Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
magana YUSUF ya shigo Ya gaida Yayan nashi XARAH takafeshi da ido tana cewa kabari direva ya kaisu man Ya gallah mata harara Momy tayi Murmushi Sagna da Safna suka fitoh daga 'dakinsu Safna Tace gaskiya banji da'din tafiyar nan taku da xakuyi bah Aunty LABEEBAH Sagna takama hannunta Tace Xanyi missing 'dinki LABEEBAH Tace karku damu bayan muna tare Haka suka loda musu kayan Su amotar YUSUF Wanda Momy ta shirya musu shatara ta arxiqi sukayi sallama wa juna Sannan suka cale garin na Kano Ko amotar soyayya sosai YUSUF ya bu'de mah LABEEBAH shafinta Sumayya tanajin Su cikin sha'awa tana Murmushi LABEEBAH ko tun tana biye mishi har tadawo tadena biye mishi bacci yayi awan gaba da ita Ahaka suka iso lafiya hankali kwance Innah da ya Usman saiganin Su kawai sukayi wayyo murna kamar suyi yaya Innah fa'da take kunyi kyau sosai yaran kirki musamman ke LABEEBAH Haka Rukayya ta damama YUSUF fura da nono mesanyi Innah takawomai abinci irin na gida dambu Nan YUSUF yaci ya 'koshi ya kora da nono Sannan suka ke6e Shida da LABEEBAH Tace yanxu sai gidan Kakah ya 'dauka ko Yace eh Xanyi mata kwana biyu kinga jibi sai in tafi. Tace toh kaishemin da ita Yace har yanxu xan qara roqarki abu Tace inajinka Yace kimin alqawarin baxaki yarda ya KAMAL ya ganki bah dukko xuqanda xaiyi Karki fitoh gareshi Tace namaka alqawarin shi kenan Yace hmm Kallansa tayi takyau Lalle kishin YUSUF ya fara damunta Tace kanada kishi ya YUSUF Yace idan banyi kishinki bah kishin waxanyi Yafa'di hakan a fusace Sunkwai dakan ta tayi Abuja 🌡🌹🌡 Koda YUSUF ya koma bai xame ko ina bah sai office 'din KAMAL Yasameshi ko Yana aikin tunanin LABEEBAH Yace sannu da aiki Yayana Yace Yauwa dafatan kadawo lafiya Yace qalau Kakah na gaida kai sosai wai yaushe xakaje KAMAL yayi Murmushi Yace Kakah ko rikici Shuru suka 'dauka nawani 'dan lokaci candai YUSUF yashi daniyar tafiya KAMAL ya kirashi Da sanyi yadawo ya xaunah Yace nalura akwai abinda yake damunka plx kafa'damin Sosa qeya YUSUF yayi Yace hmm Bakomai KAMAL Yace dan Allah kafa'damin banasan damuwarka YUSUF yajah numfashi ya sunkwai da kansa Yace Wlhi Yaya bansan yaushene nakamu da Santa ba. Plx yayah katenaken dan Allah dan Allah katemaken Saiga hawaye KAMAL ya qura mishi ido gabansa na fa'duwa ya ta6a fuskar YUSUF da dangwalo hawayansa Yace yau kai kake kuka YUSUF Yace Wlhi Yayah kusan kullun sai nayi akanta Yace wacece YUSUF ya kalleshi ka'dan Yace Aisha-Labibah Rumtse ido KAMAL yayi ha'de da dafe kanshi tashin hankali ya baiyana qarara agare shi YUSUF ya lura da hakan dan haka yaqara cewa Wlhi Yayah santa yajefani cikin tunani damuwa tashin hankali katemaken Yayah xan iya mutuwa akanta Wlhi. _xuciyarta tawace Ni ka'dai. idan nabar maka LABEEBAH baxakaji da'dinta bah har abada. nine dulmiye aranta xaka mallaki gangar jikinta ne qanina Amma banda xuciyarta. Ina sanka xan iya sadaukarma da soyayyar LABEEBAH koda Ni xan rasa nawa ran_ KAMAL ya fa'di hakab aransa xiciyarsa namasa xafi hankalinsa tashe Da hawaye ya kalli YUSUF Yace kaje qanina nabar maka LABEEBAH sai kayi qoqarin neman xuciyarta Da murna YUSUF yatashi ya rungumi Yayan nasa Yace ina sanka Yayana Allah yabarmin kai Ya gya'da mishi kai YUSUF ya fitta Hmmm Ni Rahamat Nace tab anya hakan xaiyuhu Hmm ba ruwana kudai biyoni Karku damu xuwa dare xan yo muku wani post 'din juhuta lpy KAMAL yabishi da kallo dagaske yaji da'di aransa Yanda yaga farin cikin qaninnasa Kasa aikin nashi yayi haka ya dawo gida yanasan yin jinyar kansa Koda XARAH tashigo bet room nashi ganinsa tayi cikin xaxxafan xaxxa6i Arikice take tambayarsa meya jawo mishi wannan xaxxa6in Tafa'da tamai bashi maganin xaxxa6in Kar6a yayi yasha Yace na rasata TEEMAH na rasata.... Tace wacece Yace AISHA Tace au dama sunanta kenan Yace eh kuma na rasata har abada Da xaro ido Tace yanxu kana nufin ka sadaukar ma wani ita Yace eh gamama kinsa sai yaga tatsaya cak tafa'da tunani Yace yadai Saurin gyara kanta tayi Tace hmm Bakomai. Yanxu dai kafasa auran naka Ya rumtse ido Yace eh Xama tayi agyfansa kawai tana kallansa. YUSUF ansamu abinda akeso sai murna yake yaudai yayi maganin matsalarsa Momy takallesa Tace nakwana biyu banga farin cikinka irin nayau bah Yace eh Wlhi Momy yaudai nayi maganin matsalata Tace miye matsalar taka Yace nasa mam miki sirika Takalleshi da mamaki Tace wacece wannan Yace AISHA LABEEBAH 'yarki Cikin wani farin ciki Tace kai Amma naji da'di ka biyani YUSUF kuma kodama bakaxomin da wannan vatun bah nayi alkawarin aura maka ita Yace toh gashi naxo miki da batun saiki bani tukwaici. 🌡🌡🌹🌹🌡🌡 Bayan watanni hu'du da kwanaki Tundaga ranar da KAMAL ya sadaukarma YUSUF soyayyarsa da LABEEBAH baiyi gigin kiran wayanta ba Allah sarki yayi dan gana ga Allah ya bama Allah amanar kansa Duk wani abu daxaiyi dan ya kori soyayar LABEEBAH aransa yayi yayi Amma abin yaci tira Saiyaga kamar qara mishi MASEEFAR SONTA akemai Lokaci lokaci yakan kulle kansa yayi kuka sosai ya lallashi xuciyarsa XARAH na kallansa saidai tabishi da na mujiya Amma duk da haka bai manta da ranakun al'adar LABEEBAN tashi bah Dan yanaba YUSUF maganin nata YUSUF xirga xirga tasashi agaba. Dan kusan kullun Yana kan hanyar garin na Kano Yana quqari sosai wajan ganin ya cire soyayyar KAMAL a baxuciyar LABEEBAH Yasani duk alaye take masa wajan nuna yanxu shi takeso Amma yasan har ixuwa yanxun yasan Yayan nasane aranta Momy tayima dadynsu KAMAL maganar soyayyar YUSUF da LABEEBAH kuma dasan akai ku'din Aure da saka ranah Abin ya mishi da'di sosai Dan haka yatada 'dan uwansa na kano Yace yanasan sujega gidansu LABEEBAH Hakako akayi nan Baban XARAH da Ya Usman sukayi na'am da batun Musamman da aka tambayi LABEEBAH Tace eh tana San YUSUF Dan haka aka saka ranar Aure wata biyu masu xuwa. Al'amarin daya hautsina KAMAL da LABEEBAH kenan Wanda awannan ranah basuyi bacci bah Sai tunanin junansu da suke LABEEBAH takasa jure tunanin dan haka kawai ta6are baki ta riski kukanta San ranta Washe gari sai tatsinci kanta da kiran KAMAL. Yana 'dauka tarushemai da kuka sosai Yana jinta yamata shuru candai da Kukan nata yafara qoqarin saka mishi ciwo yayi saurin cewa me ya farune baby Tace yanxu ya YUSUF shine xai xamo Miji agareni Yace eh Tace haba mana Ya KAMAL kace wani abu mana xuciyata namin xafi Yace plx my baby ki temaken ki kasance cikin nutsuwarki Tashin hankalinki shine tashin hankalina Kiyi addu'a Allah ya fiddamu daga wannan MASIFAR Cikin sanyi Tace toh Yace Yauwa babyna iyi dariya Naji Tace saidai Murmushi Yace ko shine kiyi Naji da'di plxxxxxxx Tayi murmushin cikin kuka. Yace Yauwa Babyna albishirinki Tace goro Yace saikin share hawayanki xan fa'da miki Aiko da sauri tashare hawayan kamar tana gabansa Yace yanxun nan 'Yar uwarki XARAH ta aihu..... Da sauri Tace dan Allah Yace da gaske Tace wayyo da'di kasheni me aka samu Yace namiji Tace dawa yayi kama Yace kicanka Tace toh tsaya inyi tunani Yayi Murmushi Yace axaune nake mah my baby Tace xanso yayi kama dakai Yace toh kamarmu mah 'daya kincanka Har aransa yaji dariyarta Yace my baby........ Taji sunan har ranta Tace na'am Yace wane suna kikesan asa mishi Tace Ni kuma Ya KAMAL Yace eh kee ina cikin office 'dina yanxu haka Ita kuma tanacan tana hutawa baby Yana hannunsu Momy Xanji da'din yanda nasamu nutsuwa awannan lokacin kifa'di ra'ayinki akan babyn nan Wlhi my baby ra'ayinki shine nawa Tajah numfashi Tace toh asa mishi MUHAMMED-SAUBAN Yace yayi Yayi my baby Tace toh yanxu ya xa'ayi xuwanmu Yace ya kikeso my baby Tace xataxo wankan gidane Yace hmm in yau kikesan suxo garin Kano Wlhi yau xasuxo Tace toh suyi kwana uku sai suxo Yace angama shikenan Tace eh Amma...... Saitayi shuru Ya gyara xamansa Yace Amma me Plx dan Allah kar kiqi fa'da Tace toh dama inasan in ganka ne...... Taqarashe da sanyin murya Shuru yayi Tace Amma..... Yayi saurin katsata da cewa yaushe kikesan ganin nawa Ta lumshe ido Xuciyarta na cewa kice yanxu Amma ganin rashin dacewar hakan yasata cewa. Inasan Ranar da xasuxo ya kasance inganka Yayi Murmushi dan yagane fa'din hakan kawai tayi Amma ba hakan bane Cikin ranta. Yace toh Allah ya kaimu Tace AmEEn Suka ajiye waya jiki asanyaye Rukayya Tace dawa kike waya Tace da ya KAMAL ne Tace Naji kina murna kamar XARAH ta aihu Tace eh ta aihu namiji ta aifah mah da murna Rukayya Tace kai Amma Allah ya raya Tashi tayi taxari gyale daniyar xuwa gayama inna Tace AmEEn [9:47PM, 30/09/2016] Rahamat NaleleπŸ’‹: 🌡🌡🌡 Kwana ukun ko nayi Su XARAH suka diro kano harda Momy agidanta tasauka Su Momy ko shashin Kakah Aiko ko minti biyar LABEEBAH da Sumayya basu yiba dukayi gidan Jariri na hannun LABEEBAH taqi bama kowa Sagna da Safna mah suna maqale da ita fa'di suke yau gamu gaki Aunty LABEEBAH Tace eh nayi missing 'dinku sosai YUSUF ya shigo da waro ido Yace eh lallene da gaske tunda gaku LABEEBAH Tace me yafaru Ya harareta Yace watoh nace miki hardani akan hanya kuma gareki xan fara xuwa shine kika gudo nan dan xumu'di Tace ayya MeeNi kayi hakuri kasan baxan iya ba baxan iya qara ko minti 'daya bane wajan xuwa gun baby Yace hmm ai kinganshi saiki tashi muje dan nadawo da 'daukin ganinki da San hirarki Kai Ya YUSUF ban gama ganinshi bafah Ya miqa mata hannu alamar tabashi babyn Da turo baki ta bashi Aiko direct kan cinyar XARAH ya ajiye babyn Yace kiji dashi dan nutsuwata taji dani nimah Mugun kallo XARAH tajefeshi dashi bai lura bah yajah hannun LABEEBAH suka ficce Su Sagna suka sheqe da dariya Wajan shaqatawar gidan yayi da ita nan sukasha soyayyarsu Amma xuciyar LABEEBAH na muradinga San ganin KAMAL Saidai taji da Sumayya take tambayar XARAH shi Taji XARAN Tace mata baisami xuwa bah dan ayau 'din yatashi bayajin da'di Tana ganinma sai bayan Suna xaixo LABEEBAH tayi saq dan da gaske hankalinta yatashi Aiko ke6ewa tayi takira number nashi taji akulle Kiran duniya yaqi shiga πŸ‘―πŸ‘―πŸ‘―πŸ‘―πŸ‘―πŸ‘―πŸ‘― Yau asabar Yakama kuma yaune suna dan haka akasha Suna aka ra6ashe Abin sha'awa da jin da'di. Gaskiyane duk yanda kaso ganin sunan ya xarce tunaninka. Mejego tasamu kaya na nunama sa'a Yaro yaci Suna MUHAMMED-SAUBAN Yau kwana biyu dayin Suna Amma har yau LABEEBAH taqi jin KAMAL awaya Kuma abinda ya bata mamaki XARAH bata wani damu Yanxu haka Suna tare LABEEBAH da XARAH LABEEBAH Tace niko lafiya Ya KAMAL shuru. XARAH tayi Murmushi Tace Yana lafiya dan 'daxu muka gama waya wai Yana kan hanya mah Kinga yanxu qarfe uku inaga xuwa 4 xai sauka. Ko ba komai Hankalin LABEEBAH ya kwanta Amma me yasami numbar tashi da take dashi yadena amfani da itane Wannan tambayar bata da amsa inba agun XARAH bah Ita kuma baxata iya tambayar tabah XARAH Tatashi tana kallan agogo Tace kinga xan kar6i wani Abu agidan wata qawata dataxo nan kano kuma har na gayama KAMAL ya kamata inje yanxu kafin ya qaraso LABEEBAH Tace bai dace kifitaba kimin kwatancan gidan inje in kar6o miki Kinga kar wani yaxo ganinki bakyanan Tace saikice musu na shiga wanka. Kuma baxata baki bah dole saidai Ni Kuma kinga gobe ne tafiyata gida wankan gida Kinsan kuma Innah baxata barni fittaba Dan haka plx dan Allah Kikula da SAUBAN kuma Karki bari Momy tasan bana nan Da kallo LABEEBAH tabita har tafita Hmmmmmmm Al'amarin ya farune lokacin da KAMAL ya iso kano Yana jiran direban Kakah yaxo ya 'dauke shi sai yaga wata motah ta faka a gabansa wani 'dan saurayi ya fitoh da fara'a Yace yalla6ai muje ko KAMAL yamai kallan raini Yace waya turoka Yace XARAH CE ta turoni wai dereban Kakah yabajin da'di Cike da yarda KAMAL yashiga motar. Aiko Yana shiga wani ta bayansa ya rufe mishi hanci da baki Nan take KAMAL ya sume Sai me😳 Tsintar kanshi yayi a wani fanta meman gida Ya bu'de idanshi ahankali kana ya sauke akan mutunan Su biyar ne manyan qatti masuji da qarfi kallo 'daya xaka musu kagano rashin imaninsu Kan yayi magana yaga 'daya daga cikinsu yaje je da gudu ya bu'de get 'din gidan wata mota ta shigo sai yaga wata qatuwar mata tabu'de 'kofar ta fito Qurama matar ido yayi yana tuna inda ya santa........ Saidai kan ya tuna XARAH tabiyo matar wajan fitowa Jameel ya biyo Bayan tah KAMAL ya murje idan Sa da kyau aiko yaga XARAN shice cikin shigar riga da siket tayi kyau sosai taci tabarau saikace ba kwananta Tara da aihuwa bah Ta qaraso gareshi ta xare tabarau 'din tana tafah hannu Sannan takalli wa'yannan qartin Tace wow aikinku yayi kyau Sannan taqaraso daf da KAMAL Tace kayi mamaki ko ba mamaki idan kayi mamakin. KAMAL kenan Da XARAH kake ba gixo idanka yake maka ba Kasan dalilin dayasa nasaka aka kawoka nan Xubah mata yayi baice Komai bah Hmm nasaka an kawokane dan na kashe kah KAMAL ranah ta biyu da xuwana Abujah ranar da mukaje dasu LABEEBAH A ranar na kamu da MASEEFAR SOON qaninka YUSUF Sai narasa yanda Xanyi da raina dan Ni matar kace Sai ya kasance akoyaushe inasan naga YUSUF Hankalina ya tashi dan tuna har abada baxan mallaki YUSUF ba Ina cikin wannan saiga Hajjiya turai makwaf ciyarmu gata. Tanunamai wannan qatuwar mata Tace taxone taxama aminiyata dan talura ni sabowar zuwace Niko Nayarda da batunta dan naga tadace da taxama aminiyar tawa Inba ka mantaba ina nagaya maka xan shiga gunta Dake kana ganinta aguna saika lamince akan inje gareta To sai dai me Ranar taxo taganni cikin tagumi da damuwa Tatambayeni matsalata niko nagaya mata Kasan inda Wanda xan gayama matsala toh LABEEBAH CE Amma Kasan ko karan haukane ya cixan baxan tun kareta da wannan batu bah Anan nida Hajjiya Turai muka shirya kasheka Amman saina aihu Dan inci riba biyu Tafarko idan nakasheka xan sami YUSUF Na biyu duk wata dukiyarka taxama tawa danna aihu dakai Tajah numfashi anan Sannan taci gaba da cewa In gaya maka wasan da kada'de kana bugawa tunaninka ban saniba Shine soyayyarka da LABEEBAH Akwai wata rana dana cema LABEEBAH nifah ixuwa yanxu nafara tsanar KAMAL 'dinnan Ina nufin wanda take so Bu'dar bakinta Kasan metace min Hmmm Gwarama kidena dan abin sankine Tun daga ranar nafara bin tunaninta da yanayinda nakane kaine KAMAL 'dinta Sai dai awannan lokacin baxan iya bar mata kaiba Saboda kayi tako ta ina duk Wanda Yace baka iya luv bah yayi qarya Kai gwanine musamman dana kasance matarka Nagano abubuwa da damah agame dakai Amma meyasa nakamu dasan qaninka YUSUF Kana wani maganar kakamu da MASEEFAR SON LABEEBAH YUSUF Yana cewa ya kamu da MASEEFAR SONTA Tana cewa ta kamu da MASEEFAR SONKA Ni kuma fah meca'a kirani kenan. Ina matar Aure Kaga sai ace na kamu da babbar MASEEFAR SOO dan taxarce taku Tasan wani ba Mijina bah. Kuma wanin qaninka Ni XARAH Ni yadace da akira da nafa'da ~MASEEFAR SOO~ Ayanxu ba abinda natsana kamar LABEEBAH tsana ko me muni Tunda Wanda nakeso ita yake so Baxan kasheta bah Dan tana sona Musamman yanda ta6oye soyayyar da take maka soboda Ni Lokacin da ka ankare da son da take maka ban damu bah Saboda mun rika mun gamah shirinmu Amma da kaxo min da batun kasadaukar da soyayyarka nadamu Dan hakan Yana nufin YUSUF xai samu LABEEBAH Duk wannan kukan da nake maka duk na gwajine dan Naga wane irin kisa xan maka Kidan kanuna tausayina in maka mutuwar sauki indan kuma ban baka tausayiba in maka mutuwar rashin imani Xan auri YUSUF dan nawane Ni 'daya San nan tare xai Aure mu Ni da LABEEBAH dan tahakan ne xan gasata san raina Lefinta ko shine na yanda ta yarda da auran YUSUF Baxan ta6a barin YUSUF ya Santa bah Dan baxan iya jure wannan bah Xan axab tar da ita sosai cikin makirci idan kuma takawo min matsala sai in kasheta Ta kalli Jameel Tace bani bindigar nan Aiko Jameel ya miqa mata bindiga Yana cewa karkayi mamakin ganini KAMAL haka rayuwa take. Kasan ina MASEEFAR son LABEEBAH Amma katake kafara Santa Na ha'de da XARAH ne akan wannan cin amanar da kamin XARAH Tace baxan ta6a samun YUSUF bah har sai ka mutu KAMAL Xan maka wata alfarma shine...... Taxaro wayarsa a gaban rigarsa ta qarashe da cewa xan kira maka LABEEBAH ka gaya mata kalmomi uku na soyayya Dai-dai nan numbar LABEEBAH tashiga LABEEBAH naxaune da jariri ahannunta yana qananun kuka Tace ko a ina XARAH ta tsaya oho tajah saki Sai taji wayarta na ringin tana dubawa taga KAMAL aiko da sauri ta'dauka Tace hello Ya KAMAL KAMAL yayi Murmushi me ciwo Yace na'am Babyna XARAH ta'daga mishi yatsa 'daya alamar saura mishi kalmomi biyu BABEEBAH Tace nayi fushi dakai tunda kaqi xuwa tun ran uku Yaqara yin Murmushi Yace I LUV U Sannan yajah numfashi yaqara cewa Karki yarda da kowa arayuwarki cikiko harda ~XARAH~ Gaban LABEEBAH ya fa'di Tace meyasa kace haka Shuru taji wayan tayi tana dubawa taga ankashe Tayi saqalo da wayan tana kallo A canko XARAH CE ta'amshe wayan sanda taka she Sannan Tace kalmominka sunqare sai kuma acan Karka damu nasan ka aikata kyakkyawa arayuwarka dan haka ina maka fatan alkairi Aiko jikake fas... fas.... XARAH ta sakarma KAMAL harsashi biyu 'daya a qirji 'daya a cikinsa Nan KAMAL ya riqe cikinsa da qirjinsa Tace karka damu *~MASEEFAR SOO~* ne yajah maka haka Suna kallo har yadena motsi sannan takalli qartannan Tace kusan yanda xakuyi kujefar min shi a babban rafi Wanda abubuwan ruwa xasu cinyesa yanda bawanda xai gansa Kudauko wannan gawar data dagargaje kusaka wannan fuskar da aka ha'da tasa akan ta mutumin. Kuyi yanda baxa'a gane bah Sannan kuxo Ku ajiyeshi 'kofar gidana Da 'dayanku ya tsaya dan fa'dar shuru mu Sukace an gama ranki ya da'de Jameel Yace naji basira Allah yajah da xamaninki XARAH Tayi Murmushi da cewa muje ko Haka suka shige motar da sukaxo suka ficce Su kuma qartan nan suka saka KAMAL a motarsu suma suka ficce dan aiwatar da abinda XARAH ta umarcesu dashi LABEEBAH ko saqalo tayi da waya ahannunta tana tuna me KAMAL Yace mata Nan take jikinta yayi sanyi saitaji hankalinta ya tashi. Kuma sai jitake gabanta na fa'duwa Taxauna gyefan gado tana tunani batasan adadin da ta'dauka tana tunanin ba . Saiji tayi XARAH ta dafata A'dan furgice ta kalleta Keko mexaisa saki shiga tunani haka bayan nabarki lpy LABEEBAH tajah numfashi Tace hmm haka kawai naji gabana na fa'duwa XARAH tayi Murmushi Tace ki kama salati xaki dena ji Ai nama 'dauka tunanin KAMAL 'dinki kike Tace eh harda tunaninshi XARAH Tace koda Naji Am ba wanda yaxo nemana Eh babu saidai SAUBAN ya 'danyi kuka ka'dan LABEEBAH tace da ita hakan tare da miqa mata shi Xama XARAH tayi takar6e shi da jan tsaki Tace toh mezan mishi LABEEBAH Tace ban gane mexa Ki mishi vah kibashi nono man Tace Tab ai daga yau nayanke bashi nono. Dan banaso na tsufah Cikin tsoran furucin nata da xaro ido LABEEBAH Tace me kenan kike nufi Kina nufin yau kin yanke ba shi nono saboda banxan tunaninki Cikin fusata XARAH Tace eh haka nake nufi baxan qara bashi nono bah dan banasan suxube in tsufa da wari...... Kan LABEEBAH tayi magana saiganin Sagna da Safna sukayi sun shigo agigice suna kuka. Cewa suke Aunty XARAH Aunty XARAH aunty LABEEBAH Munrasa Ya KAMAL ya KAMAL yayi hatsari ya mutu ya da gargaje ya mutu Atare LABEEBAH da XARAH suka kalli juna. Aiko XARAH tatashi gabaki 'daya saiji kake tim SAUBAN Tafa'di qasa Qararsa tayi dai dai da 'dora hannun XARAH akaπŸ™†πŸΌ ta kurma wani uban ihu Wanda duk Wanda yake makwaf taka da ita toka yaji wannan ihun Tarushe da kuka me qara tare da fallewa da gudu waje Safna tabita. Yayinda Sagna ta'dauki SAUBAN dan ba qaramin kuka yake bah LABEEBAH ko gabanta yabala'in vada dummm cikinta ya 'duru ruwa Tasaka aranta ba KAMAL bane ya mutu Dan haka XARAH na shekawa aguje itana tabita Saidai me 😳 Tana xuwa farfajiyar gidan taga Momy axube YUSUF axube da alama sumewa sukayi. Yamaida kallanta ga XARAH wacee taketa xabga kuka tana surutai. Nan taga gawar mutum fuskarshi ta KAMAL sak Ahankali taqarasa aiko KAMAL ne fuskarsa kawai xaka gane Kasan shine Jijjigashi XARAH takeyi tana kuka tana fa"din meyasa kamin haka KAMAL me yasa me yasa Kasan in bakai baxan iya rayuwa bah Na shiga uku ni XARAH Wlhi binka Xanyi KAMAL binka Xanyi wayyo Allah Duk wa'yanda suke gun saida suka tausayama XARAH Salim ya goge hawaye yajata Yana cewa kiyi hakuri XARAH Luuuuuuuuuu..... Suka ga LABEEBAH taxube a qasa ba tambaya kasan sumewa tayi....... Duk Su ukun akasa amota sai asibity Wasa gaske KAMAL ne yayi hatsari ya mutu Garin yayah Me yakai ya KAMAL hawa motar haya Bayan munyi waya dashi Yace min xai shiga jirgi kenan Meyasa yafasa bin jirgi yabi motar haya Da har 6arayi suka taresu. Ganin hakan yasa direbansu yin daji lamarin yafaru Salim ya dafah YUSUF Yace duk wa'yannan tambayoyin naka shine xai baka amsarsu. Kuma kaga yanxu Bashi dan ya rigamu gidan gaskiya YUSUF wanda ya riga Momy da LABEEBAH farfa'dowa Ya share hawayansa Yace yanxu kana nufin ya KAMAL ya mutu ya barni yabar Momy da Dady da kowa Shuru Salim yayimai dan ya fara Ganin alamun hankalin 'dan uwan nasa yafara fitta daga gareshi Momy mah batafi rabin awabah ta farfa'do Aiko sai kuka take tana ambatar KAMAL ne ya mutu jama'a ya mutu Dadyn su KAMAL mah shima da yaji lamarin yanke jiki yayi yafa'di daqer aka samu ya farfa'do Lamarin XARAH ko abin tausayi dan duk me hankali idan ya ganta saiyaji tausayinta Ahaka akakai gawar KAMAL gidanshi na gaskiya LABEEBAH fah😳 Har Bayan uku bata farfa'doba Al amarin da yasa YUSUF dasu Momy Su Innah shiga tashin hankali kenan Nan hankalinsu ya koma kanta. Akwana na biyarne tafarfa'do lokacin ba kowa dan Sumayya ta shiga toilet Aiko LABEEBAH tafashe da kuka sosai tayi tayi tayi San ranta. Sumayya tayi mata lallashin duniya Sam LABEEBAH taqi sauraronta. Itadai kukanta take tana tuna kalmomin da KAMAL ya fa'da mata YUSUF da Ya Usman suka shigo Xuwa lokacin tadena kukan dan tuna wani Abu da tayi YUSUF Yace am sorry Ta sake mishi murmushin yaqe batace Komai bah Bayan wata uku XARAH taqara kyau sosai sai kace ba wacce mijinta ya mutu bah Komai yinsa takeyi cikin jin da'di SAUBAN yayi wayo saidai ya rasa nonon Uwa dan Sam XARAH bata Bashi nono Sai aikin 'dirka mishi madara da takeyi Ita kuma sai magunguna da takesha. Dan suqara yin tsaf Innah ko bata ganewa Dan idan Yana kuka tace tabashi nono saita

Chapter 11 of 22