Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tana danna wayarta Yace sam banajin yunwa yanxu. Ya fa'da yana me duban agogon hannunsa Tace toh yanxu dai idan nagane xancanka baxa cibah yanxu. Yace eh xan dawo yanxu. Tace my luv Yace My TEEMAH. Tace plx kaxauna kaci yanxu. Inba hakaba hankaliba baxai kwanta bah. Bai yi musu bah ya xauna tatashi ta ha'da masa Komai Sannan tatura masa gabansa Nan ya fara Cin ka'dan ka'dan har dai talura Yana cine kamar ansashi dole Tace akwai damuwa fah my luv. A 'dan tsorace Yace me yafaru Tace tunda natashi nake jina wani iri bansan da liliba Yace hmm ki kwantar da hankalinki Bakomai Tace toh Allah yasa Shuru yama batare da ya amsa bah saima tashi da yayi Yace toh bari naje na duba Momy dan gobe xata tafi tashima muje. Yafa'da yana mai kama hannunta Hakako suka shiga falan kakah. Nan suka tarar da Momy afalan Itada kakah Suna tattaunawa Cikin farin ciki ta tarbi XARAH Tace madallah da 'yata datakai yammaci lafiya Cikin jin kunya XARAH ta gaishesu Suka amsa da kulawa Tace gobe Xan bar muku garinku XARAH Tace karki tafi Momy Tace tofah Karki damu Bayan baifi kuma kuyi sati biyu bama kuxo garemu XARAH ta sunkuyar dakai tana wasa da xoban hannunta Kakah Tace sutafi nikuma naxauna da suwa Momy tayi Murmushi Tace kwantar da hankalinki kakah ai KAMAL da XARAH duk nakine Bawanda ya isa kwace miki su Tace atoh ina murna gasu gani kuma Su tafi subarni KAMAL yayi Murmushi yaqe dan yasan futunan tsohuwar tasu xaisha famah da ita kafin ya koma abujah Safna CE ta shigo tana cewa barka da Safiya Aunty XARAH XARAH Tace barka Safna kintashi lafiya Tace lafiya qalau dan Allah kin iya kitso kimin XARAH tawaro ido Tace dama LABEEBAH CE ta'iya sosai Amma ba bamuwa na'iya kumbushe muje inmiki Kakah da Momy sukayi dariya kakah Tace ba'asa amarya aiki fah Safna taturo baki Tace kai kakah Momy tayi Murmushi Safna ko kama hannun XARAH tayi tana cewa muje shashinki Aunty kimin XARAH Tace toh suka fitta Da kallo KAMAL yabisu dan tunda XARAH ta'ambaci LABEEBAH hankalinsa ya kuma tashi Nan ya gyara xama suka gaisa da Momy da kakah kana suka xanta Daga nan ya gaya musu rashin da LABEEBAH tayi Suma iya furgici sun furgita Nan Momy takira dadynshi Tace xata gidan rasuwa nan tadawo Sannan talalli kakah Tace tausayin yarinyar nan ya kamani sosai tunda naganta rainan tashiga raina Kakah ta numfasa Cikin damuwa Tace Wlhi nima hakah Duk da qafata namin ciwo Amma Xan biki muje KAMAL Yace toh ina mota kusameni Momy Tace toh XARAH tasani. Yace aa ban gaya mata bah Kakah Tace gwara da baka fa'da mata bah _Mai yasa naganki Cikin damuwa haka_. _Mamah tadafah kanta Tace haka kawai nake jina wani iri_ _LABEEBAH takaryar da wiya tace Wlhi mamah tunda kika furta mutuwar nan gabana yake fa'duwa_. _Abin mamaki yanxu nake da'da jin fa'duwar gaban_ _Taqarashe da kwantar da kanta akan ciyar mamah kamar mage_ _Shafah bayanta mamah tahauyi Tace toh kiyi addu'a Allah ya tabbatar da alkairi_ _AmEEn LABEEBAH tace_ _Can mamah tajah numfashi Tace inasan gaya miki wasu abubuwa. Guda biyar duk dako kinsansu_ _Amma Xan qarah tunatar dake_ _Shuru LABEEBAH tayi ganin itama maman shurun tayi_ _LABEEBAH ta'dago da kanta Tace inajinki mamah fa'damin naxaku najisu_ *Tace* _Duk ahalin da kike ciki Karki manta dayin Sallah akan lokaci da bautar ubangijinki_ _Hakan xaisa Allah yaso ki_ _Haka kuma duk halin da kike ciki kika sance me gaskiya da tsoran Allah_. _Gaskiyarki xata jawo miki soyayyar mutane kuma Allah xai 'daukaka darajarki dan Yana tare da masu gaskiya_ _Ki kasance me ladabi da biyayya ga nagaba dake. Hakan xaisa kixauna lafiya da kowa. Dama Kinsan ance bin nagaba bin Allah_ _Ki kasance me yafiya dan Allah nasan mai yafiya haka Ki kasance me hakuri akan Komai_ _Idan Kin samu miji kimishi ladabi da biyayya iyakar gaskiyarki kiso danginshi kamar yanda xakiso naki_ _Cikin wani yanayi LABEEBAH tamaida kanta kan cinyar mamah Tace toh mamah insha Allah Xan riqe duk abinda kikace baxan tsallake ko 'daya ba_ _Cikin Murmushi mamah tadafah kanta Tace Yauwa 'Yar albarka Allah yasa naga auranki da jikokina_ _Rufe ido LABEEBAH tayi alamun kunya tace insha Allah har tatta6e kunnanki saikin gani_ _Tace Allah yasa_ Wannan xancikar LABEEBAH take tunawa Wanda shine qarshan hirarta da mamah da asubah Yanxu haka tana kwance a gadan mamanne tana tuna Xan Cikin da sukayi Jikinta ne ya mutu mu'dus ga wayarta ba caji bare takirasu taji ko sun sauka. Danna wayar tayi wajan makunnar. Aiko Cikin sa'a ta kunnu. Da sauri tafara kiran number Baban nata Amma kash wannan matar me Baqin jini tace baku'di aciki. Da jan tsaki ta'ajiye wayar Can Kamar an mun tsineta Tatashi da sauri da saka hijab 'dinta da niyar zuwa siyan katin tafito 'kofar gida kenan KAMAL yayi faking 'din motarsa da fitowa a 'kofar gidan Sai kuma taga momynshi da kakah sunfitoh Taje garesu da sauri tadurqusa har qasa ta gaishesu Da mamakinta suka amsa gaisuwarta Sannan suka maida kallansu kan KAMAL Yace bata sani ba fah qila Cikin tausayawa atare sukace tabbas ga alama kam LABEEBAH ko duk da talura akanta sukayi furucin gabanta yafa'di Amma tashare tamusu ido gidansu XARAH Malam Sallau suka gani da inna xube aqasa Suna rera kuka Cikin sauri LABEEBAH tayi kan Innah tana cewa lafiya innah meyafaru meya faru dan Allah Cikin kuka Innah talleta saita qara fashewa da kukan. Gaban LABEEBAH yaqara fa'duwa Nan taje ga Malam Sallau Tace Babah menene meya faru. Daqer ya aro jarumta ya tsaida kukansa yace bakomai Tace yaxa'ayi inyarda bayan kuka kuke kuma ban ta6a ganinku hakaba. Tana fa'din hakan tafashe da kuka. KAMAL yayi saurin rintse idanshi tare da ficcewa. Momy ce tajata jikinta tana cewa haba 'yata kwantar da hankalinki ba wani abu bane....... Usman ne yashigo KAMAL na bayansa Kallo 'daya xakama Usman ka tabbatar agigice yake. Idan nan nashi jawur hawaye na xubar masa yace na shiga uku lnnah-Babah munrasa mamah Babah Ya Suleiman Zainab yaranta hatsari hatsari........... Bai gama fa'daba LABEEBAH Tatashi afurgice idanta na samalo qasalo Tace no... no... no... Me yake faruwa ne kufa'damin. Rungumarta Usman yayi yakece da wani mahaukacin kuka Yace keka'dai kika ragemin. mamah da Babah ya Suleiman da Zainab yaranta duk sun mutu keka'daice kika ragemin keka'dai CE yaqara fashewa da kuka Kwace kanta LABEEBAH tayi tafara yin hanyar waje da baya da baya Tace dama maganar da takemin wasiyace dama albarkar da Babah yasa mana qarshen furucinsa gareni kenan. Tana kaiwa nan take talemi xubewa aqasa. Kamar KAMAL ya ankare yayi saurin tarota taxube ajikinsa Cikin yanayin mayen tashin hankalin idanta yafara juyewa Cikin wata siririyar murya Tace Ya KAMAL gaskiyane na rasa iyayena. Ya gya'da mata kai. Aiko nan take numfashinta ya 'dauke cak Agigice yafara ta6a fuskarta Yana cewa laveeba ke laveeba dan Allah kitashi karki bisu plx ki temakan Shuru wai Malam yaci shurwa LABEEBAH ba motsi Cikin tashin hankali yayi saurin kin ki marta yafita da gudu da ita yasata Cikin motah. Saiyayi asibiti da ita Usman mah xubewa yayi Malam Sallau yayi kansa Yayinda Momy tashiga lallashin Innah Kaka ko hawaye kawai take sharewa Haka rayuwa take. yau taxo maka da da'di gobe kuma sa6anin hakan Yau satin LABEEBAH uku a Asibityn Sam. batasan Waye akanta bah. Abin gwanin tausayi Yayinda Innah da Malam Sallau da Usman danginsu zainab suka garya 'da Yola Acan akayi musu wanka da kaisu gidansu na gaskiya Anan akayi bakwai Kana suka dawo gida Makwabta sun girgixa da lamarin kowa sai fa'dan alkairin mamah da Malam Sanih yake mutanan kirki ba kamarsu Kallo 'daya xakama XARAH tabaka sausayi dan kawai LABEEBAH tana kwancene Amma tashin hankali yana gareta Ayanxu Da muwarta 'daya LABEEBAH tatashi Dan kullun tana gaban gadan LABEEBAH tana xub da hawaye KAMAL Yana qoqari sosai wajan ganin ya kwantar da hankalin XARAH Gyefe guda kuma tausayin LABEEBAH na damun xuciyarsa. Gaskiyane kina Cikin jarabta kala kala Mamah da Babah kin rasasu Allah ya dubeki ya baki KAMAL 'dinki. Cewar KAMAL yanxu da yake gaban gadan LABEEBAH daya qura mata ido .Ahankali tabu'de idanta karab suka ha'da ido Sam taqi 'dauke idanta akanshi tana tunanin memah yake damunta meyasa meta meya kawota asibiti me...... KAMAL ya kase mata tunaninta da cewa na gode Allah kintashi laveeba am sorry. Duk merai mamacine karki musu kuka addu'a suke buqata Tuni kwakwalwarta tahau chaji tatuna abinda ya faru. Aiko saita 6arke da kukan tana kiran mamah BABANA wayyo Allah ka dubeni narasa kowa da komai. Na rasa KAMAL badan ya mutu bah Narasa mamah ta mutu baxata dawoba Narasa BABANA ya mutu baxai dawo bah Ya Suleiman ya tafi shi da matarsa harda...... Ya KAMAL karkace karnayi kuka dan ya kasance farillane agareni Sai taqara rushewa da kuka Iya rikicewa KAMAL ya rikice Nan haka ya kamata yana goge mata hawayan Yace bazasu dawoba Ba kuka suke nema agareki bah addu'a suke nemah Dan Allah Ki daure kiyi musu addu'a plzπŸ‘πŸ» Cigaba tayi da kukanta Yana lallashinta Ahaka XARAH da Sumayya suka shigo XARAH ta rungumeta tana tana hawaye tare da gaya mata dadda'dan lafaxuxxuka 🌡🌡🌹🌹🌡🌡 *MASEEFAR SOO* 🌡🌡🌹🌹🌡🌡 *Bayan wata takwas* Bayan wata takwas LABEEBAH ta 'dan murmure kuma sanadinga hakan shine KAMAL Dan koda yaushe ya tare da ita Ganinshi Yana sata nisha'di Tare da qara sanshi Baba zenatu qanwar mamah taso 'dauke LABEEBAH Amma innah tarufe ido da saka mata kuka akan tabar mata ita nawani 'dan lokaci kota tare mata zafin mutuwarsu mamah Haka Innah zinatu ta hakura tabar LABEEBAH ahannunta acewarta nawani 'dan lokaci *maseefar soo* 🌡🌹🌡 An 'daura Auran Usman da Rukayya Haka aka tattaro amarya aka kaita gidansu LABEEBAH dan Malam Sallau cewa yayi ya xaunah agidan dan kar'a barshi haka shuru ba kowa Dan haka Usman ya gyara gidan ya gyara 'dakin LABEEBAH Yace tadawo ciki. Innah taso hanawa Yace dan Allah tayi hakuri bawai yayi hakan da wata manufah bane. aa yayi hakanne dan yadinga kallan LABEEBAN dan ita ka'dai gareshi yanxu tana buqatar kulawarshi Sanda Innah ta zub da hawaye tace toh ba damuwa LABEEBAH CE taketa kwalliya gudu gudu dan gidan XARAH sukesan xuwa itada Sumayya Dake gobe ne Su XARAN xasu cale Abujah gidansu nacan duk da dama so 'daya su XARAN sukaje can'din Rukayya Tace nikam sha'awa kikeban idan kina kwalliya LABEEBAH tayi Murmushi Tace hmm danke bakyayi ko. Kawai Sam kwalliya bata damam bah. Rukayya tace hakan LABEEBAH Tace kar kiyi kitsaya watacan takwace miki Ya Usman Dan 'yan matan yanxu koxasu xauna da datti a gidansu daxaran suntashi fitta tsaftace jikinsu suke da kwalliya tabam mamaki Sumayya Tace hakane Wlhi Wayaga idan Aunty Rukayya lokacin da taga ya Usman da budurwa Dariya LABEEBAH tayi Tace ai idan komawa ciki xaiyi dan ya Usman mijin mace hu'dune....... 'Daka mata duka Rukayya tayi Tace wannan mugun fatan ya qare akanki dan Mijina mijin mace 'dayane har aba'da Sumayya tasheqe da dariya Rukayya ta fusata Tace kekuma meye na dariya LABEEBAH Tace kwantar da hankalinki babbar Aunty mata agun Ya Usman insha Allahu ke ka'daice agunsa Sumayya Tace. Bawata saike da yardar Allah Rukayya tayi Murmushi Tace Wlhi banasan kishiya. Tashi LABEEBAH tayi feshe jikinta da turare tare da yafa gyale sanda tatabbatar sunkai soro itada Sumayya Sannan tajuyo Cikin tsokana Tace kidena tsanarta dan Ya Usman saiya qara uku ba 'daya bah dan haka saka xama da kishiya dole Tashi Rukayya tayi xata bita. Tuni ko Su sun ficce Suna dariya Me adai-daita-sahu ya saukesu a gidan XARAH nan suka bashi ku'dinsa sukayi ciki Da KAMAL sukaci karo a farfajiyar gidan Yace gud MATAR KAMAL yanxu daman xanje gidanku dan tambayan Su Innah dan tare dake zamu ko sati ne kiyi kyaga inda XARAN Ki takeko Tace Amma.......... Yace Amma me plx karki kawomin qauli da ba'adi Takalleshi ya 6allah mata harara Sannan ya maida kallansa kan Sumayya Yace harda kefah Sumayya Tace toh Ya KAMAL Sukayi ciki shi kuma ya ficcewarsa Cike da munar ganinsu XARAH ta rungumi LABEEBAH tana cewa Yauwa hasken ki yafara dawowa LABEEBAH Tace kedai ayi sha'ani Suka xube kan kujera Sumayya Tace nikam banasan komawarki Abujah Wlhi XARAH Tace hmm yaxanyi wai baxai iya zirga-xirga tsakanin Kano da Abuja bah LABEEBAH Tace ni Yama yankan qaunah Wlhi XARAH Tace Karki damu har gida xai dinga xuwa 'daukoki Yana kawomin ke LABEEBAH Tace hmm story kenan Tace Allah da gaske nake Sumayya tace xamu gani ai in gaskiyar ne XARAH ta harareta Tace ina wasa dake ne Tace dena hararata Allah yabaki hakuri LABEEBAH Tace gidan Ku 'daya dah Momy acan XARAH Tace aa Saidai agidan xamu sauka dan qanin Ya KAMAL 'din yaxo tun shekaran jiya Atare LABEEBAH da Sumayya suka waro waje LABEEBAH Tace kardai wanda Matarsa ta mutu. XARAH tace eh shi me yara biyu bah. sadeeq da Aliyu Sumayya Tace me sunansa mah XARAH Tace YUSUF LABEEBAH Tace ayya Allah yaji qanta Sukace AmEEn XARAH tagyara xama Tace dake fah xamu dan Momy CE Tace lallai aje dake. Sumayya Tace eh Ya KAMAL 'din yafa'da mata 'daxo shifowarmu Tace Yauwa dakema mah Tace hakah Yace LABEEBAH dai shuru tayi dan itadai bataso hakabah Allah yasani batasan KAMAL da XARAH Su haifar mata hawan jini Haka suka kai yamma Suna hira abinsu Zuwa can suka tafi bayan sunje sun gaisar da Kakah Suna ko tafiya basu da'deba KAMAL yashigo Yana cewa my TEEMAH inasu laveebah ne. Tace yanxu suka tafi. Yace Ya Allah naso nagansu Tace wani abu ne Yace no bakomai. Yafa'da Yana mai janyota jikinsa yana me qarashewa da cewa ina Cikin buqata Tace haba dai. Ya cafke bakinta da cewa gaskiya Tace toh ga abincinka can na gama saika cika cikinka Xan saurareka Tafa'da da xare jikinta daga gareshi da kuma kashemai ido 'daya. Gya'da kai yayi yabi bayanta Su LABEEBAH ko Suna xuwa gida Innah Tace musu KAMAL yaxo dasan suraka XARAH Abujah Sukace ya fa'da musu Washe gari ko KAMAL yaxo ya ibesu suka luluqa Abuja Yaso subi girgi Amma dai yabiyema motar Tun da suka shiga unguwar tasu KAMAL Sumayya da LABEEBAH suka tsure dan ha'duwa XARAH bata tsoreba dan sunxo lokacin da xa'a kawota gidan nata na nan 'din Abun dama ya hana LABEEBAH xuwa shine mutuwarsu mamah dake lokacin bata gama warwarewa bah. Wani ha'dad'an gidane wanda ya amsa sunansa shi suka shiga Hmmm LABEEBAH ido πŸ‘€ waje take kalan gidan. Sumayya ko baki sake take kallan gidan KAMAL yajah numfashi Yace munxo Nan suka fitoh Suna shaqar iskar gidan me tattare da qamshin furanni 🌴 Sagna CE tafitoh tana gya'da kai tana jin waqa ta wayanta. Safna na binta a baya. Aiko nan take ta wancalar da wayan taje da gudu ta rungumi LABEEBAH yayinda Safna ma taje ta rungume XARAH Murna suke sosai naganinsu ahaka suka shiga falan Momy Ta tarbesu da qaunah tanacewa masha Allah marhaban da yarana Suka gaidata ta amsa da kulawa tana cewa maxah Safna kaisu suyi wanka yanxu suhuta gajiya suci abinci Tace toh Nan tajasu part 'dinsu KAMAL ya kalli Momy yace inah YUSUF Tace yanxu suka fitta da Salim inaganin ba da'dewa xasuyi bah Yace toh bari nima nawatsa ruwa Tace ba lefi. Yayi part "dinsa na nan LABEEBAH ko mantawa tayi da wayanta afalan dan haka tafitoh ta 'dauka Ta 'dauka kenan tajuyo arashin sani sukaci karo...... al'amarin daya furgitasu Su biyu Dan jikin nasu daya ha'du dana juna yabasu wani MASEEFAR shock A furgice YUSUF ya saketa Cikin rukicewa da sanyin murya LABEEBAH Tace dan Allah Ya KAMAL kayi hakuri Wlhi bansan ka tawobah. tunaninta KAMAL ne dan ba abinda yaraba su Shuru YUSUF yayi mata ya 'dauki wayar tata ya bata tare da ratsawa ta gyafanta ya wuccewarsa Da sanyi jiki takoma ciki tunaninta ko bai hakura bah. Har Sumayya ta lura da sanyin da tayi Tace ya dai Tace hmm ba.Komai Abinci me rai da lpy aka ha'da musu a dining Momy da kanta taje takirasu. Suka fitoh Suna Cikin cin abincinne KAMAL ya shigo shima ya xauna sunaci tare Momy Tace naji da'din ganinku sosai musamman da kukaxo min da LABEEBAH. KAMAL yayi Murmushi Yace hakane Sagna Tace Aunty LABEEBAH naji wai kin iya kitso ko LABEEBAH tayi Murmushi Tace eh ina koya dai. Xan miki ne Sagna tayi saurin cewa So sai mah. kimin wanda xai gigita qawayena.... Safna Tace tab saita fara min kafin tamiki Momy Tace kunga ku dakata. Akan me xakusata aiki daga xuwanta ko cikakken hutawa batayi bah Shuru shukayi XARAH tayi dariya Tace hmm Momy bakisan LABEEBAH bane yanxu saita baki kunya akansu KAMAL Yace kwarai kowa da gaske Momy tamaida kallan nata kan LABEEBAH Tace wai haka Sunkwi da kanta tayi tana Murmushi...... Shuru suka 'dauka nawani 'dan lokaci shunacin abincin nasu Cikin jinda'di Yayinda LABEEBAH taketa satar kallan KAMAL batare dasun ankare da itabah YUSUF dayake bakin 'kofa duk xancikan da sukayi Yana jinsu da ganinsu Yana kuma kallan LABEEBAH da maya taccen kalan da take jifan KAMAL dashi . can ya qara tsaida idanshi akan nata sosai. Nan ko ya hango MASEEFAR SOON yayan nasa KAMAL a idanta Shidai YUSUF yasan soyayya da qauna dan shi malamin soyayyarne. Yayita da mufeedat 'dinsa marigayiya Yasanta lungu da sa'ko.......... Cikin nutsuwa yaje garesu yana cewa Wlcm brother nayi farin cikin da xuwanka Cikin farin ciki KAMAL Yace wow qanina kaine haka Yace me kagani ne Yayana KAMAL Yace aa ba komai kayidai kyau ne sosai har kana qoqarin xarceni Yace aidama nafika koba hakabah momynah Momy tashafah kansa Tace hakane my son KAMAL yayi Murmushi Yace ba damuwa Allah ya dawomin da Dadyna yanxu Murmushi YUSUF yayi Sannan yayi gum da bakinsa Kamarko jiran YUSUF suke suware dan ko hira ce ta6arke tsakanin Su dukka Amma ban da YUSUF da LABEEBAH dan tunda yayi gum da bakinsa baiqara magana bah har suka gama kowa ya watse Yayinda kwakwal war LABEEBAH tashiga ru'dani Daba dan taga KAMAL da YUSUF bah. Dako aduk inda taga 'daya daga cikinsu cewa xatayi duk mutum 'dayane Dan kamanninsu 'daya saima tashen samartaka da jini ajika da YUSUF yafi KAMAL Sannan tagano KAMAL yafi YUSUF 'dan jiki ka'dan Sannan muryar YUSUF kamarta KAMAL take saima tsari da tafi ta KAMAL 'din Kuma qamshinsu ya bambamta YUSUF ko tunda yashiga 'dakinsa yarasa nutsuwarsa takota ina Ji yayi yana san ganin LABEEBAH. Duk iya tunaninsa Yagama tunanoshi tsaf yagano yafa'da MASEEFAR Santa ne Bala'i😳 Meyasa haka tafaru dani YUSUF. Haba xuciyata. Daga ganin yarinya saiki karfi soyayyarta farat 'daya xuciyar sace taqara tarwatsa mishi nutsuwarshi wajan jefa mishi tunanin MATAR yayankace fah Da sauri yawaro ido Yana furta kalmar innalillahi-wainna'ilaihirraji'un Tabbas itace Matarsa dan daga ganin irin yanda take jifanshi da kallo ya isa bama mutum tabbaci Amma 'dayar yarinyar ta gyefansa fah Wacece ita. Ya tambayi kansa 🌡🌡🌹🌹🌡🌡 *MASEEFAR SOO* 🌹🌡🌡🌹🌹🌡🌡 Shuru yayi dan bamai bashi amsa dan haka Da sauri yahau binciken hotunan bikin KAMAL. Dan ranar Safna takawo mishi baisamu ya kallabah. Aiko bin hotonan ya dingayi da ido dan yakasa bambamce tsakanin XARAH da LABEEBAH wacece matar yayan nasa Dan duk shiga iri 'daya sukayi kalace kawai take bambantasu Bayanan akayi bikin dan haka baisan Komai akansu bah Tashi yayi yayi shashin Momy da hotunan ahannunsa yaje gareta Yana cewa plx Momy nunamin MATAR Ya KAMAL anan Yafa'da yana nuna mata hotan XARAH da LABEEBAH Tayi Murmushi Tace menene my son. Saurin durqusawa yayi agabanta Yace plx Momy dan Allah dan Annabi karkicemin wannan CE matar shi. Yafa'di hakan Cikin tsoro tare da nuna LABEEBAH Momy tashafah kansa tace meya saka rikicewa YUSUF Bana san tashin hankalinka koka'dan koka manta wiyar da mukasha wayan samun kanka. Meya faru daxaka rikice haka. Yajah numfashi Yace 'daxo mun shigo da wani abokina ya ganta. Yaji yΓ na Santa shine naji tsoran kaddai itace matar Ya KAMAL Momy tasauke ajiyar xuciya Tace har hankalina ya kwanta naxata wani abunne Wannan itace matarsa. Momy ta nuna XARAH Sannan ta nuna LABEEBAH Tace ita kuma

Chapter 7 of 22