Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da kanka mana ko bakwan kane yanxu gidan Yakanyi Murmushi Yace hmmm MASIFAR SON da nakema XARAH bata kai nan ba nutsuwata. kema kyayimin fa'da haka kawai nashiga ga sirikata Ko kin manta yanxu innah suruka tace LABEEBAH takanyi shuru dan yanxu YUSUF ya canja mata gani takeyi ya dena Santa XARAH ya keso. Hakanko yana sawa taqara jin haushin ~*XARAH*~ *Bayan shekara biyu da watanni* Haka rayuwar tasu taketa tafiya yau taxo ma LABEEBAH da da'di gobe kuma 6anin haka. ga kowa mah aduniya rayuwar da yakeyi kenan . XARAH ko sai abinda yaci gabah ita da Hajjiya Turai. Inda ita Turai 'din tafara nunama XARAH toh fah lokaci yayi daxaki fara aiki da maka manki XARAH XARAH ta girgixa qafah Tace tunda na yayaye SAUBAN bah Turai Tace madallah kinga yanda kike kuwa. Wlhi kamar bakiyi Aure kin haife SAUBAN bah Kinga kayan nan maganin matane na haqiqa na mallaka awajan wani hamshaqin malami na kar6o dan kaf magungunansa bana banxa duk tsiyar namiji ya kusan ceki ya rufe shafin wata mace kenan. Wlhi ina tabbatar miki idan kikayi amfani da wa'yan nan narantse miki YUSUF baxai kalli LABEEBAH ba Dan kin tarwatsa soyayyarta axuciyarsa har abada Musumman inya kusanceta kin san Allah yabar kusantar kowace 'ya mace aduniya in ba kebah Ace shi mebin matane to daga ranar ya barsu har abada Dan kallansu xaiyi tamkar maxa 'yan uwansa *XARAH tasheqe da wata shegiyar dariya suka tafah* *Tace an gaya miki ni wawiya ce da xan bari YUSUF yasan LABEEBAH.* *inaaaaaaa.* *ta girgixa kai* *Taqarashe da cewa Wlhi Matarsa mah* *Allah ya 'dauketa ne dan in mallakeshi Ni 'daya* *Kawai xan so ya Aureta ne saboda surutun Mutane karsuga abayi mata adalci bah* *Idan muka kasance matansa ko tayayane saina rabata dashi ita dashi saidai ido👀* Kinga idan na 'dan 'dana mata axabar sanshi datayi saina San yanda Xanyi insashi ya rabu da ita Jameel ya Aureta Kinsan wannan yana cikin game 'dinmu nida shi. Turai ta waro 😳 Tace kin Allah na manta dashi XARAH Tace niko ina xan manta dashi Turai tajah numfashi Tace danayi wani tunani mexai hana kibarta da Jameel sai musan yanda xamuyi kisami YUSUF ke 'daya XARAH ta gyara xama Tace har yanxu kin kasa fahimta Auran LABEEBAH da YUSUF tamkar ba Aure bane Dan xan bari ta Aure shine saboda mutane Kuma ba abinda Auranta dashi xai taremin. Saimani daxan tare mata shi Ina tabbatar miki kan aje ko ina xata nemi ya saketa Ni kuma Xanyi ammafani da wannan damar in ingixa xuciyarshi ya rabu da ita Jameel ya samu Turai ta 'daka mata duka Tace gaskiya XARAH baki da alqawari. Xuciyarki abushe take. Dan imanin naki ya tafi. Ixuwa yanxu har nafara tausayin LABEEBAH Wlhi Bakiyi halin *Nana Fatima* bah Macan da babu kamarta aduk duniya Macen da bata da mugunta macen da......... XARAH tayi saurin katseta da cewa Allah ya bamu albarkacinta Eh inada nawa halin Amma kome nayi ke kika 'dorani akan hanya Amma kinnasan cewa wani...... Turai itama ta katseta da cewa naji abin baikai nan bah koma me kikayi MASEEFAR SONE yaja miki haka Yanxu saura wata 'daya bikin naku baki ban labarin yanda aka karke da Innah bah [12:41PM, 06/10/2016] Rahamat Nalele💋: XARAH Tace hmm Wlhi da har nayi tunanin ko Innah ba sona takeba Turai Tace meyasa Tace yanda tanuna Allah ya karta ya binne baxan auri YUSUF ba dan na LABEEBAH ne Baban mu ya biye mata ko Ita kuma shegiyar taxo tasaka Su agaba da kuka da magiya akan ita taji tagani ya Auremu mu biyu batasan rabuwa da nine Bu'dar bakin innah Kinsan me tace mata Turai ta girgixa kai XARAH taciga da cewa Cewa tayi wai tarufe mata baki ita bata da hankali Akanme xata CE YUSUF ya Aure Ni LABEEBAH tagyara xama tadinga jero mata misalai akan batasan ta rasani kusa da ita muna san junanmu dan Allah tah bari ayi auran Momyn YUSUF nagun akayi Komai daqer da si'din gashi Innah tayarda Kinsan Allah agun sanda soyayyar LABEEBAH ta motsamin Santa ya manayemin xuciyata Amma da YUSUF yakira awaje dan suta6a ta'di nan take tsanarta ta dawomin Turai tayi dariya da cewa yanxu innah ta yarda kenan XARAH Tace eh kai ba dole bah Dan LABEEBAN da Momyn YUSUF ne suka sukata a gabah da magiyar har tayarda Washe garin ranar iyayan YUSUF suka kawo sadakina. Toh kinji Komai Turai Tace toh madallah Yanxu dai yau xaki fara amfani da magungunan nan Dama na wata 'daya kinga duk ranar da YUSUF yayi gangancin ta6aki ko uwarsa qarya take ta rabaki da shi Al'amarin auran nasu yaxo da salo Yau saura sati 'daya.....☝🏻jal Amma XARAH ta nunama LABEEBAH karsuyi Komai Yayinda LABEEBAH Tace ko walima baxa muyi ba XARAH Tace toh duk yanda kikace haka xa'ayi LABEEBAH ta girgirxa kai Tace aa karmiyi Komai 'din Sumayya najinsu Itadai tarasa dalilin da yasa. Talejin haushin 'Yar Uwar tata XARAH Gani takeyi ta cutar da LABEEBAH Akanme xata yarda da ha'din da LABEEBAN tayi bata tirjeba Sai kawai ta tsinci kanta da jan tsaki Rukayya tata6e baki XARAH da LABEEBAH suka bisu da kallo XARAH takasa hakuri Tace wai meyake damunki ne Sumayya kwana kinnan kin canja daga kijah tsaki saiki dinga hararata Rukayya Tace qila kinyi abinda bai dace bane Tace menayi Aunty Rukayya fa'damin Tashi tayi tana shanya Tace inaxan sani XARAH gaki ga Sumayyan ita xaki tambaya ai Saitajah tsaki Tace banyi Komai ba. Inadai ganin iskancine kawai yake sata haka Rukayya tace hmmm ba mamaki Da yammar ranar ne Rukayya tayi qoqari wajan tursasa LABEEBAH shan tsumi na mata da abinda baxa'a rasabah Fa'di take Kinga XARAH tayi Aure tasan me yafi da'di a Aure da abinda yake kawo matsala Ba xama xatayi YUSUF yajita salam bah Dan haka kema kidage da shan kayan marmari da wannan tsumin Toh LABEEBAH Tace mata dan tun safe barartace take mata ciwo ka'dan ka'dan Abin bai caf keta da kyau bah sai gab magriba Nan ta nemi sumewa Usman ya furgita dan yasan yanda ciwan nata take Ya shiga 'dakinsa dan tuna wani magani da wani me magani yabashi Yace insha Allah inya tashi mata tajiqa tasha xata samu lafiya Cikin sauri Rukayya ta ji'ka maganin suka bata tasha. Nan bacci yayi awan gaba da ita Bata farkaba sai kusan asubah takoga al'adar Sumayya tayi mata sannu Tace kina buqatar wani abune Tace aa Nan tatashi sai tajita garau sumul Saidai tana 'danjin ciwan ka'dan Da tayi karin safe Usman ya qara bata tasha. Rukayya Sumayya Innah XARAH duk sata sukayi agaba Suna yimata kallan tausani SAUBAN na maqale da ita fa'di yake cikin gwarancinsa yana cewa me yasameki momyna Ta shafah kansa Tace bani da lafiya SAUBAN Amma na samu Sauqi Saiya kwanatar da kansa a qirjinta yayi lamo Innah taja numfashi da kallan Usman Tace aiko tunda yayi mata magani ka qara kar6o mata ta ajiye saboda wata ranah Yace akwai da yawa nama bata. dan me maganin baya xama yau yana wannan gari gobe yana wannacan Innah Tace Allah mah ya rabata dashi gabaki 'daya AmEEn duk sukace Da yamma Momy ta aiko wasu attajirai mata da kayan Auran LABEEBAH dana XARAH Komai iri 'daya Kaya masu kyau da inganci da sha'awa 🌵🌵🌹🌹🌵🌵 ~*MASEEFAR SOO*~🌹 🌵🌵🌹🌹🌵🌵 Toh yau dai alqawarin ya cika *An 'daura Auran YUSUF da LABEEBAH & XARAH* Me xai faru 😳 Bayan Amare sunsha nasiya sunsha kuka 'yan kaisu sun luluqa dasu Abuja inda suka diresu a gidan Momy suka Sha nasiyarta sai suka kwashesu suka kaisu tangamemen gidan inda yaba mutane sha'awa Dan part 'din XARAH daban na LABEEBAH daban saidai akwai wani falo atsakaninsu Wanda xai sadasu da juna in sunso Wannan aikin Dadyn YUSUF ne dan shi yasa aka Komai tunda yaji maganar 'dan nasa Su biyu xai aura yasa aka hau gini ahankali har aka gama Komai Haka Mutane suka musu addu'ar xaman lafiya sukayi gidan Momy acan xasu kwana [1:28PM, 06/10/2016] Rahamat Nalele💋: YUSUF ko yana tsakiyar abo kana yansa. yayi musu shuru yanajin tsiyar da suke masa yau xai qara angwancewa Salim 'dan uwansa Yace toh 'dakin waxai fara shiga oho Yace LABEEBAH bah 'Daya daga cikinsu Yace habah dai kasani tunda akayi maganarka da XARAH batakayi gigin da kasake ha'duwa da itaba ko ka ganta kanta ankare da kai kakeyin fuska Yace hmm kunga xaku rakani ne ko in tafi da Kaina Sukace wane mu sai munje munga kwul Uwar dakah XARAH safa da marwa daketayi cikin bet room 'dinta jiki ya jiqa da magani yana buqatar maxa Fa'di take aranta Allah yasa yafara shiga gun LABEEBAH yana xuwa gunta ta rufe kofah shikenan baxai koma gun LABEEBAH bah. A sannan in Komai ya wakana ta tarwatsa tsakanishi da LABEEBAH LABEEBAH ko tsoro ne ya shigeta hankalinta yatashi tasani ba makawa YUSUF agunta xai kwana tana tsoran mexai biyo baya itadai batasan ya abin yake bah Amma acan baya XARAH ta ta6a gaya mata ba da'di har sumewa mutum yake Dariyace ta kamata data tuna tanamah period me xai mata mah tana cikin jini Wata xuciyar tace mata ba gobe xaki gama bah Abayyane Tace ba gama XARAH bah....... Shugowar YUSUF ne ya katseta da xama kusa da ita Yace iye kaga Uwar gidana Ta harareshi Yajawo ta jikinsa Yace yau kin xama tawa nutsuwata. yau xan bu'de miki wata rayuwa. Baxaki qara ciwan marar da kikeyi bah Shuru tayi mishi Shima shurun yayi can Yace nabar mutane a Babban falo tashi muje Su muku Nasiha Ta'dan bugi qirjinsa takai harda kai 'Dago fuskarta yayi yakai bakinsa cikin nata ya hau yimata kiss baji ba gani..... Can wayarsa tayi qara. Hakan yasashi barinta tako langwa6emai ajiki Ya 'dauki wayan idanshi alumshe Salim Yace xamu tafi kasa in kira XARAH ka kuma shanyamu kamar kayan wanki Xare LABEEBAH yayi daga jikinsa ya miqe da riqo hannunta Yace muje Ahaka sukaje har falan hannunshi Cikin nata taxauna kusa da XARAH Nan abokanaye suka hau addu'o'e dayi musu fatan alkairi dasu xauna lafiya Sannan suka ajiye musu kaji da madara suka tafi YUSUF yadawo da kulle falan bayan ya rakasu XARAH Tatashi tana cema LABEEBAH saida safe Bata jira cewar LABEEBAN bah tayi part 'dinta YUSUF ya bita da kallo LABEEBAH ta kalleshi ka'dan ya kashe mata ido 'daya Yace bara inje imma XARAH saida safe sai inxo ko 'daga mai kai tayi Ya qaraso da saka hannunsa ya shafi fuskarta ka'dan Sannan yayi part 'din XARAH Ita kuma tayi part 'dinta . [2:55PM, 06/10/2016] Rahamat Nalele💋: Abune wannan bai saba dashi bah Abune Wanda yake tunanin ta ina xai fara yinshi Shiyasa da ya shiga bet room 'din XARAH ya xauna gyefan gadanta yayi shuru Itama da take kan gadan shuru tayi xuciyarta nayi mata xafi yanda 'daxo yaje ya da'de a 'dakin LABEEBAH Uwar me ya tsayayi Can dataga shurun yayi yawa saita fashe mai da kuka wiwi Hankalin YUSUF yatashi sai yarasa yama xaiyi da ita Yasani in LABEEBAH namai kuka saurin ha'data yakeyi da jikinsa nan xata mishi shuru Amma XARAH dako hannunta bai ta6a riqewa ba ya xai mata Tashi yayi yadafe kansa Yace kiyi shuru dan Allah Aiko taqara rushewa da kuka....... Shikansa tsintar kansa yayi agabanta ya rungumeta still bata dena kukan bah Ciro hankicif 'dinsa yayi yana gige mata hawayan Yace plx XARAH kiyi shuru meya faru Tace meyasa baka sonah Jin Kalmar yayi tamkar saukar aradu da kah Yace ina sanki mana Tace ban yarda bah dan kafisan LABEEBAH dani Shuru YUSUF yayi yarasa me xaice mata Itako taxare jikinta daga nasa taci gaba da kukanta Yaqara dafe kansa yana kiran sunan Allah Yace yanxu me kikeso na miki na nuna miki ina sanki Tace sonake ka kwana anan dan ina bala'in furgita inna kwana ni 'daya ni bakamar LABEEBAH bace da bani tsoro Da sauri ya kalleta kana yajah numfashi yayi shuru kawai yana kallan qasa Can Yace toh bari nafa'dama LABEEBAN saina dawo Matsowa jikinsa tayi tashige mishi ta fara kuka tana cewa Wlhi LABEEBAH ba Komai xatace bah tasan halin tsorona plx karka futa in ka fita sumewa xanyi dan hakama 'daxo naga kamar mciji ya wucce Shuru YUSUF yayi danjin wani furgitatcan qamshi dayake shaqa daga gareta wanda yasa yafarajin kanka na juyewa wani maseefaffan filing na na sha'awa na kusantoshi. Sai tsintar kanshi yayi da rungumarta yafara kissing 'dinta tako ta ina Sanda ya samu nutsuwa na kiss 'din Sannan ya rabata da jikinsa yayi toilet dayin wanka da alwala Bayan yafitoh Yace itama taje tayi Kafin ta fito ya canja Kaya Dake tunkan suxo tayi wanka sai kawai ta'dauro alqala suka hau lafula raka'a biyu dayin Addu'a Sannan ya 'dauko mata kaxarta da madara yasa a gaba sukaci ka'dan yanata mamakin kansa da ita. Bayan sun gama XARAH tayi gado Ba wani nuqu nuqu YUSUF yabita Ya rabata da Komai nata ya hau sarrafata kamar injin YUSUF yaga bala'i da MASEEFA ganin idansa ya kasa gajiya da XARAH Sam Yi yake Amma yaqi barinta Itako sumewa tayi dan batayi tunanin aika aikan da tayi xaikaita hakaba Can YUSUF ya fashe da kuka danjin wani MASEEFAR SON XARAH daya cafki xuciyarsa Badan yaso ba ya barta dan karya illata kansa Xuba mata ido yayi kawai yana kallanta SOONTA na shigarsa LABEEBAH fah😳 Gani tayi shuru YUSUF bai dawo bah taje tayi wanka tasaka kayan bacci tayi addu'a da kwantawa abinta sai bacci yayi awan gabah da ita Ta cikin baccin natane tayi mafarkin KAMAL _cikin wani ni'iman taccan gida me kyau_ _Yana wajan furanni Sai qamshin furannin ne me tashi agun_ _KAMAL yana xaune kan sallaya yana addu'a Amma batasan me yake cewa bah_ _Ya juyo ahankali suka ha'da ido_ _Wannan abun dayake fitowa a idansa ya shiga nata idan shi yafitoh daga idan nasa ya shiga natan_ _Ta lumshe ido Tace Ya KAMAL wata duniyace wannan._ _Yayi Murmushi ya nuna mata wani gu da hannunshi. Tabi gun da kallo_ _XARAH tagani da YUSUF maqale da juna. Amma hankalin YUSUF nakanta dan sai miqo mata hannu yake alamar daje gare shi yana hawaye still yana rungume da XARAH_ _Saiko ta maqale kafa'da cikin tsoro Tace baxan xo bah_ _KAMAL yayi Murmushi da girgixa kai Yace plx Babyna kibarsu ahaka Karki shiga rayuwarsu_ _kijirani kiriqemin alkawarin kanki_ _Nufu shi tafayi. Saidai wani xare me qarfi yayi mata katanga da_ _KAMAL Tace dan Allah Ya KAMAL kaxo kayanke igiyarnan kar Ya YUSUF ya kamani_ _Yace bani da damar yanke igiyar_.... Furgigit LABEEBAH tafarka lokacin yayi dai-dai da qala kiran sallar asubah. 🤔 Amma fah kumin afuwa masu xagina Nagode Sai dai inasan kusani baxan canja tsarin littafina bah Fa'di take aranta nariqe maka alqawari Ya KAMAL Sannan kuma kar in shiga rayuwar XARAH YUSUF In jiraka Me hakan yake nufi Shuru tayi xuwacan xuciyarta tacemata kishare kawai karki sakama kanki damuwa ai mafarki ba gaskiya bane Aiko tatashi tayi toilet ta gyara jikinta dayin wanka kana ta share falan nata duk da bawani datti bane dashi Ta fesa turara. Sannan. Ta koma ta kwanta tana tuna YUSUF daga cewa bari yayima XARAH saida safe Amma shuru Bayan YUSUF ya tsaftace kansa yafitoh ya'dan yarfama XARAH ruwa Aiko nan ta farfa'do da jan numfashi Ya xauna gyefan gadan yana kallanta Yace in 'daukeki in miki wankan ne ko Yah Ta harareshi tare da tashi tayi toilet ahankali dan ta 'dan 'dana ko'darta YUSUF yayi Murmushi Yace yanxu aka fara Koda tagama tsaftace nata jikin xama tayi a toilet 'din tana rayawa aranta eh Lalle YUSUF bashi da imani Tun take da KAMAL bai ta6a bata wahala irin yanda YUSUF ya bata yau bah Shurun yayi yawa inji xuciyar YUSUF Dan haka sai kawai yafa'da toilet 'din Aiko ganinta yayi cikin tunanin Yace Kinga malama ke nake jira Tace Menene Dariya yayi dan Ganin yanda ta tsorata Ya qarasa shiga toilet da kamota suka fitoh da kwantawa Nan ya rungume abinsa XARAH dai Tace tayi kwanan farin ciki Yayinda YUSUF yayi na Mamakin kansa da ita Farkawar YUSUF yayi dai-dai da farkawar LABEEBAH da Asuba haka yatashi XARAH sukayi Sallah Washe gari kusan qarfe takwai Momy ta tauro musu su Sagna da Safna da breakfast Shashin LABEEBAH suka farayi. Dake kofar abu'de take sai suka shiga kawai Nan suka ganta kwance tana bacci hankali kwançe SAUBAN ya saki hannun Safna yayi kan gadan da gudu ya 'dane da hawa kanta yana dariya Ai nan LABEEBAH Tatashi da sakar musu Murmushi Tace yaushe kukaxo Suka gaisheta Sagna Tace yanxu mukaxo Safna Tace kinsan kukan da yarannan yamana agida kowa Sagna Tace Wlhi hanamu bacci yayi Wai shidai mamansa akaisa gun mamansa Aiko Momy Tace mutawo dashi ya xauna gun wacce batada da Ya YUSUF LABEEBAH taqara rungumarsa Tace ai kun kyautamin da kuka kawoshi ina kayansa Sagna Tace yana falo Tace Yauwa da kama fuskarshi Suna wasa Safna Tace breakfast muka kawo LABEEBAH Tace toh Sannunku. Nan suka ta6a hira kana sukayi part 'din XARAH dan gaisar da ita Da sallama suka shiga falan shukaji shuru Sagna Tace mushiga bet room ko itama baccin take Safna Tace baki dakai bakiga bamuga ya YUSUF a 'dakin Aunty LABEEBAH qila anan ya kwana Sagna Tace anya mudai shiga. Safna tayi waje tana cewa Wlhi baxan shigaba Aiko Sagna ta leqa ta windan Bet room 'din Nan taga XARAH maqale ajikin YUSUF Suna bacci hankali kwance Futuwa tayi itama Tace mah Safna dagaske Suna tare Wlhi xoki gansu Safna tace bacci suke Tace eh Nan itama Safna taje taleqasu Suka fito Suna dariya dayin gun LABEEBAH sukace Ashe basu tashiba LABEEBAH Tace suwa Sagna Tace Ya YUSUF da Aunty XARAH man mun leqasu sai bacci sukeyi hankali kwance Gaban LABEEBAH ya tsinke ya fa'di dammm Tayi saurin qaqalo Murmushi da kallan agogo ganin takwas da rabi Tace yanxu xasu tashi Safna tace mu xamu tafi Aunty tace mungode kugaida momy suka toh xataji dayi mata sai anjima suka tafi Akan hanyarsu ne Safna Tace Wlhi naxaci ya YUSUF agun Aunty LABEEBAH xai kwana Sagna Tace nima nayi tunanin haka Amma kamar baidace abinda yayibah Safna Tace ina ruwanki kika sani ko ita Aunty LABEEBAN CE Tace yaje guntan kin santa da gwaninta Sagna Tace aikowa akwaita da gwanintar Allah yasa karya xame mata matsala dan Wlhi Aunty XARAH tafita wayo kuma Kinga shi namiji kamar kwallo yake duk wacce ta iya cillashi itace dashi Safna Tace toh malamar soyayya kice Aminu har yanda xaki mallakeshi ya koyar dake Sagna Tace eh aimu xaman Auran mu da kallo Safna Tace xa'asha kalle kalle ba kallo bah Sagna tajah tsaki LABEEBAH tashiryama SAUBAN kayansa tsaf a durowa Sannan. Suka baje sulayi breakfast 'dinsu kana taje Babban falo tajera sauran a dining Sannan suka dawo suka da'da bajewa itada SAUBAN 'dinta tadinga biyema shirmansa. Amma hankalinta yana kan XARAH da YUSUF abin ya bata mamaki yanda taji Su Sagna sunce wai har yanxu bacci suke basu tashi bah. Me hakan yake nufi Yana nufin anan ya kwana abinsa. Xuciyata tabata amsa YUSUF da XARAH sai xuwa goma suka tashi Sukayi wanka YUSUF yafitoh falo yanata mamakin Kasan cewarsa da XARAH Can tabiyoshi falan tagaidashi idanta a qasa Ya amsa da kulawa sai kuma sukayi shuru Dake YUSUF yasan kan tamace tashi yayi yaxo gabanta ya durkusa Yace farin cikina kisoni plx kamar yanda nasoki na qaunaceki adaran jiya Fashewa da kuka tayi Tace inasanka YUSUF son da wata mace bata ta6ayi maka shiba Nafa'da ~*MASEEFAR SONKA*~ saidai xan kasance cikin damuwa da tashin hankali ha'de da baqin ciki Ya share mata hawayanta Yace fa'damin me xai yawo miki haka Tace kishinka ne xai jawomin haka Inasan 'Yar uwata LABEEBAH Amma akan kishinka xamu samu babbar matsala da ita dan baxan iya jure kaje gareta Sannan kaxo gareni ba Xuciyata xata iya bugawa Taqarashe da rushemai da kuka [8:19PM, 08/10/2016] Rahamat Nalele💋: -------------- Ba qaramin bugawa xuciyar YUSUF tayiba. atake hankalinshi yatashi. Sam ya manta da LABEEBAH tunda ya shiga 'dinkin XARAH jiya Tashi yayi ya dafe kai Yace innalillahi....... XARAH Tace wani abune Ya kalleta har xaiyi magana saiya fasa ya nufi part 'din LABEEBAH Ganinta yayi a falo tanata taya SAUBAN wasa Ta kalleshi ya sakar mata Murmushi ta mayar mishi Ya qaraso da xama kusa da ita Yace am sorry nutsuwata Wlhi XARAH CE Tace tana da tsoro wai bata iya kwana ita 'daya bah shiyasa baki ganni ba Shuru LABEEBAH tayi dan axahiri itace matsoraciya mejin tsoro ba XARAH bah Amma meyasa Tace mishi tanajin tsoro. Ganin tayi shuru yasashi cewa dan Allah kiyi......... Bata bari ya qarasa ba Tace ina kwana da fatan kuntashi lafiya Yace lafiya lau Amma baxan qara kar6ar wannan gaisuwar ba. Dan ba ita nake buqata bah Tace toh wacce kake buqata Ya kama fuskarta ya manna mata kiss a goshi da hanci da baki Yace xaki iya rungumata kiyi min kamar yanda namiki yanxu plx kar kice Komai Tace bin umarninka shine numfashina Karka damu xamma yanda kakeso Nagode sosai Tace ya kwanan XARAH. Ananne ya Sosa qeya ka'dan yace lafiya Tace haka akeso ga breakfast can Momy ta aiko tun'daxo Ya 'dan waro ido da kallan agogo Yace kai ya akayi lokaci ya qure haka. Sai yanxu takaicinsa ya kamata Tace gaskiyane ka huta da yawa shiyasa lokaci ya maka baxata Tashi yayi yana cewa aransa yarinyar nan neman magana take Amma afili cewa yayi toh muje kiban mana Tace toh bara in kira XARAH ko Yace no bari na kirata Yafa'da da sake SAUBAN wanda tun shigowar shi ya maqale mai Toh LABEEBAH Tace mai kawai da binshi da kallo Yana komawa falan XARAH ya ganta tana kuka wiwi Cikin tashin hankali yayi kanta da tambayar lafiya Tace watoh dan LABEEBAH tafini darajah agunka shine ina ambatarta kayi gunta YUSUF ya dafe kai Yace toh yi hakuri ba haka bane ke da LABEEBAH 'dayane aguna plx Ki fahimceni Cigaba tayi da kukanta. Ya rungumeta yana lallashinta Can dai tayi shuru tana sauke ajiyar xuciya Yace Yauwa.tashi toh muje muyi breakfast Tace nidai saidai kaxauna anan in kawo mana Komai nan Bayanda YUSUF xaiyi sai gya'da mata kai da yayi ta ficce Direct part 'din LABEEBAH tayi suka gaisa Sannan ta tambayeta breakfast 'din Tace yana can falan XARAH tayi Murmushi Tace gaskiya hankalina yayi gunki banda haka yaci ace naci karo da shi kafin in qaraso nan LABEEBAH ma tayi murmushin Tace Hakkane Amma me yasami fuskarki kamar kinyi kuka Tace haka kawai natashi da ciwan ido ina addu'ar Allah yasa karnah xama ke Tace ayya sannu ciwan ido ba da'di Tace ina xuwa Tace toh SAUBAN wasanshi yake Sam be waniyi 'daukin Ganin maman nashi XARAH ba Kamar ance LABEEBAH leqa Babban falo aiko Tatashi ta leqa nan taga ba YUSUF ba dalilinsa haka ba XARAH da abincin da tajera Tadawo ahankali tana tunanin wai me yake shirin faruwa ne can dai ta'daga kafa'da takori tunanin xuciyar tata Abinda yabata mamaki shine yanda taga YUSUF da XARAH sun fitoh Suna dariya da kagansu kaga Masoya YUSUF ya kama hannun XARAH batasan me yake CE mataba ya shige mota ta 'dagamai hannu ya ficce Saita XARAH Koma part 'dinta Shuru LABEEBAH tayi kawai taqi 'dauke idanta a window dan tafa'da wani birkitaccen tunani Da yamma ne LABEEBAH tana kitchen tana ha'da musu abinci dan taga Komai na buqata a kitchen 'din akwai harsu nama kifi gasunan a refrigerator shi yasata San yin girkin. Kuma takira Momy Tace karta turo musu da Komai sai kayan gwari Aiko taturo musu harda Su kayan Qamshi XARAH ta shigo kitchen 'din tana qare mishi kallo Komai yayi daidai saikace yaran sarauta ko 'yayan shugaban qasa. Tace wow gaskiyane kitchen din yayi kyau LABEEBAH Tace eh Momy tayi qoqari Allah ya biyata Tace AmEEn Bara natayaki Nan sukayi girkinsu me da'di da rai da lafiya. sukaci Wajan 6:00pm YUSUF ya shigo gidan. Tabbas part 'din LABEEBAH yayi niyar shiga duk dako ya dawo da buqatar San Ganin XARAH Saidai me😳 Yana fitowa daga motar XARAH tafitoh tariqe mai hannu Tace Wlcm my luv da fatan kadawo lafiya Farin ciki ya cika xuciyar YUSUF musamman data Sha wankan Riga da wando tayi kyau sosai kamar ya sataceta ya gudu Yakai bakinsa Cikin nata ya tsotsa ka'dan kana yajata part 'dinta Anan suka baje suka fara aikawa junansu sakwanni luvvvvv Hawaye ne

Chapter 13 of 22