Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
XARAH Ahaka taci gaba da 'daukar dakwan sanshi. Batare da yasani ba itama XARAN bata sani bah Ahaka Qanin KAMAL 'din yaganta yanaso suka fara soyayya. A lokacinne kuma KAMAL ya Ankara da soyayyar da LABEEBAH takemai shima ya kamu da santa duk da sun 'dan samu cakwakiya atsakanin KAMAL 'din da qaninsa YUSUF Amma KAMAL yana barma YUSUF 'din LABEEBAN Saidai YUSUF bai kaiga cimma burinsa bah. Dan kwana 9 da aihuwar XARAH suka buga wani wasa takashe mijinta KAMAL akan afkawa MASEEFAR son qaninsa YUSUF da tayi kuma taci alwashin auransa koda ko ya Auri LABEEBAH ne Munso mugano inda suka yada gawar KAMAL Amma oga bamu gano bah Sai dai sun buga wani wasa akan kai wani amatsayin shiya mutu XARAH tanacin ganabar Auran YUSUF ta sanadinga ita LABEEBAN Saidai bincike yanuna da akayi Auran sam XARAH taqi yarda YUSUF ya kusanta da LABEEBAH saboda kishi Tasa meshi yanda takeso Tun LABEEBAH nayin hakuri da ita har hakurinta ya kasa 'daukar hakan Har sukayi musayar yayu akan shi YUSUF 'din Ana cikin haka kawai wani Jameel wanda yasan komai akan shirin da su XARAH sukayi dan harda shi acikin wa'yanda aka kashe KAMAL mijinta ya nemi da XARAN data saka YUSUF ya saki LABEEBAH. Ita kuma takowo mishi gaddama har dai takaisu da musayarsa kalamai me xafi Daga qarshe XARAH tasa akashe mata shi Tamkar Jameel ya ankare ya kira YUSUF ya gayamishi Komai akan hanyar da tabi dan tamallakeshi Sanadinga sanin hakan da YUSUF yayine yasashi kamuwa da ciwan xuciya Wanda har takaishi da xuwa qasar indiya jinya acan ya mutu....... Anan MALUDDEEN ya katseshi da cewa ya mutu. Kana nufin YUSUF ya mutu Yace ko shakka babu oga YUSUF ya mutu Sannan yaci gaba da cewa Munsami labarin rayuwar gidan YUSUF ne abakin qawar XARAH Hajjiya Turai wacce. Itama muka 'dora bincike kanta ta kasance 'yar mafiya CE 'yar ma'digo CE Farkon Ganinta da XARAH jitayi tayi mata aharkarsu ta ma'dogo lesbian shine tadinga bin tunaninta harta sameta yanda takeso Amma har yanxu bata futoh mata da martarta filiba tabari sainan gaba yanxu haka shirinta akan XARAN yake tana San shigar da ita Cikin kwingiyarsu ta mafiya Sannan tana San 'dauke SAUBAN 'dan XARAN tabama shugabansu na kwingiyar tasu dan wata rana yaga shi SAUBAN 'din Yace mata yana buqatar jininsa. Itako tamishi alqawarin xata kawo mishi shi....... Buga table 'din gabansa MALUDDEEN yayi Yace impossible.... Da 'daukar wannan ledar da wannan mutumin ya ajiye agabansa yabu'de Hotunan LABEEBAH ne kaca kaca. Wanda Sam bata San an 'dauketa bah. Sai qarin bayanai akanta cikin wani book Sai wani plash da yagani Nan ya 'dauka yasaka jikin laptop. Aiko yayi toxali da videos 'din da aka 'dauka nata Duk na dumuwar da tashigane bayan mutuwar YUSUF da kai SAUBAN skull data keyi tadawo dashi Sai na qarshe daya gani Wanda yaga abinda ya wakana tsakaninta da XARAH Wajan neman yafiyarta da XARAH tanema da kuma ro'karta ita LABEEBAN tayi akan tabar mata SAUBAN karta rabasu MALUDDEEN ya runtse ido kallo 'daya xakamai Kasan ba qaramin xafi xuciyarshi take maiba Yace YUSUF ya mutu Hajjiya Turai xata kashe SAUBAN wanda LABEEBAH takeso ayanxu kamar ranta takaima shugaban tsafinsu Hmmm yayi murmushin yaqe wanda yafi kuka ciwo Yace kusan yanda xakuyi kuba SAUBAN tsoro banasan LABEEBAH ta rasashi plx Mutumin Yace angama ogo ya fa'di hakan da duqawa ka'dan Sannan ya ficce daga office 'din Abayyane MALUDDEEN Yace Plx my baby kici gaba da SON KAMAL shima Yana nan tare da ~MASEEFAR SONKI~ luv u XARAH am sorry...... Gida Nigeria Yau takama Asabar LABEEBAH Tatashi da aiki tuquro Bayan ta tsaf tace gidan tayi wanke wanke. Taxo kan wanki kenan Rukayya tafitoh daga 'dakinta tana hamma Tace habah LABEEBAH waike bakya gajiya da aiki ne. Tace wata rana baxanyi bah Aunty Rukayya. Kinga bai kamata nayi wasa da lokacina ba Tace hmm kibar wankinnan anjima xan mana Tace aa ki barshi kawai bayan ba yawa Sumayya CE tashigo ita da SAUBAN Kanta ankare yayi saurin figge hannunsa yaje ya rungumi LABEEBAH yana cewa oyoyo momyna Tadurkusa tarungumeshi Tace oyoyo Yarona. Yace Kinga abinda Momy Sumayya ta shiyamin. Yafa'da da nuna mata chocolate Tace shan xaqinka yayi yawa Yarona kadena kaji Yace toh in sammiki Tace eh sammin. Nan ya gutsuro ya saka mata a baki. Ta tauna da lumshe ido Tace lalala wannan da'di haka qaramin Yayi dariya da saketa yayi gun Rukayya da 6uya abayanta Yace 6oyeni Aunty karta cinyemin Duk sukayi dariya Rukayya tajanyo shi suka xauna kan taburma Tace xauna abinka. Gaka gani baxata cinye maka bah Sumayya takalli LABEEBAH Tace Aunty LABEEBAH Karki manta dayaune reception 'din LABEEBAH tawaro ido Tace Ya Allah Kinga na manta Rukayya tace wane reception ne Sumayya Tace na wata qawarsu CE Jamila data halacci duk bikinsu tana da kirki matuqa Tace ayya Jamila aina Santa LABEEBAH Tace kin gayama XARAH Tace ban shiga gidanba tukunna Tace gaya mata toh Futa Sumayya tayi tana cewa toh Rukayya Tace niko LABEEBAH in tambayeki man Tace ina jinki Aunty Rukayya Allah yasa dai lafiya Tace ba shakka ba lafiya bah Meya ha'dakune keda XARAH niga Sam kuncanja ba kamar yanda kowa ya san kuba Tayi Murmushi Tace atunanina dai ba Komai ba abinda ya ha'da mu Qaryane wlhi qaryane dole akwai abinda yashiga tsakaninku kifa'da min kawai. Rukayya Tafa'di hakan cikin tuhuma Daidai nan XARAH tashigo Saiko LABEEBAH tafara wanki XARAH taxauna kan turmi Tace Barka da ranah Aunty Rukayya Rukayya tajah numfashi Tace Barka da fatan kintashi lafiya Tace lafiya lau Tafa'da tana mai shafakan SAUBAN Tace SAUBAN ba gaisuwa Yace good Mrning. Mrning my son ya katashi lafiya. Yace lafiya lau 'daxo ai naxo gaisheki kina bacci tayi Murmushi Tace shine baka tashan bah Ya kalli LABEEBAH tatake wanki cikin nutsuwa kamar ansata dole Yace momyna tace min kar intashi mutumin daya ke bacci wai yayi baccinne dan yasami hutu kuma idan na tasheshi nashiga hakkinsa Kuma Allah bayasan Mutane masu shiga hakkin mutane 'yan uwansu....... Shuru XARAH tayi can ta kalli LABEEBAH ka'dan kana tadawo da kallanta gareshi Tace Hakkane toh sammin chocolate 'din. Yamiqa mata dukka batare da yace Komai ba. Ta gutsiri ka'dan Sannan tabashi Rukayya Tace ya kamata kuma kanku fa'da kudawo yanda kuke da wannan rayuwar da ayanxu kuka xa6ama kanku ba inda xata kai muku sai jawo muku abin kunya. LABEEBAH takalleta har xatayi magana saita fasa Hawaye ya xubuma XARAH Tace bansan ya Xanyi da itaba Aunty Rukayya. Nefine nayi mata Amma yanxu nagane kuskurena harta yafemin Duk wani qoqari nayishi akan tasake dani Amma taqi ya xanyi da ita saita fashe da kuka Itama LABEEBAH hawayan ne ya xubu mata taguge taci gaba da wankinta Rukayya ta jinjina kai tabbas abinda XARAH tayima LABEEBAH babbane tunda ta'iya fitta daga har karta kwata kwata. Rukayya tafa'di hakan aranta Tace toh kinji ke LABEEBAH abinda XARAH tace Ban sanki da gaba ba LABEEBAH ban sanki da riqo ba. Haka banyi tunanin xaki 'daukema XARAH haka bah Shuru Rukayya tayi itama XARAH tsayawa tayi da kukan nata Ganin da sukayi SAUBAN yaje Yana gogema LABEEBAH hawayanta Yace momyna tashi muje yawo kidena kuka kinji. Ta share soran hawayan nata tace toh naji yarona jirani in qarasa wankinnan ko Yace toh nima intayaki Tace aa xaka jiqa jikinka kuma ciwo xai kamaka Yace toh ke baxai kamakiba. Tace eh Yace aa xai kamaki kibarma momy tayi ko Aunty Yafa'di yana mai nuna mata XARAH da Rukayya Harararsa Rukayya tayi Tace kaga me uwa. Wato mu ciwan ya kamamu karya kama maka momynka ko Ya ko 'daga mata kai Yace eh yana yanye hannun LABEEBAH daga ruwan wankin Tatsame hannun nata Tace nabari toh shikenan Ya 'daga mata kai alamar eh Tashi tayi takama hannunsa sukayi gun XARAH LABEEBAH ta dur'kusa agabanta tare da kamo hannunta Tace nariga da nayafe miki Komai kuma nadawo miki kamar yanda muke dah ina sanki XARAH ina kuma rokwanki da Allah kidawo da halinki Wanda nasanki dashi. Kishare xugar qawaye dan duk ba masoyanki bane Murmushi XARAH tayi Tace Komai xai tafi yanda kike so fatanadai kidinga bani kulawarki. Tace kinsamu 'Yar uwata shikenan Tace eh Tashi LABEEBAH tayi Tace wai qarfe hu'du reception 'din Jamila ko Tace eh Sumayya tagaya min Haka suka sake awannan rana sunyi qoqari Sosai wajan kamanta San junansu kamar da Dubai🌌 Daidai nan MALUDDEEN yarufe laptop 'dinsa Wanda tunsafe ya bu'de Facebook 'din sakwan mutanan nasa yashigo mai Yace plx my baby Karkiyi kuskure na biyu wajan qara yarda da XARAH. Ya dafe kansa tare da 'daukar wayan shi ya danna numbar 'daya daga cikin mutanan nashi ya kara wayan akunnansa Yace banaso Laveeva taje wayan reception 'din nan. Yace toh oga Amma meyasa Ya runtse ido Yace saboda tafi kowace mace tsari da kyau hankali nutsuwa rauni kamala tausayi aguna. Xan shiga tashin hankali da 'dimuwa tare da damuw idan har wani ya ganta ya furta kalmar so agareta plx kukiyaye hakan. Yace an gama megida yanda kaso haka Komai xai kasance maka MALUDDEEN ya ajiye wayar tasa. kujerar da yake kai tafara juyi dashi ahankali yanabin hotunan LABEEBAH da kallo wa'yanda suke manne ajikin kowane bango na office 'din nasa . [3:56PM, 13/10/2016] Rahamat Nalele💋: Gida Qarfe hu'du nayi su LABEEBAH lokacin sungama shirin tafiya reception din Tagama shirya SAUBAN Sun feshe jikinsu da turare. Sumayya ta shigo tana cewa ku muke jira ga Ya Ameer yaxo kaimu LABEEBAH tayi Murmushi Tace Gaskiya Ameer da wayo yake dan kar ayi mai kwace shine harda wani xuwa kaimu Sumayya tayi Murmushi da rufe ido Tace kai Aunty LABEEBAH Tace ba wani kai ai gaskiyarsa gwara ya killaceki dan yanayin kuskuran barinki bashakka xaiyi babbar asara Sumayya tayi dariya Tace nidai inkungama kusamemu agida Tace toh tana sakama SAUBAN takalmi Basu wucce 2 minutes ba LABEEBAH tayima Rukayya sallama Tace wow wannan kyau haka kamar kece Amaryar ta lumshe idanta tare da kallan kanta Atamface kalar pink da ratsin ash colo riga da siket ne 'dinkin Saidai siket 'din ya kamata daga hp dinta xuwa gwiwarta. Daga nan yay bala'in baxuwa yanda kowa ya kalleta saiyaso gaqa kallan 'dinkin Rigar tayi mata daidai jikinta sai 'daurin datayi na wayayyun mata wato ture kaga tsiya Fuskarnan ba wani tarkacan make-up sai Qamshi takeyi Tayi kyau Sosai Cikin wannan shigar Tace kai Aunty Rukayya ina wani kyau anan Tace xagidai kanki dai kiji da'di Murmushi tayi Tace mudai muntafi Sunfitoh kenan xasu shiga gidansu XARAH wani saurayi ya tsaida ita Ta kalleshi araine dan ita dai bataso Sam maxa sutsaida ita Yace Allah yajah da xamaninki plx kexe LABEEBAH Tace eh Yace dama naji wasu 'yan iskane Suna tattauna cewa xaki wani reception wai xasu saceki sukaima ogansu ke. Dan Yana sanki kuma ke kinqi bashi dama Da xakibi shawarata dakin fasa xuwa. Tabbas hakan shine yafi dacewa LABEEBAH taklleshi dakyau Tace toh waye shi Ya juya kai yace ina xansani kawai naji suna maganar ne Tayi shuru cikin tunanin waye. can dai taqara kallansa Tace toh idan sunyi hakan miye ribarsu Ya waro ido Yace suko suke da ribah dan xa'a biyasu kuma ogansu yayi yanda yaga dama dake Kawai kishare xuwa. Ta juya idanta tare da ta6e baki Tace Nagode Sosai kamar yanda kacetar da rayuwata Allah ya dubeka ya tseratar dakai daga sharrin maqiyan ka Yace Nagode nima yana fa'din haka ya shiga motarsa ya tafi. Ita kuma tayi gidansu XARAH Anan take cema XARAH tafasa xuwa Atare XARAH da LABEEBAH suka kalleta ta gya'da kanta da cewa Wlhi baxanjeba dan kainane naji yana ciwo Xahiri sunyarda da gaske ciwan kanne xaihana xuwa nan suka mata addu:'a XARAH Tace itama baxataba Sumayya taje kawai Cikin daran ranar LABEEBAH takasa bacci dan ciwan mararta da ya xo mata. Dama wata uku daya wacce mata haka tasha fama Gashi maganin gargajiyanta da yake mata ya qare duk da Ya Usman ya samammata wani Amma yaqi kar6ataba Da asubah ya matsanta mata Nan sukayi asibity da ita Aka bata temakwan gaggawa dan tasume. Sanda takwana kafin tasami kanta. Rukayya XARAH Innah suka mata sannu ta'daga musu kai Kwana 'daya taqara aka sallamota Ba lefi taji da'din jikinta Da yamman ranar Momy taxo gidan nasu. Nan tacika ta murna ta maqaleta tsam Tace ayya Momy nayi missing 'Dinki XARAH Tace ke ka'dai ko Momy tayi Murmushi Tace harda ke Innah tadirema Momy fura da nono me sanya tana cewa kinsha hanya Tace aitun jiya naxo Dama naxone in gayama yaran nawa Su shirya jibi xamu qasar Saudiya da Dubai mu 'dan huta dan Su Sagna sun sami hutu a makaranta dukka Inna tayi Murmushi Tace Allah Sarki bakya dai gajiya da hidima dasu Tace ko ka'dan Innah baxan gaji vah dan Allah Karki damu da hakan. tafa'da da shafa kan LABEEBAH Haka suka dinga hira cikin jin da'di Bakin LABEEBAH yaqi rufuwa dan taji xuwa Saudiya. Sagna da Safna mah murna sukayi da sukaji da Aunty nan nasu xa'a Dubai🌌 MALUDDEEN dake kwance kan gadansa ya ture laptop 'dinsa gefe dayin Murmushi Yace xanji da'din ganinki my baby. Yana fa'din hakan ya kira Marwan awaya Yace 'dan uwana Yace na'am 'dan uwa Yace plx ka shirya mana tafiya qasar Saudiya gobe. Yace wani abu ya farune Yayi juyi ka'dan Yace xanga abinda yafimin da'di da'dine Marwan yayi Murmushi Yace toh angama ina maka fatan alkairi Yace Nagode da kashe wayan Sannan Yace abayyane xaki dena ciwan mararki my baby daxaran kin shigo hannan KAMAL Gida Agidan Sagna ta kwana manne da LABEEBAH Washe gari tayi gidan Kakah XARAH Tace da LABEEBAH sushirya suje gidansu Jamila tunda baxu samu xuwa reception 'din jiya bah LABEEBAH Tace Gaskiya kam Haka suka shirya sukayi Gidansu Jamila akan hanyarsu ta xuwane suka ha'du da wani wai shi ALIYU ya nace waishi San LABEEBAH yake LABEEBAH taqare mishi kallo from up to down Tace me sunanka Yace ALIYU Tace kash kayi rashina dama sunanka KAMAL Tana fa'din haka tayi gaba XARAH da shi subita da kallo XARAH tayi Murmushi Tace kayi hakuri tayi nisa asan matacce da gaske daka kasance KAMAL da kaxama Miji agareta dan tace baxata auri wanda bai kasance sunansa KAMAL bah Itama tana fa'damai haka tayi gaba Jamila tayi fushi dasu Sosai Amma dake sun shirya kar6ar fushin nata nan suka bata hakuri da siyeta da baki Ta hakura ko Sanda sukakai magriba Sannan suka bar gidan nasu Agajiye suka dawo Washe gari direban Kakah yaxo ya 'daukesu suka yima su innah sallama Usman Yace kukala da kanku dakyau suka toh Qarfe Tara jirginsu yatashi xuwa qasa mai tsarki Sun sauka lafiya Saidai tunda LABEEBAH tasa qafarta a garin na Saudi taji gabanta ya tsinke ya fa'di Ahaka suka sauka agidan dasu Momy dama suke dashi acan . [8:00PM, 13/10/2016] Rahamat Nalele💋: Bayan sunyi ibada sunci sunsha sunyi bacci sun tashi Still LABEEBAH bata denajin fa'duwar gaban nata bah Fitowa falo tayi taje takwantar da kanta acinyar Momy tayi lamo Momy tashafah kanta Tace LABEEBAH Uwar 'yansan jiki Me yake damunki jikinki yayi sanyi haka Tace ba Komai Tace kodai kinasan axaga daku cikin garine Da sauri ta 'dago da kanta Tace eh Tace toh kibari sai gobe ko Maida kan nata tayi kan cinyarta da cewa toh Washe gari da ranah duk sukayi ka'aba <'dakin Allah> Kowa xagewa yayi acikinsu Yana addu'a Hankalin kowa baya kan kowa MALUDDEEN da yake ganinsu yace 'dan uwa bari inje ga babyn can naji qamshinta ka'dan Marwan Yace ok ka ankare fah Tafiya MALUDDEEN ya farayi yana cewa ba matsala Gaban LABEEBAH yaje ka'dan ya durkusa ya fara addu'a Gaban LABEEBAH ya tsinke ya fa'di dammmm Sakama kwan shamshin KAMAL da taji daga wannan bawan AllahN Ta qorama bayansa ido gabanta naci gaba da fa'duwa sai taga kamar KAMAL nema Dan yanayin jikinsu iri 'daya Saita cigaba da addu'arta Amma Sam batasan me take cewa bah Fa'di take Allah ka dubeni kabani farin ciki Arayuwata Allah ka bani mijin Aure me Suna KAMAL Me hali irin nasa Wanda xai soni fiye da sanda KAMAL yayimin fiye kuma dasan da YUSUF yayimin Allah ka bamu dacewa anan gidan duniya da kuma gidan lahira Allah na roqeka karka barni cikin kunci kuma karka barni cikin tashin hankali Saita fashe da kuka Dan turaran wannan bawan Allan yana tarwatsa mata kwanya cikin kuka Tace axuciyarta ga wani yaxo me yanayin KAMAL ko wanene MALUDDEEN yaji kukan nata har Cikin ransa. Ji yayi tamkar ya rungumeta koya samu sauqin xuciyarshi Bai ankare ba sai jinta yayi ta kwantar da kanta abayansa Tace bawan Allah turaranka me da'di Jan ajiyar xuciya yayi tare da lumshe ido da kuma bu'dewa ya xaro bairo cikin aljihun gaban rigarsa da qaramar fefa yayi rubutu ajikin farar dakardar kamar haka *na gode my baby* Sannan ya tura mata tabaya..... Raba kanta tayi da bayansa ta 'dauki fefar ta waro ido Sosai dan ganin abinda ya tubuta. Daidai nan yatashi yafara tafiya anutse. Aiko tatashi da niyar binsa sai idanta ya sauka akan wata fulawa mekyau da zube a samanta Tayi saurin 'dauka tabishi yana tafiya tana binshi abaya Marwan ya 'daga mishi gira dayi mishi nuni da ido alamar ya ankare tana binshi abaya Saiya tsaya cak Itama tatsaya Sai yaci gaba da tafiya itama taci gaba da binshi Dariya takama Marwan. Yayinda MALUDDEEN ya gallah mishi harara da qara tsayawa cak yana cije baki Cikin shagwa6a LABEEBAH Tace kamanta da abinka ne shiyasa nabiyoka nabaka Ya bu'de baki xaiyi magana sai yayi saurin rufe bakin da hannunsa Yana 'dan girgixa ma Marwan kai alamar ya kawo mishi temako Sam Marwan baisan me yake nufi bah dan haka yaci gaba dayi mishi dariya...... Gashi.... LABEEBAH Tace dashi By Hajju ~*MASEEFAR SOO*~ Dan Allah kumin afuwa masoyana kamar MALUDDEEN saiyi kuka ya girgixama Marwan kai Tausayinshi ya kama Marwan yayi saurin xuwa garesu da shan gaban LABEEBAH Ganin haka yasa MALUDDEEN saurin baringun LABEEBAH tabishi da kallo. Marwan Yace baiwar Allah me yayana ya miki kike binshi Tace mantawa yayi da abinshi shine nabiyoshi nabashi. Tafa'da tana mai nuna mishi wannan fulawar da xuben kai Yace ayya ai shi haka yake idan yayi mantuwar Abu toh Wanda ya tsinta ya barmishi kenan dan haka kiriqe ya baki Ta kalli xoban me kyau sai sheqi Yace kallo na'daya xakamai kagane 💎 ne Tace aa gashi dai kabashi abunsa Yace Wlhi baxan kar6aba in bakyaso kiyar. Yana fa'din haka yayi tafiyarsa ya barta nan Shuru LABEEBAH tayi tana kallan zoben da kuma kallan takaddar...... Safna ta dafata Tace Aunty munata nemanki. Tayi Murmushi Tace toh muje Haka suka dinga xaga garin na Saudi idan LABEEBAH dana XARAH ya qara bu'dewa Dan kallo 'daya xaka musu kagane Suna cikin jin da'di Agajiye suka dawo gida LABEEBAH tayi xurfi atunanin waye wannan bawan Allan me yanayin KAMAL. Qamshinsu iri 'daya. Jikinsu iri 'daya Saidai ganin da tayima hannun wannan ya 'danfi KAMAL haske Tadafe kanta dataji yana juya mata Tace Allah kaban haske akan wannan bawa naka Washe gari XARAH LABEEBAH Sagna Suna xaune wajan shaqatawa wata budurwa tashigo kyakkyawa da ita Tayi musu sannu Suka amsa mata da kulawa Ta kalli LABEEBAH tamiqa wata takadda Tace wanine yaban Yace na baki Tace wani..... Sagna rakar6a Tace toh tagode Budurwar tafita Sagna tamiqa mata tana Murmushi Tace Aunty xamu koma da 'dan saudiya LABEEBAH ta kar6a da Murmushi tabu'de. *dan Allah kisaka xoban nan* *dan masoyinki KAMAL* Shuru LABEEBAH tayi taxumaba takaddar ido. Dan qamshin KAMAL buganta yake tajikin takaddar Sagna Tatashi tabar gun XARAH tayi Murmushi Tace naji qamshin turaran KAMAL ajikin takaddar nan LABEEBAH ta kalleta da sauri. Saitaga tayi maganarne batare da takalleta bah Saita nanna'de takaddar tare da Murmushi Tace nima haka naji Tashi XARAH tayi tana Murmushi tafara tafiya tana cewa koma Waye nasan xaki soshi ko da ko baixo da sunan KAMAL ba. Dan ya mallaki abu 'daya wanda xaisa kisoshi. LABEEBAH tabita da kallo duk da taga saura ka'dan tashige falo hakan baisata hakura da furucin nata bah Ta 'daga murya wajan cewa dagaske xan so shin kuma na aureshi idan ya baiyana agareni dan kam yaxo da qamshin daya ke sani nutsuwa aduk sanda na tunoshi. Bare kuma nashaqa ba shakka kowaye shi xai juyani yanda yakeso saboda darajar qamshin ruhina XARAH da tatsaya abakin 'kofar falan tajuyo ta kalleta da Murmushi. Tace koma Waye shi haka. Xanso ya baiyana kansa in jinjina masa akan biyowa da yayi mishi ta bayan qasa LABEEBAH ta harareta Tace imma ta bayan gida ya biyomin nidai yatafi da xuciyata. Plx in kin shiga Ki turomin SAUBAN Dariya XARAH tayi tashige falan Aiko haka LABEEBAH tasaka wannan xube tana cewa koma Waye kai nasaka xobanka dan naji qaunarshi tun ganina dashi Tundaga ranar LABEEBAH bata qara ganin wannan bawan Allan ba. Ga mamakinta sai tanemi rasa nutsuwarta Satinsu 'daya sukayi Dubai. Anan ne MALUDDEEN yaga LABEEBAH san ranshi dan duk inda sukayi Yana biye dasu LABEEBAH ko daurewa kawai take dan ko'ina sukaje saita dinga jin qamshin KAMAL. Toh wai meke faruwane. Ta tambayi kanta Gaskiya sunyi yawan bu'de ido a qasar ta England cikin garin Dubai Dan nan sukayi sati biyu suka kuma Saudi Anan suka qarashe sauran satin nasu dake wata 'daya Momy ta tsara musu Ana gobe xasu tafi ciwan marar LABEEBAH ya tashi ganga ganga Su Momy sukayi asibiti da ita Kwananta biyu tasami kanta Yau sukaje siyayyar tsarabarsu sukayo kayansu rigijib. washe gari sukayo gida Nigeria. Sukabar qasa me tsarki🕋 Kowa yayi murna da dawowarsu Kwanan Momy biyu a kano suka tattara ita da yaranta Sagna Safna sukayi abujah Dubai🌃 MALUDDEEN Yana office 'dinsa ya tasa laptop agaba Yana kallan LABEEBAH ya rufe laptop 'din Yace o my baby am sorry dole KAMAL yayi saurin bayyana miki koxai rabaki da wannan ciwan Marwan Yace Gaskiya 'dan uwana babyn nan tana chaja maka tunaninka Yayi Murmushi Yace wlhi Marwan ita ka'daice matsala ta rayuwa Yace toh miye dalilinka na 6oye mata kanta Murmushi MALUDDEEN yayi Yace dalilin hakan kakesan sani Yace eh Yace xakasan dalili Amma kafin nan kashirya Mana tafiya Armiyaniya inasan dubah Sarki kasan mun kwan biyu bamu laqa subah Marwan yace toh MALUDDEEN ya danna numbar mutanan nashi ogansu ya 'dauka Yace inasan ku'dora bincikenku akan XARAH mah da Turai Yace angama oga Gida🏘 Toh Madallah Su XARAH sun huta yanda suke so suka rabah tsabarsu XARAH CE ta shirya tsaf tanasan xuwa gun Hajjiya Turai dan sunyi waya Turai Tace mata taxo garin nasu kano taxo gidanta Su xanta Amma tatawo mata da SAUBAN Tace mata toh Bayan tayi sallama da Innah tayi gidansu LABEEBAH Anan tsakar gida taganta Suna wasa da SAUBAN Tace toh nayi gidan Hajjiya Turai saina dawo SAUBAN xomuje. LABEEBAH ta kalleta ka'dan Tace saikin dawo Amma kibarni da SAUBAN XARAH ta harareta Tace wai meyasa bakisan Hajjiya Turai ne kike katange kanki da ita gashi kinasan katange SAUBAN da ita LABEEBAH ta kalleta da kyau Tace kajimin mata dole ne saina sota kamar yanda kike santa. Kinga malama idan tana da iko dake aibada iko akan SAUBAN kedai kije SAUBAN baxaije ta gur6atamai tarbiya bah Cikin Takaici XARAH taqara kai mata harara tayi kwafah da cewa dan kawai tace tanasan taganshi shine xaki kawo wani alaye cikin na'di. LABEEBAH tashi tayi takama hannun SAUBAN suka shige 'daki tasake mata labule Tace bacci mukeji malama saikin dawo Da Takaici XARAH tabar gidan Sumayya da Rukayya suka bita da dariya HAJJIYA TURAI tana xaune cikin bet room 'dinta. ita da wata qawarta. Duk jikinsu baqaqan kayane sai wani qelle jah da suka 'daura akansu. Kallo 'daya xaka musu gabanka yafa'di dasu. Turai takalli qawarta kilishi Tace yanxu yaxanyi. Banaso nasami matsala da oga Kilishi Tace hmm kefah kikaso Amma ya xa'ayi yaro qarami ya gagareki kamawa Turai tayi Murmushi Tace Yana tare da tsoro yaran Sosai agida da waje Naga wasu ma'aikatan sirri Suna bashi tsoro Duk yanda naso na sace yarannan abin yaci cira Kilishi Tace toh ba gashi kinbi ta hannun uwarsa bah Tace share XARAH bai xama lalle taxo dashiba Dan nidai ban ta6a ganin tafitta unguwa dashi bah Kilishi Tace ya maganar sata cikin rayuwar tamu Turai tace yau nake san bata MALTINA kinsan tana sha munbo'de

Chapter 16 of 22