Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
nuna jin kunya tashige 'daki Ta ha'damai madararshi tabashi dan ko innah taga tana bashi madarar bata dumuwa dan tasan Yana Sha Qawancan XARAH da Hajjiya Turai ko ya bayyana dan har su inna sunsan da xaman Hajjiya Turai. Dan ko yaushe Suna. Tare da juna Suna kwillah tsiyar yanda xasu sami YUSUF hankali kwance A yanxu dai XARAH fatanta 'dayane shine SAUBAN ya shekara Tace ta yayeshi. Dan bata bi takan lamarinta da LABEEBAH da YUSUF dan sun shirya abunda ya dace musu. Al'amarin ko daya dami LABEEBAH fiye da tunaninta Kwana kuka take tana tuna kalaman KAMAL Ayanda lamarin yake LABEEBAH tafi kowa shiga tashin hankali . [10:56AM, 04/10/2016] Rahamat Nalele💋: Yanxu haka wayarta ta kurama ido tana kallan hotan sah. Wanda ta tura awayan XARAH batama sani bah Hawaye ne yake xubah mata kamar famfo Rukayya tashigo ta tsaya akanta na tsawan minti biyar Kana ta xauna tare da dafatah Tace kidena kukan nan LABEEBAH haka mana Danko XARAH bayin irinsa takeba. Ta hakura da KAMAL dan binshi da addu'a kawai take Amma ke kinbi kinsa damuwa aranki kin tsan gwami kanki Bayan mutuwar nan muma jiranta muke Tace Aunty Rukayya dole inyi kuka dole ne in shiga damuwa dole in tamgwami kaina Da fusata Rukayya Tace Toh kodai shine KAMAL 'dinki LABEEBAH takalleta ka'dan Tace meyasaki min tambayar nan Tace hakka dai dan naga tashin hankalin da kowa ya shiga naki na musammanne Tace hmm nidai ki tayani da addu'a kawai. Miqewa Rukayya tayi Tace toh Allah ya yaye mana matsalolinmu. tafitta....... Wayan LABEEBAH ce tayi qara tana dubawa taga YUSUF ne Share hawayanta tayi ta 'dauka da gyara muryarta Tace hello YUSUF Yace ina 'kofar gidanku kifitoh. Tace toh da kashe wayan Kyara kanta tayi da qara feshe jikinta da turare taje gareshi Tunda tafitoh YUSUF ya xubah mata ido harta iso gareshi Yace kinyi kuka ko Tawaro ido Tace aa meka gani Yace abu buwa da yawa Tace kwaro ne ya shigarmin ido Yace ba mamaki kam. Dama naxo ganinki ne ko nasamu nutsuwa axuciyata da kuma maganar bikinmu kinga anqara wata 'daya saboda rashin da mukayi na Ya KAMAL Tace eh Hakkane Yace toh yanxu ya kike san ayi Ta kalleshi Tace duk abinda kayi MeeNi 'dayane Kayi abunda ya dace kawai Yace koda gobe jumma'a in mallakeki a matsayin matata Tayi Murmushi Tace eh Yace toh Ki saurari 'yan xuwan 'dau karmin ke gobe Tace toh ina jira 'Dan 6ata fuska yayi ka'dan Yace axahirin gaskiya idan naganki kinyi kuka xuciyata xafi takeyi min hankalina na tashi. Plx kicire rashin Ya KAMAL mugina wata gantacciyar rayuwa. Wacce xanji da'dinta kiji da'dinta kema sun kuyar da kanta qasa hawaye nasan xubu mata Amma tayima kanta gata dan tasan yanxu ita da YUSUF bada bane tasan ya jure abubuwa da yawa abaya Amma yanxu baxai iya jurewa ba. Tace kayi hakuri insha Allah baxan qara saka wata damuwa bah Yace gud✅ Ina buqatar ganin murmushinki tayi murmushin Tace saidai dariya.... Yayi saurin katse da cewa nafi buqatarta Aiko takalleshi suka sheqe da dariyar gabaki 'dayansu Shuru XARAH tayi tana kallan LABEEBAH dan tagama fa'da mata maganar Auran nata da YUSUF LABEEBAH ta xungureta Tace azahiri kallona kike Amma a ba'dili damuwace tayi saurin shigarki yanxu nan meya faru Ya akayi kika gane XARAH ta tambayeta da kalar tausayi LABEEBAH tata6e baki Tace ayanxu damuwa ko yaya take agangar jikin mutum ko fuskarsa ina ganewa dan jina nake bawanda yafini Sanin kanta Saboda me. Xara taqara tambayar Saboda Ni kullin bana rabo da ita LABEEBAH ta fa'da da kafe XARAH da ido Tashi XARAH tayi Tace hmmm ba shakka Amma Wlhi ayanxu nafiki kusanci da damuwa da tashin hankali Ya xanyi da munafukar xuciyata. Yaxanyi da abin kunyar da tajaji6omin. Ya xanyi da raina Na shiga uku ni XARAH yaxanyi da ~*MASEEFAR SOO*~ Saiga wani kuka ya kub cema mata fa'di take LABEEBAH kiyafemin Ina so abinda kike shirin mallakarsa Xuciyata ciwo takemin. Jinake tamfar in kashe Kaina dan ba'in cikin abinda xuciyata tamin Cikin tashin hankali LABEEBAH Tace me yake damunki XARAH meya kawo miki ~*MASEEFAR SOO*~ a al'amuranki Me kikeso wanda ya kasance ina gab da mallakarsa XARAH tayi shuru LABEEBAH ta dafatah Tace karki damu abuna nakine. Naki kuma nawane. Nayi miki alqawarin duk abinda kika so indai mallakinane Wlhi xan baki shi yanxun nan. Kitemaki xuciyata ki gayamin dan Allah dan inyi saurin faranta miki XARAH takalleta qasa qasa cikin wani salo Tace nakamu da soyayyar *YUSUF*........ Shin xaki iya lamincemin ya aure mu mu biyu. Na sani xaki amince Amma koda xan mutu bayan yarda da hakan ba Ahankali LABEEBAH tayi baya hankalinta ya tashi hawaye ya xubu mata Amma tayi saurin maida tashin hankalin tare da saka bayan hannunta tagoge hawayan nata Tace Dan wannan xuxiyarki take miki ciwo Dan wannan kikeji kamar kikashe kanki Dan wannan hankalinki ya tashi Hmmm Karki damu nasan ciwan ~*MASEEFAR SOO*~ Na bar miki YUSUF har abada Cikin nuna tsoro XARAH Tace me ne..... Abinda kunnanki yajiye miki shi na fa'da. tunda narasa KAMAL bawanda xanji ciwan rabuwa da shi. Eh da gaske inasan YUSUF Amma XARAH kinfini sanshi tunda har kika iya furtamin Naji da'din hakan dan burina in faranta miki. Inasan Ki da YUSUF dan harna hangoku a ma'aurata LABEEBAH tabata amsa da hakan hawaye na xubar mata XARAH ta qaraso kusa da ita cikin kuka tadur 'kusa tace Ki fahimceni LABEEBAH soyayyar da nakema YUSUF bashi xaisa na tauye miki hakkinki bah Wlhi baxan iya xaman Aure da YUSUF bakya tare da shiba Wlhi saidai in mutu da ~*MASEEFAR SONSHI*~ indai baxaki aureshi bah Menayi kenan nayi xalinci LABEEBAH ta girgixa kai Tace baxan iya ha'da kishi dake ba XARAH baxan iyaba Abin tausayi XARAH kuka LABEEBAH kuka Candai XARAH Tatashi Tace nikuma Wlhi da in auri YUSUF inyi rayuwa ni dashi bake gwara in kashe Kaina.... Ya isa haka LABEEBAH ta katseta da fa'din hakan. Tace ya kikeso ayi Tace yanda nakeso shine inhar xuciyarki ta amince da Kin barmin YUSUF toko saidai ya Auremu mu biyu baxanyi xaman kishi dake bah Wlhi LABEEBAH yanda mukesan junanmu baxamu bari kishi yaci galabah akammu ba Saboda Son da nakema YUSUF xaki juyani yanda kikeso LABEEBAH Tace toh naji shikenan XARAH ta girgixa kai Tace ba shikenan bah YUSUF beta6a yimin kallan so bah Kuma baxai a mince da hakan bah Ki barmin Komai xanji da Komai LABEEBAH Tafa'di hakan da 'daukar SAUBAN Wanda yaxame mata jinin jikinta saboda tana kallansa kamar KAMAL dan tsantsar kamannin KAMAL daya bayyana a gareshi ko yaushe LABEEBAH na tare da SAUBAN dan har ya ganeta sosai fiye da XARAH LABEEBAH tasan XARAH bata bashi nono Amma tayi shuru da bakinta dan ganin madarar ta kar6e shi Amma abin na mata ciwo hakan nawasa tanajin bala'in haushin XARAH. Dake bayanda xatayi shiyata kawar da fuskarta akan hakan Tana shiga gidan nasu taxube kan taburma Rukayya dake wanke Wanke Tace Innah da Sumayya sun dawo ne Shurun da LABEEBAH tayi mata ne yasata juyowa Aiko ganinta tayi tana xubda hawaye tana kallan SAUBAN Rukayya ta tsame hannunta daga ruwan wanke wanken taxo gareta Tace habah LABEEBAH so kike hawayanki yaqare Ba ranar da Allah xai wayi gari bakiyi kukaba Me yasa haka yake faruwa dake Goge hawayan nata tayi Sannan tayi Murmushi ha'de da kissing 'din SAUBAN Tace wannan na dabanne Aunty Rukayya Nan takwashe yanda sukayi da XARAH tagaya mata Rukayya ta furgita da wannan batu cikin baqin ciki tare da tausayin LABEEBAN Tace tab Amma ke wawiyace Shawarar daxan baki anan itace tunda kunyanke haka shine Ki hakura YUSUF 'din kawai kibar mata shi. Xaman Aure fah xamuyi ba xaman wasa bah Wlhi kishi ya shiga tsaninki da XARAH kedai kinasan YUSUF Abinma Takaici plx ki barmata shi ai Bashi ka'dai bane 'da namiji aduniya da xata nuna miki wani alaye akansa LABEEBAH ta kalleta nan ta hango 6acin rai a tartare da ita Tace Karki damu Aunty Rukayya abun bai kaini nan ba Inasan YUSUF kuma xan yarda ya ha'damu dukka ya Aunremu dan nariga na yardar mata da hakan Da fusata Rukayya Tatashi tayi 'dakinta xuciyarta nayi mata xafi LABEEBAH tabita da kallo. Kana tadawo da kallanta kan SAUBAN ta rungumeshi tsam hawaye bai bar xuba mataba XARAH LABEEBAH na fitta tasheqe da dariya Tace Ashe xan iya buga wasan haka Toyanxu yaxanyi da YUSUF dan ban san ya xai 'dau lamarin bah Shuru tayi nawani 'dan lokaci can kuma ta'dauki wayanta takira Hajjiya Turai ringing biyu ta'dauka Tace ........... shegiya yane XARAH tagyara zama Tace Turai ke dai bari yau nafama LABEEBAH MASEEFAR SON da nakema YUSUF Tace ke habah kuma da gaske kin iya fa'dan Tace mamakin dana yima kaina kenan Ashe xan iya buga wasan Turai tasheqe da wata dariya Tace tunda kika iya kashe mijinki XARAH wane wasane baxaki iya bugawa bah. XARAH tajah numfashi Tace ina tsoran randa xan buga game over Turai Tace bana tunanin ranar xata xo danke 'din shegiyace me fuska biyu Tace naji dai ai wasu halayan ke kika koyamin Su kika 'dorani akan hanya Plx barwan nan mah yaushe xamu aha'dune Tace ina abuja yanxu Amma jibi xan shigo kano Tace plx Ki shigo ban san ya YUSUF xai 'dauki lamarin ba Turai Tace koda yaji lamarin Karki sake dashi afuska koda kun ha'du kinuna mai bakisan xancan bah Kinga sai yayi tunanin ha'din LABEEBAN ne kinga baxai rainaki bah Tace wow hakane fah Amma Kinsan inyaxo ganin SAUBAN bana iya 'dauke idona akansa Tace toh yanxu kidinga 'daukewa plx Tace Xanyi qoqari Wannan dare XARAH tayi baccin farin ciki Yayinda LABEEBAH tayi na Baqin ciki Tasaka aranta koxa dauwama cikin Baqin ciki sai YUSUF ya auri XARAH ya ha'dasu dan da gaske ta hango MASEEFAR SON Sa acikin idan XARAH Koda ya kirata bata mishi xanxan bah tafisan saigata gashi Haka abin yake yau yammacin jumma"a YUSUF yaxo gidan nasu Gidan su XARAH ya shiga ya gaida innah Sannan ya kalli XARAH wacce takasa jurema kallansa Yace saina roqa xakiban 'dana Tayi Murmushi Tace Nina isa yanacan gun mamansa Ya tabe baki cikin muryar qasa qasa wacce Innah baxata jiyo shiba Yace na kusa 'dauke matata ai dan gaskiya nagaji da Wahalar da kike bata ta raino baji ba gani Tace hmm indai LABEEBAH CE munanan dakai tana gidan nakama baxata fasa kar6ar wannan wahalar bah Tashi yayi Yace xan baki mamaki dan xan shagwa6ata yanda gyaran kanma saidai namata bare tasamu damar 'daukar wata wahala Tata6e baki da galla masa harara yayi Murmushi da yima innah sallama. Yana fitowa ko LABEEBAH tafitoh Ta sakar mai Murmushi da cewa kayimin xuwan baxata Ya kar6i SAUBAN Yace nasan xakifijin da'din hakan Tace eh najikam da'din fiye da tunaninka toh ya hanya Ya kalleta yayi Murmushi dacewa muje motah kiji Haka suyi Cikin motar tana gaida shi Yace.baqaramin nisha'di nake jiba idan ina tare dake Tace nimafah haka inban gankaba har wani xaxxa6ine yake caf kata. yace gud Kinsan dasu Momy mukaxo Da murna Tace ayya momyna xanso in ganta Yace xaki ganta yanxu dai bani labari Tace aikwai labari kam Amma bansan yanda zaka 'dauke shi bah Gabansa ya fa'di yaja numfashi Yace tunkan kice ga labarin naji gabana ya fa'di plx karkice Komai dan Allah👏🏻 Tace hmm ka yimin afuwa ince ko ka'danne Yaqara jan numfashi Yace inaji toh Tayi kalar tausayi Tace dan Allah dan Annabi karkiqi abinda xan fa'da Yace Wlhi koma miye ba alkairi bane tunda naji banasan ji Tasunkuyar da kanta qasa Tace dama inaso ne ka.... Auremu.... mu biyu Ya kalleta da kyau Yace ban gane in aureku Ku biyu ba keda wah Ta'dan Sosa qeya Tace Ni da_________ XARAH Waro ido yayi waje 😳 Yace what Me kikace Tace sunake ka Aure mu Ni da XARAH...... Sumayya CE ta kwankwasa mishi gilashin motarsa yaxuge. Tace ina wini ya YUSUF 'daxu najika lokacin ina Sallah Yace ayya lpy lau Sumayya ya gida Tace lpy da kallan LABEEBAH Tace mata xanje gidan Ya Bashir ne Aunty LABEEBAH in jiraki. LABEEBAH Tace aa jeki Tace toh nan ta'dauki SAUBAN Tace Ya YUSUF sai anjima 'daga mata hannu kawai yayi tayi gaba Sannan ya dawo da kallansa kan LABEEBAH da binta da wani mugun kallan da batasan ya iya yin shiba. takoyi saurin sunkuyar da kan nata qasa Yace Wlhi nutsuwata kinada Takaici yanxu ji nayi tamkar in miki dukan tsiya kona hucce wannan takaicin naki Tace aiba Takaici ne Yace ko Tayi shuru. Yaci gaba Ba shakka abin xaiyi kyau ga Fatima-zarah ga Aisha-Labibah ko Ta kalleshi ka'dan da cewa bakaji da'din hakan bama a bakinka Kawar da fuskarshi yayi Yana rayawa aransa bai ta6a ganin wawiya sha-sha-sha me abin Takaici irin LABEEBAH bah. Haushinta ya cikasa danjin kukanta da yaji tana cewa Ka temaken MeeNi ka Auremu mu biyu dan Allah. Tah qarashe da qarama kukan nata volume Ya kalleta cikin bala'in takaici Yace ke fita min amota Ta kalleshi Tace dan Allah kayi hakuri kakar6i rokona Yace ko Ta gya'da mishi kai Yace Kinsan Allah in baki rufemin baki kin fita daga motar nan ba saina tsinka miki mari Fitta tayi tana binshi da kallo ha'de da hawaye ya gallah mata harara dajan tsaki yaja motar kamar xai tashi sama LABEEBAH ta'dura hannu aka xata rushe da kuka sai kuma tafasa tashige gidansu Rukayya ta kalleta da ta6e baki Tace baiyarda bane. Dan 'daxo na leqo naganki da YUSUF LABEEBAH tamata shuru Saiko tasheqe da dariya Tace damarki xatayi kyau yarinya tunda kinada kyakkyawar xuciyar da xakiso amiki kishiya tunkan kisan meye Auran Kallanta LABEEBAH tayi taci gaba da sharar hawayanta...... XARAH CE tashigo ganin LABEEBAH na kuka taqarasa gareta da sauri tana tambayarta dalilin kukan Tace ba komai XARAH Tace yaxakice ba Komai bayan gashi kuka kike Tace cikinane yake min ciwo XARAH tayi Murmushi dan tasan ba hakan bane Amma dake dama tasan hakan xata faru bataqi kar6ar qaryar tatabah Tace koda naji bara in baki magani Shuru LABEEBAH tayi harta 'dauko maganin tabata Da gaske ko LABEEBAH takar6a Tasha Rukayya tajinjina kai XARAH Tace dama wai Su Sagna ne xasuxo anjima sunkira wayarki basu jikiba Nan farin ciki yacika xuciyarta Tace toh Allah ya kawosu Bayan isha ko sai gasu farin Cikin LABEEBAH yaqi 6oyuwa dan harda Momy Sagna da Safna Suna manne da ita Suna fa'din sunyi missing 'dinta Bayan sungama gaisawa Momy Tace anya ba tafiya Xanyi da SAUBAN ba Innah tayi Murmushi Tace da yau LABEEBAH baxatayi bacci bah dan kuka Momy tayi Murmushi da kallanta Tace toh kwantar da hankalinki 'Yata dan ko 'dakinki kikaje bame rabaki da SAUBAN LABEEBAH tayi Murmushi kawai Momy tabasu tsarabarsu sannan ta suka fitoh dan tafiya LABEEBAH ko ganin hankanin kowa yayi gaba Tace dama Momy inasan magana dake Tace toh gobe xan turo YUSUF ya kawomin ke sai kifa'da minko ina yayi Tace eh yayi Momy tace yauwa toh Allah ya kaimu Hakako suka tafi abinsu Sumayya da LABEEBAH basuso tafiyar tasu bah Washe gari kusan sha 'daya YUSUF yaxo ya kira LABEEBAH ta wayanta yana cemata Yana jiranta. Yana fa'din hakan ya kashe wayan [1:14PM, 05/10/2016] Rahamat Nalele💋: LABEEBAH Murmushi tayi dabin wayar da kallo Tace wannan fushi yake dani. Saita girgixa kai Tace 'Yar uwata xan temaka akanka dan baxan kasance dakai bah. Ita tanacan tana kuka Saka qaramin hijabinta tayi akan doguwar rigarta tayima Rukayya sallama Yana kallo ta shiga gidansu XARAH tayima inna sallama suka fitoh da Sumayya dan tare xasu Koda suka shiga motar kallan Sumayya YUSUF yayi suka gaisa baibi takan LABEEBAH ba yaja motar LABEEBAH tayi Murmushi Tace fushinka balaqine a gareni Kayi hakuri mijina Kamar xaiyi magana sai kuma yafasa Itama shuru tayi har suka isa gidan Kakah Yana yin faking saiga Sagna taqaraso da sauri. Tana murna. Dai-dai nan Sumayya tafitta Sagna ta rungumeta taleqa cikin motar Tace toh saikin shigo Aunty LABEEBAH ta'daga mata hannu alamar toh. Sukayi ciki YUSUF ya harareta Yace kibisu Tace haba MeeNi fushi kake dani Yace inkun gama da Momy kiyi sauri namaida Ku Wato baxai bama xancan nata mahimmanci bah Ta fita ya bita da harara itama tagalla mishi hararar Yayi kwafah da cewa xaki fitone A falan taga momy da Kakah nan taje har qasa tagaidasu Momy tayi Murmushi Tace toh gani 'Yata LABEEBAH tagyara xama yayinda Kakah Tace ina zuwa ta ficce daga falan yarage daga LABEEBAH sai Momy afalan Tace dama Momy so nake Ki roqi Ya YUSUF ya Auremu mu biyu nida XARAH Shuru Momy tayi yayinda LABEEBAH tasunkuyar da kanta Kamar Momy baxatace Komai can tajah numfashi wai ance ta yaro kyau take Amma bata qarko Tace meyasa keko kikesan YUSUF ya Aure Ku kubiyu Tace banasan rabuwa da XARAH ne Kuma nasan Ya YUSUF xai iya riqemu amana Momy tayi dariya da girgixa kai dan tagano quruciya na damun LABEEBAH Dan haka cikin siyar siyasa Tace niko da kinbar XARAH ta auri wani dan xaman Aure xa kuyi ba wasa bah Ina ganin baxaku sami xaman lafiya yanda ke kikeji aranki bah Xuciya bata da qashi LABEEBAH kuma yau da gobe tafi qarfin wasa. LABEEBAH tayi shuru Can Tace Wlhi momy xamu xauna lafiya tana sona ina Santa fah Momy ta girgixa kai Tace shi YUSUF Yace miki Yana Santa ne LABEEBAH ta girgixa kai hawaye nasan xubu mata Momy tajah numfashi da danna number YUSUF a wayanta dan kira. Aiko nan take ya shiga Ya 'dauka Yana fa'din my mom Kaxo falo kasaman yanxu. Toh Yace da kashe wayan Ko cikakken motsi basuyi ba yashigo falan da xama kusa LABEEBAH Yace gani mom Tace LABEEBAH taxomin da xancan tana SO ka Aureta da XARAH shin ya kagani Ya waro ido😳 Yace Wlhi bala'i nagani mom Plx Karki biye wawiyar yarinyarnar Ban ta6a jin XARAH araina ba Akanme xan Aureta...... Aiko saijin kukan LABEEBAH sukayi takama hannun YUSUF Tace dan Allah dan Annabi Yayana ka Auremu mu biyu naroqe da Allah Yace Waike me yake damunki ne kishiya xan miki fah 😳 Tace toh ai 'Yar uwatace kuma ba xamuyi xaman kishi ba... Takai kallanta ga mom da tasake baki tana kallan ikwan Allah Tace dan Allah Momyna kisashi ya Auremu mu biyu plx Taqara Jan numfashi Momy tayi Tace toh naji 'Yata yaushe kikesan ayi bikin Cikin murna Tace idan XARAH ta yaye SAUBAN. Ko Momy Momy tayi Murmushi da gya'da kai Tace toh yanxu sai ada'da 'daga bikin. YUSUF ka shirya Auransu Su biyu ankashe wannan xancan kikwatan da hankalinki kinji 'Yata LABEEBAH tayi Murmushin jin da'di Tace toh Momy xamu tafi Tace tun yanxu Labeebah tace Aunty Rukayya batajin da'dine banaso nayi nesa da ita Momy Tace Yana kyau hakan. Ta kwallama Safna kira Sai gasu dukkansu da Sumayya. YUSUF ko kukane kawai bai sake bah. ranshi ya bala'in 6aci Amma yacije ya tashi Yace ina jiranku amota da sauri LABEEBAH Tace toh Sukaje sukama Kakah sallama Momy tabi LABEEBAH da kallan tausayi dan taso ta mallaki YUSUF ita 'daya dan tasan xai gina musu rayuwar da xusuji da'di kuma ya hucce mata takaicin wasu al'amuran A motar ko bame magana Candai Sumayya tagaji da shurun Tace Aunty LABEEBAH wai yau yana jiku shurune bamai magana acikin ku Shuru LABEEBAH tayi mata YUSUF yayi murmushin yaqe Yace kekuma gwulma ko Tayi dariya Tace Wlhi ba gwulma bane Ya YUSUF kawai naga ba haka kuka Saba bah Yace Auntyn naki ta6amin raine Tace ayya kayi hakuri dan Allah ka yafe mata tayine bada saninta bah Murmushi yayi Yace Karki damu Sumayya xanbi hanyar daxan hukuntata dan baxan barta haka bah LABEEBAH ta kalleshi aiko suka ha'da ido ya sakar mata murmushin mugunta Sumayya Tace kai ya YUSUF baxa dai ka hakura bah Yace Wlhi kuwa Sumayya Dai-dai nan yayi faking kofar gidan nasu Sumayya tafita tana yimai mungode ya 'daga mata hannu alamar Bakomai Sainnan ya juyo da kallansa ga LABEEBAH Yace toh Uwar gida ya akayi ne Tace plx MeeNi karka cutar dani akan abinda tausayine yasani aikata Komai Yace kinga Uwar gidana kwantar da hankalinki ba wani abunda xan miki. Kawai inasone Ki gayamin kalmomin da xanji cikin raina susani nisha'di ako yaushe idan na tunasu Tayi shuru . Yace no fah inkin shiga wani hali karkice Komai. Bani numvar XARAH kinga inna nema agunta nasan baxata jamin ajiba Gaban LABEEBAH yabada dam takalleshi ya kashe mata ido Cikin sanyi Tace I luv u Yace shikenan Tace toh Xanyi missing 'dinka MeeNi Tana fa'din haka tafitta daga motar tashige gida. Ya bita da harara xuciyarshi na mishi xafi akan yanda ta qaqaba mishi XARAH gashi ya shirya musu rayuwar da yakesan suyi yanxu ta6ata mishi shiri Koda yaxo Washe gari jona mata hauka yayi yabarta Abin da ya faruko shine bayan sungama gaisawa Yafara maida hankalinsa ga 'kofar gidansu XARAH Tace me kake kallo ne Yace Wlhi XARAH ce nakesan tafitoh in ganta ko nasamu Sauqin xuciyata Tace what 😳 Har kafara santa ne Yace eh sosaima ayanxu ke da ita bansan wacce nafi sobah Tun jiya dana koma gida hotanki da XARAH na 'dauko ina gwada acikin ke da ita wacece tafi kyau Ashe tafiki kyau ke'din axuciyata kawai kike Gaskiya XARAH ta ha'du inasan tah sosai Kuka LABEEBAH ta fashemai dashi dan Wlhi wani irin 6acin raine ya kamata Wanda inxa'a kasheta baxatace ga abinda yasa bah Cikin nuna tashin hankali YUSUF ya janyota jikinsa yana cewa me ya faru Tace nidai kadena min xancan XARAH Yace oho XARAN taki kuma yau itace bakya san amiki xancanta Ta 'dagamai kai Yayi Murmushi yace toh baxan qaraba. Haka yata lallashinta daya tashi tafiya harsunyi sallama takai 'kofar gidansu ya biyota Yace tabashi number XARAH Miqa mishi wayanta tayi kawai Tana takallo yaciri numbar haryana matsowa kusa da ita wajan rubuta suna Itako har tana leqawa taga sunan daxai sah Nan taga yasa *farin ciki na* Sai yanuna mata numbarta Yace kinga ke *nutsuwata* ita kuma farin cikina. Yayi dai-dai ko nacanjah Cikin Takaici ta kar6i wayan nata tayi cikin gida da gudu Shiko cikin 'daga murya Yace nutsuwata banji an kiraki bafah....... Ko kulashi ba tayi bah YUSUF yayi murmushin mugunta ya shige motarsa ya tafi Tuqi yake Amma fa"di yake aransa ina sanki LABEEBAH ina qaunarki Amma Baxan ta6a yafe miki akan yanda kikesan ha"dani da XARAH bah. Xan hukuntaki dan in gyara miki tunaninki Tun daga ranar YUSUF yasaka LABEEBAH agaba Duk abinda yasan idan yayi xai cakalo kishinta shi yakeyi. Haka xai saita kuka kuma ya lallasheta Amma bashi xaisa anjima ya kuma sata ba Ga shi yaqi yarda Sam ya ha"du da XARAH dan baya buqatar hakan Amma sai ya dinga nunama LABEEBAH kullun suna tare da XARAH a waya Suna hira Gaskiyane LABEEBAH na ganin ayah arayuwarta Yanxu ciwan kishin YUSUF ne yasata agaba Haushin XARAH takeji kamar ta shaqeta Amma saboda iya xama da Mutane ko afuska bata ta6a nunama XARAN ba Abinne ya ha"du mata biyu Na farko takasa mantawa da KAMAL dan kullun saitayi kukan rashinsa cikin dare Batayi wasa da wata sarqa me zobe da abin hannu dashi KAMAL 'din ya ta6a siya musu ita da XARAH ba. Kullun kallan zoben takeyi tamkar shi KAMAL 'dinne ya saka mata ahannunta Takan 6ata lokaci wajan Ganin hotansa Takanyi kuma dariya idan ta kalli SAUBAN XARAH tagama shaqer LABEEBAH aranta dan ba wacce ta tsana aduniya kamar LABEEBAH Tsanarko taqarune saka makwan 'dauke qafar da YUSUF yayima gidansu Dama tahakanne take samun Sauqi axuciyarta Dan Ganin shine samun nutsuwata Amma ya 'dauke qafah Ko zuwa yayi saidai yasaka Sumayya ta kar6o mishi SAUBAN in lokacin baya gun LABEEBAH LABEEBAH ko saidai tata6e baki Tace kana wani alaye kashiga gidan

Chapter 12 of 22