😳 tunanin nata yaci qarfinta Wanda yasa kanta sarawa tayi saurin dafe kanta sai kuma qirji ya 'dauka ta dafe tana wani nishi..... Daidai lokacin Usman ya shigo gidan ganinta cikin wannan hala ya kwallama innah da Sumayya kira suka fitoh Sun gigice da lamarin dan haka Usman ya fita yakira me kekenafe nan suka sata akayi asibiti da ita Wanda alokacin tariga da ta sume Kowa xuba mata ido yayi dan duk bincike yanuna damuwace tayi mata yawa kuma damuwar ta kama xuciyarta Sosai dan haka Su bincika sugano meye wannan damuwar tata yanxu haka koxata farfa'do xata 'dau sati 'daya ko sama da hakan Da kuka Sumayya takira LABEEBAH tagaya mata Lokacin LABEEBAH Suna Dubai inda take kan cinyar KAMAL tayi nauyi aihuwa yau ko gobe tana zubamai shagwa6a. Hira suke akan Momy tace yayi Maza ya kawo mata LABEEBAH karta aihu anan. Sai kawai taji wannan lamarin ciwan XARAH agun Sumayya Aiko saita fashe da kuka duk hankalinta ya tashi KAMAL yajah tsaki Yace to miye. cemiki akayi tamutu da xaki tada hankalinki haka Ko kulashi batayi bah taci gaba da kukan ta Haushi yasashi sauke daga cinyar tashi dasan fitta daga falan Ta kwalla qara Ya tsaya cak Taje da gudu ta rungumeshi tana wani kuka me dakatar da fushin masoyi Saiya hau lallashinta tako ta ina Sannan ya samu tayi shuru Yace yanxu me kikesan nayi Tace nidai kawai inasan naganni a kano kawai Ya waro ido tare da cewa tab baxai yuhu bah Sai taci gaba da kukanta Daqer yasami kanta Bayan Yace mata xaiyi tunani Dan shi sam baya san tashin hankalinta sam Duk dama ta Cikinsa yakeyi daya kusa fitowa duniya👌🏻 Har tsawan sati biyu XARAH na asibity kwance xuwa lokacin ta farfa'do Amma bata magana Dan in tace xatayi magana jitake qijinta kamar xai fitta Suna cikin wannan halin ne Rukayya ta haifi 'danta na miji me kama da Usman yaxo kamar LABEEBAH CE ta haifeshi Sumayya Takalli Rukayya tace Aunty dafa yanxu haihuwarki biyu Tace eh 6ari ya yimin yankan qauna Tace kina San yara Tace Wlhi Sosai nake sansu Allah yaban 'yan biyu AmEEn Sumayya Tace Anyi Suna inda yaro yaci sunan babansu LABEEBAH Wato Malam Sanih Suna kiransa da khalit KAMAL yasan da aihuwar Rukayya Amma koda wasa bai gayama LABEEBAH bah har akayi Suna ya aiko musu da kayan baby cikin akwati da sunan LABEEBAH CE ta aiko Dama shi KAMAL tunda tatada mai hankali akan rashin lafiyar XARAH ya 'dauke wayanta Sai dai Yata xabga mata qarya akan XARAH tasamu lafiya Ta tambayeshi ina wayanta Yace shima bai gani ba Ranar yana kallanta tanata uban duba wayan har tana kuka Yayi Murmushi aransa Yace wannan yarinyar inda hawaye na qarewa da nata sunqare Haka ko yabarta tanata nema data gaji sai taxo taxauna kan cinyarsa tana cewa toh meyasa kai baka da numbar kowa agidanmu Yace ina dashi man my baby Amma a'dayar wayata dana bari a gida Ta kwantar da kanta aqirjinsa Tace inasan inganni a Kano dan Allah mubar garinnan Yayi Murmushi dan shi yasa aransa baxai bar Dubai bah har sai ta aihu Yace xan kaiki Amma saikin aihu Ta 'dago da kanta da sauri Tace ai ina watan aihuwan ina basai kawai muje in aihu acan ba Yace ke wawiya anan ake samun allurar nan me 'dauke xafin ciwan aihuwan Tace toh mutafi da ita mana can Yace kan muje xata dena aiki Tace yanxu Lalle sai anan Eh in kuma bakyaso saimu tafi Shuru tayi can Tace ina so XARAH Al'amarin ya farune qarfe biyar na safe Wato idan XARAH abu'de yake a wannan lokacin Innah nakan sallaya tana laximi dake jiya anan takwana A kwancan XARAH tayi wani qaramin rubutu tayi qarfin halin cewa Innah...... Innah Tatashi da sauri taje gareta Saita miqa mata wannan takaddar Tace saka a lalitarki. Ba musu Innah tasaka XARAH takama hannunta Tace kiba LABEEBAH ita ka'dai innah kiyafemin duk lefukan dana miki. Kisa baba ma ya yafemin. innah mutuwa Xanyi Ina sanku ina sanku Xan mutu da MASEEFAR SON KAMAL Ina sanshi innah ina MASEEFAR SON SHI Na aikatamai abun da yasa shi barina Na cuci kaina innah Idan kun ha'du kice masa ya qara yafe min Tana fa'din hakan tafara dafe girjinta da sanyin kalmar shaha'da Allah ya temaketa tayi Me xai faru 😳 Hakan akeso ga dukkanin musulmi Innah sake hannun XARAH tayi cikin furgita da lamarin Tabbas XARAH ta mace sai dai muce Allah yaji qanta ******* Usman yayi kuka yayi kuka haka Rukayya Sumayya Duk San shiga wani hali Usman ya 'daga waya yakira Su Momy ya gaya musu Nan cikin tashin hankali suka nufu Kano Anyi bakwai 'din XARAH inda tasha addu'o'i Ba lefi XARAH tasamu sheda tagari agun jama'a da dama dan bawanda ya fa'di sharrinta dan bata musu Wanda haka akeso ga dukkan musulmi Momy ta gayama KAMAL batun muwar XARAH Amma tahana ya gayama LABEEBAH dan cikin da yake tare da ita Ba qaramin furgita KAMAL yayiba Da gaske ya shiga tashin hankalin mutuwar XARAH Dan haka ya yayi duk wasu abubuwan da xaiyi asati 'daya ya shirya musu LABEEBAH na xaune tana kallan wani film 'din hausa na Rahma sadau wai Sirrin dake raina KAMAL ya shigo falan yana qare mishi kallo Gaskiya LABEEBAH tayi dan duk da Cikin dake jikinta bai hanata tsafta da kwalisa ba. Ko ina a tsaftace yake sai qamshin turare falan yake Batasan da shigowar tashi bah Sanda Yaxo ya sha'ki qamshinta ta baya wajan xuro da kansa kan kafa'darta Yace nadawo my baby Tace Wlcm my YaYaNa Naji da'di dan tunda kafita nake Allah Allah kadawo injini ajikinka kona samu Sauqi araina Yadawo gabanta ha'de da rungumaita Yace nimah haka my baby Yanxu dai albishirinki Tace goro fari qal Yace gobe qarfe Tara jirginmu xai tashi. Xaki ganki a kano. Yafa'da da 'dan kama kumatunta yana Murmushi Saurin yimai kiss tayi tace Amma naji da'di YaYaNa Yace hmm baxakiji da'din xuwan naki bah Tace me yasa Yayi Murmushi Yace saboda ko acan ba barinki Xanyi ba Ta daki qirjinsa ka'dan Tace hmm kasan wani Abu Yace aa Tace Wlhi akwanakin nan gaba sai fa'duwa yake abin ya fara damuna Yace hakan ya kamata kiji Tace meyasa Ya kawar da xancan da cewa nidai naxaqu babyn nan ya fitoh duniya Tace hmm duk ya wani hurani yasa naxama qatuwa KAMAL yayi Murmushi danjin yanda tayi maganar kamar xatayi kuka Yace kar kimin dan Allah Tayi Murmushi Tace ba xanyi ba to Ya gyara xama Yace yanxu bara namiki wanka na shiryaki muje siyan tsaraba ko Da murna Tace toh Duk rabin siyayyan LABEEBAH kayan XARAH ne KAMAL na kallanta yana girgixa kai dan tausayinta Sunxo kano lpy inda suka sauka agidan Kakah Tayi murna da xuwansu Sosai har take yima LABEEBAH gaisuwa LABEEBAH batare da tasan wacce ta mutu ta'amsa mata Sanda suka kwana suka hucce gajiya Sannan. KAMAL yace suje gida ko LABEEBAH Tace kamar yanxu nakesan yima magana Haka suka fitoh gwanin sha'awa hannunshi cikin nata ya sata amota Takalli kanta a madubi Tace tab xasu ganeni kuwa KAMAL.yayi Murmushi da tada motar Yace mai xai hana babyna LABEEBAH taqara kallan kanta Tabbas tayi wani MASEEFAR kyau Fatarta ta goge tayi qiba matsalar tata 'dayace cikinta daya mamayeta gabaki 'daya Ita dai tana ganin masu ciki Amma bata ta6a Ganin me irin nata bah Tace nayi muguwar qiba YaYaNa Yace hakan ne yadace me sona Tace LA munyi mantuwa Yace tamefah Tace ya xamuyi da allurar da xakamin ta xafin aihuwa. Yace natawo da wacce xatayi amfani har anan. Tace Yauwa YaYaNa Daidai nan yayi faking 'din motartasu a kofar gidansu Fatima-zarah Tace wow sainaji da'di Sosai gani a kofar gidanmu Yace na tayaki murna Kanyi yayi wani yunquri harta ficce a motar Ya bita da kallan tausayi har tashige gidansu XARAH Yace am sorry my baby Inaga yau xaki aifemin cikin nan Yana fa'din haka ya fitto daga motar yabi bayanta LABEEBAH da murna tashiga gidan tana cewa Innah XARAH Sumayya Aiko innah tafitto daga kicin da sauri yayinda Sumayya tafitto da gudu daga 'daki Ta rungume LABEEBAH tana kuka Innah Tace LABEEBAH Tace na'am innah KAMAL ya shigo ya durqusa yana gaida innan Ta'am da fara'a tana fa'din sannunku da xuwa Cikin sanyin yanayi LABEEBAH tace menene Sumayya me yasaki kuka haka Aiko taqara fashewa da kuka taraba jikinta da LABEEBAH tace Aunty XARAH ta mutu.... Da ba dan KAMAL yana ankare da LABEEBAH ba da tabbas Saidai taxube aqasa Dan haka ajikinsa taxube cikin furgita Tace Ya KAMAL XARAH......... Ba abinda KAMAL ya tuna sai ranar da taji mutuwar iyayanta data nemi xubewa ya tarota haka Yace eh ta rasu am sorry Aiko ta qulla qara tare da sumewa ajikinsa Innah ta girgixa kai cikin kuka Tace Sumayya baki da hankali bakiga yanayin da take na juna biyu bah Tafa'di hakan da miqama KAMAL ruwa Tace Wlhi Innah bansan ya akayi na fa'da mata ba Shuru KAMAL yayi kawai da kar6ar ruwan Ya yayyafa mata nan ko tadawo hayyacinta Tace Ya KAMAL ta mutu da gaske Ya 'daga mata kai cikin damuwa Aiko sai cikinta ya mur'da tayi saurin dafe cikin tafashe da kuka tare da cewa wayyo cikina wayyo XARAH Innah Tace aihuwa CE wannan Maza kuyi asibity Nan ya kinkime ya kaita mota Sumayya tashiga Innah Tace gata nan biyosu bara ta gayama Usman. KAMAL Yace toh Sanda suka biya ta gidan kakah ya 'dau kayan haihuwan nata Sannan suka wucce asibitin Sosai abokin KAMAL yace duba LABEEBAH ganin hankalin KAMAL ya bala'in tashi KAMAL ko ganin baxai iya jurar jinkirin abokin nasa bah. Sai yasa hannu akanta kawai Ganin haka abokin nasa ya barsa LABEEBAH kuka takeyi tana cewa mutuwa Xanyi Ya KAMAL mutuwa Xanyi Yana jinta yana Binta da kallanta Ahaka ta sullu6a 'yarta mace Kan ya gama ankarewa ta kuma yun 'kurin fitto da wata..... aiko sai Ganin wata yayi

Chapter 21 of 22