Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kigayamai daga yau karya qara kashe kudinsa haka kuma Ku ajiye kudin idan yasake dawowa abashi abinsa Yafa'da Yana mai kallan XARAH Tace toh Babah Innah Tace toh madallah tunda kasanshi mah da Sauqi. Mamah ce tayi sallama da Kaya niqi niqi Tace Kaya wani yaro yashigo dashi wai inji KAMAL a ajiyema Aisha-Labibah Tafa'da tana mai bu'dewa Komaidai iri 'dayane dana Fatima-zarah har ku'din KAMAL bai bambanta bah Inna Tace kinga mah na XARAH nan yanxu muke tattaunawa Malam Yace ya shedashi danya gabatar da kansa agunshi Malam Sallau Yace hakane Karku damu Mamah Tace Amma amaida mai da ku'dinsa Ko Malam Sallau Yace abinda Nace yanxu kenan koya kuka gani Mamah Tace hakan shiyafi. Nan tabashi ku'din ya ha'da dana Fatima-zarah Yace xai tsamayi xuwanshi gobe Koda Malam Sanih yadawo mahaifin Aisha-Labibah mamah takoramai Bayani. Kayan da KAMAL yakawo musu baqaramin mamaki yayiba Yadinga sanya mishi albarka Yace gaskiyane gwara amaidamai da ku'dinsa. A ranar baccin farin ciki LABEEBAH tayi. Dan tariga tasa aranta ganin KAMAL kojin muryarsa kojin qamshinsa shine farin cikine agareta. XARAH Tace sai murna kike lafita Tace lau lau Tace toh Allah yasa Washe gari da KAMAL yadawo. malam Sallau da malam Sanih sunci sa'a suna gida. Dan Yana xuwa suna fitowa dan xuwa Kasuwa Dan haka Malam Sallau yakoma gida ya 'dauko kudin KAMAL ya danqama mai Amma Sam KAMAL yaqi kar6a Yace Wlhi Babah munfara kenan Haka nake da bayarwa bana gajiya Bare kuma Ku baxan iya in bakuba koda kowa ranku xai 6aci. Haka xaku kaqura dan bana dawowa na kar6i abinda nariga na bayar. Bayanda Malam Sallau da Malam Sanih basuyiba akan KAMAL ya kar6a Amma yaqi saima nuna musu da yakeyi mah yanxu yafara bayarwa Haka suka hakura suna samai albarka suka tafi KAMAL ya kalli XARAH Yace my TEEMAH kinfi jiya kyau Takalli shigarta Duguwar rigar atamface sai hijab 'dinta da 'dan takalminta mekyau Tace ina kyan yake my luv kawai kaso xolayane Yace da gaske nake Tace toh naji yanxu dai bani labari Yace namefah. Kata6ayin budurwa. Tafa'da tana me kafeshi da ido Yace eh aa Tace ban ganeba Yace inada masu sona Amma ba wacce tadace da xa6ina kamarki da fatan xaki riqeni amana....... Hmmm Allah sarki LABEEBAH tana jinsu dake akan dakalin kofar gidansu suke hirar wanda dakalin yayi 'dan kwana yanda mutun na fitowa xaici arba dasu Dan haka taxauna a jikin katangar da suke dama da bishiya agun kuma lokaci lokaci tana xama agun dan shan iska Toh yaudai abin ba haka yakeba. Dan tanajin muryar KAMAL har Cikin xuciyarta Hankankk na mata da'di. Sai Murmushi take ita ka'dan tana addu'ar Allah yasa karya tafi da wuri dan bata qoshi dajin muryarsa ba me da'din dauraro da kashe jiki Tajah numfashi taleqa tajikin wani huji daya 6ule Wanda yabata damar ganin KAMAL 'din nata hankali kwance Tako quramai ido ko qiftawa batayi dan idan tana kallansa manta kanta take Tayi nisa acikin kallan nasane. Sai taji ranta na 6aci kuma😳 Xuciyarta na soya. Hankalinta yafara tashi Can kuma taji zuciyarta namata zafi. Saka makwan jin wasu kalmomi da masoyan suke gayama juna Inda KAMAL Yace banta6a soyayyaba. Amma tunda Allah ya ha'dani dake namiki kallo 'daya qaunarki da soyayyarki suka caki xuciyata. Ina sanki XARAH tayi dariya Cikin jin da'di Tace dama haka so yake. Yakan shiga xuciyar mutum batare daya shiryaba Nima na soka sosai Yace ban gani bah Akwai wani abu da kakesan namaka dan katabbatar da hakan Yace eh kai. Sunanan da yawama Tace toh fa'desu dan har naqagu najisu Yace baxan fa'da miki ba. Danke yadace ki ganosu da kanki Tace toh Karka damu badai muna tarebah Yace yah mutu ka raba takalmin kaxa inji.... Da dariya XARAH Tace inji yara Yace gud Inasan akoda yaushe idinga ganin dariyarki. Tasun kwiyar da kanta qasa Tace gashi ban cika yintaba. Nina yima mamakin yanda nake maka dan gaskiya bancika dariya bah Yace sone ya kusan toni shiyasa komaima xakimin batare da saninki ba...... Juyowa LABEEBAH tayi da kallanta tsakar gidansu hawaye naxuba daga fuskarta. Meyasa yau taji tsanar XARAH. meyasa yau takejin xuciyarta na mata xafi Waime yake shirin faruwa da kene LABEEBAH Akan wane dalili xakiji tsanar XARAH Shin kin manta itace qawarki 'yar uwarki Me baki shawara kema kibata Shin kinmanta keda ita kunxama tamkar ciki 'daya kuka fitoh Xuciyar LABEEBAH CE take mata wannan tambayoyin Tashi tayi anutse tayi 'daki tasaka sakata tarisgi kuka San ranta kana tayi bacci tana rokwan Allah ya rabata da MASIFAR SOO Sai kusan biyar 5:00pm tatashi Tabu'de 'dakin tare dayin kicin ( kitchen) inda mamah take girkin dare Tace mamah kawo intemaka miki Tace aa kibarshi keda bakijin da'di Tace naware fah Juyowa mamah tayi da kyau taxuma mata ido dan taji muryarta tacanja tamata alamun tawanda yayi kuka Tace LABEEBAH meyasaki kuka. Tayi saurin qaqalo yaqe Tace ba Komai fah me kika gani inbaki fa'da yanxuba kya fa'da gaba Mamah tayi furucin da 6acin rai Cikin 'dan Murmushi Tace hmmm ciwan idonane yatashi fah. Kawai banasan in ba'da mikine Da sauri mamah tamaida kallanta kanta Cikin tausayawa Tace Ayya shine Tace eh shine Tace toh aini lamarin ciwan idan nakine yaqijin magani yaxamuyine Tace hmn addu'a mamah karma kisamomin wani magani kibarshi kawai zaidena Mamah Tace toh bari muganidai Kedai kina shan jarabtar ciwuka. Ga ciwan Mara ga ciwan ido. Fitowa tayi daga kicin (kitchen) 'din ta'dauko taburma taje gindin bishiyar gidan nasu tashinfi'da taxauna tana cewa mamah XARAH bata shigoba lokacin da nake bacci Mamah Tace af namanta taxo. Ciduba 'dakina ta ajiye miki wasu Kaya da KAMAL yabata da naki harda ku'dima inkin ganshi kyayimai godiya LABEEBAH tamiqe tayi 'dakin da gudu Aiko waro ido tayi tana kallan kayan Atamface guda biyar les biyu Sai takalmi da gyale Gyefe kuma turarukane da kayan kwalliya (make-up) Nan tashiga shinshina turarukan tana addu'ar Allah yasa da irin turaransa aciki Sai dai kash........ Duk iya shinshinanta bata shin shino irin qamshin KAMAL bah MASIFA Nan kuma hankalinta yatashi taji aduniya qamshin turaran KAMAL takesanji. Cikin sauri tafitoh tsakar gida tana waigen inda tasaka hiyabinta. Aiko tahango shi kan igiya nan tasaka tayi waje Kan dakalin da XARAH da KAMAL suka xauna nan taje taxauna dai-dai inda KAMAL yaxauna.......... Tasauke wata sanyayyiyar ajiyar xuciya saka makwan qamshin turaran nasa dataji Tayi shuru tana jan numfashi akai akai dan ganinta qamshin yanasan barin gun gashi tanajin da'din hakan. bataso taga yatafi qamshin Akallah Aisha-Labibah ta'dauki awa 'daya gun tana shaqar qamshin KAMAL agun Tana kuma mamakin wannan wane shegen turarene daya kasa barin 'dan gurin nasu. Komadai wane irine itadai batajin xata tashi agun wani abin da'di. Bawanda yayo tagun bare yaganta xaune ya tambayi me take agun Tana Cikin wannan halinne saiga XARAH tafito daga gidansu daniyar shiga gidansu LABEEBAN Mexata gani LABEEBAH xaune kan dakali tana shinshinar bango Taqaraso tana cewa wani saban salan iskanci ne kuma yau agunki da shinshinar bango Bama wannan ba. Asanyinnan kike xaune anan Cikin fa'duwar gaba Tace yanxu fah nafito kuma naji qamshin qasane jikin bangwan shiyasani shinshinawa Tace aikowa Amma meyasami idanki Allah dai yasa ba Ciwan idankin bane yadawo Meqewa LABEEBAH tayi da alamun tafara gajiya da tambayoyin XARAH. Kuma yakaicinta 'daya xata rabata da qamshin KAMAL da take shaqa. Tace shine Cikin tausayawa Tace Ayya sorry sannu kinji Allah yasa ya tafi da wuri Tace AmEEn Naga kayafah muje muqara gani XARAH tayi dariya Tace hmm gaskiya KAMAL yayi Dan qarshene shi Ina sanshi LABEEBAH kitayani da addu'a kar Allah ya jarabceni da son da nake masa yafiwanda yakemin Cikin Murmushi Tace toh Nan suka shiga gidan sunamasu qara ganin kayan suna yabawa mamah na tayasu har axuciyar Aisha-Labibah taji da'din kayan tayi murna sosai Cikin ranta tana ganin kayan tamkar KAMAL nagun Tafiya tayi tafiya hardai mamah da Usman da XARAH da Innah suka saka LABEEBAH wai sai tagaya musu meyake damunta. Dan kallo 'daya xaka mata Kasan tafuta daga hankalinta kuma ba tambaya akwai abinda yake damunta Amma LABEEBAH takafe akan itabah abinda yake damunta Haka Su mamah suka rabu da ita. Amma XARAH tanace saita gaya mata dumuwarta LABEEBAH takalleta Tace Wlhi XARAH ba abinda yake damuna sai MASIFAR SOON KAMAL Ina sanshi ina qaunarsa. Yana burkitana. Tunaninsa yafara cutardani Kuma gashi koxan mutu akan qaunarsa baxan sameshiga Cikin bala'in tausayi XARAH tafara share mata hawayanta Tace ina jin tausayinki LABEEBAH Kinfa'da Cikin fa'da Cikin MASIFAR SOO Abin takaicin shiwanda kikeyi danshi bakisan wayeba Bakisan daga ina yakeba Bakisan a ina xaki samoshi bah Shin tunda kika mishi ganin farko kinqara masa Cikin kuka LABEEBAH Tace aa banqara ganinsaba Tace toh kiyi hakuri muta addu 'a Allah ya baiyanasa Shuru LABEEBAH tamata tana tausayin kanta dajin haushin xuciyarta da takamu dasan Wanda har abada ko sanshi da qaunarshi xasuka kasheta baxata ta6a auransa bah Awannan ranar Sam XARAH rasa sukuni tayi har da KAMAL yaxo gunta yake tambayarta lafiya yaganta hakah Kuka tasamai tana labartamai ciwan San da 'Yar uwarta LABEEBAH take ciki. Taqara dacemai yanxu hakama tana kwance batajin da'di Yace subhanallahi waye yayi gigin shigewa xuciyar qanwata harya haifar mata da ciwo 💘 haka XARAH tata6e baki Tace hmm sunanshi KAMAL Yawaro ido Yana cewa no no no plx kicanjamai suna dan baidace yaxo da sunanaba dan ya aikata Babban lefi Tace Allah sunanshi KAMAL my luv KAMAL ya girgixa kai taredajan tsaki Yace Wlhi my TEEMAH banso sunanshi ya kasance KAMAL ba.. Dan da gaske nabama LABEEBAH wani matsayi axuciyata Banso me sunana ne yake wahalar da itaba Shuru XARAH tayi tanaci gaba da kuka Daqer ya lallasheta Yana cewa taje tagayama mamah xaishigo ya dubu LABEEBAH. Nan ko tagayama mamah Mamah Tace yashigo Yashigo Cikin nutsuwa suka gaisa da mamah tana yaba kyau da tsari da nushuwa irinna KAMAL Nan LABEEBAH tafitoh suka gaisa Yace ya jiki. Cikin sanyi Tace da sauqi tana mejin kunyarsa Cikin murya qasa qasa Yace bama xuciyarki hakuri my qanwa insha Allah xaki kuma ganin KAMAL akaro nabiyu. Kuma xakisha mamakin yanda xaixo miki da Kalmar SOO Cikin tsoro LABEEBAH takalleshi Tace waya gayama asirin xuciyata iye Ya KAMAL Yayi Murmushi cikin jin da'din muryarta Yace me qaunarkice tagayamin XARAH dan natayaki da addu'a ko bakyaso Saurin girgixa kai tayi Tace inaso. Kuma dan Allah idan xakamin addu'ar ka roqimin Allah yaciremin qaunarsa acikin xuciyata kwata kwata...... Saiyanxu ta ha'da ido dashi. Aiko wani dafin sanshi yafito daga idansa yacaki nata idan Nan take tasaukar da idanta qasa tare da xubar da hawaye KAMAL Yace toh Xanyi yanda kikace MATAR KAMAL........... Da sauri takalleshi takuma kawar da kallannata daga kallansa Xuciyartace tabuga dam Tabbas bata ta6ajin kalma meda'di kamar yanda yakira da MATAR KAMAL bah Tajah numfashi tare da sauke ajiyar xuciya Shiko KAMAL ganin hawayanta yasashi tabbatarwa tana Cikin MASIFAR SOO Ya girgixakai da dumbun tausayinta Yace plx kar kibari San KAMAL ya haifar miki da ciwan xuciya dan Allah Daurewa tayi tace toh xankiyaye dan muryarshi kashe mata jiki take tare qamshinsa Ahaka yatafi yanamaijin tausayinta. Yayinda ita kuma baqin Cikin tafiyarshi yaxiyarci xuciyata kai hatta da gangar jikinta 🌹MASIFAR SOO.....🌹 Bayan wata uku LABEEBAH tashiga tashin hankali dajin da'di kala kala Dan duk qarshen sati sai KAMAL yaxo. Kuma idan yaxo kwana biyu yakeyi yake komawa Abuja Yanxu LABEEBAH tagane ganin KAMAL da XARAH baqaramin bala'i da MASIFA bane agareta Dan yanxu tagane kishin XARAH ne yake damunta tare da qarin MASIFAR SOON KAMAL da take 'dawainiya dashi Dan haka idan yaxo saita xauna na minti biyar tana leqansa tajikin hujin ginin gidansu tanajin da'di da sanyi aranta tare dajin tsanar XARAH da kuma takaicin xuciyarta Daga nan saita Koma dakinta tariski kuka sanranta saita kulle kofah tanajin XARAH tana nemanta insun gama xance. Amma saitama kunnan uwar shegu daxuwan bacci take XARAH nayin gida saita fitoh tayi gun xaman KAMAL tata shaqar qamshinsa tana sauke ajiyar xuciya 〰〰〰〰〰〰〰〰〰 Toh yau KAMAL yaxoma XARAH da babbar magana Wai xai toro iyayansa asaka ranar bikinsu Ta kalle shi da alamar 'Yar tsorata agareta. Tace aa kabari sainan gaba Yace Mene Tace nasan kaji my luv Bana san. Nayi Aure LABEEBAH batayiba. Yace idan nagane xanxanki baxaki xama mallakina bah. harsai 'Yar uwarki tasamu miji amuku Auren tare Tace eh haka nake nufi. Amma dan Allah kayi hakuri Yace no karki damu xanyi tunani Yau LABEEBAH Tatashi da masifaffan menstruation ciwan ciki na al'ada. Toh Dama haka yake mata kuma idan yatashi baya mata Nada'di dan jitake kamar xata mutu Nishi take tana hawaye daka ganta Saita baka tausayi Innah Tace sannu AISHA Allah yabaki lafiya Mamah Tace AmEEn Ni Malam yabani wani magani nabata. Kinga nanemeshi sama ko qasa narasa Innah tajah numfashi Tace nidai lamarin ciwan nan nata Yana 'dagamin hankali Wlhi. har banaso wata yaqare XARAH Tace mukaita asibity karta suma kunsani idan hakan tafaru bata farfa'dawa tada'di Mamah Tatashi ta'dauki gyalanta. Tana cewa kuma gaskiyarki FATEEMA Innah ta'dagata tana cewa Allah ya rabaki da wannan kiwo kihuta Sunfitoh daga gidan kenan saiga KAMAL yafaka motarsa Da sauri yafitoh yana cewa Subhanallahi meya sameta Mamah tagayamai Cikin sauri ko yabu'de mota Yace kushiga muje asibity XARAH Tace kamarko Kasan nan xamu Bawani bane yadubata a Asibityn Aminu kano fa ce KAMAL Ya tausaya mata sosai dan sanda tasuma sau biyu. Cikin tausayawa yaxauna yaxuba mata ido Yana naxarinta. Yau kwananta 'daya kenan batasan wanda yake kantaba Qura mata ido sosai KAMAL yayi Fa'di yake aransa Tabbas baxata rabu da ciwan nan bah har sai tayi Aure. Yayi shiru Yana kissimawa aransa shidai beta6a ganinta da saurayiba. Gashi yanda yakeji aransa saiso ace tayi Aure nan kusa. Dan ba qaramin tausayinta yaji ba.Sam jiyayi bayasan takai wani month 'din.... Mustafah ne ya katseshi daga tunanin da ya keyi tawajan shigowa da yayi Bayan yaxaunane Yace yau qarfi da yaji ka kwacema ANAS aikinsa Wai wacece ita agunka ko amaryace KAMAL yayi Murmushi Yace nasan daxaka shigo kaga wata beauty baby Yace eh naganta KAMAL ya kalleshi dakyau Yace toh da ita xa'asha bikin Da dariya sosai Mustafah Yace Amma natayaka murna Allah yasa nan kusa xa'ayi Cikin wani yanayi KAMAL Yace ina buqatar iyali nan kusa Mustafah. Amma Tace sai wannan tasamu miji Sannan xatayi Auren. Yaqarashe da nuna LABEEBAH da ido Cikin nuna damuwa Mustafah Yace halin mata saisu. Banda haka yaxa Tace haka Wannan ai na Allah ne Kuma shiyasan lokacin kowa KAMAL Ya'dan ta6e baki Yace Xanyi tunani dan sanin yanda Xanyi Da wasa Mustafah Yace Kasan Allah tayimin. Wlhi tunda kuka kawota zuciyata tacika da soyayyarta. Xuciyata sai bugawa takeyi ina addu'ar Allah yasa ba budurwarka bace Da farin ciki KAMAL yadafah kafa'dansa Yace Amma naji da'di Plx kafito da wuri. Dan Naqagu naganni da baby Dariya sosai Mustafah yayi. kana Yace naxama katangarka....... KAMAL xaiyi magana wayan Mustafa tayi qara Nan ya 'dauka yana cewa ganinan. Yamiqe. Bari naje gun doctoh ANAS in ka6i Abu Toh KAMAL Yace mai Sannan yafita. Bu'de ido LABEEBAH tayi karab suka ha'da ido da KAMAL Cikin sauri tajuyar da fuskarta Dam xuciyar KAMAL tabuga. Shiya rasa dalilin dayasa yake tsintar fa'duwar gabah da xaran ya ha'da ido da ita Sannu MATAR KAMAL Allah yabaki lafiya Yace da ita Daqer ta iya furta Kalmar AmEEn. Shima ahankali Badan kunnansa sun kafa dukar 'daukar duk wata bagana tataba da baxaiji metace bah Itako LABEEBAH kuka take mara sauti dan yanxu ko magana KAMAL yayi da ita ko da wani tofah ji take tana mata yawi ajikinta kamar yanda jininta ke yawo ajikinta Wannan wane irin soyayya takema KAMAL wacce takeji aranta duk duniya baxata ta6a Aure bah har sai tasamu me yanayin KAMAL da Komai nasa. Wannan alqawari ta'daukarma xuciyarta. Ya kikayi shuru KAMAL Yace da ita Aiko kamar jira take tarushe da kuka. Ba taso yadinga mata magana da sanyin muryar nan nashi hakan na haifar mata da mutuwar jiki da taso mata da MASIFAR SOON shi Ayya sorry qanwata insha Allah xakiji sauqi kinji Shuru tayi Shima bai qara magana bah ya ha'da mata tie kakkaura. Tashi kisha Banajin yunwa Wannan xai temaka miki wajan saka maganin daxaki Sha yanxu yayi aiki yanda yadace Dan Allah Ya KAMAL kabarni haka banajin yunwa Xako muyi fa'da dake Wlhi. in baki shabah toh Xan Sha tafa'da Cikin wani yanayi me saka namiji jin wani filing Tajuyo ahankali tare da tashi Amma Sam batayi gigin kallansa bah takar6a Ka'dan ka'dan takesha. KAMAL nabinta da kallo Cikin sha'awa Suna Cikin haka Usman ya shigo shida XARAH Cikin farin ciki Usman Yace a jiki yayi kyau. XARAH Tace mekabata haka Yakalleta da Murmushi baice Komai LABEEBAH Tace Naji Sauqi Ya Usman mutafi gida KAMAL yawaro ido Yace ina. aisai gobe. Taturo baki dasan yin kuka Tace naji Sauqi fah Abin yabashi sha'awa yanasan mace 'yar shagwa6a me yanayin yarinta shiyasa yakejin wani yanayi idan Aisha-Labibah na magana kodako badashi bane Yace plx kibari sai gobe a sallameki Him um kakasheni kenan da salanka tace aranta Afili ko kuka tafashe dashi Usman yace aa yi hakuri yau xamu tafi Dan Allah Ya Usman mutafi Wlhi baxan kwana ba Tafa'da da miqewa Toh shikenan bara inkar6ar muku sallama KAMAL Yace tare da ficcewa. XARAH ta harare tah Wlhi muka koma gidah kika damemu da ciki na ciwo sai kinsha mari Yan zune dariya taxoma LABEEBAH Tace gaskiya kin rainani kidinga tuna cewa awa uku kikaban a aihuwa Ko minti 'daya nabaki nice dai sama dake. Kuma dole idan kikayi lefi inmiki hukunci LABEEBAH Tace hmm kibari nasamu sauqi sosai bakina yabu'de kisha mamaki Murmushi Usman yayi Yace XARAH dasan girma LABEEBAH da tsiwa da surutu. Nidai inasan caftarnan taku KAMAL ne ya shigo hannunshi 'dauke da magunguna. Yace muje angama Komai Usman Yace sannu fah da qoqari Allah yabiya Yace no karka damu Yace Ni Kasuwa ma Xan hucce KAMAL Tace toh sukayi masa baha Amota ne KAMAL yasamu damar da Yace qanwata ki temaken XARAH taxama tawa nan kusa gabanta LABEEBAH ya fa'da Cikin rawar murya Tace haba Ya KAMAL ai XARAH takace Yace a ina....... Cewa fah tayi baxata auran bah har sai kin fitoh da Miji ayi tare Da sauri LABEEBAH takalli XARAH Tace me hakan yake nufi Tab xaki danqare dan Wlhi baxanyi aurebah har sai naga KAMAL Baki da hankali. Wai har sai yaushe xaki gane Annabi yakafu. a ina xakiga KAMAL. kinga malama inxaki tsaya kigane hanyar me 6ellewa toh kitsaya kifitar da wani KAMAL aranki dan baisan kinayiba. Kitsaya kixa6i 'daya daga Cikin Masu sanki muyi Aure tare. Dan baxan iya yin Aure nabarki bah XARAH CE me wannan furucin Cikin 6acin rai Nayima xuciyata alqawarin baxan ta6a Aure ba. har sai nasamu me yanayin KAMAL Me qamshinsa me muryarsa Kada san rai yasaki cutar da Ya KAMAL kibashi dama ya turo maga batansa LABEEBAH nafa'din haka tayi yunkurin fitta daga motar KAMAL Wanda yayi faking 'dinta yanxu dai-dai kofar gidan nasu...... KAMAL Yace gud qanwata yanxu ke my luv saiki sakemin Mara inyi futsari tunda wacce kikayi furucin dominta tabaki dama. Cikin yanayin tausayin LABEEBAH XARAH Tace shikenan Allah ya tabbatar da alkairi Dai-dai nan LABEEBAH tasaka kanta Cikin gidansu xuciyarta na bugawa Tana shiga taci karo da mamah. Cike da mamaki mamah tasaki kayan hannunta tarungumeta Tace yanxu muke shirin tahowa da innanku ashe jikin da sauqi ke dawa kuka tawo Cikin shagwa6a LABEEBAH Tace naji Sauqi dan farkawa nayi kawai najini garau. Nida XARAH da KAMAL ne Cikin farin ciki mamah tajata xuwa 'daki sun xauna kenan Innah tashigo da farin ciki Tace eh gaskiyane jiki yayi kyau. Mamah Tace kinganta nan muna qoqarin xuwa saigasu Tace aikowa jiki yayi kyau kome suka bata oho...... XARAH CE tashigo da magunguna ahannunta Tace gashi injishi wai dan Allah kidaure kisha zakiga Komai arubuce Tace toh takar6a Mamah Tace Allah ya saka mishi da alkairi. Duk sukace AmEEn Kwana biyu ta warware dan kam batayi sawa dashan magungunan bah Mustafah Yaxo ga LABEEBAH da gaskiyar xan cansa nasan Auranta Amma tarufe ido Tace bata san shi. Abinda ya baqanta ran XARAH kenan har tace ixuwa yanxu nafara tsanar KAMAL 'dinnan ke nama tsaneshi Cikin 6acin ran meyasa xatace tatsaneshi LABEEBAH Tace dama kindena dan abin sanki ne KAMAL ya turo da magabatansa ga Mahaifin XARAH kuma sunyi bincike sun tabbatar KAMAL daga gidan mutunci yafito Dan haka take Su manyan suka bada sadaki da saka ranah nanda wata takwas. Asha biki KAMAL da Auwal a kofar gidansu XARAH. Fa'di Auwal yake plx kakira 'daya daga cikinsu mana lokaci na tafiya. KAMAL yayi Murmushi toh agogo sarkin aiki. Inban mantaba yanxu muka dawo daga wajan siya musu waya koka mantane Auwal ya dafe goshi Yace ya Allah Wlhi namanta shaff... Bai qarasa furucinsa bah Su XARAH suka fitoh Sunyi kyau sosai Cikin shigar dogayan riguna kamar kasacesu kagudu _Zuciyar Auwal fa'di take sarki ya tabbata daga Allah yake LABEEBAH sarauniyar kyawawa. shidai gani yake Aisha-Labibah tafi Fatima-zarah kyau Yayinda xuciyar KAMAL take qaryata hakan danta shagaltu da soyayyar TEEMANSA_ Tatuqi yake Cikin gwanin cewa Ga wayoyunku 'yan gatan KAMAL. Auwal yafa'di hakan da dariya Suma dariyar sukayi Wayoyin sunyi kyau duk *LG* ne kuma iri 'daya Cikin farin ciki sukamai godiya Yace no karku damu XARAH takashe mai ido 'daya da cewa Kanaji damu my luv gaskiya inajin da'din hakan Allah yabarni da sahibina Kunfi haka TEEMANAH kuma inbanji da kuba dawa xanji Kinkasance masoyiyata abin alfaharina ina sanki TEEMAH plx kiqara sonah Nayi rantsuwa xan soka har qarashen rayuwata Xan kyautata maka har sai kace ya'isa Xan bika har qarshen numfashina. Amma inajin tsoron kar wata rana kaqini kaso wata ka wulaqantani.......... Parking yayi a Cikin gidan kakarsa inda dama sunxo gaisheta ne kallanta yayi Cikin kulawa tare da kafeta da wani mirgi 'dad'dan kallo Yace xuciyata tacika dam da qaunarki. bawata *'YA* *MACE* daxanso bayanki Karkiyi kokwanto balle shakka. kisaka axuciyarki narike miki alkawari dan Allah kiyarda dani sannan kicire xargin... hakan axuciyarki Itama Cikin nata kalan kallan takalleshi Tace karka damu ko 'daya baxargi acikin xuciyata. nayarda dakai sosai Da wani shegen kallo Yace Allah yabarni dake Sam KAMAL-da XARAH sun manta da LABEEBAH da Auwal acikin motar sukaci gaba da hirar soyayyarsu Ixuwa lokacin ko LABEEBAH takai maqura dan haka batasan lokacin data da qarqare ba. Ta fashe da kuka tana rayawa aranta KAMAL da XARAH xasu kasheta kwananta beqareba Nan suka farga da inda suke. Cikin mamaki da Al'ajabi Su uku sukace lafiya LABEEBAH me ya faru Cikin kuka sosai ha'de da shagwa6a Tace kai... Nane.... Yake... Min ciwo.. Muyi sauri mukoma gida KAMAL ya kalli Auwal shima Auwal 'din kallansa yayi Yace my TEEMAH haka MATAR KAMAL ta ke XARAH tajah numfashi Tace hmm haka take da shegen shagwa6a musamman agun mamah da innah. Kai ga kowama na gidanmu Amma nalura ha'duwarta da KAMAL yaqara ta6ara mana ita Auwal Yace ikwan Allah kenan. toh yi shuru yanxu xamu koma Cikin wani yanayi KAMAL yamiqa mata hankicif Yace sorry ko. Ga wannan ki goge fiskarki Kar6a tayi tagoge fuskar tata tana cewa a _axuciyarta ko Ba komai dai na katsemuku soyayyarku 'yan rainin hankali_ Haka suka fitoh Suna

Chapter 3 of 22