Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
bah sai tasa kanta LABEEBAH ko na ajiye waya tayi shuru kawai tafa'da tunani XARAH Tace hmm da aljanin kikayi waya LABEEBAH ta kalleta Tace eh XARAH tayi murmushin yaqe dayin shuru Sumayya tayi Murmushi Tace kudai bakwa rabo da matsala Wannan na fitta daga nan wancan xata 'dauka Rukayya tace kiji wai aljani Ke yanxu da aljani kike soyayya LABEEBAH Tace eh atare Rukayya da Sumayya sukayi dariya Rukayya Tace wannan ai story ne. Sumayya Tace babbama kuwa Shuru LABEEBAH tayi musu da Qara kashe wayanta. Washe gari tun qarfe tara direba yaxo ya kwashi LABEEBAH da XARAH Sumayya xuwa garin na Abuja A gajiye suka Isa murna tacika Momy Safna da Sagna Dady Kowa yayi murna da xuwansu Hajjiya Zainab matar Alhaji Nasir qani ga Dadynsu KAMAL tadinga yaba LABEEBAH da XARAH tana masha Allah Kakah mah tayi murna Sosai da ganinsu Bayan sun huta sunci sun sha LABEEBAH Tace hmm nagaji bari na'dan kwanta Sumayya tayi gunsu Sagna XARAH ko xagawa tayi Bayan gidan tana buqatar ka'daicewa...... Saidai me😳 Tana xuwa tahangi KAMAL da Marwan Suna hira cikin nisha'di Gabanta ya tsinke ya fa'di. Nan nutsuwa tabayyana agareta Hawaye ya xubo mata Tabbas KAMAL ne wannan dan tatabbatar ma kanta shine tun ganin da tamasa a kano Aiko tarushe da kuka wiwi KAMAL ya kalleta ka'dan. Shiko Marwan xuba mata ido yayi kawai xuciyarsa tatafi tunaninta Ya rinya kyakkyawa da ita gata kalan tausayi Amma ta aikata wannan aika aikam Bai Ankareba ya ganta durqushe gaban KAMAL tana wani kuka me ban tausayi Tace nayi nadama nayi dana sani nayi Allah wadai da rayuwata nayi asarar da har in mutu baxan maida itaba Na sani Kai KAMAL ne Dan Allah dan Annabi karufamin asiri Karki tona wannan abin Allah wadai dana aikata maka....... Ta qarashe da rushewa da kuka Wani abune ya muntsini xuciyar KAMAL Wanda ya Haifar mai da tausayinta Sai kawai ya tashi ya bar gun Taqara rushewa da kuka Marwan bai 'dauke idansa akantaba yayi Murmushi Yace XARAH ko Ta kalleshi ka'dan tare da 'dauke kallan nata tacigaba da kukanta Yace Kinga malama baxafah Ki takuramin bah Ki tashi kibar nan dan Allah inajin kukanki har cikin xuciyata Plx dan Allah temakeni kibar nan gurin XARAH tatashi da jifan shi da harara Tace baxan bari bah kai katashi mana A rayuwar Marwan yana San mace me tsiwa da rawar kai Shiyasa Sagna tayi saurin shiga xuciyarsa. Wannan ra'ayinsa kenan Yayi Murmushi Yace wow gaskiya ne in bakiyi tsiwa bah a tambayeki Irin wannan harara haka. Kinga bacewa nayi ina sanki ba. Daxa kimin hararar Masoya Ya ta6e baki ka'dan yaci gaba da cewa Kumama ni matsoracine koda kin soni aranki baxan aureki bah. Dan ina tsoran kar na Aureki wata ranah kiga qanina Ki kashe ni kice shi kikeso .......... Tun da ya fara magana XARAH tasaki baki da hanci ido tana kallansa da mamakinsa Akanme daga ganinta xai mata sharrin tana sanshi daga harara saiya juya mata manufah Lokacin da yaxo furucinsa naqarshe abin ya 'kona xuciyarta tafashe da kuka me ban tausayi Ya kalleta ka'dan da murmushin mugunta ha'de da tausayinta Yace am sorry...... Tafiya tafarayi tana cigaba da kukanta Yace na'danji sanki ka'dan Tajuyo ahankali takallesa sai taga ba ita yake kallo ba wata fulawa yake kallo. Ya juyo ahankali ya kalleta Yace ina san Sagna Sannan ina 'dan sonki shin ya ha'din xai kasance Cikin fusata XARAH taqara kai mishi harara Tace bana sanka bana sanka bana sanka Yace da gaske naji sanki ka'dan. Amma Wlhi soyayyar da nakema Sagna taninka taki so dubu. Kina wani maganar baki sona keyanxu idan da xa'aji abinda kika aikata waxai aureki da wannan mummunar xuciyar taki. wacce Sam ba Allah acikinta. Wlhi tausayinki naji kuma nasan baxa kiqi na'am da soyayyata ba. Saidai kitsaya wani alaye. Gashi kuma inda xakiyin baxai ta6a tasiri ba. kawai ki share dan nima qarfin hali nayi kawai nayi dan nasan da wahala na Aureki bakiyi min abinda kikama yayanah KAMAL bah XARAH takece da wani kuka Tace natsaneka Tana fa'din hakan tafice daga gun Marwan yayi Murmushi yace story kenan. banji sanki bah XARAH Amma xan dinga binki da kalamai har sai nadamarki tafi haka XARAH 'dakin Momy taje takwanta tana tuno kalaman Marwan. Wanda talura baqar magana ya gaya mata KAMAL ko part 'dansa yayi ya kwanta yana tunanin rayuwa Can yaji yanasan Ganin LABEEBAH saiya kira Safna awaya. cikin sauri ta'dauka Tace Yayah Yace inasan kigano min me LABEEBAH takeyi Tace bacci take Yaya Yace. A ina Tace tana 'dakinmu Yace OK saiya kashe wayan. Ya tashi direct part 'dinsu Sagna yayi ananko yaga LABEEBAH tana bacci hankali kwance yayi Murmushi da qare mata kallo. Ya da'de yana kallanta ahaka kafin ya koma part 'dinsa batare data sani ba Marwan Yace mai gata kyakkyawa XARAH Saidai ta6ata wayanta KAMAL ya kalleshi ka'dan yayi murmushi yace kar kayi wani alaye idan tsuntsun ya koma kan tane kagayamin in baka ita karka duba abinda tamin dan kasameta xakaji da'dinta. Marwan yayi Murmushi Yace aa Wlhi Yayanah kawai dai nafa'di abinda yakef hakane. Da ace nafara ganinta kannaga Sagna ba shakka da tayi Babban nasarar sace xuciyata Amma maganar gaskiya son da nakema Sagna yafi Wanda naji yanxu araina Kawai kashare KAMAL ya dafa kafa'darsa Yace kayi dai tunani duk wacce takwanta maka nayi alqawarin baka ita Marwan yayi Murmushi Yace toh Sagna KAMAL Yace tunani Nace kayi . Yace toh Yayanah Xanyi . [1:47PM, 23/10/2016] Rahamat Nalele💋: LABEEBAH ko bata tashi ba sanda ta'dauki kusan awa 'daya XARAH ma bacci tasha abinta. Saidai bana kwanciyar hankali bane kamar na LABEEBAH Mexai faru 😳 Bayan isha'i sunci abinci XARAH Sam takasa cin Komai duk tawani hargitse lokaci 'daya Sagna da Safna sun tambayeta me ya hargitsa ta haka Tace ba Komai Sumayya tajah numfashi Tace toh Allah yasa ba Komai 'din LABEEBAH ko tunani tayi qila har yanxu tunanin wannan aljanin nata takeyi Wanda ta'dauka KAMAL ne KAMAL yakira Momy awaya Yace plx my Momy 'dan turomin 'Yar taki man Momy tayi Murmushi Tace naqi baxa'amin hira agida bah Yace ayya momyna dan Allah kituromin ita magana 'daya xan gaya mata Tace toh naji. Takashe wayan tana Murmushi Can takira Sagna Tace mata taturo mata LABEEBAH Nan ko LABEEBAH taxo Momy takalleta da Murmushi Tace ga abinci nan inaso ki kai part 'din KAMAL toh Momy. LABEEBAH tafa'da da 'daukar abincin Tunda ta doshi part din gabanta yake fa'duwa danjin qamshin turaran KAMAL Tayi sallama tashiga falan da ajiye abincin kan table Juyo wannan da xatayi sai taga KAMAL xaune akan kujera yana danna waya Marwan na gefanshi yana kallanta Taje kusa da Marwan Tace dan Allah kaima kana ganin aljanin nan Yace eh Sosai mah Tace ko kaima aljaninne Yace aa ni mutum ne kamarki Yana fa'din haka ya fitta daga falan yana mata dariya LABEEBAH xatayi saurin bin bayansa sai taji kawai KAMAL ya rige mata hannu Yace xauna Ba musu taxauna a kusa dashi inda ya buqata Ya tattara hankalinsa da nutsuwarshi waje 'daya ya kama hannayanta dukka biyu yana kallanta ido cikin ido Yace lokacin da na sauka a jirgi. Na tsaya jiran direban Kakah yaxo ya 'daukeni Amma abin mamaki sai wani yaxo akan wai anturo shi ya 'daukeni Ba musu nashiga motar tasu Ashe rayuwata suke nema my baby. Dan ban tashi tsintar kaina bah sai a wani gida wanda baxan iya cewa ga inda mukabi mukaje wannan gidanba Sai ogansu ya harbeni harbi biyu. Sannan yasa yaransa suka jefar dani a ruwa Daga nan sai tsintar kaina nayi a qasar Armiyaniya. Nafa'da hannun sarkin garin Shiya bani temakwan gaggawa Har nasami matsalar 'daukewar tunani. Daga baya tunanina ya dawo Sarkin ya nunamin qaunah Sosai my baby ya 'dorani akan wani business 'dinsa da yake qasar England garin Dubai Ni ba aljani bane my baby Ni KAMAL 'dinki ne LABEEBAH ta kura mishi ido Tace toh me yasa da aka kawoka mugaka fuskarka akan kaine wanda ka mutu. Yace duk shirin mutanan ne ban san dalilinsu nayin hakan ba Tace yanxu kai Ya KAMAL ne Tashi yayi ya buqaci Tatashi Nanko Tatashi ya ware hannunsa Yace rungumeni Ki gane Ahankali taje ta rungumesa Nan ta lumshe ido Tace gaskiyane kaine kai Ya KAMAL..... Ya rabata da jikinsa da qura mata ido Yace xaki Aure ni....... Hawaye ya xubu mata Tace ina sanka Ya KAMAL ina sanka Wlhi ina sanka ina qaunarka. Amma ya xanyi da XARAH tana sanka. Kuma baxan iya kishi da ita bah Ni kam na haqura da kai kawai Ka maida matarka kawai Yace ko Ta'daga mai kai Yace shi kenan Ta qara 'daga mai kai yaja numfashi. magana ta gaskiya Baxan maida Auran XARAH ba Idan har ban Aure kiba Wlhi baxanyi Aure bah Kuma nayima xuciyata alkawarin Auranki. Baxan ta6a barinki ba my baby Yana fa'din hakan ya manna mata kiss a baki da nuna mata hanyar 'kofah Ta kalleshi Yace jiki dan Allah Sai kawai ta rungumeshi tarushe mai da kuka A duniya KAMAL bayasan kukan LABEEBAH daurewa kawai yake Ya 'dago da fuskarta data rimtse idanta. Yace ki temaken dan Allah kidena kukannan yana ta6a xuciyata plx karkisa na aikata miki abinda baidace ba yanxu Ta bu'de idan nata da 'dauke sautin kukan Amma hawaye bai bar xuba mata cikin shagwa6a Tace meyasa baxan rayu cikin farin ciki bah Yayi Murmushi Yace xakiyi rayuwa taban mamaki me da'di da gar'di da laushi da Santsi idan kikabi Komai asannu Cikin kuka ta raba jikinta da nashi tafita daga falan. KAMAL yayi Murmushi Yace bana san matsala tadawo min Wlhi Ya 'daga kansa dama Allah ka dubeni dan darajar Manzanka Annabinmu LABEEBAH kare fuskarta tayi daga mutane tashige 'dakinsu Sagna Anan taga XARAH duk jiki amace dan kallo 'daya xaka mata ka tabbatar a hargitse take Aiko sai LABEEBAH bu'de shafin kuka XARAH na kallanta Tace meya saki kuka LABEEBAH Shuru LABEEBAH tayi mata XARAH tayi Murmushi Tace kinga Aljanin naki yace miki shi KAMAL ne ko Da sauri LABEEBAH ta kalleta Na gaya miki tun farko KAMAL ne kika musamin da aljanine Na ganshi 'daxo ai. Hakanne ya qara tabbatar min da cewa shine Toh mai xai dameki Bayan kinsami abinda kikeso. Ya dawo gareki da muradin Auranki Kibashi ha'dinkai kawai. kuma kishare Komai aranki. Karki dubeni bare kiyi yunkurin aikata abinda ko xaki mutu baxai yuhuba XARAH na kaiwa nan ta kece da kuka. Fa'di take na cuci Kaina LABEEBAH na aikata abinda har namutu baxai dena damuna ba Na rasa KAMAL rasawa irinna har abada Na aikata mishi abinda Ku xan mutu baxai qara maidani matsayin matarsa bah Hajjiya Turai ta cuceni tasakani na aikata abinda in jama'a sukaji xasuyi Allah wadai dani Ba xan rufe miba LABEEBAH ayan duk duniya ba abinda yake damun xuciyata kamar MASEEFAR SON KAMAL Saidai baxan qara Kasan cewa Matarsa bah LABEEBAH tayi shuru kawai tana jinta tana hawaye Haka suka Kasan CE XARAH na kuka LABEEBAH na kuka Washe gari walima XARAH da LABEEBAH sunyi kyau Sosai cikin shigar dogajan riguna da Momy tabasu Tace shi xasusa XARAH da LABEEBAH sunyi mamakin Cikan da akayi. Duk wani abokin KAMAL sanda ya halacci gun Haka kowa na Momy da Dady sanda suka bayyana kowa nuna farin Cikinsa yake na bayyanar KAMAL Dake harabar gidan irin babbar nance. anan akayi Komai akagama anci asha abin dai sai Wanda yagani Haka taro ya watse cikin jin da'di Hajjiya Kakah da Hajjiya Zainab ne sai Su LABEEBAH ne wa'yanda suka rage Suma gobe xasu cilla garin nasu na kano Momy ta kalli Kakah Tace ai tare dani xamu Kanon dan maganar shi KAMAL 'din da LABEEBAH. Kakah Tace toh Allah ya kaimu Hajjiya Zainab Tace AmEEn. Aiko gwara ayi saurin mishi wannan gatan Momy tayi Murmushi KAMAL ne yayo shashin Momy dan yana San kar6ar Abu agunta. Yayi kyau Sosai Cikin shigar suit dan yanxu duk shigarsa haka take Aiko sukaci karo da XARAH gaf Nan ta durkusa qasa takama qafarsa takece da kuka Tace dan Allah ka yafe min dan Allah na roqeka dan soyayyarka da Allah kamin rai nayi nadama nayi nadama nayi nadama ka rufamin asiri Dur 'kusawa agabanta yayi shima Yace XARAH kenan. Hmmm Kinga rayuwa ko Haka take daman tunda ba ahannun mutum takeba Na yafe miki har abada bawanda xaiji wannan batu. Mutum 'daya nema wanda na gayama shine kuma Marwan Namiki alqawarin ba nabiyunsa aji Temako 'daya xakimin Ki birgeni shine inaso idan Momy taxo gidanku da maganar Aurena da LABEEBAH inaso kice na nemi kikoma gidana kece kikaqi Idan antambayeki dalilin dayasa kikaqi hakan kice............ Saurin katseshi XARAH tayi cikin kuka Tace karka damu da wannan nasan abinda xance musu Ni fatana kayarda da tubana kuma kayarda ayanxu duk duniya ba Wanda nake MASEEFAR SOO sai kai ina SONKA ina QAUNARKA Saita qara fashewa da kuka mai ban tausayi Yayi Murmushi Yace watoh XARAH SO maseefa ne SO balaqine SO damuwa ne. SO ba da'di bane. nayarda da hakan dan nagani akan MASEEFAR SAN da nakema LABEEBAH ina santa ina QAUNARTA duk duniya ba wata macen da xatasha gabanta aguna Yana fa'din haka ya tashi ya barta nan xaune cikin kuka LABEEBAH taji Komai da suka tattauna dan itama 'dakin Momyn tanufa dan baxata iya jure shu'umin Kullan da KAMAL yake jifanta dashi ba Dan haka tana ganin yabar inda suke tace bari tayo 'dakin Momy Toh saitayi gamo da XARAH da KAMAL tanajin tafiyarshi yanda yanajin kukan XARAH yayi burus da ita shiyasata sulalewa ta xube aqasa tana hawaye. To wai wane lefi XARAH tayi mishi hakane Ita dai tana San XARAH tanasan farin cikinta gashi farin cikin nata ya bayyana agareta Saidai yaqi yarda ta ra6eshi Sam Gashi ita kuma abinda takeso shine farin cikinsu dukka ita da XARAN tanasan KAMAL Amma baxata iya Auransa XARAH tana gani bah Ta kece da kuka ta'dora hannu aka Tace wai har sai yaushe xan dena shiga matsala asoyayya har sai yaushe Haba soyayya meyasa baxa kimin adalci bah Meyasa kike tarwatsa nutsuwata Meyasa in nan ya toshe saiki 6ullomin tawani gun Wai KAMAL ne ka'dai namiji aduniya. Daxaki nace mishi xuciyata. Haba haba haba xuciyata meyasa kikesan KAMAL Sam banyi dace da soyayyaba Na tsina kaina na tsani kaina taqara rushewa da kuka XARAH najinta tatashi taxo lungun da take takama hannunta Cikin xubar da hawaye Tace KAMAL nakine LABEEBAH tun farko Tabbas nayarda da qaunar da kikemin Amma kisani idan MASEEFAR SON KAMAL xata kasheni baxan kumama Auransa ba har abada Nabar miki KAMAL LABEEBAH Tace banyi mah kaina adalci ba XARAH natsani Kaina KAMAL shika'dai namiji da xuciyata xata nace sai shi Na rasa wanda xanso sai mijinki XARAH tafara goge mata hawaye duk da nata ba dena xuba mata yayi ba. Tace kimanta abinda namiki akan YUSUF ne Kin manta irin budurcin dana miki akansa Kin manta cewa banji tausayinki ba akansa Toh mexaisa kidamu dan KAMAL ya bayyana agareki Yana sanki LABEEBAH tun ranar Farko Ki temaken ki rama abinda namiki mana akan YUSUF LABEEBAH Tace kishare wannan XARAH yarigada ya wucce. Ki fahimceni yanxu . ina ina ina baxan iya Auran KAMAL kina kallo bah XARAH Tace hmm ni kuma nayi miki alqawarin sai kin Aure KAMAL ina kallo dan KAMAL baxai ta6a barinki bah In gaya miki wani sirri Wanda idan kaka jure a Auran KAMAL xaisa ya qara sanki LABEEBAH ta girgixa mata kai Tace aa Karki gayamin komai dan ke xaki koma 'dakinki mijinki XARAH ta miqe Tace ko kiso ko karkiso LABEEBAH sai kin xama MATAR KAMAL...... XARAH tayi tafiyarta LABEEBAH tabita da kallo Wannan ranah kowa yasan XARAH da LABEEBAH basa cikin nutsuwarsu KAMAL yakira LABEEBAH awaya taqi amsa kiransa Murmushi yayi dan yasan abinda takeso dai bamai yuhuwa bane Washe gari haka Su LABEEBAH da Momy kakah Hajjiya Zainab Safna Sagna Su salima 'ya'yan Hajjiya Zainab suka garyatu garin na kano Sun sauka lafiya Inda direba ya kai su LABEEBAH Gidansu Su innah sunyi da murnar dawowarsu ba kamar SAUBAN daya maqale maman nasa LABEEBAH Bayan sun huta LABEEBAH tafa'da tunanin yanda suka wanye da KAMAL harya rikita mata kwanya Abin da ya faru ko shine Bayan sun tashi da safe KAMAL yaje ya marairai cema Momy Yace plx momy xanyi ganawar qarshe da 'yarki kafin sutafi Tayi Murmushi Tace hmm dakayi hakuri tare damu ni da Dadynka xamu Kanon dan maganar Auran naka da ita Da sauri ya kama hannun Momyn cikin murna Yace naji da'di momy dan kin rufamin asiri dan Wlhi 'Yar taki ta har gitsamin tunanina Tace yanxu dai ina bakayi breakfast ba Yace eh Tace kaje xan turo maka ita. Yace Yauwa momyna Yana fitta ko Momy takira LABEEBAH Tace takaima KAMAL breakfast 'dinshi LABEEBAH dai toh tace mata Amma xahiri bata so ba Da sallama tashiga falan nashi ta ajiye Komai kan table. Marwan ya kalleta Yace gdmning my Aunty da fatan kintashi lafiya Tace lafiya lau. Sannan Ta kalli KAMAL ka'dan Tace ina kwana Ya KAMAL Yace daban kwanaba zakiganni Tace atunanina banyi lefiba......... Marwan ne ya fitta dan basu guri KAMAL ya kalleta da kyau. Sai tayi saurin sunkuyar da kanta Tace akwai abinda kake buqatane dan..... Katseta yayi wajan tashi ya nufeta. Yace jiya lefin menayi kikaqi 'daukar wayata lumshe ido tayi dan jin qamshin sweet 'din bakinsa Tace wayan fah bata gurinane Yace tana gurin waye Tace Sumayya. Yace yaushe kika fara qarya Taqara lumshe ido dan qamshin sweet 'din yana neman takura mata dan jinshi take kamar ita takesha Yayi Murmushi Yace xaki Sha ne Tabu'de idanta ahankali bata san lokacin data 'daga mai kai bah Ya qarayin Murmushi xaiyi magana XARAH tashogo falan duk suka bita da kallo Ta koyi saurin runtse idanta dan baqaramin mummunan gani tayi ba Dan xuwa lokacin da tashigo falan hannayan KAMAL Suna kan qugun LABEEBAH yayinda fuskarsu ka'dan ta rage ta ha'de da juna dan kusanci Cikin saurin XARAH tamaida kanta qasa takasa cewa Komai danta manta abinda ya kawota mah tayi KAMAL ya maida Kallansa ga LABEEBAH cikin 'daure fuska yayi furucin nashi ahankali yace bu'de bakinki tayi narai narai da ido tanasan xubo da hawaye. Yaqara 'daure fuska Aiba shiri LABEEBAH tabu'de bakinta yasaka mata sauran sweet 'din da yake bakinsa tare da manna mata wani shu'umin kiss a wiya. Nan tasaki wata qaramar qara wani Abu ya caki xuciyar XARAH hawaye ya xubo mata nan taficce da gudu batare da tayi abinda ya kawota ba. Hawaye ya xubuma LABEEBAH cikin kuka Tace Ya KAMAL........ Yayi katseta da cewa ke kike da damar mallakarsa Tayi shuru Yaci gaba da fa'din Wlhi daga yau kika qara min xancan XARAH ko ina tare dake kika ganta kika wani Sha jinin jikinki kin san Allah ba abinda xai hanani hukuntaki Cikin shagwa6a tace to ya Xanyi. Yace wannan kuma ke kika sani Tace ai matarkace koka manta kata6a Auranta harda arxiqin 'da....... Cikin jin haushinta da maseefa ya raba kansa daga gareta ya nunata da yatsa Yace Wlhi daga yanxu kika qaramin manarta saina miki dukan tsiya Tace toh meyasa baxa duba halin son ka da yake damunta kayi mata afuwa sai ka maida ita gidan....... Wani wawan mari ya sakar mata wanda tunda take ba'a ta6a yimata irinshi bah Dan haka cikin sauri ta durkushe agabansa tarushe da kuka KAMAL ya yabi hannunsa da kallo tare dajan wani shegen tsaki. Yakama kansa cikin takaicin abinda ya aikata Yace am sorry Tashi LABEEBAH tayi daniyar fitta daga falan yace kitemaken ki yafemin my baby. Tayi banxa dashi. Ganin haka yasashi saurin jawota jikinsa cikin sanyin yanayi yana shafa bayanta cikin lallashi Yace am sorry Cikin sanyin itama LABEEBAH Tace dan Nace kamaida....... kanta qarasa yayi saurin katseta da cewa idan kika qarasa saina sharara miki marin dayafi wannan yanxu wlhi Shuru tayi kana taraba kanta dashi sannan ta fitta daga falan Ya bita da kallan Takaici da harara XARAH ko dama Hajjiya Zainab CE tasata kiran LABEEBAH dan shirinta ne yarage musu Qaddara tasata amsawa dabin umarninta Tafitoh falo ne Sagna Tace naga tayi shashin Ya KAMAL 'daxo gaban XARAH yafa'di har xatace Sagnan ta kirata sai kuma tafasa Ashe da raban xatayi mummunan gani Tafashe da kuka tanajin wani MASEEFAR SON mijin nata ga qaddarar mummunan halinta tayi mata yankan qauna. Cikin kukan Tace Turai kin cuceni...... Sumayya dake kallanta Tace hmm Allah ya kyauta XARAH ta galla mata harara da ficce daga 'dakin Koda LABEEBAH taje 'dakinsu Sagna bataga XARAN ba Nan takafa tagumin me xatace mata Aiko tana cikin tunaninne XARAH tashigo 'dakin Sai dai LABEEBAH ta tsinci kanta da basarwa tayi kamar basuyi Komai da KAMAL 'din a gabanta bah...... SAUBAN ne ya katse mata tunaninta da cewa menene momyna me yake damunki kikayi shuru Tashafah kansa tare da kai masa kiss agoshi Tace Dadynka ne yake damuna SAUBAN Yace toh meya miki. Waro ido tayi danjin ashe a bayyane tayi furucin tayi Murmushi Tace kanajin bacci Yace eh Tace toh xumu kwanta haka ko suka kwanta abinsu Sai dai kuma Suna kwantawae taji sa'ko ya shiga wayarta Nan ta 'daubah da dubawa _momy xata baki maganinki dan a lissafina yau saura kwana uku al'adarki taxo miki plx kitemaken kifara Sha goben pls my baby_ [10:13PM, 27/10/2016] Rahamat Nalele💋: Tayi Murmushi tace abayyane Ya KAMAL Cikin sauri tarubuta mai _Baxan shaba_😔 Sakwan na isa ga KAMAL yayi Murmushi ya mayar mata da _ai baki isa ba. Kina sone Ki hargitsani inrasa tunanina da nutsuwata_ _tace hmm fuskata fah ta kunbura_ KAMAL ya waro ido. Cikin sauri ya kirata Ashagwa6e tace hello Yace am sorry my baby pls Ki kiyaye gaba banasan kiramin xancan XARAH plx Tace to Amma...... Ya katseta da fa'din Ya salam Cikin sauri Tace toh kayi hakuri nadena Yace gud kin temaki kanki. Yanxu dai bani labari kina inane me kikeyi me yake faruwa Taturo baki tamkar tana gabansa Tace ina kwance nida SAUBAN muna San muyi bacci Yace da kyau babyna kuhuta lafiya. Am gobe xani qasar Armiyaniya ina buqatar addu'ar Ki Tace Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lpy Yace AmEEn AmEEn Tace Ya KAMAL...... Yace ke kike da damar mallakarsa Tayi Murmushi Tace dama inasan sanin duk xamanka a qasar baka ta6ayin budurwa bah Yace hmmm fa'da miki ne banyi bah. inada mata acan. Tayi saurin tashi cikin wani yanayi Tace yanxu kana da mata kuma kakesan mallakata. Yayi Murmushi Yace karfa Ki damu my baby tana sanki ba 'dan ka'danba Dan Kullun xan canta gareni yaushe xata ganki. Fa'di take ina San Aunty Laveevah dan Allah kakaini gunta Nakan ce mata xan kawota gunki......... Cikin wani yanayi LABEEBAH ta katseshi da cewa Wlhi qarya take dan ba matar da takesan budurwar mijinta. KAMAL ya gyara xama Yace aa fah😳 da gaske khadi take tana sanki Cikin maseefa tace toni bana santa kuma baxan sota ba danna tsaneta...... Tana fa'din haka takashe wayan gabaki 'daya KAMAL yayi Murmushi axuci yake fa'din bawacce xata qara gigin mallakata saike my baby ina matuqar sanki LABEEBAH kuka tafashe dashi tsakaninta da Allah tanayi SAUBAN na tayata dan ganin kukan da take ba nawasa bane Daqir KAMAL yasamu kanta da daddare Bayan ya qaryata kansa dace mata wasa yake mata Washe gari XARAH na xaune agidansu takalli Innah da baba da suke karin kumallo Tace BABA Yace na'am Tace dama KAMAL ne yakesan LABEEBAH Babah da Innah fuskarsu tacika da fara'a atare sukace kai Amma ko munji da'di Kinga sai ya ha'daku tunda bakwa tare da matsala XARAH tagirgixa kai Tace xan cutar da LABEEBAH tabbas inna qara kasan cewa da KAMAL kamar yanda nacutar da ita a gidan YUSUF Kuma kafin KAMAL ya 6ata na aikata mishi wani lefin da baxan iya komawa gidansa ba Koda ko ya buqaci hakan Innah tayi sak hakama BABAH Candai BABA Yace toh keko XARAH wane lefi kika aikata mishi haka Hawaye ya xubu mata tace Wlhi Babban lefine mummuna Kuma baxan iya gaya muku ba. Dan sirrine tsakanina dashi Ni dai ina roqarku da Allah karku saka wani abu aranku dan gane da Auransa da LABEEBAH Cutace dai na cuci Kaina Dan Allah ya ha'dani da hatsabibiyar qawa wacce takasa bani shawara tagari KAMAL yayi min halacci tunda ya iya 6oye abinda namasa. Hakan yasa nima baxan iya furtama kowa ba. Innah Tace tomu kigaya mana mana......... Babah ya katseta da cewa aa Karki matsa

Chapter 19 of 22