Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya xubuma LABEEBAH sharr Dan tana xaune kan kujerar da take kallan windan farfajiyar gidan Tana kallan dawowar YUSUF da kissing 'din daya yima XARAH Share hawayanta taji anayi. Takalli SAUBAN daya xage yana goge mata hawayan Yace momyna kidena kuka banaso kinji Tayi Murmushi Tace ban san lokacin da nayi shiba SAUBAN Amma karka damu baxan qaraba kaji Yace toh Tunanin da LABEEBAH tayi 'dayane shine YUSUF xaiyi kwana bakwai a'dakin XARAH qila ya biyema XARAH hakanne dan karya shiga hakkinta Idanko Hakkane mexaisa tadamu gwara tabarsu sukagama kwana bakwai 'dinsu yadawo gareta Qarfe takwas na safe LABEEBAH tagama Komai Farfesun naman ragone tayi Sannan tayi musu ha'din tia wanda yasha kayan qamshi Ta yaba aikin Momy sosai dan duk abin buqata ta saka musu cikin kitchen 'din Saita gasa buredi da kwai ajiki Tajera musu a dining kana ta ibi nasu ita da SAUBAN sukayi falanta. XARAH da YUSUF suka fitoh sukayi breakfast 'din YUSUF Yace Amma fah yayi da'di farfesun nan Tace eh aitana qoqari LABEEBAH Gaban YUSUF yafa'di Wlhi shi Sam mantawa yake da LABEEBAH in yana tare da XARAH Bala'i😳 Yayi shuru da tsayawa dayin Komai XARAH Tace lafiya Yace nayi tunanin Momy CE ta aiko dashi Tace ai LABEEBAN CE tace karta aiko dashi dan xamu dinga bata wahala ne kawai Tashi yayi Yace yayi kyau nixan ficce Tace muje in rakaka Hakako suka fitoh hannunsu saqale da juna ya shige motarsa LABEEBAH na kallansu ta falanta XARAH tamanna mishi kiss💋 yajah motarsa ya ficce. wani masefaffan kishi ne ya caki xuciyar LABEEBAH Hankalinta yatashi Bata ankareba XARAH tashigo falan nata Tace kiyi hakuri banxo na tayaki aiki bah Wlhi..... LABEEBAH ta katseta da cewa ina kwana Tace lafiya da fatan kuntashi lafiya Qalau LABEEBAH Tace sai sukayi shuru duk kansu. Ita LABEEBAH game takeyi a wayarta itako XARAH shuru kawai tayi tana kallan SAUBAN da yake wasansa Wanda kallo 'daya yamata ya 'dauke fuskarsa Tace SAUBAN kaba ganni bane Abinka da yaro saiya kalleta Yace naganki mana Momy Tace shine baxa kamin oyoyo bah Yace aikema bakyayimin in kika ganni momyna nace me mun yafa'di hakan da nuna LABEEBAH. Lokaci 'daya kuma yabi boll 'dinsa yaci gaba da wasanshi LABEEBAH najinsu. Saitaji bataji da'din hakan bah Takalli XARAH ka'dan Tace mexai hana ki ware lokaci kidinga bah SAUBAN kulawa saboda halin rayuwa Tata6e baki Tace banda wannan lokacin Bawai kuma nadamu da abinda ya faru yanxu bane Kinsan dai Ni yara ba damuwa nayi dasuba LABEEBAH Tace ko Tace da gaske mana Ke bakiga hakan bah Tashi LABEEBAH tayi Tace nada'de da gane hakan Bara nayi wanke wanke nasan kungama ko XARAN ma tashi tayi Tace eh tun'daxo. Muje in tayaki Suna cikin wanke wanken ne Hajjiya Turai tasawo kanta Babban falan nasu tana ko'da sallama XARAH tafita da gudu ta rungumeta tana cewa nayi missing 'dinki xauna kisha labari Turai taxauna XARAH taxauna daf da ita Tace kan ubah haka maganinnan yake da aiki. Wlhi bakiga yanda ya gigita YUSUF bah. Gaskiyane maganin mata shine mace agun 'da namiji bala'i Turai tasheqe da dariya Tace angaya miki wannan magungunan na wasane. XARAH tace gaskiyane nayarda ba nawasa bane Turai tace Yanxu mah wasu nakawo miki dan yafi wancan aiki. Amma fah da ku'di XARAH Tace Kinsan banda matsala dasu bani kawai nagani Turai tayi Murmushi da cewa ina shegiyar taki....... Saurin waro ido XARAH tayi tana leqa kitchen cikin tsoro takama hannun Turai cikin murya qasa qasa Tace tana cikin kitchen Turai tayi qasa da murya Tace kai habah Tace Wlhi Kinsan na manta da ita nafitoh inata baragada Turai tajah tah part dita tana cewa kemadai Wlhi sai ahankali yaxaki saki baki haka ninayi tunanin tana part 'dinta ne Tace tana kitchen Amma ina ganin bataji bah Nan Turai tabaje mata harka Wanda XARAH tafara cilla ido tana ta6awa Shuru LABEEBAH tayi. tabbas taji abunda suke cewa kuma tagane abunda suke nufi Itama tunda taga Hajjiya Turai taji ta tsaneta kuma dama tana ganin sauyi agun XARAH tuncan baya Yanxu tafara xargin tana tusama XARAH wasu halaye Shuru tayi can da taga tsayuwar tata bata da amfani saita 'dauraye hannunta tasaka aranta yanxu xata fara bin tunaninsu Yau kwana bakwai kenan ☺☺☺☺ Haka ko ya faru dan LABEEBAH tagano bakin xaran manufarsu akanta Abinda yabata mamaki yasata kuka shine yanda XARAH takasance haka. Tayi sabo da hu'dubobin Turai Sam sai yanxu tagane XARAN data sani da ba itace yanxu bah Wato ayanxu duk xamanta da XARAH raina mata hankali kawai takeyi Meyasa Ni LABEEBAH ban gano hakan tunda wiri ba Meyasa kikamin baxata XARAH Saiga hawaye ya wanke mata fuska tana tuna hirar da taji sunayi jiya inda taji XARAH nacewa har abada YUSUF natane ta 'dan'dani xumarsa kuma baxata ta6a bari wata 'ya mace tasanshi bah Dan xata toshe kowace 'kofah yanda ba wata sai ita agaban YUSUF Turai Tace shegiya LABEEBAH dai taxama hoto XARAH tayi dariya Tace aida hotoce da Sauqi tunda xa'a dinga kallanta. Kango xata xama Wlhi ba photo bah Turai Tace yaudai Karki manta kwananta ne dan kin cika kwana bakwai 'dinki yau XARAH Tace Lalle naga alamar bakya 'daukar karatun nawa. LABEEBAH ta share hawayanta dan kammala tuno wannan furucin nasu Tace namiji ya ha'damu XARAH idan najure wata ranah ina tsoran ranar da xankasa kasa jurewa hakan Da YUSUF ya dawo XARAH fitowa tayi ta tareshi suka yi part 'dinta Duk da LABEEBAH taji furucin XARAH akan baxata bari YUSUF yaxo gareta bah Amma tayi mamakin yanda yau ya kasance kwananta Amma YUSUF baibi ta kantabah Yau kusan kwananta hu'du rabanta dashi Amma ko ajikinsa Shuru shuru har kusan goma 10:00pm YUSUF baixo gareta bah Sai tajah musu bargo ita SAUBAN suka kwanta abinsu Haka Washe gari tagama Komai tajera musu ba kunya suka fitoh suka cika cikinsu XARAH ta rakashi mota Sannan tayo part 'din LABEEBAH suka gaisa LABEEBAH sai binta take da kallo tana mamakinta Amma XARAH tayi tamkar batasan kallanta takebah saima tashi da tayi Tace ina jin bacci dan jiya ban samu yiba bari naje nakwanta kibarmin wanke wanken Xanyi Tana fa'din haka tayi part 'dinta bata jira cewar LABEEBAN bah LABEEBAH tasaki baki sakaka 😼 Can Tace mutum kenan ashe ba abinda yafi mutum saurin canjawa lokaci 'daya Itadai ko amafarki akace mata XARAH xatayi mata wannan budulcin baxata ta6a yarda ba bare a baiyane Abun fah haka yaci ga da tafiya XARAH qememe tamantar da YUSUF wata LABEEBAH Yau watansu uku Watan Farko ciwan cikin marar LABEEBAH ya tashi mata cikin dare aiko Allah ya temake ta taxo da maganin da Ya Usman yabata watan bikinsu nan tajiqa tasha Allah ya temaka bai wahalar da ita ba Haka wata na biyu tana cikin kitchen ciwan ya tasar mata lokacin tare da XARAH a kitchen 'din Dan haka tayi saurin jiqa mata tasha maganin tabata tasha Toh wannan watanne tayi amfani da maganin gabaki 'daya Hankalinta ko yatashi tunaninta wani watan yaxatayi dan Ya Usman Yace mata me bada maganin har yanxu bai dawo garin na kano bah Amma yaje gun wani ya kar6o mata Allah yasa adace kamar wancan xaixo da kansa Abujan ya kawo mata Tace toh ya tawo mata da Aunty Rukayya da Sumayya toh kawai Yace mata Amma daya tashi xuwa shika'dai yaje mata Ayanxu dai saidai LABEEBAH ta dafah ma YUSUF da XARAH abinci sulamishe Wato sun maida ita 'Yar aiki I xuwa yanxu LABEEBAH tagane Komai da Komai Yau tayi al'kawarin xata yimah XARAH magana. Dan haka Bayan ta idar da sallar La'asar dayin laximinta da addu'o'inta dama tayi wankanta taci Riga da siket na material tayi kyau aciki sosai dan kayan sun ka6eta Sai tanufi part 'din XARAN Aiko tasameta tana waya dagaji Kasan da mijinta takeyi Tace OK yanxu kana hanya tanaji YUSUF Yace eh Tace toh sai kaxo takashe wayan da kallan LABEEBAH Tace in aka ganki da magana nasan mungama abinci bare kice kinxo tambayar mexa mudafa LABEEBAH taqara jinjina rainin hankali irin na XARAH tare dajin wani tsanarta (Kishi kenan mesa mutum manta mutunci bare adalci) . [8:44PM, 08/10/2016] Rahamat Nalele💋: Tace ba wannan bane ya kawoni Ke 'yar uwatace XARAH Baidace aji kanmu bah Ban san yaushe bane ha'kurina ya gaxa 'daukar wannan Naxo ne in roqeki kitsaya akan hakkinki kawai. kidena shiga nawa Naga la'amar kin manta cewa mu biyune Matan YUSUF acikin gidan Xaqewarki tayi yawa Koda da ballagaxa kike xaune da ita matsayin abokiyar xamanki yaci ace kinji tausayinta kin bata mijinta. Ban San da'din maxa bah adaaaaa Dan ban damu da in sani bah Shiya yasa nabar miki YUSUF tunda nalura kinsan ya da'dinsu yake Shiyasa namiki uxiri nabarki ba wata 'daya ba. Ba biyu ba. har uku Nasan yanxu inba San xuciya bah kin lashi xumar YUSUF har kin saba da ita na roqeki kibarni da Mijina haka Baxan iya tauye miki kwananki bah. Amma baxan iya bar miki nawa yanxu bah XARAH XARAH XARAH nakira Ki sau uku A yanxu inasan inji da'din maza Maza ba Inji ya suke Ya akejin su Sannan ya abin yake Atakaice yau ina buqatar Mijina Na roqeki da Allah karkisa mukai matsayin daxa muyi abunda xa'aje akaimu gaba. LABEEBAH CE mai wannan furucin ga XARAH 🤔 Afurgice XARAH Tatashi takalli LABEEBAH Tab gaskiyane takaita mu'kura tasan LABEEBAH tana mata kawaici akan Komai Saidai itadai baxata iya yi mata kawaici akan YUSUF bah Kuma al'awari tayima kanta ita ka'daice da YUSUF Dan haka takalli LABEEBAH a wulaqance cikin raini Tace meyasa kikayi gangancin Auran Wanda xuciyata take so Akan MASEEFAR dana afka ta MASEEFAR SOO Xan iya yimiki abinda yafi haka mah YUSUF nawane Ni 'daya Ina sanshi kuma baxan bari wata mace tara6e shiba. Me kike nemah me kika sani akan maxa da xakixo kina magana akan nabar miki mijinki Wlhi ko yanxu isata CE tasa YUSUF maqale mun Namantar da shi kowace mace ba wacce xaigani agabansa saini Ina baki shawara LABEEBAH kifita daga harkar YUSUF dan yanxu yafi qarfinki ..... Ta numfasa ha'de da dariya kana taci gaba kin iya rasa KAMAL kuma kikayi hakuri akan wane dalili xaki damu da YUSUF meyasa........ Kinga malama da kata magace kinyi akan baxaki barni da YUSUF bah saboda nake ne ke 'daya Hmmm ba shakka kinkai nan gurin Bada abinda kika fini XARAH saima abubuwan da nafiki dasu wajan 'daukar hankalin maxa Kina wani cewa isarki CE tasa YUSUF maqale miki ni koba maganin mata saina koya miki hankali kirubuta ki'aji Kinyi furucin yafi qarfina ko. Nikuma saina nuna miki nice nafi qarfinsa daga shi harke Tana fa'din haka tayo waje Tafito kenan YUSUF yana sawo kan motarsa Baqamin bugawa gabansa yayi bah da ganin LABEEBAH bah. Shidai ya rasa abinda yake damunsa akanta Sam mantawa yake da ita arayuwarsa Part 'dinta tayi takama hannun SAUBAN Tace xomuje unguwa Yace yauwa momyna Nan taxaro gyalanta ta tajanyo kofar ko kullewa batayi bah tayi hanyar waje Da sauri YUSUF yafitoh daga motarsa yasha gabanta Tare da dur'kusawa aganta Yace dan Allah dan Annabi kiyafemin Wlhi bansan meyake damuna bah Tace ko Yace Yah Wlhi dagaske Tace koma me yake damunka kai kasani dan Allah tashi kada wani yaxo yaganka yayi tunanin wani abu Tashi yayi jikinsa asanyaye Yace ina xaki Tace inda nayi niya. Yace kin tambayeni ne Tace akanme xan tambayeka mijinane kai Yace plx nutsuwata.... Karmiyi haka dake Kisani duk matar da tafita unguwa batare da sanin mijinta bah tsinuwar Allah ta tabbata akanta Dan duk wani taku 'daya idan tayi Mala'iku tsine mata sukeyi Tace Au yanxu ne Kasan da cewa ni matarka ce Yace tunda aka 'dauramin Aure dake nasan ke matata CE Xatayi magana ya katseta da cewa kitemaken dan Allah kiyafemin sannan Nayarda da duk inda xaki amma Ni xan kaiki Tayi Murmushi dan ganin XARAH tafitoh daga part 'dinta Tace toh muje kakaini Har xasu shiga motar XARAH Tace my luv ya daga xuwa sai fitta Bayan Kasan tun safe nake da muradinga San kasan cewa ajikinka YUSUF ya kalli LABEEBAH yaga tayi fuska yamaida kallansa ga XARAH nan ya hango rikicin so kala kala kamar yanda shima yadawo dasu Yace ki'dan min afuwa nakai LABEEBAH unguwa nadawo Tace buqatata tafi tata mahimmanci LABEEBAH talalleshi Tace kaga Malam je ka biya mata buqatarta dama fah munsan hanya Tafa'da dasan ficce Yaqara shan gabanta Nan taga tashin hankali a idansa kamar xai mata kuka Yace plx Ki temaken dan Allah Shuru LABEEBAH tayi hawaye ya xubu mata saijin hannunshi tayi kan kumatun nata yana goge mata Kallansa tayi taga shima hawayanne ya xubu mishi. Ganin haka yasata juyawa tayi part 'dinta tana hawaye Sauke ajiyar xuciya YUSUF yayi da runtse idansa ya sauke akan SAUBAN Wanda yayi shuru yana kallansa Yace Dady kasaka momyna kuka metayi mah YUSUF ya rage tsawansa ya kama hannun SAUBAN Yace batajin da'dine my boy jeka lallasheta kace ina xuwa kaji SAUBAN Yace toh meyasa kaima kayi kuka. Yace saboda banasan kukanta ne maxa jeka kaji Aiko da gudu SAUBAN yayi part 'din LABEEBAH yana kiran momyna momyna XARAH tata6e baki Tace kar lamarin LABEEBAH ya dameka xo muje kasha milk me sanyi Wanda xai kwantar maka da hankali Kallanta YUSUF yayi Yace inajin ina aikata ba dai dai ba. Tace koma miye kaxo muje kahuta saimu fuskanci mafuta Haka yayi part 'din XARAH Duk abinda tasan xatayi ta'dauke tunanin shi akan LABEEBAH shi tayi Kuma taci galaba dan LABEEBAH tanajin futarsa Sallah ko kallan shashinta baiyiba Kan ya dawo ne XARAH tashiga tunanin wane hukunne ya dace da LABEEBAH Saiji tayi wayanta na ringing Jameel tabani ta'dauka Yace Kinga nacanjah tunani baxan iya jure har sai shekara tayi xan mallaki LABEEBAH bah Na baki kwana uku kiyi abunda xaisa ya saketa inba hakaba mufuskanci matsala Cikin fusata XARAH Tace ai Kasan igiyar Auranta a guna take daxaka bani kwana uku So kake inje ince masa saketa kuma ya saketa Yace Lalle XARAH bakisan Waye nibah Amma namiki magana tun muna mu biyu kije kibi hanyar da kikabi kikayi makircinki kika sami YUSUF yanda kikeso. Toh wannan Hanyar nakeso kibi kisaka ya saketa. Kwana uku nabaki Wlhi kikayi gigin in aikata hakan Wlhi saikin nemi Auran Ki kinrasa Dan YUSUF sai yasan Komai akan yanda kika sameshi Yana fa'din hakan ya kashe wayansa Yayinda hankalin XARAH yatashi nan takira Hajjiya Turai tagaya mata Komai Tace dallah bar 'dan iska Ki saka Su Musa jage Su kau miki da 'dan iska Aiko nan take takira wa 'yanda suka satoh mata KAMAL alokacin baya Tace tanasan Su kashe mata Jameel xuwa gobe su ha'du a gidan Turai taga pix hota kisan Sukace angama ranki ya da'de Amma sai gobe Komai xai wakana Tace ba matsala Tana sauke wayan YUSUF na shigowa Taje ta rungumeshi suka fara ya mutsa juna Washe gari XARAH Tacema YUSUF xata gidan qawarta plx suje ya sauketa adawowar shi ya biyo ya 'dauketa Yace toh Sun fitoh danyin breakfast sukaga dining wayan ba Komai🙅🏼 YUSUF Yace ya haka XARAH tacije yatsa Tace bara in shiga kitchen yanxu in ha'da maka Yace OK Tanayin kitchen ya tsinci kansa dayin part 'din LABEEBAH Bayan ya shiga falan saiya kulle 'kofar falan harda key [8:55AM, 09/10/2016] Rahamat Nalele💋: LABEEBAH na kallansa ya qaraso gareta Nan yaga soyayyan dankali da egg ha'de da kakkauran tia suna karyawa ita da SAUBAN abinsu Ya xauna dab da ita Yace ina kwana Takalleshi ka'dan aciki Tace lafiya Yayi Murmushi Yace xan samun turare dan Allah Ta kalleshi sosai Tace mexai hana Yace Yauwa toh tashi Kiban Tayi shuru dan baxa taso Tatashi a haka bah Dan kayan da tasaka shegun kayane Riga da wandone sun matseta tsam Komai nata ya baiyana....... Yakatse mata tunaninta da cewa tashi mana yaqare dabin surarta da kallo Tashi tayi ahankali tayi bet room Aiko yabita Saiji tayi an rungumeta ta baya Batada buqatar sanin waya mata hakan tasan sai mijin nata Nan tafara kici kicin kwatar kanta Ya riqeta tsam yafara magana cikin sanyayyiyar murya. Yace plx nutsuwata Ki fahimceni Wlhi bansan me yake damuna bah kiya femin Saita fashe mishi da kuka mecin rai Dama yasan kan abinsa Dan haka ya juyo da ita gabansa ya rungumeta tsam yana shafah bayanta alamar lallashi Nan tayi shuru Yasami yanda yakeso dan haka ya kwantar da ita kan gado ya hau kissing 'dinta tako ta ina Yanda ya rikice mata shi kadai yasata tausayinsa Tana jinshi yana qoqarin cire mata riga tabarshi saidai da taji yafara tsotsarta tayi yunqurin kwatar kanta ya 'dago da kansa ya dire afuskarta yace karki hanani abinda yadace nayishi tuntuni tureshi tayi hawaye na xubar mata Tace Nina yafe maka Amma na roqeka kabarni haka... Yace rayuwar baxata ta6a tafiya ahaka bah plx kibarni Share hawayanta tayi tatashi da kallanshi Tace xakayi breakfast ne Ya harareta Yace saidai luv... Breakfast Xatayi magana wayanshi tafara ringing Bakuwar number CE ya 'dauka da hello Sai yaji abokin Yayansa Jameel ne Yace mai yanasan Su ha'du yanxu a office 'dinsa akwai gaggarumar maganar daxai gayamai YUSUF Yace toh insha Allah xaka ganni yanxu Yace Yauwa LABEEBAH Ta kama hannunsa suka fitoh falo Annan ta ha'da mishi Komai tabashi Aiko ya cika cikinsa dam Sanman Yace mata xaikai XARAH unguwa yana sauketa zai dawo Toh LABEEBAH Tace masa dan tasan ba dawowa xaiyi bah. Kuma yau tasaka aranta saita kwana da mijinta ko sama da qasa xata ha'de Har 'kofar falan XARAH ta rakashi ya manna mata kiss Yace ina sanki Tace nima haka Sannan takwaci kanta tayi shashinta Komai XARAH ta shirya mishi tana dai xaman jiransa ne dan taci nata Tunaninta waje ya fita shiyasa daya shigo tatareshi da murna tana cewa na gama ha'dama Komai Yace lokaci yatafi muje kawai Tace bakaci Komai bah xamu tafi. Yace naci gun LABEEBAH Tace dama can kaje Yace eh Saitayi shuru Yagane bataji da'din hakan bah. Sai ya yafah mata gyalanta da kama hannunta suka ficce Har ya sauketa agidan Hajjiya Turai tashiga gidan bata kula shibah yayi Murmushi yajah motarsa Direct asibity yayi bayan yakai office 'din Jameel ya nufa Anan ya ganshi tanata safah da marwa Yace lafiya Ya Jameel Hawaye ya xuboma Jameel Yace na cuci Kaina YUSUF naci amanar KAMAL na yau dareshi na biyema she'daniyar matarsa YUSUF Yace duk meyasa haka yafaru Yace kafin in fara baka labari inasan kaya femin YUSUF Yace bakamin Komai bah mexaisa na yafe maka Kuka sosai Jameel yafashe dashi dan tuna 'daxo da safe daya fitoh dan Xuwa office 'dinsa daqer yasha ahannun Su musa jage Dan qiri qiri yaga mutuwa Allah ya temakeshi yasha ahannunsun..... YUSUF Yace plx Jameel kasa hankalina yafara tashi meya farune Gyara xama Jameel yayi ya kwashe duk abinda XARAH tayi dan ta mallake shi matsayin mijinta Ihu YUSUF yasake lokacin dayaji XARAH CE ta kashe Yayansa KAMAL Idanshi ya fara juyewa Hankalinsa ya tashi Ya bala'in furgicewa da lamarin XARAH Ya tashi afurgicen Tare da kama kansa Ya fashe da wani gigitaccen kuka Wanda kallo 'daya xakama YUSUF kaji kana san tayashi kukan Yana kuka Jameel na kuka Sun 6ata lokaci ahaka YUSUF yafara tafiya cikin layi Jameel yayi 'ko'karin San rigeshi YUSUF ya 'dagamai hannu Yace karka ta6ani Yana fa'din hakan yayi waje. Jameel ya bishi da kallo Shiga motashi yayi hankalin shi na neman gushewa Ayanda ya figi motar ka'dai ya isa ya tabbatar maka da cewa bame hankali bane ya figi motar Tuqi YUSUF yake yi ahaukace Dan kowa kauce mishi yakeyi dan Tsira da ransa Ahaka ya iso gida dayima megadi wani kira cikin muyar buqatar temako Da sauri ko megadi ya bu'de mai. Dabadan megadin yayi saurin kauce mai bah daya begeshi YUSUF yayi parking Amma yakasa fitowa dan jin yanda girjinsa yake mishi xafi Ba shakka yaji wani ciwo ya caf Ki xuciyarsa yayi saurin dafe girjinsa yana hawaye Aman jini ya fara yi Yana cikin wannan halin ya danna numbar XARAH ya kirata Xuciyarshi tacika fam da tsanarta Lokacacin sun baje ita da Hajjiya Turai Suna kwulla sharrin yanda xasuyi da LABEEBAH da kuma jiran hotan gawar Jameel Sai taga Kawai kiransa da baxata 'dauka ba Sai kuma taji gabanta ya fa'di ta'dauka Cikin muryar can qasa wacce bata ta6a jin YUSUF cikinta ba Yace kisameni agida yanxu na baki minti biyu. A rikice XARAH tamiqe tana cema Turai YUSUF ne bari naje naji muryar shi wani iri wai yana gida Turai tayi dariya Tace kodan kishin Ki kyatafi tunda kikaji Ya ambaci gida. Dan karya ka'daice da LABEEBAH Tace eh da wannan dan wannan Amma gabana ya fa'di LABEEBAH taga shigowar YUSUF tayi Murmushi Tace aranta Ashe da gaske xai dawo Da sauri tayi bet room tafara kici kicin canja Kaya YUSUF ko aman jini yake sosai kanshi sai juyawa yakeyi ga xuciyarsa sai yawaita xafi takemai Duk yajiqa wayar tashi da jini Har LABEEBAH tafitoh falo sai kuma takoma taje gaban madubi ta qarema kanta kallo. Eh tayi sosai Cikin wata dogowar riga me hannun shimi Tamatseta tsam hakan ko ya bayyanar da surarta Tafitoh falo SAUBAN Yace Momyna canja kaya kikayi Tace eh SAUBAN nayi kyau Ya'dage baki Yace eh Amma bakiyi kwalliya afuskarki bah kamar na Momy Tagane XARAH yake nufi Tace toh anjima inxanyi sai kamin ko Yace toh Tafitoh kenan XARAH tasawo kan motar Turai dan cema Turai tayi tabata motar tata LABEEBAH tatsaya har tafitoh sai kuma suka tsaya Suna kallan kallo Can XARAH tayi part "dinta tunaninta ko YUSUF yanacan LABEEBAH tana niyar xuwa gun motar YUSUF saiga Safna da Sagna sun sawo kan motarsu tatsaya suka fitoh Da sauri Sagna ta rungumeta Tace wow kinyi kyau sosai Aunty LABEEBAH tayi Murmushi Tace Nagode Safna Tace toh gyara muyi Hotoh Tagyara sukayi Suna cemata sunxo gaya musune wata yayar Momy CE ta aihu........ XARAH CE tafitoh tace da LABEEBAH. Ina YUSUF LABEEBAH takalleta ka'dan daninsu Sagna yasata cemata. Kamar yana mota Da sauri tayi gun motar da bu'dewa........ Wani uban qara tasake wanda Ya furgitasu sukayi gun da gudu Ganin YUSUF sukayi asume baya motsi XARAH fa'di take ya mutu nashiga uku Wlhi YUSUF ka mutu nima mutuwa Xanyi katemaken karka mutu dan Allah na riqeka saita fashe da kuka wiwi tanayi Su Safna sunayi Kunsan LABEEBAH bata raina abin sumewa dan haka saiji sukayi taxube a qasa jagwab Saurin janye YUSUF gefe sukayi Sannan suka saka yayyafama LABEEBAH ruwa Amma ko alamar motsawa batayi bah. Dan haka suka sakata amotar da YUSUF yake sukayi Asibityn hankalinsu tashe Suna kaiwa Sagna takira Momy da Dady cikin kuka Tace musu suna Asibity ya YUSUF ya sume LABEEBAH ma haka Cikin tashin hankali Momy da Dady sukayi asibityn Qasar Armiyaniya 🌵🌵🌹🌹🌵🌵 ~*MASEEFAR SOO*~ 🌵🌵🌹🌹🌵🌵 Gidan sarautane Wanda ya amsa sunansa Dan kallo 'daya xakamai kaso ace dama Kaine kake da mallakinsa Sarkin garin Allah ya hore da mishi mata biyu da yara biyu mata Kowacce 'yarta 'daya kuma kansu 'daya Dan Uwar gidanshi maryam tana aihuwar 'yarta Khadijah da sati 'daya Amaryarsa Zainab ta aifu tata 'Yar Halima Haka yaran suka tashi Kansu 'daya. Amma babu qaunar juna atsakaninsu Dan kowaccansu fatanta Baban nasu yafi santa Yayinda shi Baban nasu sarki suka kasance basa gabansa. Dan Allah yayishi dasan 'da namiji Toh sai kuma Allah bai bashi bah. Hakan yasa koyaushe a addu'ar Allah ya bashi 'da namiji yake Yanxu haka yana tare da fadawansa Suna yimasa hira me kwantar da kankali Wani kyakkyawan mutum me kyawun sura yaxo gareshi Yace Allah ya temaki BABANA da fatan nasameka lafiya Sarki yayi Murmushi da shafah kansa. kallo 'daya xakama Sarkin kagane yana yana qaunar wannan saurayi kuma yaji da'din xuwanshi gareshi Yace lafiya lau nake Shamsu ina xaka haka naga baka tare da kayan sarauta. Wanda Sarki yakira Shamsu Yace Allah BABANA Sam kayan sarauta basa birgeni. Xanje wajan Marwan ne Sarki Yace toh Allah ya dawo dakai lafiya Yace AmEEn da miqewa Sarki yabishi da kallo har ya bar gun yana tuna ranar da yasami Shamsu Shekara uku da suka wucce ******** Sarkin ya kasance mesan kasan cewa agefan ruwa dan Allah yayoshi dasan hakan Ba qaramin nisha'di yake ji bah akan hakan Kwasam ranar yana tare da fadawansa Yace naje bakin ruwa 'daxu yanxo kuma inasan komawa 'Daya daga cikinsu Yace Allah ya temakeka ai sai mukoma Hakan ko suka koma Saidai komawar tasu taxo musu da

Chapter 14 of 22