Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
mamakinta. Ga KAMAL ko jin shi yayi wani iri Tsohuwace me kalar kamala da nutsuwa suka gani afalan tare da Momyn KAMAL har dasu 'yan biyu wato Safna da Sagna Da murna sosai kakah ta tarbi su XARAH Tace lale barhaban da xuwanku jikokina Auwal yayi dariya Yace waya gaya miki anama kishiya lale mar haban Tace um um Auwalu wannan nayi shekara da shekaru ina jiranta sai yau Allah yayi Cikin ladabi XARAH da LABEEBAH suka xauna a qasa suka gaisheta Ta amsa da farin ciki. Safna da Sagna suka gaishesu Sannan suka gaida Momy Cikin wani irin *SOO* da qauna ta amsa tana cewa Sannunku 'yan albarka gaskiya naji da'din ganinku Kakah Tace wacece kishiyar tawa. LABEEBAH tanuna XARAH Momy Tace eh lallene sirikar tawa kyakkyawa CE KAMAL Yace ai nagaya miki Tayi Murmushi Tace ga 'Yar uwartama kyakkyawa Yace hmm momy sai shagwa6a ta'ajiye Tace ai da ganinta Safna ce ta ajiye musu kayan marmari Sagna ta'ajiye abinci Ganin kan XARAH aqasa yasa Safna Tace Aunty XARAH Ki 'dago kanki man naganki Shuru tamata tana wasa da hanunta Momy ta qurama LABEEBAH ido. haka kawai taji qaunarta nashigarta KAMAL Yace yaushe kika xone Momy Kakah Tace yan xun nan shigowarsu kenan sai gaku Tashi Momy tayi. Tayi wani shashi na falan tana Murmushi xuciyarta cike da qaunarsu XARAH Kakah tasake sai jansu take da hira LABEEBAH na biye mata Al'amarin daya bah KAMAL da Auwal mamaki kenan ganin bata da'de da gama musu kukan shagwa6a bah Can sukace xasu tafi. Nan take fuskar kakah ta sauya Auwal Yace Xan da'da dawo miki dasu Tace toh Allah yasa Yace AmEEn kakale Safna tagayama Momy xasu tafi nan tafitoh hannunta 'dauke da kayan kwalliya taba Sagna takai musu mota Sannan tamusu fatan alkairi Kakah ko har Mota tarakasu tana samusu albarka. Suka tafi Safna Tace kai Amma budurwar Ya KAMAL akwai kunya da kyau naji Santa Cikin raina da 'Yar uwarta Tsaki Sagna tajah Tace hmm Ni 'Yar uwarta tafimin kyau kuma nafi Santa Safna Tace eh tanada kyau Amma shi XARAN yagani saikije kice ya canja da ita Tace kinga malama ba magana nanema bah. fa'dar ra'ayinki kikayi. Nima nafa'di nawa wani abune. Ta qarashe da mata kallan tuhuma. Cikin takaici Safna tayi ciki batare da tace mata komai bah Sagna tajah tsaki ha'da da kara wayarta akunnanta Su XARAH ko suna xuwa gida LABEEBAH tayima kanta gata ta shige gida Dan mutanan nata sunfara xaxxagama junansu kalaman *SOO* Sai dai murnarta 'daya bataba KAMAL hankicif 'dinsa bah Wannan dare baccin farin ciki LABEEBAH tayi Dan kowane juyi tayi. To saita shaqi qamshin turaran dake jikin hankicif 'din KAMAL Har washe gari XARAH Tace dama xaki tsaya ahaka mana LABEEBAH Tace ban gane bah Yanda kike Cikin farin Ciki yau dama kullun kike haka XARAH tace da ita hakan Murmushi LABEEBAH tayi tace ba lefi nasamu wani abu na KAMAL wanda duk lokacin da naga abun jinake tamkar ina tare dashi Ta6e baki XARAH tayi Tace hmmm qarya Allah dai yakawo miki sauqi *a MASEEFAR SOO.* Cikin wani yanayi Tace nafa'da *MASEEFAR SOO* Yaxanyi 'Yar uwata, Xuciyata ta cuceni da taso wannan koda ya baiyana agareni baxan ta6a Auransa bah Da nuna mamaki XARAH tadena game 'din da takeyi takalleta gami da cewa Me yasa. Bayan kina sansa. Towaima me kenan kikayi Ya baiyana agunki Amma kiqi auransa sabodame _saboda ke. Xan'iya kishi da kowa Amma baxan iya dakeba. LABEEBAH tafa'di hakan aranta_ Afili ko cewa tayi. Haka kawai Shuru XARAH tayi dan jinta kawai tayi 〰〰〰 Yau take jumma'a Kuma yaune aka tashi ta tirqewar hadari a garin na kano Tunda Allah ya wayi gari LABEEBAH take Cikin farin ciki dan sanda kowa yagane hakan Dake yanxu 'yan gidan sunsa mata hawainiya me canja kala akowane lokaci shiyasa bawanda ya tambayeta farin Cikin me takeyi Itako yau tashi tayi da MASEEFAR SON ganin KAMAL Sai xuciyarta tabata hakuri dan ganin gobene ranar xuwansa Sumayya ce takasa hakuri Tace mamah nifa ina ganin dan Aunty LABEEBAH taga hadari ya ha'dune shine take farin ciki Da sauri mamah Tace kumafah gaskiyarki Sumayya Dan gashi har tayi shirin tarbarsa XARAH tayi dariya Tace Allah LABEEBAH yau Karki shiga ruwa kin manta shakaran jiya yanda kika kwana hanci a tushe Tace kudai kunkasa ganewa ne. dan ba'abinda yafi farin ciki kamar anayin ruwa mutum yashiga yana juyi aciki. Wow Wlhi ina tsintar Kaina cikin farin ciki. Kunga nayi kofar gida. Bata jira cewarsu bah tayi kofar gida abinta XARAH tagyara kwanciyarta tace da Sumayya yanxu ruwa xai tsinke Tace aikowa dai LABEEBAH na fitta taga wata lafiyai yiyar motar tayi faking a kofar gidansu Tabbas gabanta yafa'di dan har tayi tunanin ko KAMAL ne Tuni xuciyarta tabata bashi bane dan baicika xuwa awa'dannan ranakun bah Gilashin motar me duhune dan haka bata gane wanda yake ciki bah Shaaaaaaaaaaaaaaa Ruwan sama ya yanke kamar da bakin kwarya Ai tuni LABEEBAH tayi 'dan kwanan da take tsayawa idan hakan tafaru Ruwa ne ake zab gawa sosai Yanda yake sauka a qasa haka yake sauka akan LABEEBAH Sai tsalle take tana murna tana 'daga kai sama tare da lumshe ido tana Murmushi Lokaci lokaci kuma take 'dan juyi Kallo 'daya xaka mata kagane tana Cikin farin ciki Mamaki da Al'ajabi gami da Takaici suka cika KAMAL Dama shine a motar. Kuma tunda aka fara ruwan idanshi yake kanta Eh tabashi sha'awa Amma shi mutum ne mesan yaga mutum na tattalin kansa. Kodan gujema kamuwa da ciwuka Shuru yayi yana naxarinta. Watoh itadai Sam bata da damuwa. yarinta na damunta. bata da matsala Zuwa can cak ruwan ya 'dauke Aiko taturo baki irin bataso haka bah Yaxatayi dole tafitoh daga gun daniyar shiga gida Xuge gilashin motar yayi. Yace Laveeba....... Tun daga tsikiyar kanta taji wani xirrrrr har xuwa babban 'danya tsanta na qafah jitayi wani sanyi ya shigeta ha'de da birki cewa Ya lura da birkicewarta Ta juyo ahankali. Karaf suka ha'da ido. Ya ko dallah mata harara. Tayi saurin sun kwiyar da kanta Zonan Yace da ita Ahankali taje gunsan jiki shaqaf Yace bakyasan lafiyarki ne Ta girgixamai kai. Alamar aa Baki da bakine Takalleshi tare da qara girgixamai kai Cikin fusata Yace baxakiyi magana bah Cikin sanyi ha'de da nuna tsuro tace xanyi fah Yaqara galla mata harara Yace xan qara ganinki ne Taturo baki Tace waitoh menayi Quqarin bu'de motar yakeyi dan fitowa Aiko tafalle da gudu tashige gida Abin yabashi dariya Abaiyane Yace wannan mijinki yanada aiki In kaine yaxakayi Xuciyarshi tatambayeshi Innine maqure xan dinga yi. inyi maganin shagwa6arta....... Da sauri yayima kansa dariya ha'de da cewa abaiyane. Toh bama nibane. Tanada aibine Xuciyarshi taqara tambayarshi aa Yabata amsa still abaiyane Mamakin kansa yafarayi ganin xuciyarshi na mishi wasu tambayoyo masu kama da Wanda yakesan fa'dawa wani yanayi Na me kenan Na SOO Xuciyar tabashi amsa da sauri Ga bansane ya bala'in fa'duwa. Yayinda yayi saurin kawar da tunanin Yana murmushin tsoro Fatima-zarah & Aisha-Labibah Yace abaiyane Tuni yakori tunanin xuciyarsa ya 'dauko soyayyar TEEMAN Sa yasaka agaba hankalinsa kwance Kun gani ko taje ta jiqe shaqaf. Cewar Sumayya Mamah ta galla mata harara Tace Naji kince min kanki namiki ciwo ko mura na damunki XARAH ma harararta tayi taqara da cewa kokuma ta'ishe mutane da jan hanci bah Shuru ta musu dan jikinta ya mutu mu'dus ba abinda takeso ayanxu kamar taka'daice tayi tunanin masoyin nata KAMAL Ana kiranki awajefah tafurtama XARAH hakan kamar xata fashe dakuka Sumayya tayi dariya Tace dan an'dauke ruwanne kikesan kiyi kuka Ta harareta Tace ban saniba Wa yake kira na KAMAL tabata amsa Cikin sauri Kan XARAH taqara magana wayanta ya 'dau ruri My luv ganinan gareka masoyinah Haka kawai Tace Tatashi ta ficce LABEEBAH ta shige 'dakin mamah tana xubar da hawaye Wane irin soh nake maka KAMAL Duk lokacin dana ganka saika sani kuka ha'de da burkitani Take fa'dar hakan axuciyarta Wayarta ce tafara ringing tana 'dagawa taga KAMAL ne Nan take mamaki ya kamata. Ta'dauka Kitemaka kiyi gaggawar canjah kaya dan Allah Yace da ita hakan Murmushi tayi Tace toh Yace ban jiba Tace cewa nayi toh Kashe wayar KAMAL yayi yamaida kallansa kan XARAH asanyaye Ya rasa dalilin dayasa yake bala'in jin da'din muryar LABEEBAH Ashe awayama tana da'di haka Kaji shuru my Luv kana kallona kamar ka shiga tunani Yayi saurin kawar da kansa Yace kyanki nake wara gani Wanda yake hanani bacci maye sirrinne Tayi dariyar jin da'di Tace bawani Sirri my luv Yace da gaske yanxu LABEEBA baxata canjah kayan jikinta yanxu bah Tace karka damu tasaba Amma tunda kamata magana xata canjah Yace kice inada darajah sosai haka Tace kaima kamanta ne. sunanka 'dayafah da KAMAL 'dinta. Ai ina ganin idan aka cire iyayanmu xakafi kowa daraja a idanta Yayi Murmushi Xuciya da abinda takeso ai ko minti 'daya LABEEBAH bata qaraba ta canja kayan jikinta tana 'dan Murmushi dan kulawar da KAMAL yabata tamata da'di hakan ne ya kori kukan da takeyi MASEEFAR SOO 〰〰〰〰〰〰 Rayuwa kenan Yau taxo maka da da'di gobe taxo maka sa6anin hakan Haka watanni suka shu'de masu XARAH da KAMAL & LABEEBAH Toh yau Allah yayi saura sati biyu bikin XARAH-da-KAMAL Tun yanxu suka cika da shagalul lukan biki 'Din kunane baje akan gadan Innah na XARAH da LABEEBAH Wanda KAMAL yakawo musu Ko wacce kala goma goma Shiri suke dan tafiya sweet-faty Sanyi kyau sosai Cikin shigarsu ta doguwar Riga ta materiyal jah me ratsin ash Colo sunyi kyau sosai dan kam kallo 'daya xakama shigarsu kagane sunyi shigar alfarma dan tsadar kayan Aikin KAMAL ne Qawayansu na islamiya dana skull ne sunkai Su ashirin kuma kowacce tayi shiga takerema sa'a Jamila 'daya daga cikinsuTace kai habah LABEEBAH lokaci na tafiya yaushe kukaje make-up kuka dawo har mutafi Au namanta anqara awa 'daya ban fa'damiki ba. LABEEBAH tace da ita hakan Sumayya Tace kunga kutashi mufara gaba tunda dama daga canne xasu hucce Sukace toh sukayi can Su XARAH na fitowa Auwal Yace 'yan gatanka sunfito Cikin sauri yakai kallansa Kan XARAH nanko suka ha'da ido tasakarmai Murmushi Yace wow. Kyau haka tunkan ayi make-up ya dire kallan nashi akan LABEEBAH Wacce tunfarko tayi qasa da kanta tana wasa da xoban hannunta Tace toh munji. Yanxu dai muje mutane sunfara qorafi Yace aikowa dan muma yanxu muka gama bada hakuri dan haka ku shiga da sauri Hiyana make-up beauty sukaje Nan tagyara amarya XARAH tsaf ha'de da LABEEBAH Duk iya hangenka qaryane kagane wacece amarya tsakanin XARAH da LABEEBAH Tun amota KAMAL yaketa satar kallansu Wani abokinsa Jameel Yace dan Allah XARAH kiban 'yar uwan nan taki plx dan Allah Tace wa ni😳 Rabani da LABEEBAH karkasa saidai inga tana yima wasu dariya bani Da mamaki Yace ban gane bah Shuru tamishi Yayinda LABEEBAH tayi fuska kamar ba akanta ake maganar bah Jameel ya maida kallansa kan KAMAL kamar xaiyi kuka Yace tayimin shuru KAMAL yayi Murmushi yace wacce acikinsu Yace XARAH da ita 'din mana KAMAL Yace hmm. ai indai MATAR KAMAL CE baxaka ta6ajin ta bakinta bah My XARAH ko bata da abin cewane shiyasa yin shuru Cikin sauri yace MATAR KAMAL. Kana nufin ita'din matar Aure ce. kuma mijinta ya barta haka KAMAL Yace aa fah. Ba haka nake nufiba Sunan saurayin natane KAMAL me sunana Jameel ya ta6e baki danuna kishi Yace yabada sadakine Bana tunanin hakan Amma ban saniba. KAMAL yabashi amsa ataqaice Yace wow Allah Nagode mah dani xa'ayi Cikin sauri XARAH Tace hmm Allah yasa Shima da saurin Yace AmEEn LABEEBAH najinsu ita jin da'dinta 'daya yau XARAH da KAMAL sunkulle bakinsu basuyi kalaman so ba bare susa mata damuwa da tashin hankali Wajan shaqatawane qayataççe Jameel abokin KAMAL ya paka motarsa Kallo 'daya XARAH da LABEEBAH sukama wajan gun ya basu sha’awa Kowa idansa akan motar. sunasan ganin fitowar ango da amarya LABEEBAH ce tafara fitowa aiko masu photo suka fara 'daukarta tunaninsu amaryarçe Ganin haka yasata saurin bu'dema XARAH kofah Yayinda Jameel ya bu'de KAMAL Aiko suka jera abin sha'awa. Kamar yanda suka dace da juna. haka xanso ki'daga idanki ki kalleni Wlhi ni dake mun dace da juna. Jameel yace da LABEEBAH hakan Cikin sanyayyiyar. Tace ko Yace gaske Ba mamaki kai kaga hakan. Tafa'da tana mesan wucce shi Cikin sauri yasha gabanta Yace haba LABEEBAH bakyau wulaqanta mutum fah Tace toh na wulaqan taka ne Yace Kwarai kowa dan kema kinsan hakan. ina sanki LABEEBAH. Wlhi ba KAMAL ba koma waye baxan ta6a bar mishi keba Tayi murmushin daya qara mata kyau. Tace Ka ha'du. Ka iya wanka. Kana da kyau. Ba macan daxata ganka ta qika. dan kayi tako ta ina Amma gareni banga hakan ba. Dan matsalar 'daya CE Kai ba KAMAL bane. Baka da wani abu takaxo dashi irin nasa. Da ace xaka kasance kome irin qamshinsa ne dako na soka..... Tana kaiwa nan tashige shi abinta Shuru Jameel yayi xanci kanta na yawo akunnansa Duk sai yaji kansa namasa ciwo. Dan haka sai kawai ya koma Cikin motarsa LABEEBAH ko bayan taxauna duk sai idan maxan gun ya dinga sauka akanta. Taji takasa sukuni. Hakadai ta'daure ha'de dayin fuska tana kallan XARAH da KAMAL tana kissima abubuwa da dama aranta Ki'de kidene suka ji ha'de da ciye ciye dashan kayan Su drink dasu fruit abindai ya qayatar. Dan kallo 'daya xakama duk wanda yake gun kagane yana Cikin farin ciki Allah Allah LABEEBAH takeyi atashi dan xuciyarta tafara mata xafi qirjinta ko ciwo ya fara mata dan irin soyayyar da KAMAL yake nunama XARAH awajan Hankalinta ya farah tashi ba 'dan ka'dan ba Bama wannan ba. Gani tayi kowacce mace agun jifan KAMAL take da wani fitinannan kallan wanda kallo 'daya xakama kallan nasu kagane na sone Ni ka'dai nalura da hakan Xuciyar LABEEBAH tatambayeta Nan take. Tabata amsar eh kai. Dan kinfi kowa sansa ne Hawaye ne yanemi xubo mata tayi saurin mayar dashi. Lokacin kuma yaxo dai-dai data ha'da ido da XARAH Cikin wani yanayi tasakar mata murmushin yaqe Ba'awani da'deba aka tashi. Kowa Yakama gabansa Qawayan Su suka dinga yabah taron. Hadai aka watse Al'amarin daya yima LABEEBAH da'di kenan dan tana qara cigaba da ganin KAMAL da XARAH ne. Qirjinta namata xafi. Tun amota XARAH take tambayar LABEEBAH lafiyanta qalau kowa Tace lafiya lau kaina ne ya kemin ciwo Cikin muryar qasa qasa XARAH Tace kodai soyayyar KAMAL ne Murmushi LABEEBAH tayi Tace ko 'daya Toh Allah yasa XARAH tace hakan LABEEBA tace AmEEn Haka suka dawo gida. Ga mamakin LABEEBAH ko shine tun awajan sweet faty da qirjinta yafara mata ciwo har yanxu bai dena bah Tunaninta ko ganin XARAH da KAMAL ne. To yanxu dabata ganin ciwan ya 'dauke man Kuma Data rintse ido saita dinga ganin hoton XARAH da KAMAL Suna dariya a wajan sweet faty 'dinnan Saiko hankalinta yaqara tashi Abu kamar wasa saida taxo kwanciya dan hutawa Bacci Yace baisan xancan bah. Dan qirjinta ciwo yafara mata yayinda xuciyarta tacika dasan ganin KAMAL Kuka take sosai tana Allah wadai da xuciyarta data so Wanda yake San XARAN ta Ban yima kaina adalci bah tunda nasoka KAMAL Allah katemaken kaciremin soyayyar KAMAL Haka taketa fa'da a baiyane tana dafe girji Kallan agogo tayi taga 11:00pm na dare. Tamaida kallanta gun Sumayya da XARAH da suke bacci hankani kwance Kuka ya da'da kubce mata. Numfashinta yafara fitta sama sama. Nan hanakalinta yanemi fitta daga gareta. Al'amarin daya tashi XARAH kenan taganta Cikin wannan halin Cikin tashin hankali Tace lafiya me yake damunki innalillahi meyasa meki Cikin wani yanayi Tace qirjina XARAH qirjina temakeni Xan mutu Kwalla qara XARAH tayi tana kiran mamah Cikin tashin hankali Mamah tafitoh daga 'dakinta da sauri tana tambayar lafiya Nan tanuna mata LABEEBAH tana cewa kinga mamah xata mutu wayyo Allah mukaita Asibity Itama mamah Cikin rikicewa Tace me yasa meta haka Wlhi ban sanibah najidai tace qirjinta na ciwo wai xata mutu Mamah taje tagayama Malam Sanih shima Cikin wani hali yace muje asibity kunga tasume mah Subhanallahi Aiko nan XARAH da Sumayya wacce tafarka itama suka 'dagata mamah tatemaka musu suka fitoh waje Xarah Tace mamah bari atashi ya Usman saiya kaita a ababur 'dinsa mu sai mushiga adaidaita sahu Malam Sanih Yace Yauwa kinkawo shawara. nan Usman suka fitoh da XARAH Yana cewa meya sameta. Wai qirji mamah Tace dashi Nan Cikin sauri mamah da XARAH suka sata kan babur 'dinsa Sumayya taxauna abaya dan riqeta sai Asibity XARAH ta kulle gidan mamah tafitoh daga gidansu dan tagayama Innah sukayi titi dan binsu Da sauri nurse suka kar6i LABEEBAH dan bata temakwan gaggawa Duk iya binciken doctor ya gane damuwa CE da saka abu arai yayima LABEEBAH yawa Cikin wani yanayi ya kalli Malam Sanih da mamah Yace kutemaki 'yarku kubata abinda takeso inba haka bah xaku rasata dan xuciyarta tafara kumbura Cikin tashin hankali suka ce xuciyarta ta fara kunbura Yace yes Cikin mamaki mamah Tace a'iya sanina LABEEBAH bata Cikin damuwa dan ba'abinda tarasa Doctor Yace akwai. Lurane bakiyi da yanayinta bah Ki saka ido akanta xakice nace miki Da mamaki da damuwa suka fitoh daga office 'dinsa Cikin sauri Usman da XARAH suke tambayarsu me doctor Yace Nan suka gaya musu Usman yashiga damuwa. Yayinda XARAH take kissimawa aranta tabbas MASEEFAR SOON KAMAL ne yafara ta6a xuciyarta ba wani abu bah Washe gari da qarfe goma sha biyu na ranah XARAH ta kira KAMAL tagaya mai Komai Cikin tashin hankali da damuwa Yace what. Xuciyarta tafara kumbura Cikin damuwa XARAH Tace eh haka Yace KAMAL Yace akwai matsala my TEEMAH. Dole asan yanda xa'ayi dan gaskiya xa'a iya rasata Tace yanxu kana inane Yace ina abujah yauxu dan ko minti ishirin banyiba da shigowa gida Tawaro ido kamar Yana ganinta Tace abuja fah kace Eh Wlhi. wani kiran gaggawa nasamu gun Dadyna shiyani bin jirgi naxo Tace aikowa sai aikin jirgi yanxu dai bara na Barka ka huta mayi magana anjima Yace toh my TEEMAH luv u Tace me 2. Kwana biyu LABEEBAH ta'dauka a Asibityn. Ba lefi ta'dan samu sauqi yau tunda har tana iya magana Cikin hankalinta Amma bata cin abinci sai ruwan da ake qara mata Yan xuma Mamah CE tasata a gaba wai saitaci abinci dan bayan da doctor dasu nurse basuyi da ita bah akan taci taqi ci dan Ita bajin yunwa take bah. aa ganin KAMAL take sanyi. Ga ninshi shine kwanciyar hankalinta. Tatabbatar mah kanta tana ganinsa ciwanta ya warke Ta kalli mamah Cikin xubar hawaye Tace Allah mamah banajin yunwa Tace toh meyasa LABEEBAH Tace hakka dai. Innah Tace ki daure kici kinji Tace Wlhi banajin yunwa. Shuru sukayi Suna mata kallan tausayi Can mamah takalli Innah Tace muje gida mubarta da Sumayya dan bake bani ai baiyiba Innah taja numfashi Tace hakane XARAH mah ta dawo da matar Suleiman ko ta Bashir Mamah Tace gaskiya kam dan hakan shiyafi Suntashi xasu tafi kenan doctor da KAMAL suka shigo Cikin ladabi KAMAL da doctor suka gaishesu. Suma suka amsa Cikin kulawa Doctor Yace D KAMAL narasa yanda Xanyi da yarinyar nan. KAMAL ya kalli LABEEBAH data juya musu qeya Yace metayi Yace taqicin Komai Wlhi. Da sauri KAMAL ya waro ido Yace what 2 days bataci Komai bah Yes doctor ya tabbatar masa tare da qarawa da cewa ranar kabata wani da kaxo ne Yace eh tasha tie Sumayya ha'da mata. Sumaiya Tace Allah Ya KAMAL ko anha'da mata baci xatayi bah.... Mamah Tace Hakka nayi fama da ita kinga innansu xomu tafi Innah Tace toh Amma dan Allah kusakata taci wani abu KAMAL Yace toh innah insha Allah Suka fitta Sumayya tabisu tana cewa bari in rakaku bakin titi mamah Tace toh xomuje sukayi gaba Doctor ya kalli KAMAL Yace ina xuwa Allah yasa kanna dawo kacika mata ciki danni nayi nayi abin yaci tura KAMAL Yace bakadai San yanda xakayi bane Yace Allah ko. Toh ai gaka gata Allah yasa tabaka kunya Dariya sukayi doctor ya fitta KAMAL yaja kujera ya zauna Yace nasan darajar KAMAL xanci kamar yaumah atemaken kar aban kunya kici abinci dan Allah Tace banajin yun...... Yayi saurin katseta da cewa kijuyo kikallan inyaso saikimin qaryar Allah ba qarya.... Bakiji me naceba kenan ya qara katseta Wayyo Allah masoyayina karka takura xuciyata akan kallanka. Xaka tafi kabarta Cikin tunaninka Inasan KAMAL dan Allah kasoni ko sau 'dayane. Duk da nasan ko kasoni baxamu ta6a kasan cewa tare bah LABEEBAH ce me fa'din hakan aranta. Yayinda hawaye ke xuba mata. Kitemaka dan Allah kici Goge hawayanta tayi tajuyo karab suka ha'da ido Al'amarin yafaru biyu wato bugun xuciyarsu. LABEEBAH tasaba da hakan. Yayinda shi ako da yau she yake tambayar kansa meyasa hakan take faruwa dashi akanta Toh fa'damin yace da ita Bana jin yunwa tafa'di hakan cikin sanyayyiyar murya Shuru yamata yamiqa mata abincin da yasa mata Batayi musu bah takar6a. shinkafa da miya ce dai. taxubama abincin ido tana mamakin kanta dan sai yanxu taji wani bala'in yunwa. Wato dai ya tabbata KAMAL ne farin Cikin ruhinta Shiko Cikin jin da'di Yace Yauwa koke fah. Yi maxa kici Tayi shuru ita bataci bah kuma taxuba mishi ido Ganin haka yasashi tashi yasama

Chapter 4 of 22