Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tsorata Tace waifah aunty XARAH CE tace tanasan ganin Aunty LABEEBAH shine yaxo 'daukarta yakai mata ita Atare suka sauke ajiyar xuciya LABEEBAH ko tunda Sumayya ta ambaci KAMAL jikinta yamutu. Tuni xuciyarta takwa'daitu dasan taganshi Dan haka dasauri tafa'da 'daki tahau shiryawa. Mamah na cewa kiyi sauri karki barshi yagaji da jira danke shirinki daban yake dana mutane Innah tayi dariya Tace ai AISHA akwai da'dewa wanjan fante fanten fuska yanxu bari kiga tafitoh tamkar sarauniya xata xama Wata jar shadda tasa riga da siket 'dinkin ya kar6i jikinta dan ba qaramin kyau tayi bah Tasaka gyalanta mekyau da takalminta me'dan tudu 'Daurinta irinna wayayyun matan nanne watoh ture kaga tsiya. Sai xubah qamshi take. Sumayya Tace kai Amma fah kinyi kyau bah 'dan ka'dan bah Tace Nagode Haka tafitoh tayima Su Innah sallama tafitta Tunda tafitoh idan KAMAL yake kanta har ta'dan duqa tagaisheshi bai 'dauke idansa akanta bah Bayan tashiga motarne sunfara tafiya Yace kinyi kyau sosai. Ji tayi wani da'di yacika xuciyarta Tace Nagode _Nagode_ ya akwai kwayi muryarta. Duk sukayi dariya Tace inafatan 'Yar uwata tana lafiya Yace ina kika ta6agin aikai amarya 'dakin mijinta da kwana 'daya ace lafiyarta qalau Cikin tsoro LABEEBAH tawaro ido hankalinta a'dan tashe Tace toh me yasa meta Ka'dan yarage KAMAL bai fashe da dariya ba Yace nima ban sani bah Taturo baki gabah. qiris take jira ta6arke da kuka Tace dan Allah dan Annabi Ya KAMAL kagayamin me yasa meta hankalina ya tashi me yafaru da ita. Taqarashe maganar dasan fashewa da kuka Tamkar ya ankare yayi saurin cewa wasafah nake miki karkimin kuka kisani ka'de mutane dan rikicewa Jan ajiyar xuciya tayi tare da sake fuskartata Tace harnaji dadi Da Murmushi ya kalleta baice komaiba. Itama shuru tayi tana jin farin ciki aranta yanda take shaqar qamshinsa ahaka suka isa gidan Yana faking ta ficce da sauri dan ganin XARANTA Murmushi KAMAL yayi yajuya motarsa ya qara ficcewa XARAH ko na kwance nan na'de agado. 'dan ciwan Kaine yake damunta kuma KAMAL yabata magani Amma ciwan bai barta bah Ganin LABEEBAH yasata miqewa da sauri ta rungumeta Tace Ashe haka Aure yake LABEEBAH Ashe KAMAL mugune Mara tausayi saita fashe da kuka Yayinda hakalin labeebah ya tashi cikin wani hali Tace meya faru fa'damin dan Allah Nan XARAH tagaya mata yamata kaca kaca narashin tausayi sam bai mata da Sauqi bah. dan haka baxata qara yarda dashi ba Yanxu LABEEBAH tagane Komai tadinga lallashinta da nuna mata hakkin shine dole tayarda dashi inba hakabah taha'du da tsinuwar mala'iku Daqer dai da si'din goshi LABEEBAH tashawo kanta Dan haka XARAH tasake har tanemi ciwan kan tarasa LABEEBAH Tace kinje kin gaida Momyn shi da kakah XARAH Tace eh kai tare dashi mukaje Bakiga yanda suka kar6eni bah Wlhi Cikin farin ciki da kulawa LABEEBAH Tace gud hakan yayi kyau yanxu akwai abinda Xan miki ne Tace ba Komai dama wanke kayan da mukayi breakfast ne 'daxo kuma qanwarshi Safna tayimin sai nayi shara kawai LABEEBAH Tace yanxu dai ba wani aiki Tace eh kam babu.......... Sallama sukaji anatayi dan haka LABEEBAH taleqa. Safna CE da Sagna Cikin fara'a Tace la Sannunku kushigo Nan suka shiga. Sagna taxauna gefan gado yayinda Safna take tsaye suka gaishesu XARAH da LABEEBAH suka amsa da kulawa Sagna sai wani 'daure fuska take wai adole batasan LABEEBAH da XARAH surainata dan taga ba wasu masu shi bane Ita ko LABEEBAH tanace saita kula Sagna tun Sagnan na sharewa hardai tasake da LABEEBAH Safna ko ba ruwanta dan bata nuna musu Komai bah Ganin haka yasa XARAH tafi sakewa da ita Safna Haka suka dinga hira abinsu can suka tafi XARAH takalli LABEEBAH Tace nalura Sagna 'yar jin kaice. LABEEBAH tawaro ido Tace kai habah ni ban gani bah Tace Allah Safna tafita sauqin kai LABEEBAH tata6e baki Tace tun yanxu kin fara qorafi. kimata uxiri ila wani abunne yake damunta ne XARAH tajah tsaki Tace bawani ni bana san rai nine Shuru LABEEBAH tayi dan tasan XARAH sarai basan raini takeba toh koya xasu Kaya da Sagna oho Natuna gobe xaku Yola ko. XARAH tatambayi LABEEBAH Eh Amma nida Innah da Ya Usman saijibi xaimu. Tace-da'ita Allah ya kaimu naso aje dani. XARAH taqara fa'din hakan LABEEBAH tatashi tayafah gyalanta Tace Allah baiyi ba toh. Ki xauna a'dakinki mungode. Barah naje nagaidaisu kakah daga nan saina wacce tashi muje Kamar XARAH xatayi kukah Tace haba dan Allah tafiya yanxu LABEEBAH Tace xanjefah gidan Aunty Zainab Kinsan ta kuma dasa mutum aiki bai xama Lalle tabarni nakoma gida da wuribah taqarashe maganar da ficcewa nan tabita tana cewa da wannan dan wannan A harabar gidanta XARAH tatsaya yayinda LABEEBAH tashige shashin su kakah Tako same ta afalo taje kusa da ita tagaisheta. kakah tadafa kanta ta'amsa Cikin farin ciki Kana Tatashi tamata sallama xata fitone kakar tace ga momynku na wanka dakun gaisa LABEEBAH tayi murmushi Tace LA Bakomai agaisheta Tace toh xataji Nagode sosai 'Yar kirki Murmushi tayi tafito XARAH Tace toh kigai shemin dasu mamah kice xanxo da daddare. LABEEBAH ta harareta Tace agarin jakuna xakixo ko XARAH Tace Allah da gaske LABEEBAH Tace hmm ba mamaki kam dan naga xafin luv 'din jiya bai barki bah. Tana fa'din haka taficce tana dariya tare da qarawa da cewa Allah yasa yauma ya qara Sanda gaban XARAH yafa'di Tace ta Allah ba takiba LABEEBAH taje gidan Zainab bata sameta bah Akan han yarta taxuwa gidane taga wani makawo da alama yanasan atsallakar dashi titine dan haka taje takama hannunsa ta tsallakar dashi yanata samata albarka Tace ya Isa godiyar haka Babah tabu'de jakarta tabashi laira 'dari biyun da takesan hawa adai-daita sahu tabashi Sannan tayi gaba abinta duk abinda ya faru akan idan KAMAL ya faru dan danja na tsaida shi ya xuge gilashin motar tasa dan yaga kamar LABEEBAH yako tabbatar da ita 'dince. Ahaka yaga abinda yafaru. Itako LABEEBAH Sam bata gansa bah haka kawai takesan tafiyar qafah yau dan sai tafiyarta take hankali kwance Cikin nutsuwa Jimana 'yan mata KAMAL yace da ita Cak tatsaya dan har abada muryar KAMAL baxata ta6a 6ace mata bah Ahankali tajuyo ta xuba mai ido. Ya 'daga mata gira da cewa kin tsaya kina kallona kina 6atamin lokaci kixo mu tafiko Murmushi tayi tabu'de motar tashiga Sannan takulle Tace barka da yamma. Batare da ya kalleta bah Yace Barka dai da fatan kinsha tafiyar qafah lafiya Lau Tace dashi Meyasa baki bari nadawo na maidake gidaba Tace dan xanje gidan yayana ne shiyasa kuma mah ai bai can canta nasaka wahala bah Xan can ki bai gamsar daniba nafi yarda da kawai kina sanne ko xakiga KAMAL 'dinki. Dan in amota ne ko mashin bai xama lalle Ki gan sabah. Ya qarashe da kallanta Murmushi tayi Tace lallema Ya KAMAL waya gayama. Yace aiba sai angaya min bah gani nayi a kwayar idanki Lalle ko idan nawa ya nuna maka qarya Tace da shi Ko ya bata amsa Da sjagwa6a Tace Allah da gaske Ganin xata fara yimishi shagwa6a yasashi batar da xancan da cewa Yauwa namanta Auwal Yace min am muku rasuwa wai gobe xaku mah Yola ko Tace eh Allah yaji qansa ya gafarta masa Tace AmEEn Nagode sosai Batare da ya amsa godiyarta ba Yace In tambayeki man Kallansa tayi Tace Allah yasa nasani Faking yayi a kofar gidan nasu ya kalleta Yace meyasa muryarki take yimin da'di A'dan tsorace ta kalleshi Tace banji bah Yace nasan kinjini Inasan muryarki Laveeva. Wanda idan kina magana banasan kidena. Ya qatashe da sanyin murya da kuma jefah mata wani shu'umin kallan da yasa jikinta mutuwa lokaci 'daya. Batare da yasan ya mata shibah Cikin wani yanayi Tace nima ban sani bah. _nima ban sani bah_ shima yafa'da da kwai kwayan muryarta ashagwa6e Dariya tayi Tace Allah Ya KAMAL kadena bana so tafa'da a shagwa6en Ni kuma inaso. Ya bata amsa tare da kafeta da ido Ya salam LABEEBAH Tace axuciyarta wannan mutumin nasan kasheta lokacinta baiyi bah Jan yo duk wata jarumta tata tayi wacce tarasata yanxu Tace toh ka gai shemin da XARAH tafa'da dasan ficcewa Yayi saurin cewa baxan fa'daba. Tajuyo da kallan sa Tace meyasa. Yace saboda ban gama jin muryarki bah. Tace toh aikai ba KAMAL 'dina bane kai KAMAL 'din XARAH ne. Kamar yanda Komai namu yaxo 'daya ni da ita haka mah muryo yunmu 'daya ne Yayi Murmushi dan ya raina wayanta Yace hmm ai XARAH tafiki da'din murya idan tana magana bawanda yake gajiya da ita wasa nake miki bakida da'din murya Aiko tarkwanshi ya 'danu dan turo baki tayi kamar xatayi kuka Tace toh ina ruwana koma tafini ai nida ita 'daya. Taqarashe da harararsa Gimtse dariyarsa yayi Yace To miye na turomin baki kamar xakiyimin kuka in hakan ne me yasaki 6ata fuska Harararsa tayi taficce daga motar sanda takai 'kofar gidan nasune tajuyo ta kallesa Shiko ya 'daga mata hannu anamar bye bye.... Gya'da mai kai tayi kana tashige gida Shiko ya jah motarsa xuciyarsa na tuno mishi da ita Yayi gidansa gun XARAN Sa LABEEBAH ko bata samu kowa a tsakar gida ba. dan haka Cikin san'da tashige 'dakinta da kwantawa kan yaloliyar katifarta dan bataso wani ya katse mata tunanin da xakeyi yanxu.. Nu tsuwa tayi sosai tana tunanin KAMAL. Meyasa Yace mata yanajin da'din muryarta. Ita harwata murya me da'di take da ita Ajema a haka. Amma kallan da yake mata fah. Yayi kama da wanda yake yima XARAH Idan ko hakane me yake nufi Shuru tayi tana neman amsa Amma kaf tunaninta yakasa bata amsar Mararta ce ta'dan mur'da mata Cikin tsoro tatashi xaune tana ta6a marar tana kuma xaro ido Jiki asanyaye tafara lissafin yau kwananta talatin Wato dai al'adarta CE xataxo mamah Kuka tafara tana kiran sunan Allah yau kuma wahalarta taxo kenan Cikin sauri talalli gyfanta inda take ajiye magungunan da KAMAL yake kawo mata duk qarshan wata tabu'de tana addu'ar Allah yasa akwai saura Addu'arta taci dan taga sauran sha 'daya Dan haka ta6alle jiki na rawa rawatsa a baki takora da ruwa Sannan takwanta tana addu'ar Allah yasa karta Sha wahala a ciwan Da haka bacci ya 'daketa me tattare da mafarkin KAMAL Kiran sallar magriba ne ya tasheta tana tashin taga ko al'adar taxo mata fitowa tayi tsakar gida mamah da take alwala takalleta da mamaki. Yaushe kika dawo Tace 'daxo Amma banji shigowarki bah Eh nadawo agajiyene kuma ban ganki a tsakar gida bah shiyasa nashige 'daki na kwanta Amma ko kinada shirme har Sumayya tashigo Nace baki dawoba Yi hakuri toh mamah Nayi toh. Mamah tabata amsa Cikin murmusawa. Tare da cewa ya XARAH Tace lafiyanta qalau tacema agaisheku Muna amsawa Zainab fah Naje na same ta bata nan Toh ba damuwa mijinta xaixo an jima ai LABEEBAH tagyara tsayuwa Tace A kwai wani abunda Xan miki ne aa je kiyi wanka kiyo alwala kiyi Sallah na gama Komai Tace ina fashi 'daxo yaxo Gaban mamah yafa'di cikin tsoro Tace yaxo 'daxo fah kikace Tace eh na'danji ciwan ka'dan 'daxo Shuru mamah tayi taqarasa alwalarta tana addu'ar Allah yasa karya wahalar mata da ita LABEEBAH ko bayi tayi ta tsaf tace jikinta tsaf tayi wanka Sannan tadawo 'daki. Bayan tasaka kayane Sumayya tashigo Tace yanxu kika dawo Tace aa tun 'daxo Amma bacci nayi mamah mah batasan nadawo ba. Wai harkin shigo tace miki ban dawo bah ko Eh hakane ya Aunty XARAH dai Lpy yanta qalau tanamah gaisheki Ina amsawa Sumayya tace LABEEBAH tace 'danjeki kicin ki ibo mana abinci dan Allah Tace toh Bayan sunci abincinne ne Suleiman da Usman suka shigo tagai dasu Tace mah Suleiman Yayah naje gidanka 'daxo Aunty Zainab batanan ai Yace eh wai taje suna ne Tace aiko........ wayarta CE tayi qara. Koda taduba sai taga Jameel ne. da 6acin rai a fuskarta ta'dauka da sallama Yace ran gimbiyata ya da'de dafatan xan sami ganinki yanxu ina kofar gidanku Shuru tayi. Yace dan Allah karki qi fitowa Wlhi xuciyata xata iya bugawa. Tausayinsa ne ya kamata dan har abada baxata so shiba KAMAL ne aranta Tace toh ganinan takashe wayan. Qara feshe jikinta da turare tayi Sannan tagayama mamah tafitta Jameel ya runtse ido Yace qamshin kine ya sanar dani xuwanki gimbiyata. Tace Hmmm toh Barka da dare Yace barka da fatan nasa meki lpy Tace lafiya lau nake ya har kokin yau da kullun Yace lafiya Amma akan soyayyarki Wlhi bana cikin lafiya Tace toh naji yanxu me ya kawoka Yace idan masoyi yaxo gun budurwa me yake akawo shi gunta SOO Tabashi amsa Cikin sauri Yace toh nima so ne ya kawoni. Shuru tayi. Shima shurun yayi Can takatse shurun da cewa banaso na yaudare ka. kayi hakuri kanemi wata dan Allah Yace LABEEBAH kenan tsoran mekike Plx kibani dama in shiga birnin xuciyarki in saka miki qaunata. Na miki alqarin saikin manta da wani KAMAL Ina San KAMAL so na haqiqa Baxan iya ha'da sanshi dana kowa bah Kadena ha'da kanka dashi Wlhi xuciyata tayi nisa a soyayyarsa Son sah ya xamemin MASEEFAR SOO Banasan mu gina rayuwarmu nida kai ta farnin yaudara Plx dan Allah ba danni bah ka hakura dani. LABEEBAH Tace dashi hakan Yayi Murmushi yace idan na hakura dake inyi yaya kenan Gaskiya baxan iyaba Idan har kika bani dama. Nagaya miki saikin soni fiye da KAMAL din Toh wai waye shi Sanin koshi waye bashine abu me mahimmanci agareka bah Rabuwa dani shine yafi dacewa dakai Kaina na min ciwo dan haka saida safe. Tace dashi hakan tare da shigewa gida batare da taji cewarsa bah Shima jinjina kai yayi yashige motarsa Yana cewa aransa Wlhi baxan bar kiba Sannan yajah motarsa Ita ko tana shiga gida Bayan taxauna ciwan marah yace salamu'alekum Nan tafara juyi ka'dan ka'dan....... Sumayya ta miqa mata wayarta dacewa ana kiranki Ya KAMAL Da sauri takar6a tana cije baki Yace Me kikeyi Tace banajin da'dine. Yace ya salam dama nakawo miki maganinki ne gani a kofar gida Tace Yauwa nagode dan 'daxuma yaqare Yace shaf na manta kituro wani ya kar6ar miki plx dan bana so yafara wahalar dake Tace ga Sumayya nan Nagode Yace Karki damu. Yana fa'din haka ya kashe wayan Nan tagayama Sumayya takar6o mata Komai arubuce yake dan haka duk tashasu batare da 6ata lokaci bah Cikin ikwan Allah ko. Ko rabin awah bata yibah taji ciwan ya'dan 'dauke Mamah Tace Allah yasakama KAMAL da alkairi tunda yasan ciwan nannata baita6a mantawa da kwanakin watanba Sumayya Tace AmEEn ai Yana kirki sosai Shuru LABEEBAH tayi dan qara son shi take ba'dan ka'dan bah Da gaske dai ciwan bai takura mah LABEEBAH kamar yanda yasaba bah. Tayi dai baccin nutsuwa. Yayinda abin ya kasance ga KAMAL ba haka bah Yana rungume da Matarsa XARAH wacce ta amince ne da hakan idan baxai mata Komai bah. Yayi Murmushi Yace habah my TEEMAH wannan fah hakkinane Naji dai baxan miki Komai bah shikenan. Ta'dagamai kai Nan ya jawota jikinsa Yana shafata har tayi bacci. _Toh nashi baccin ne yaga wasu kyawawan yara sunkai 6 awajan shaqatawa_ _Gyefansu LABEEBAH CE tana danna laptop tana hawaye ya shigo gun_ _Yaran sukaxo da gudu suka rungumeshi Cikin farinci da annushuwa suke. Hakama shi_ _Nan ya dinga sumbatarsu yana godiya ga Allah daya bashisu_ _Can ya kalli LABEEBAH Yace me kike ganine a laptop 'din_ _'Daya da ga Cikin yaran Tace Dady hotan nan take kallo meyasa Momy take santa_ _Bayan ita kuma bata Santa tunda ta iya tafiya tabarta_ _Yayi Murmushi ya shafi fuskar yarinyar Yace qaddarace yasata barinmu_ _Tace qaddara menene qaddara_ _Yace o momyna kincika tambaya jeku qarasa wasanku_ _duk suka sakeshi suka koma gun wasansu_ _Shi kuma yaxo gunta yana kallan fuskar laptop din_ _XARAH yagani_ _Sai kawai ya rufe laptop din yamaida kallansa kanta Yace nagaji da hanaki kuka akanta_ _kuma nafa tunanin saita kaiki wutta akan na._ _agigice takalle shi yako gya'da mata kai_ _Cikin kuka Tace kayi hakuri dan Allah_ _Ya ta6e baki Yace ai kullun a hakuri nake dauke._ _yanxu dai tashi Ki kula dani nadawo da MASEEFAR SONKI_ _gya'da kai tayi ya rungumeta Cikin so da qauna_.......... Agigice KAMAL ya farka daga wannan mafarki. Yayi shuru Ayanda dai ya gansa da LABEEBAH ba shakka matarsa ce. Toh ya abin xai kasance innalillahi-wa'inna'ilaihirraji'un me xai faru dani ni KAMAL Abaiyane Yaketa furta cewa LABEEBAH LABEEBAH LABEEBAH Cikin mamaki XARAH data farka tace metayi metayi my luv menene Cikin murmushin yaqe Yace Bakomai Tace ban yarda bah ka gayamin menene dan Allah Xuba mata ido yayi na minti 'daya kana Yace mafarki kikeyi shine naji kina ambatar LABEEBAH Shine nima na furta hakan kikaji Dafatan dai ba mugun mafarki kikayiba Tayi Murmushi Tace tab Ni Wlhi ban san ma ina ambatar sunantaba Kuma kasan wani abu. Ya girgixa mata kai alamar a'a Taci gabah. bana mafarki kuma koma nayi mantawa nake dan Wlhi yanxuma bansan nayi mafarkinta bama harnake ambatarta Yace hakane Allah yasa mudace Tace AmEEn Sannan yatashi yayi Alwala yayi Sallah raka'a goma Sha biyu ya ruqi Allah akan ya bashi haske akan lamarin shi da LABEEBAH ya kuma bashi fahimtar abunda yake faruwa ya kuma sah albarka acikin lamarin. Washe gari ko mamah da Malam Sanih da Suleiman da Matarsa Zainab da yaranta kaf suka loloqa birnin Yalo 😭😭😭😭😭😭😭 Hatsarin ya faru ne lokacin da motarsu take gaf da shiga Yola Rai yayi halinsa Dan wata babbar motace tabugi tasu motar nan take takama da wuta Amma anyi nasarar fitar dasu. Saidai inba kasansu ba. Baxaka ganesu bah Toh Malam Sanih da mamah da Suleiman da Zainab da yaranta kaf duk sun rasu rai yayi halinsa Harda wasu tsirarru da direban motar Wani ne yalura da wayar da take jikin Malam sani shine ya 'dauka duk da ta 'kone Amma haka yacire sim 'din yasa a wayarsa Nan sunan mutane takwas ya baiyana Wato innansu LABEEBAH KAMAL XARAH Suleiman Usman Malam Sallau Bashir Sai kawai ya tsinci kansa da kiran KAMAL Amma har tagama ringing ba'a'dauka bah Dan haka sai yakira Malam Sallau ringing 'daya ya'dauka yanacewa kunsauka lafiya Mutumin Yace kayi hakuri bawan Allah Amma rai yayi halinsa kaf Cikin motar sun mace sakamakwan hatsarin daya afku dasu Suna daf da shiga Yalo............... Kasan cewar wayar tashi baji yake bah dan haka yaqara volume tunda ya 'daga wayan Toh dama Innah na gyefanshi a tsaye tanajin komai Dan haka da mutumin yagama xancan atare suka xu6e qasa. Inna ta sume yayinda shi kuma yaxuma mata ido hankalinsa amatuqar tashe ya fito daga wanka kenan yaga wayan tashi da miss call sai yaji gabansa ya fa'di ganin BABA 2 watoh mahaifin LABEEBAH dan haka da sauri yakira number Yana cewa BABA Barka da safiya Murumin daya 'dauka Yace Bashi bane tare da gaya mishi hatsarin daya faru 😳Iya gigicewa KAMAL ya gigice Yace what kana nufin sun mutu gabaki 'daya Cike da tabbaci mutumin ya bashi amsa ha'di da rarrashi. Dai-dai nan XARAH tashigo 'dakin ganinshi hankali tashe ga waya akunne yasata kafeshi da ido Tace yadai naganka haka lafiya. Sake wayar tasa yayi a qasa tabi wayan da kallo shima yabi wayan da kallo. Atare kuma suka kalli junansu . Shuru nawani 'dan lokaci Suke kallan junan nasu. Can dai XARAH ta'aro jarumta taje ta'dauki wayar tashi tasa a gado Tace my luv ka........ Yayi saurin katseta da cewa Karki tambayeni plx👏🏻 Tace meyasa Yace Hakka kawai Tace OK dama naxo gaya maka ne anturo mana da abinci nd is so delicious Yace dat is luvly I will be wit u in a short while. Tace OK. Sai tafuta Shuru KAMAL yayi Yana Cikin furgicin lamarin. Xama yayi gyefan gado yana tunani ya'da kansa yakalli agogo ya nuna mishi 6:00pm Can kamar an muntsineshi yatashi Cikin sauri ya kasa kayansa ha'de da 'daukar wayarsa da keey 'din motarsa yafito falan Nan yaganta a dining

Chapter 6 of 22